Showing 6001 words to 9000 words out of 20315 words

Chapter 3 - BEELAL BUK BOOK 2 COMPLETE BY MAMAN AFRAH.txt

jin hankalinta bai kwanta da kasancewar Beelal a wajen Idrisu tana bin sawun duk da tana haɗuwa da mutane jifi-jifi har da masu tambayarta ko lafiya. Amma bata da ƙwarin gwiwar amsa musu tambayarsu sai dai kawai ta gyaɗa musu kai, ganin sawun Idrisu ya nufi hanyar fita gari a take wata mummunar faɗuwar gaba ta ziyarci zuciyarta duk da ta kasa gane menene hakan ke nufi.





Mmn Afrah 09030283375



❤️❤️❤️❤️❤️❤️

*BEELAL*

💦💦💦💦💦💦


NA



MAMAN AFARAH


*FCW*💛

Book 2


page7️⃣➡️8️⃣



Idanu Fatima ta zaro cikin tashin hankali, tun da dai ta san ita ma da ta tashi da asuba bata ga Beelal ko Idrisu ba, to kenan tun kan asuba suka fito, ko kuma ma ya aka yi bata ganin sawun Beelal sai na Idrisu kawai, wannan tambayoyin take jefawa kan ta hankali tashe, dan ita dai ta san waye ɗanta babu yadda za a yi Beelal ya fita ko da nan da ƙofar gida ne bai faɗa mata ba, ko da, da rana ne bare kuma dare bare ma Beelal ba ya yawo dama gidan su Hameeda ne yake zuwa amma tun da iyayenta suka mutu su kuma wanda take hannunsu wato Yayan mahaifinta da matarsa sun tsani Beelal ɗin ya raɓi Hameedar ma ban da ma uwar wahalar da suke bata kamar baiwa, bare ma yanzu ta kwana biyu bata ga Hameedar ba gashi ko gidan ta je matar gidan ta ringa ci mata fuska, kuma ba za ta bari ta ga Hameedar ba hakan ya sanya ta daina zuwa.

Wani uban birki ta ja ta tsaya ganin sawun Idrisu dai ya nufi hanyar barin gari ko lanƙwasa babu gashi kuma ta ma rasa wane irin tunani za ta yi ta ina za ta fara. Hawaye ne suka shiga zarya a fuskarta wani irin jiri ta ji ya fara juyawa da ita hannu ta miƙa ta dafe wani maina da ke kusa da inda take tsaye.

"Wai ni ke Fatima me kike dubawa a ƙasa ne ko kuɗi kika jefar ne, tun daɗewa kowa zai wuce ana tambayarki lafiya amma sai ki ɗagawa mutane kai kamar wata ƙadangaruwa, kuma lafiyar ce ta sanya yanzu kike zubar da hawaye har kina neman faɗuwa sai da kika riƙe maina" Cewar wani matashi da yake mata magana cikin muryar ƴan shaye-shaye sai wani tangaɗi yake idanun nan jajawur.

" Wayyo Allah na Beelal nake nema wallahi ban ganshi ba da na tashi"
Wani uban tsaki ya ja sannan ya ce

"To kuma menene dan baki ga wannan mai ƙafa a lanƙwashen ba, ke ba ma kya ganin irin baƙin jinin da yaron nan ya jawo miki a garin nan tun da kika haifeshi amma har wani ruwan hawaye kike dan baki ganshi ba ai na zata mur...

"Ba wai na faɗa maka bane dan ka ci mini mutunci, kamar yadda kowacce uwa take so da ƙaunar ɗanta to haka ni ma nake matuƙar ƙaunar nawa ɗan in ma ban fi wata uwar ƙaunar ɗana ba, kuma wani baƙin jini a wajen mutane bai dameni ba dan jahilci ne yake damunsu suna mantawa da cewa Allah shi ke halittar mutane shi ke yin kowa yadda ya so shi ke barin kowa a yadda ya so babu wani mahaluƙi da zai ja da ikon ubangiji ko ya canja halittar ubangiji ko da kuwa ta kiyashi ce bare kuma ta ɗan adam, dan haka ina ƙaunar Beelal ko da kuwa gabaɗaya mutanen duniya za su tsane ni su ƙyamace ni, ni na san ubangijina yana so na, kuma yana sane da ni, sannan soyayar ubangiji a gareni ne yasa ya bani Beelal bayan ya hana miliyoyin mutane haihuwa ni kuma ya bani dan haka ina daɗa gode masa a bisa ni'imarsa gareni" Ta ɗora da cewa

"Wallahi da a ce mutane za su san waye Beelal wace irin baiwa Allah ya yiwa yaron ta fili da ta ɓoye, baiwar ƙwalƙwalwar da ba kowa yake da ita ba, Beelal Allah ya halicceshi da nakasa amma kuma ya bashi ɗinbin baiwar da mararsa nakasa basu da ita ga kyan zuciya. Ni na kasa gane kan mutane na kasa gane kansu bare ƙafarsu ɗan adam da bashi da ikon canja mutum amma yana adawa da yadda aka halicceshi, shin sai yaushe ne mutane za su farga, sai yaushe ne za su farka daga baccin da suka yi mai nauyi su gane cewa Allah dai ɗaya ne kuma bashi da abokin tarayya a komai shi ke halitta kowa kuma babu wani wanda ya isa ya canja dan haka kowa ya godewa Allah a yadda ya halicce shi ba wai a tsaya kai da fata sai an samu wanda za a tsangwama dan kawai Allah ya masa halittar da ya so, shin jiki da fata da ƙasusuwan da za a maida su cikin ƙasa menene na damuwa da su? Komai daren daɗewa mutuwa ce za ta ɗauki kowa kuma cikin ƙasa za a sanya kowa duk kyau da tsarin halittar mutum, fari ne ko baƙi ne, ƙasa ce makomarsa, duk mulki da sarautar mutum bashi da makomar da ta wuce cikin ƙasa dan haka babu abin da ya dace da kowa face yin biyayya da bin dokokin ubangiji da yin ibadah da ƙasƙan da kai domin samun rabauta da kuma samun sakamako mai kyau domin bautar Allah ita ce gaba da komai ƙauracewa shirka da manyan zunubai su ne abin gudu. Saɓawa Allah ba shi ne abin yi ba ga wanda bashi da tabbacin ƙara second ɗaya a koyaushe a duniyarsa,mutane su bar kiwon mutane ƴan uwansu su maida hankali da abin da ke gabansu, shi ne ya fi dacewa da kowa ba wai lura da rayuwar wasu ko ƙyamatarsu dan wata halittarsu ba" Fatima ta kai ƙarshen maganar tana kuka sosai, lokacin har mutane maza da mata sun taru yara da manya duk suna sauraron abin da take faɗa kowa sai jijjiga kai yake alamar tausayawa da kuma da na sani a kan abubuwan da ake musu a gari ita da ɗanta, basu da damar su raɓi mutane, basu da damar su sake, su yi rayuwa irin yadda kowa ke yi, ɗanta bashi da halin ya shiga cikin yara ya yi wasa, bashi da damar ya je makarantar boko ko ta arabiya sai an rakoshi har gida ana tsokanarsa, kuma ba dan ya yi komai ba sai dai suna yi ne a kan abu ɗaya kawai wato NAKASAR da ke tare da shi nakasar da bashi ya yi kansa ba, Allah ne ya yi shi, nakasar da ita kanta wacce ta haifeshi a haka ta ga ta haifeshi amma aka ɗauki gabaɗaya laifin aka ɗora a kansu, ita da ta haifa da shi wanda aka haifa, hatta wanda suka haɗu suka haifi ɗan bai barta ba wato uban ɗan shi ma ƙyamatarsa yake, to shin ina suke so Fatima da Beelal su sanya ransu?.

"Dan Allah Aunty Fati ki yi haƙuri ki bar kukan nan wallahi waɗannan kalaman naki sun sanya na ji gabaɗaya duniyar ta ishe ni, sun sanya na ji nadama a kan duk wata ƙyamatar wata halittar ubangiji koda kuwa masu nakasar da ta fi ta kowa abin ƙyama kama daga kuturu makaho da dai wasu masu nakasa kowacce iri ce, tabbas yau kin zama madubi da kika haska mini abubuwa da dama da suka shige mini duhu" Cewar wannan matashin mashayin yana share hawayen fuskarsa.

"Ba komai kar ka damu ni zan bi sawun nan domin zuwa in ga inda Idrisu yake ko Allah zai sa in ga Beelal a tare da shi in samu sassauci duk da na ga ban ga sawun takalmi ko ƙafar Beelal ba amma na tabbata Beelal ba zai fita daga gida ba tare da sani na ba. Dole zan bi sawun Idrisu dan na san tabbas akwai lauje cikin naɗi"

"Zan faɗa miki inda Idrisu yake kuma ina tabbatar miki suna tare da Beelal sabodanna gansu da idanuna a daren jiya su...

"Dan Allah yana ina ka faɗa mini dan girman Allah" Cewar Fatima cikin tashin hankali dan jin ya ce suna tare kuma tun daren jiya sai ta ji hankalinta ya yi mummunan tashi.

" A daren jiya bayan dare ya tsala, duk da bansan ko ƙarfe nawa ba amma na san tsakiyar dare ne, na dawo daga yawo wurin wani abokina da ke ƙauyen sama da mu, to tare muke da abokin nawa ya ɗakko ni a machine amma dama tun daga can yace ba zai kai ni har cikin garin nan ba, tun da dare ya yi zai ajiye ni a bakin bari in ƙaraso shi ma ya koma dan yana tsoron Babansa ya san baya gida, dan ba a san ya fito ba ta katanga ya ƙetara ya fito muka je mu da sauran abokananmu muka haɗu muka yi shaye-shaye, amma in sha Allahu ni da shaye-shaye har abada dan kalamanki na yanzu sun shigeni har na ji cewar ina so in zama mutumin kirkin da za a yi alfahri da ni. Ina cikin tafiya sai na hango wani machine ya taho daga bayana ya samu wuri ya faka ua sauka ya tsaya kamar dai yana jiran wani abu, to bai ganni ba da yake akwai duhu, sai na ɓuya inaso in ga mai zai aikata, duk tunanina cikin ƙauyen zai je yin sata, zuwa can sai na hango wani mutum ya taho da yaro a saɓe a kafaɗarsa, cikin mamaki sai nake tunanin masu satar yara ne, gabana na faɗuwa ina so na fito amma ina tsoro dan ni a buge nake duk da dai ba sosai ba amma dai babu wani ƙarfi a tare da ni, mutumin na ƙarasowa sai na ga ashe Idrisu ne ya ɗakko Beelal a kafaɗarsa dan yana zuwa wajen mai machine ɗin suka fara magana ya ɗora Beelal ɗin da ke bacci da alama ma bai san ya ɗakkoshi ba, sai da ya ɗora shi a machine ɗin ya falka.


amma haka Idrisu ya tsawatarwa yaron dan dole ya yiwa bakinsa linzami ba dan ya so ba, cikin mugun gudu abokin nasa ya ja machine ɗin suka bar wajen, ni kuma dama da na ga ƴan garin nan ba ƙaunar yaron kowa yake ba sai kawai na ga an samawa kowa lafiya duk da ban san ina zai kai yaron ba bare kuma da na ga Babansa ne ma duk da kowa ya san ba ya ƙaunar yaron, sai kawai na taɓe baki na fito daga moɓoyata na tafi, amma ki gafarceni "

Kallonsa kawai Fatima take da idanunta da ke zubar da hawaye tamkar an kunna famfo ita kan ta ba za ta ce ga irin tsananin damuwar da ta kaiwa zuciyarta farmaki ba lokaci guda, ban da wacce take ciki. Ji take tamkar a jijjigata a ce ta tashi bacci ne take komai da ya faru ba a gaske bane mafarki ne.

"Dan Allah jama'a ku jijjijgani in falka daga wannan mummunan mafarkin da nake, mafarkin nan da yake kokarin rabani da wanda na fi ƙauna duk cikin duniyar nan, shin ya mutum zai ji a lokacin da aka rabashi da wanda ya fi ƙauna? Ya uwa take ji a lokacin da mutuwa ta rabata da ɗanta, duk da ta san mutuwa dole ce kuma wanda ya karɓi kayansa dama shi ne ya bata kuma ya fi ƙaunar ɗan nata fiye da yadda take ƙaunarsa, amma a haka take jin damuwa ta mutuwar ɗan nata shin ni kuma da wane kwatance za a kwatanta halin da nake ciki, har gwara mutuwa mutum ya ce mutuwa ce amma fa a raba uwa da ɗanta bayan yana raye shi kuma wane irin ƙunci zuciyar uwa za ta shiga? Shin matan aure da mazanjensu suke sakinsu su rabasu da yaransu ya suke ji a duk lokacin da suka koma gidan iyayensu , ji suke tamkar an rabasu da wani sashe na farincikin rayuwarsu, a koyaushe uwa tafi so ta kasance a tare da ƴaƴanta, idan har wacce ta baro yaranta a gidan mijinta za ta shiga damuwa duk da ta san inda yaran suke, to ina kuma ga wacce bata ma san inda yaronta yake ba, sannan ta san yaron yana hannun wanda baya ƙaunarsa, dan Allah jama'a ku kwantanta yadda nake ji yanzu a cikin raina, kowa ya san Idrisu ba ya son Beelal saboda nakasar dake tare da shi, kamar yadda mutanen gari ma basa son sa basa ƙaunar ya raɓi inda suke ma, yau kuma ya ɗauke min shi cikin talatainin dare ya gudu dashi dan Allah ku taimaka min" Fatima dake bin mutanen wurin ɗaya bayan ɗaya tana kuka tare da neman agaji a garesu dan ta kasa dakatar da zuciya da kuma hawayenta, babban tashin hankalinta ma shi ne ina Idrisun ya kai yaron. Kowa na wurin babu wanda za ka kalli fuskarsa ba tare da ka yi arba da hawaye sun gama wanke masa fuska ba, gabaɗaya wurin sun matuƙar tausaya mata irin tausayin da kaf garin babu wanda ya taɓa musu, haka suke rayuwa a cikin garin tamkar wasu haure da basu da kowa da komai a cikin garin, amma sai gashi yau sanadin kalaman Fatima kowa ya ji tausayinsu ya kamashi, kalaman Fatima kalamai ne wanda akwai hikima, ilimi da kuma iya furta kalma kowacce a mazauninta an bata haƙƙinta. Haƙuri aka shiga bata wata dattijuwa ce ta kama Fatimar ta rungume ta dan ta samu sassauci, dan tabbas a duk lokacin da ɗan adam ya tsinci kansa cikin damuwa to idan har aka rungumeshi aka lallashe shi to ko da a ce damuwar nan bata bar shi duka ba zai samu sassauci ko da kaɗan ne a cikin ransa. Musamman a ce wanda zai rungumi mutum ya kasance uwa ce wato mahaifiya dan ita uwa ɗumin jikinta da ban yake haka nan soyayyarta ta zarta ta kowa ta kuma wuce a misalta ta. Fatimar kwa kamar jira take sai kawai ta kwantar da kanta a jikin matar da ta mata ƙawanya da hannayenta a bayanta, Fatima idanu ta rufe hawaye na kai koma a fuskarta, ji take tamkar a jikin mahaifiyarta, ko Kakarta, ko Yayarta take domin su ne duk duniya suke bata mafaka a baya kafin barinsu duniya, yanzu kuma sai Yayarta Hajiya Laɗifa kawai wacce kuma yanzu ta yi nisa da ba za ta samu taimakon gaggawa na runguma da lallashi a gareta ba.



Da a baya ko Yayarta bata nan idan tana cikin damuwa mijinta wanda ya kasance abin so da ƙauna a gareta wato Idrisu shi yake sanyata farinciki a duk lokacin da ta shiga damuwa in Yayarta bata kusa, kafin ya juya mata baya, kafin ya sauya mata daga Idris zuwa Idrisu, kafin ya manta da so da duk wata ƙauna da yake mata ya maye gurbin ƙauna da ƙiyayya, haka kuma ya yi watsi a duk wata kulawa da nauyinta da ke kansa, kafin ya canja daga fari zuwa baƙiƙƙirin wanda har yau bata san dalilin yin hakan ba, duk da an ce mata da dama su kan auri namiji aure irin na so da ƙauna amma idan an je gidan daga baya komai ya kan canja, sukan rasa duk wanann abubuwan zaman ya dawo sai na haƙuri da zaman ƴaƴansu, amma ita nata salon da ban yake da na saura dan ita abin ya wuce misali sai dai fatan Allah kawo ƙarshen abin.


Dattijuwar nan bata cire Fatima daga jikinta ba har sai da ta ji ta ɗan tsagaita kukanta tana sauke ajiyar zuciya, sannan kuma Fatimar ce da kanta ta ɗago kanta daga jikin tsohuwar tana share hawayenta, dan kuka ya zame mata jiki dan ita kullum idan har za ta tuna da damuwarta to kuwa za ta kasance ne ciki kuka, kuka kamar matar marigayi, dama kuma Beelal shi ne yake ɗauke mata kewa da duk wata damuwa, zama da ita ne da kuma halin da suka tsinci kansu shi da ita ya sanya yaron ya zama tamkar wani babba, ya iya lafazi da kalamin da yake kwantar mata da hankali waɗanda a wajenta yake koya saboda da su take amfani wajen lallashin sa da kuma koya masa zama da mutane da haƙuri da rayuwa a duk halin da mutum zai tsinci kansa daɗi ko akasin haka.


"Bari na je na bi sawu na karɓo Beelal ɗin na gane garin kusa da Kazaure ne wajen abokinsa ne zan je in gani" Ta faɗa tana runtse idanunta ta buɗe su ko ta ke gani sosai saboda kukan da ta yi sun kumbura suntum, har bata iya gani sosai.

"Babangida ɗakko machin ka kaita" Cewar wani mutum da ke tsaye ya faɗa wa ɗansa, da to matashin ya amsa ya je ya ɗakko machine ɗin Fatima ta hau ya ja suka tafi kowa yana tsaye ana jimantawa har sai da suka daina gango machine ɗin su Fatima sannan kowa da ya taru ya watse dan lokacin sosai rana ma ta fito wajen ƙarfe tara saura ne.



MMN AFRAH 09030283375



❤️❤️❤️❤️❤️❤️

*BEELAL*

💦💦💦💦💦💦


NA



MAMAN AFARAH


*FCW*💛

Book 2



Page 9️⃣➡️1️⃣0️⃣


*KATSINA STATE*

*UNGUWAR* *KAFIN SOLI*


~HAMEEDA~


Tun lokacin da Ramma wacce za ta kaita wurin aiki ta je ta taho da ita, Ramma tana kai yara ƴan mata da yara mata gidan masu kuɗi su yi aikace -aikace kama daga shara wanke-wanke goge-goge raino da dai sauransu. Ta tafi da Hameeda da sauran wasu yaran a inda ta yiwa iyayen kowacce yarinya alƙawarin idan an biya kuɗin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login