Showing 6001 words to 9000 words out of 26566 words

Chapter 3 - Miftahuzzarbil Book 1 Complete By Abdulaziz Sani Madakin Gini.txt

kenan na rasa abokina,na rasa aminina."
Nan dai muka yi ta rarrashin sa har ya daina kuka.Sannan muka tsaya saida duk raquman nan da alfadaran nan masu dauke da dukiya sama da dubu dari uku suka gama fita daga cikin kogon Baitul Husuk,sannan muma muka fita.A bakin kogon na tsaya na bude littafin nan zuwa shafin karshe na karanta wadansu kalmomin tsafi.Take kogon ya fara ruftawa cikin kasa.Kasa ta kama girgiza bisa dole muka ruga da gudu tare da raquman mu da alfadaran mu.Har muka yi nisa daga wajen kogon nan bai gama nutsewa ba a cikin kasa.
Daga inda muke muna iya hango nutsewar kogon.Anan ne na tsaya na dubi jarumi Miqdad da mahaifina Shaubatul Azman ina mai murmushi kawai saina rungume su muka kama tsalle gaba daya cikin matuqar farin ciki.Mu uku kacal muka tsira daga cikin miliyoyin mutanen da suka shiga cikin kogon Baitul Husuk.Ba tare da 6ata lokaci ba muka kada raquman mu da alfadaran mu muka yi ta tafiya har muka iso birnin mahaifina Shaubatul Azman.Anan ne aka daura aurena da jarumi Miqdad.
Bayan an daura aurene yayi sallama dani yace zai tafi kasar su in yaso na riske shi a can.Lokacin da Miqdad yaje birnin Shauqib inda dan uwansa ke mulki saiya iske ana yaki har an kashe dan uwan nasa.Nan take ya kai dauki ya kashe abokan gabar gaba daya.Bisa wannan dalili ne aka ba shi mulkin kasar.Saida ya kwana ashirin akan mulki sannan mahaifina Shaubatul Azman yasa aka shirya mini tafiya tare da dakaru dubu dari 'yan rakiya.Sannan ya bani dukkanin raquman nan da alfadaran nan masu dauke da dukiya muka tafi ga mijina sarki Miqdad.Bamu shigo nan birnin Shauqib ba sai la'asar sakaliya.Raqumana da alfadarai na kuwa sai da kwanaki bakwai suka shude suna shigowa cikin garin sannan suka qare saboda yawa.
Koda gimbiya suhaila tazo nan a labarin ta sai kuyanga suzaila tayi ajiyar xuciya tace,"ya shugabata a gaskiya kinyi butulci ga sarki Miqdad domin ba don shi ba da baki kawo iyanzu ba.Ya kamata ace kinso duk abinda ya ke so.Ki tuna baqar wahalar daya sha a yakin da yayi a cikin garin ku,duk saboda ke kuma ki tuna yadda ya saida rayuwar sa a cikin kogon Baitul Husuk.Ina mai shawartar ki kije ki nemi gafarar sa bisa qin bawa Mozur da kika yi tunda farko."
Koda zulaiya ta gama wannan jawabi sai Suhaila ta kama dariya tayi ta dariyar kamar ba zata daina ba.Al'amarin daya firgita Zulaiya kenan ta miqe tsaye zata gudu.Cikin zafin nama Suhaila ta cafkota ta shaqe mata wuya da hannu biyu.Tun Zulaiya na harba kafafunta da hannayenta harta kasa motsi harshenta ya zazzago waje.Suhaila tayi jifa da gawar Zulaiya tace,"wace ce ke da har za ki bani shawara akan abinda ya dace nayi?
Ke baiwa ce ya kamata ace kin tsaya iya matsayin ki."
Tana gama fadin hakan ne ta miqe tsaye ta shige cikin turakar ta.Nan da nan fadawa suka dauke gawar Zulaiya suka tafi da ita.Wannan shine abinda ya faru ga Suhaila matar sarki Miqdad bayan ta gama bada labarin yadda ta hadu da sarki Miqdad har ta zamo matarsa.
A can nahiyar kasashen baqaqen fata kuwa a cikin birnin Malhiya inda sarki Amzadu ke mulki anan ne bawa Mozur ke bauta a wani 6angare na gidan sarautar.Da yake Mozur ya kasance kakkarfa sai aka kaishi cikin wani wani dakin wata na'urar dutse wadda ake nuqa hatsi da ita.A kalla sai kato arba'in sun taru suke iya juya dutsen dake nuqa dawar,amma bawa Mozur shi kadai yake juya dutsen kuma saiya yini yana aikin da kato arba'in za suyi cikin kwana biyu.
***********
Tunda aka siyo bawa Mozur a birnin Shauqib aka kawo wannan daki na nuqan hatsi bai ta6a fita wajen dakin nan ba na tsawon wata tara.Kai bai qara ganin hasken rana ma ba.Ko yaushe yana cikin aiki.Da daddare ne kadai yake samun damar hutu,kuma sau daya ake ba shi abinci da ruwa.Wani lokacin idan bawa Mozur ya tuno da irin rayuwar sa ta da sa'adda yake can kasar Shauqib tare da sarki Miqdad saiya fashe da kuka domin ya san cewa ya rasa babban masoyi,wanda har abada ba zai sake samun kamar sa ba.Kuma rayuwar sa tazo karshe domin karfinsa gaba daya a cikin daki na nuqan hatsi zai kare.
Sarki Amzadu nada wata kyakkyawar 'ya budurwa 'yar shekara goma sha takwas wacce yake matuqar kauna,ana kiran ta da suna gimbiya Laslaiya.A iya rayuwar gimbiya Laslaiya babu abinda take so face kallon 'yan kokawa.Bisa wannan dalili ne take shirya wasan kokowa bayan kowane kwana talatin.Duk wanda yaci gasar sai ta kawo kyautar dukiya mai tsananin yawa ta ba shi.Jaruman dake wannan kokowa sukan zo ne daga kasa-kasa.
Akwai wani babban bafaden sarki Amzadu mai suna Azmandu wanda shine da alhakin kula da gidan nuqan hatsin sarki inda bawa Mozur ke aiki.Duk sa'ar da za'a yi wannan gasa ta kokawa ya kan tafi neman babban jarumi yazo da shi,domin idan jarumin yaci gasar ya sami dukiya mai yawa suyi kashe mu raba.Yanzu anyi gasar har sau uku amma duk jaruman da yake kawowa basa nasara.A ranar da ya rage saura kwana bakwai ayi gasa ta gaba sai hankalin Azmandu ya dugunzuma saboda jin cewa dukiyar da gimbiya Laslaiya zata bayar a wannan karon tafi ta duk wadda ta bayar a baya.Ba wani abu ne ya tayar da hankalin Azmandu ba face sanin an gama qureshi bashi da sauran wani jarumi wanda yake ganin zai iya cin gasar saboda an kawo zakwaquran jarumai fitattu wadanda suka yi shuhura a wasu 6angararo na duniya.
Gefen magriba ne Azmandu ya shigo cikin ɗakin nuƙan inda bawa Mozur ke kishingiɗe yana hutawa saboda gajiyar aikin da yayi.Azmandu ya kewaya cikin ɗakin yaga cewa Mozur ya niƙa buhun hatsi da yawa sama da yadda ya saba yi a kullum.Koda ganin haka sai yayi murna nan take yasa aka ƙarowa Mozur abinci da ruwan sha ishasshe.Sannan ya zauna kusa dashi yana tambayar sa yace,
"Ya kai Mozur ya akayi yau kayi aiki mai yawa fiye da yadda ka saba yi?"
Koda jin wannan tambaya sai Mozur yayi murmushi yace,"ya shugabana kayi sani cewa a duk sa'adda raina ya ɓaci ina iya yin abinda kowa zaiyi mamaki.Kayi sani cewa a yau na tuno da wani tsohon mai gidana ne wanda ke matuƙar ƙaunata fiye da komai a rayuwar sa amma saida matarsa ta rabamu.Sa'adda na tuno da irin makircin data ƙulla mini ne don ta kashe ni nayi ta aiki a ɗakin nan fiye da yadda na saba yi."
Koda jin wannan batu sai Azmandu yayi shiru yana tunani.Daga can ya dubi Mozur yace,"shin ka taɓa yin wasan kokowa kuwa a can garinku?"
Mozur yace,"eh na taɓa yi sau ɗaya harma na ci gasar."
Yayin da Azmandu yaji haka sai murna ta kamashi ya dubi Mozur yace,"ina son na shigar dakai cikin gasar kokawa wadda gimbiya Laslaiya ke shiryawa a kowanne kwana talatin,zaka iya?"
Cikin murna Mozur yace,"ƙwarai kuwa zan iya kuma zan baka mamaki."
Ba komai ne yasa Mozur yake son a shigar da shi wannan gasa ba sai don kawai ya sami damar fita daga cikin wannan ɗaki yaga hasken rana wanda rabonsa da shi yau wata tara kenan da ƴan kwanaki.
Tun daga wannan rana ya dinga ɗokin zuwan ranar gasa,saboda jin daɗin hakanne ya cigaba da hazaƙar aikinsa fiye da yadda ya saba.Azmandu kuwa yasa a rinƙa bashi abinci mai kyau kuma isasshe.Nan da nan jikin Mozur yayi kyau a cikin kwana bakwan ya zamana ya mayar da duk komaɗar jikinsa da ramarsa.Kyawunsa da kwarjinin sa suka ƙara bayyana ƙarara.
Da ranar gasa tazo tunda sassafe Azmandu yazo ya riski Mozur ya kawo masa abinci da abin sha na musamman tare da waɗansu kyawawan tufafi.Bayan Mozur yaci ya ƙoshi sai Azmandu ya bashi waɗannan tufafin gasa,sannan ya dube shi yace,"ya kai Mozur ka sani cewa kai bawa ne na sarki kuma a ƙa'ida bai kamata na ciyar da kai abinci mai kyau ba kuma isasshe,amma gashi tun daga ranar daka yi aikin nan mai yawa kawo iyanzu ban fasa ba.Idan har kana son na cigaba da kyautata maka dole kayi iya ƙoƙarinka kaci gasar wannan kokawa.Kai in dai kaci wannan gasa nayi maka alƙawari zaka rinƙa samun hutun kwana uku a sati,kuma duk sanda kake da muradin mace zansa a kawo maka ɗaya daga cikin bayi na."
Koda jin haka sai bawa Mozur yayi murmushi yace,"ni kuwa da izinin abin bautata mai girma Lazzatul sakaru saina sami nasara a cikin wannan gasa."
Haka dai Azmandu da bawa Mozur suka cigaba da tattaunawa har lokacin tafiya fada yayi inda za'a gabatar da wannan gasa ta kokawa.

MU HADU A PART E DON JIN CIGABAN WANNAN KAYATACCIYAR HIKAYAR.**MIFTAHUL-ZARBIL**
LITTAFI NA BIYU✍️✍️❤
PART E 👌✌
NA: ABDUL'AZIZ SANI MADAKIN GINI✍️✍️
TYPING: AHMAD MUNNIR.
POSTING:NAJIBULLAH MUHAMMAD 🙂❤👌

Tom jama'a kyan alkawari cikawa, kamar yadda na maku alkawarin kawo maku cigaban wannan littafin a yau din nan, to gashi na cika.
Allah ya Temake mu akan cika duk irin alkawarin da muka ɗauka.

MARUBUCIN YA CI GABA DA CEWA..

Koda jin haka sai bawa Mozur yayi murmushi yace,"ni kuwa da izinin abin bautata mai girma Lazzatul sakaru saina sami nasara a cikin wannan gasa."
Haka dai Azmandu da bawa Mozur suka cigaba da tattaunawa har lokacin tafiya fada yayi inda za'a gabatar da wannan gasa ta kokawa.
Lokacin da su Mozur suka isa ƙofar fada sun makara domin tuni an fara gasar kuma wasu jarumai biyu ne akan wani faffaɗan gini mai tudu suke kafsawa.Jama'a sun kewaye wannan tudu an cika maƙil sai shewa da ihu da tafi ake yi.Daga can ɓangaren gabas kuwa nesa kaɗan sarki Amzadu ne da ƴarsa gimbiya Laslaiya zaune bisa karagar mulki dakaru sun kewaye su suna kallon wannan kokowa.Kallo ɗaya mutum zai yiwa gimbiya Laslaiya ya san cewa yau tana cikin matuƙar nishaɗi domin fuskar ta cike take da murmushi da annuri.
Gimbiya Laslaiya ta kasance kyakkyawa ta kwatance domin Allah yayi mata kyakkyawar surar ƙirar kalangu.Tana da dogon gashi baƙi siɗik mai ƙyalƙyali wanda ya sauko har ƙasan cibiyarta,tana da dara daran idanuwa,ɗan ƙaramin baki da dogon hanci.Ƙirjinta cike yake taf,kuma tana da tsukakken ƙugu.Ƴan yatsun hannayenta dogaye ne zara zara gwanin ban sha'awa kuma tana da dogon wuya.Duk da kasancewar ta baƙar fata ba balarabiya ba,bata da duhu ta kasance wankan tarwaɗa.A zahirin gaskiya babu wani ɗa namiji da zaiga gimbiya Laslaiya bata ɗau hankalin sa ba.
Koda shigowar Azmandu da Mozur cikin wannan taro sai Azmandu ya kama hannun Mozur ya kaishi wajen alƙalan gasar ya gabatar dashi a matsayin sabon gwanin sa.Cikin mamaki alƙalin gasar wanda ake kira Daraz ya dubi Azmandu,sannan ya ƙarewa Mozur kallo ya bushe da dariya yace,"haba Azmandu ya zako zo mana da wani ƙaramin mutum haka kace shine gwanin ka?
Anya kuwa ka dubi jaruman bana da kyau?"
Azmandu ya waiga inda jaruman suke tsaye wajen su talatin.Gaba ɗayansu gabza gabzan ƙarti ne masu ƙwanji da murɗaɗɗen jiki,babu wanda girmansa bai ninka na bawa Mozur ba sau uku.Azmandu ya haɗiyi miyau gami da ajiyar xuciya yace,
"Ba komai ɗan hakin daka raina shi ke tsone maka ido,kai dai kawai ka shigar dashi cikin gasar."
Nan take Daraz ya ƙara bushewa da dariya yace,"lallai yau da rabon zaka ji kunya kenan amma tunda kace a shigar dashi zan shigar."
Daraz ya dubi Mozur a wulaƙance yace,"mene ne sunanka?"
"Suna na Mozur bin Miƙdad."Ya bashi amsa.
Daraz ya sake tambaya yace,"daga wace ƙasa?"
"Daga birnin Shauƙib."
Koda jin haka sai Daraz ya ƙurawa Mozur idanu cikin yanayin mamaki har saida Mozur ɗin yace da shi,"Ina zan tsaya?"
Sannan ya nuna masa inda jaruman gasa ke tsaitsaye suna kallon waɗanda ke kafsawa.Kai tsaye Mozur ya tafi inda jaruman suke ya shige cikin su ya tsaya.Jaruman kuwa suka rinƙa kallonsa cikin mamaki don basu san dalilin da yasa yayi wauta ba ya shigo cikin su.Tsayuwar Mozur keda wuya sai idanun sa suka kai inda sarki Amzadu da gimbiya Laslaiya ke zaune.Koda yayi arba da Laslaiya sai ya ƙura mata ido yana mai mamakin tsananin kyawunta.Nan take ya tuno da gimbiya suhaila ya kasa tantance wadda tafi kyawu tsakanin Laslaiya da Suhaila,amma sai yace a ransa,"ni dai inda zaɓi za'a bani dana zaɓi wannan baƙar fatar ƴar uwata,domin tafi burgeni akan suhaila."
Yana gama faɗin haka ne hankalin sa ya koma kan jaruman dake kafsawa a kan wannan gini mai tudu.A lokacin ne ɗaya daga cikin su mai suna Zarto ya ɗaga abokin gwamin nasa sama ya dunga hajijiya dashi har saida ya jigata shi sannan ya kwaɗa shi da ƙasa.Take jarumin ya sume fili ya cika da shewa aka yi ta yiwa Zarto tafi.
Zarto ya kasance ƙaton gaske domin duk cikin ƴan kokawar babu mai girmansa da kwarjinin sa.Lokacin da Mozur yaga Zarto saida zuciyar sa ta kama bugawa da ƙarfi domin yasan cewa ka ba'a gwada ba linzami yafi ƙarfin bakin kaza.Nan dai Zarto ya sauko daga kan tudun gumurzu ya koma cikin jarumai ya tsaya.Shi kuma waccan jarumi da suka kafsa da Zarto sai da aka yayyafa masa ruwa sannan ya farfaɗo.Alƙalin gasa ya ƙara kiran wani jarumi waishi Kambus.
Kambus ya hawo kan tudun kafsawa yana mai tafiyar taƙama,jin kai da hura hanci.Shima Kambus ƙato ne na gaske domin da kaɗan Zarto zai fishi,amma kuma yafi Zarto tsawo sosai.Ba zato ba tsammani sai Mozur yaji an kirawo sunan sa cewa ya hawo kan tudun kafsawa shine zai kara da Kambus.Nan fa hankalin Mozur ya dugunzuma,amma sai ya dake ya hau kan tudun cikin ƙarfin hali.Koda ya tsaya a gaban Kambus sai ya zamo kamar ɗan tsako a gaban shirwa domin tsawon sa ma iya cibiyar Kambus ya tsaya.
A wannan lokaci ne gimbiya Laslaiya ta ƙurawa Mozur idanu tana mai mamakin tsautsayin da ya shigo da shi cikin wannan gasa domin shine mafi ƙanƙanta a cikin jaruman.Kambus ya sunkuyo da kanshi ƙasa fuskar sa ta tsaya daf da Mozur yana muzurai yace,"kai ɗan tatsitsi mai tsautsayin wahala wane irin karambani ne ya shigo dakai cikin wannan gasa?"
Mozur yayi murmushi yace,"neman suna da neman arziki ne ya kawo ni kamar yadda ya kawo ka."
Kambus ya ƙyalƙyale da dariya kuma ya murtuke fuskar sa a lokaci guda yana mai cewa,"yaro kayi ganganci,yau zan koya maka darasi domin kasan cewa bakin rijiya ba wajen wasan ka bane."
Kafin Mozur yace wani abu tuni Kambus ya shaƙo wuyansa da hannu ɗaya saiga Mozur na wutsil wutsil da ƙafafu a sama kamar jelar ɓera a bakin kyanwa.Nan fa filin wajen ya cika da dariya,kowa sai ƙyaƙyatawa yake.Azmandu ne kaɗai sai kuma gimbiya Laslaiya wacce ta shiga cikin tashin hankali saboda tausayi.Shima Kambus sai yayi ta ƙyalƙyala dariya yana zagaya wa akan tudun kuma yaƙi sakin wuyan Mozur.
Nan da nan idanun Mozur suka yi ƙulu ƙulu suka yi jawur.Koda yaji numfashin sa na neman ɗaukewa saiya harzuƙa cikin tsananin zafin nama ya tattare ƙarfinsa gaba ɗaya yasa hannu biyu ya ɓanɓare hannun Kambus daga wuyansa kuma yayi wurgi da Kambus can gefe ɗaya.Saiga Kambus na katantanwa a ƙas.Al'amarin daya jefa kowa cikin mamaki kenan filin gaba ɗaya yayi tsit kuma sai da kowa ya miƙe tsaye aka zubawa Mozur idanu ana mai al'ajabinsa.Shi kuwa Azmandu saboda farin ciki bai san sa'adda ya kama wuyan alƙalin gasa ba yana tsalle da shewa.Kamar haɗin baki sai kowa ya kama yiwa Mozur tafi.Gimbiya Laslaiya kuwa saita miƙe tsaye daga kan karagar ta tana ta tafi da kallon jarumi Mozur tana murmushi.
Koda ganin haka sai sarki Amzadu ya kamo hannun ta ya zaunar da ita yana mai harararta.Laslaiya ta nutsu ta kau da kai gefe ɗaya.Dama ƙa'idar wannan gasa itace indai mutum ya faɗi ƙasa to an cinye shi.Koda Kambus yaga yaje ƙas sai idanun sa suka ciko da ƙwalla saboda tsabar takaicin cewa ƙanƙanin mutum kamr Mozur ya kayar da shi.Haka dai Kambus ya sauka daga kan tudun cikin jin kunya da baƙin ciki har yana kuka.Bai tsaya a filin ba gaba ɗaya ya bar wajen gasar.Nan dai aka cigaba da wannan gasa.Duk wanda Mozur ya kara da shi sai yayi nasara.Sai da takai ta kawo cewa gaba ɗayan jaruman nan na tsoron kafsawa da Mozur face mutum ɗaya wato Zarto,kuma ba'a haɗasu ba sai a zagayen ƙarshe na gasar.Koda ƴan kallo suka ga jarumi Mozur da jarumi Zarto tsaye a kan tudun kafsawa sai filin ya kaure da shewa da ihu kowa na zaɓin gwanin sa.Wasu suce Zarto ne zaiyi nasara a wannan gasa,wasu kuma suce Mozur ne.Nan fa ƴan caca suka fara fito da kuɗaɗe don neman sa'a.A wannan rana ƴan caca sun zuba dubunnan dirhami masu yawa akan wannan gasa.
Zarto da Mozur suka fara kallon kallo.Sannan suka hau zagaya filin kowannen su zuciyar sa ciki da saƙe saƙen hanyar da zaibi ya sami nasara.Cikin shammace Zarto ya kawowa Mozur cafka da niyar ya rungume shi ya matse shi.Mozur ya goce cikin zafin nama ya wuce ta tsakankanin ƙafafunsa.Takaici ya kama Zarto ya ciza yatsa domin a tarihin kokawarsa bai taɓa kaiwa wani wannan hari ba ba tare da ya sami sa'a da nasara ba.Zarto ya juya ya sake fuskantar Mozur ya sake kai masa irin wannan hari a karo na biyu.Ai kuwa sai Zarto ya sami nasarar damƙar Mozur ya zamana ya matse masa baya da hannu biyu.Mozur ya kwarara ihu saboda tsananin jin zafin ruƙon da yayi masa.
Al'amarin da ya razana kowa kenan a wajen.Gimbiya Laslaiya kuwa bata san sa'adda ta miƙe tsaye ba zumbur cikin alamun razani.Sarki Amzadu ya sake danƙwafar da ita zaune yayi mata raɗa a kunne yace,"idan kika sake miƙewa kin gama kallon gasar kenan."
Cikin fushi Laslaiya ta kau da kai ta cigaba da kallon abinda yake faruwa.Mozur yayi iya ƙoƙarinsa akan ya ɓamɓare hannayen Zarto daga bayansa amma ya kasa kawai sai ya yiwa Zarto karo da ka a fuska.Bisa dole Zarto ya saki Mozur ya dire ƙasa da ƙafafunsa.Fuskar Zarto ta cika da raɗaɗi har idanun sa suka rufe ya zamana yana ganin mutane dishi dishi,saida ya girgiza kanshi sannan ya watstsake.Zarto ya ruga kan Mozur yana ruri da nufin ya sunkuce shi.Saida ya rage saura taku ɗaya ya riskeshi Mozur yayi tsalle sama ya shallake Zarto ya dira a bayansa.Cikin zafin nama ya juya ya shaƙo wuyan Mozur da hannu biyu saiga Mozur yana wutsiltsila ƙafafu yana kakarin mutuwa.Zarto ya ƙara haɗa ƙarfinsa duka yana mai daɗa shaƙe Mozur.Tabbas niyarsa kawai ya kashe Mozur murus har lahira.
Nan da Mozur

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login