Showing 12001 words to 15000 words out of 26566 words
Chapter 5 - Miftahuzzarbil Book 1 Complete By Abdulaziz Sani Madakin Gini.txt
zama a cikin ƙunci har ya rage saura kwana goma ranar gasar kokawa ta kewayo.
Koda sarki ya fuskanci kusantowar ranar sai ya kira Azmandu yace da shi,
"Ya kai sarkin gida kayi sani cewa ba zan hana wannan taro ba na gasar kokawa kuma bazan hana ka zuwa da bawa Mozur ba, domin idan nayi hakan duniya zata zage ni bisa abinda aka saba yi na al'ada a ƙasa ta.
Na yarda ka fito da Mozur ranar wannan gasa,amma sai na zuba masa dakaru dubu arba'in masu tsaronsa don kada ya gudu.
Kuma a ɗaure za'a zo da shi cikin sarƙoƙi a hannayen sa da ƙafafuwan sa da kuma wuyansa.
Ba za'a kwance shi ba face zai kafsa da abokin gwaminsa.
Yana gama kafsawar sai a ɗaure shi.
MU HADU A PART G DON JIN CIGABAN WANNAN HIKAYAR TA MOZUR✍️✍️😁😁👌**MIFTAHUZZARBIL**
LITTAFI NA BIYU ✍️✍️
PART G ❤❤💯
NA ABDUL'AZIZ SANI MADAKIN GINI 🧝♀️🧝♀️
TYPING AHMAD MUNNIR..
POSTING NAJIBULLAH MUHAMMAD 🥰🙏
Marubucin ya CI GABA DA CEWA..
Kuma a ɗaure za'a zo da shi cikin sarƙoƙi a hannayen sa da ƙafafuwan sa da kuma wuyansa.
Ba za'a kwance shi ba face zai kafsa da abokin gwaminsa.
Yana gama kafsawar sai a ɗaure shi.
Ba za'a gushe ana yin hakan ba har sai an kammala wannan gasa.
Ka sani cewa wannan karon gimbiya bata da lafiya tana kwance,don haka nine zan wakilce ta wajen bayar da kyauta ga wanda yaci gasar."
Koda sarki Amzadu yazo nan a zancen sa sai Azmandu ya sunkui da kansa a ƙas yace,
"Ya shugabana kayi sani cewa duk yadda kake son a tsara wannan al'amari haka za'a yi."
Sarki Amzadu ya bushe da dariya harda doka ƙafa.
Sannan ya kira sarkin yaƙinsa sadauki Akurga yace da shi,
"Na umarce ka daka shirya dakaru dubu arba'in waɗanda za suyi wa Mozur rakiya daga cikin gidan nuƙan abinci zuwa filin gasa don kada ya sami ƙofar guduwa."
Akurga ya rusuna yace,
"An gama ya mai duniya."
Nan take sarki Amzadu ya miƙe ya shiga gida,fada ta watse kowa ya kama gabansa.
Da ranar gasa tazo sai filin fada ya cika maƙil da jama'a ko'ina ka duba kawunan mutane ne birjik ba adadi.
Wannan karon dai jaruman kokawar basu da yawa,ba sufi su ashirin ba kuma akwai jarumi Zarto a cikin su.
Ga wanda baisan Zarto ba in ya ganshi a wannan lokaci ba zai gane shi ba saboda ya ƙara girma fiye da wancan karo da aka yi gasar har jarumi Mozur ya cinye shi.
Akwai alamun cewa wannan karon Zarto ya dawo da cikakken shirin,don ya karɓi kambun gasar daga hannun Mozur.
Har sarki Amzadu ya fito daga cikin gida ya zauna akan karaga don kallon wannan gasa ba'a kawo jarumi Mozur ba.
Wannan tasa jikin mutane yayi sanyi ya zamana ba'a wata hayaniya a filin gasar da kambama jarumai domin kowa so yake kawai yaga hallarar jarumi Mozur musamman masu goyon bayan jarumi Zarto saboda sun ci burin cewa wannan karon suke da nasara.
Har an kirawo jaruman farko sun hau tudun faɗan za su fara kafsawa sai aka hango dakaru dubu arba'in sun sako jarumi Mozur a tsakiya yana tafe yana jan sarƙa wacce ta ɗaure hannayen sa da ƙafafuwan sa kuma ta zarge wuyansa.
Duk da cewar fuskar Mozur ta cika da gashi kuma ya rame sai da masoyansa suka shaida shi.
Nan da nan filin ya kaure da shewa aka rinƙa ambaton sunansa ana cewa,
"Mozur!
Mozur!!
Mozur!!!"
Sautin wannan kiran suna ne yabi iska ya riski dodon kunnen gimbiya Laslaiya wacce ke kwance akan gado magashiyan tana jinya a cikin gidan sarautar.
Rabonta da miqewa zaune kwana ashirin da bakwai kenan.
Koda taji ambaton wannan suna na masoyinta sai ta miƙe zumbur ta fara waige-waige domin a tsammanin ta yana kusa ne.
Laslaiya ta dubi gabas da yamma,kudu da arewa ba taga kowa ba a cikin ɗakin data ke wannan jinya ba face wata baiwa guda ɗaya wadda ke kula da ita.
Ita ma kuma ta kishingiɗa a jikin bango barci ya kwashe ta,wataƙila saboda gajiyar aiki ne.
Gaba ɗaya gidan sarautar yayi shiru kamar babu mutane.
Sautin nan na kiran sunan Mozur ya cigaba da yawo a kunnen Laslaiya.
Nan take ta tuno cewar ai yau ne ranar zagayowar gasar jarumai.
Kawai sai Laslaiya ta ruga da gudu ta nufi hanyar fita daga cikin gidan sarautar.
A wannan lokaci wata doguwar farar rigace kawai a jikin ta mai shara-shara wadda ke nuna duk ilahirin surar jikinta babu takalmi a ƙafarta kuma babu wani ado a tare da ita.
Tana gudu gashin kanta na tarwatsewa a cikin iska.
Haka dai tayi ta gudun tana wuce tsirarun bayi da dakarun gidan masu hidima, kuma duk suka kasa ganewa cewa gimbiya Laslaiya ce a cikin wannan hali, saboda an san cewa ita kwance take cikin matsananciyar rashin lafiya.
A can filin gasa kuwa koda sarki yaga an zo da jarumi Mozur sai yace a janye kafsawar waɗannan jarumai na farko da suka hau kan tudu don buɗe taron a fara da karon jarumi Zarto da jarumi Mozur.
Koda jin haka sai jama'a suka sake ruɗewa da ihu da shewa domin dama kowa ya ɗagu saboda yaga yadda za'a yi wannan mugun karo ya zo.
Ba tare da ɓata lokaci ba aka kwance jarumi Mozur daga cikin sarƙa aka rako shi har bakin wannan gini mai tudu na gasa.
Mozur ya taka matattakala ya hau kan tudun.
Sannan jarumi Zarto ya hawo suka fuskanci juna aka fara kallan-kallo.
Nan da jama'a suka ƙara kaurewa da shewa.
Ko shakka babu ya karaya da wannan karo da zai yi da jarumi Zarto domin yasan cewa akwai yunwa a jikin sa da kuma ƙarancin lafiya.
Sai dai duk da haka masoyansa na ɗan ƙara masa ƙwarin gwiwa, saboda ganin yadda suke masa jinjina.
Ba tare da ɓata wani lokaci ba aka buga gangar fara gasa.
Yin hakan ke da wuya Zarto ya juya ya dubi sarki Amzadu yayi sujjada a gare shi yana mai kwasar gaisuwa.
Sarki Amzadu ya duƙar da kansa ƙasa kaɗan alamar ya karɓi gaisuwar.
Sannan ya nuna masa inkiyar ya kashe jarumi Mozur murus har lahira ta hanyar nuna kaifin hannu a wuya.
Zarto ya jinjina kai gami da murmushi alamar cewa ya fahimci buƙatar sarki.
Cikin zafin nama ya ruga ga Mozur.
Kafin Mozur yayi wani yunƙuri tuni Zarto ya matse shi da hannu biyu a gadon bayansa.
Mozur ya fara ihu saboda tsananin zafi da zugi tamkar ƙasusuwan bayansa zasu kakkarye.
Nan fa Mozur ya cigaba da ƙoƙarin ya cire hannayen Zarto daga ruƙon da yayi masa amma ya kasa.
Mozur ya yiwa Zarto karo da ka a fuska har sau huɗu,amma a banza,baiji komai ba bare ya sake shi.
Nan fa Mozur ya cigaba da rusa ihu saboda azabar da yake ji a bayansa.
Shi kuwa Zarto sai ƙara taƙarƙarewa iya ƙarfin sa kuma yana bushewa da dariya.
Saida kusan rabin sa'a ta shuɗe a haka Mozur bai fasa ihu ba shi kuma Zarto yaƙi ya sake shi.
A wannan rana dai Mozur yaci baƙar wahala tamkar zai mutu.
Da ƙyar ya samu ya ware 'yan yatsun hannunsa ya luma su cikin ƙwayar idanun Zarto.
Zarto yayi ihu ya saki Mozur saboda raɗaɗin da yaji a cikin idanun nasa.
Mozur ya tafi taga taga zai faɗi amma sai ya daure ya tsaya da ƙafafunsa.
Koda ganin haka sai masoyansa suka kaure da shewa aka hau yi masa tafi.
A lokacin ne Zarto ya dawo cikin hayyacinsa idanunsa suka buɗe.
Cikin tsananin fusata da shammata ya sake rugawa ya shaƙo wuyan Mozur shaƙa bata wasa ba.
Nan take idanun Mozur suka zazzaro kamar zasu faɗo ƙasa ya fara wutsil-wutsil da ƙafafuwan sa da kuma hannayen sa.
Tun yana motsa su da ƙarfi ya fara ɗaga su da ƙyar wata irin kumfar wuya da majinar wahala suka fara dalala.
Nan take gana ɗaya jikin masoyan jarumi Mozur yayi sanyi,wasu ma suka fara kuka don gani suke tabbas mutuwa zai yi.
**************
Sarki Amzadu kuwa banda ƙyaƙyata dariya babu abinda yake yi.
A daidai wannan lokaci ne gimbiya Laslaiya ta iso filin gasar cikin matsiyacin gudu.
Koda tayi arba da jarumi Mozur a hannun Zarto taga halin da ya shiga sai ta kwarara ihu tana mai kiran sunan Mozur.
Cikin shiɗewa Mozur ya jiyo wannan kira kuma ya shaida muryar mai kiran.
Ba zato ba tsammani,sai aka ji Mozur ya kwarara uban ihu shima yana mai kiran sunan Laslaiya.
Nan take ya ɓanɓare hannayen jarumi Zarto daga wuyansa da ƙarfin tsiya.
Sannan ya ɗaga shi sama ya dinga wulwula shi kamar yana wasa da majajjawa.
Lokaci guda kuma ya damfara shi da ƙasa.
Bisa tsautsayi sai Zarto ya cake da ka.
Take wuyansa ya karye ya mutu,ko shurawa bai yi ba.
Faruwar hakan ke da wuya gimbiya Laslaiya ta ruga da gudu ta hau kan matattakala ta isa kan tudun da Mozur ke tsaye.
Da zuwa ta faɗa kan ƙirjinsa suka rungume juna cikin tsananin farin ciki.
Sarki Amzadu ya miƙe zumbur a fusace yana mai bawa dakaru umarnin su hallaka jarumi Mozur.
Kafin dakarun suyi wani yunƙuri sai aka hango ƙura ta turnuƙe gabas.
Nan fa kallo ya koma gabas ɗin kowa ya tsaya ƙyam.
Kawai sai aka ga ashe wasu dubunnan mayaƙa ne a sukwane bisa dawakai suka kawo farmakin sumame.
Nan fa gari ya ruɗe,waje ya hargitse akayi ta gujeguje da iface-iface.
Shi kansa sarki Amzadu da rarrafe ya samu ya ruga ya kama doki ya hau.
Sannan ya sukwani dokin a guje izuwa cikin gidan sarautar baima kula da batun 'yarsa ba, gimbiya Laslaiya.
Su kuwa dakarun nan guda dubu arba'in waɗanda aka sasu tsaron jarumi Mozur sai suka riga suka tari waɗannan baƙin mayaƙan sumame aka fara kafsa yaƙi.
Koda jarumi Mozur yaga yadda waje ya hargitse sai ya ɗauki gimbiya a hannunsa ya ruga da ita zuwa inda wani farin doki ke ɗaure.
Koda ya iske dokin sai ya ɗora gimbiya akai.
Sannan shima yayi tsalle ya haye kan dokin ya fincike igiyar aka.
Sannan shima yayi tsalle ya haye kan dokin ya fincike igiyar da ta ɗaure ƙafar dokin da ƙarfin tsiya har turken da aka ɗaure igiyar a jiki ya tumɓuko daga cikin ƙasa.
Mozur ya zunguri dokin da ƙafafunsa ya sukwane shi a guje.
Maimakon subi hanyar cikin gari sai suka kewaye ta bayan dakarun dake gabza yaƙi da mayaƙan sumame suka nausa cikin daji suka yi ta gudu ba ƙaƙƙautawa.
Al'amarin sarki Amzadu kuwa lokacin da suka isa fada shi da fadawansa cikin gudu sai suka tsaya aka fara shirye-shiryen yaƙi,don akwai waɗancan dakaru dubu arba'in na ɗaukin gaggawa, domin kuwa mayaƙan sumamen na da matuƙar yawa fiye da ƙima.
Nan da nan aka shirya dakaru masu yawa aka yi hawa har da shi kansa sarki Amzadu inda ya bayar da umarnin cewa lallai a nemo jarumi Mozur da gimbiya Laslaiya a duk inda suke kuma a ƙarar da waɗannan abokan gaba da suka kawo farmakin sumame.
Nan take sarkin yaƙi ya jagoranci dubunnan ɗaruruwan mayaƙan garin suka sukwani dawakai cikin matsanancin gudu suka nufi ƙofar filin fada inda ake yaƙi.
Idan mutum yaga wannan zuga a wannan lokaci sai yayi zaton mayaƙan duniya ne kaf suka fito yaƙi.
Ƙarar kofaton dawakai ma kaɗai ya isa ya firgita mutum bare kuma ihun mayaƙan da kuma ƙarajin su wanda ya cika garin gaba ɗaya ya firgita ƙananan yara da mata suka kama koke-koke.
Tsofaffi kuwa suka tsure da gudawa.😅😅
Lokacin da mayaƙan kawo ɗauki suka iso filin yaƙin sai suka iske an yiwa 'yan uwansu lugude an karkashe su saura ƙalilan.
Nan fa aka sake kaurewa da sabon yaƙi.
Karafkiyar ƙarafa ta yawaita.
Jini ya ringa fallatsa yana malala a ƙas.
Nan fa kasuwar ɗaukar rayuka ta kama ci.
Masu ƙarfi da jarumta suka rinƙa ciniki ba sassautawa.
Jarumi Mozur da gimbiya Laslaiya kuwa saida suka kwana suka yini suna tafiya akan dokin nan tana kwance akan ƙirjinsa basu tsaya ba saboda gudun kada a biyo bayansu a cim masu.
Saida suka iso wani ƙaramin gari dake cikin nahiyar ƙasar.
Sannan suka tsaya gaban wata rijiya suka sauka.
Anan ne suka sha ruwa,suka zauna suna kallon juna.
Koda suka ga yadda kowannensu ya rame sakamakon ƙuncin rashin ganin juna sai suka fashe da kuka.
Gimbiya Laslaiya ta rungume Mozur tace,
"Ya kai masoyi na haƙiƙa na san mun shiga cikin mugun ƙunci da azabar cutar bege.
Amma yanzu ina jin farin ciki tamkar ban taɓa shiga damuwa ba, saboda kasancewa tare da kai a yanzu.
Lallai kuwa ba zan sake yarda wani abu ya raba mu ba face mutuwa."
Jarumi Mozur ya janye jikinsa daga cikin nata suka fuskanci juna.
Sannan yace,
"Ya ke abar begena dare da rana kiyi sani cewa zuciya ta da raina sun kori komai daga cikin su.
Ba za su bar abin da ya kai ƙwayar zarra ba face ke.
Ina tabbatar miki da cewa ji da gani na , tafiya da kwanciya ta begenki ne ke musu jagora dare da rana.
Nayi miki alƙawari daga yau ko ruwa ko iska ko wuta ko guguwa,komai yawan bala'i da masifa ba zan yarda mu rabu ba face babu ruhin numfashi a cikin gangar jikina."
Koda jin wannan batu sai farin ciki da daɗi suka lulluɓe gimbiya Laslaiya ta sake rungume Mozur.
***
Koda sarki Muhucul yazo nan a labarin sa sai yayi shiru ya dubi su Ruziyal yace,
"To lokaci yayi halinsa,anan zan dakata sai gobe kuma idan muna raye ku dawo na cigaba da wannan labari."
Yana gama faɗin haka ya miƙe ya shiga gida,fada ta watse kowa ya kama gabansa aka bar su Ruziyal a zaune cikin matuƙar damuwar rashin jin ƙarshen wannan labari.
*******
Al'amarin su aljani Markahus sabus kuwa bayan sun sami nasarar ɗebo narkakken dutse daga cikin dutsen da yafi kowane dutse girma,sai aljani Durmazalu ya cigaba da tafiya da su a cikin sararin samaniya.
Sai da suka yi tafiyar sa'a bakwai cif.
Sannan suka sauko ƙasa suka dira akan wani ƙaramin tsuburi.
Saukar su ke da wuya aljani Durmazalu yayi gyaran murya yace,
"Ya ku abokan tafiya ina kira a gare ku da kowa ya shirya, domin yanzu ne zamu yi tafiya mai haɗarin gaske fiye da wadda kuka gani a baya.
Kuyi sani cewa yanzu ne zamu shiga cikin ƙarƙashin ƙasa don mu isa duniyar ƙarshe mu ɗebo dutsen wuta.
Ina sanar da ku cewa ita dai wannan duniya ta ƙarshe itace ta bakwai kuma kafin mu risketa sai mun ratsa ta cikin duniyoyi shida a cikin kowacce duniya akwai irin halittun da ke cikin ta,kuma duk sun kasance masu ƙarfin mulki da ƙarfin sihiri.
Bai zamo lallai ba mu wuce ta cikin waɗannan duniyoyi shida lafiya.
Babu mamaki wasun mu su hallaka ko kuma mu duka mu halaka.
Saboda bala'in dake tattare da waɗannan halittu na duniyoyin ƙassai.
Ina mai shawartar mu damu jajirce,musa a ranmu cewa muna tare da nasara in kuwa zuciyoyinmu suka karaya ba zamu taɓa samun dacewa ba."
Koda aljani Durmazalu yazo nan a zancen sa sai markahus sabus,boka jinshan,durfus,boka sulbaini da yarinyar nan ta birnin duwatsu wato salusa suka yi tsuru-tsuru da idanu,tsoro ya baibaye su kuma hankalin su ya dugunzuma don basu san irin bala'in da zasu riska ba a cikin duniyoyin ƙassai.
Ba tare da ɓata lokaci ba Durmazalu ya nutse cikin ƙarƙashin ƙasa ɗauke da su markahus sabus,yayi ta tafiya.
Saida suka yi tafiyar kwana uku.
Sannan suka iso duniya ta ɗaya wadda ake kira Madinatul Aslik.
Koda bayyanar su a cikin wannan duniya sai duk suka zama ƙauyawa suka kama kalle-kalle suna masu mamakin irin gine-ginen birnin da suka tsinci kansu a ciki da kuma irin halittun dake rayuwa a cikin sa.
Shi dai wannan birni na Madinatul Aslik an gina gidaje a cikin sa da zallan darma.
Ko ina ka duba a garin babu ƙasa saidai ka taka shimfiɗaɗɗiyar darma mai kama da tabarma, domin za'a iya naɗeta.
Babu wani wuri wanda za'a iya yin shuka bare tsuro ya fito.
Su kuwa halittun sun kasance 'yan wadanni dugul-dugul babu wanda tsawonsa ya wuce kamu ɗaya,kuma sun kasance'yan ƙanana sirara,shafal-shafal basu da nauyi.
Babu abin mamaki face yadda suke iya ɗaukan gunguma-gunguman ƙarafa.
Wani ƙarfen ma ko markahus sabus bai isa ya iya raba shi da ƙasa ba,bare su boka jinshan 'yan ƙananan alhaki.
Fuskokin waɗannan halittu irin na mutane ne haka ma hannayen su da ƙafafuwan su,amma kuma wani irin dogon baki ne da su,wanda daga ƙarshen sa yayi doro da tsini,kamar bakin aku,kuma ƙwari ne da shi kamar ƙarfe,duk abinda suka caka da shi take abin zai huje ya burma koda kuwa dutse ne.
Gaba ɗaya ƙarfin waɗannan halittu a jikin bakin na su yake, domin ƙarafan ma da suke ɗauka masu nauyi da bakin na su suke ɗauka.
Basu da abin hawa kamar dawakai,ko jakai,amma suna yawo ne akan wasu irin manyan jemagu masu siffar ban tsoro.
Koda ganin dirar aljani Durmazalu a cikin wannan birni ɗauke dasu markahus sabus sai mutanen garin suka tsaya cak suka daina komai suka zuba musu na mujiya.
Su kuwa sai suka cigaba da tafiya bisa ƙafafunsu.
Su shiga nan su fita can.
Su dai ba su yiwa kowa magana ba, kuma babu wanda yayi musu magana.
Duk ta inda suka ratsa sai a tsai da harkoki ayi ta kallon su.
Haƙiƙa su markahus sabus sun ga abubuwan al'ajabi a cikin wannan duniya fiye da sauran abubuwan da suka gani a baya tun farkon shigowar su cikin wannan aiki na nemo abubuwa uku don ƙera kubar MIFTAHUL ZARBIL.
Babu abinda yafi basu mamaki face wata siririyar kwalba wacce mutanen wannan birni suka ajiye ta a tsakiyar birnin.
Saboda tsananin tsawon kwalbar sai kaga kamar zata tokare da hadarin sama.
Idan kuwa mutum yace saiya kewaye kwalbar to tabbas sai ya kwana arba'in yana zagaya ta bai dawo kan inda ya fara ba.
Ita dai wannan kwalba a cike take da ruwa,kuma anyi wani famfo a jikin ta wanda ke zubar da ruwa.
Kowa saika ga yazo ya tari ruwan yayi gaba don amfanin kansa.
A lokaci guda sai mutum dubu su zo su ɗiba suyi gaba,amma ruwan baya ƙarewa duk da cewar girman kwalbar baikai na mutum ɗaya ba,kawai dai tsawo gareta.
Markahus sabus ya dubi kwalbar da kyau yace,
"Jau wanda bai yawo ba a duniya bai more kallo ba.
Kun ga inda labari aka bamu aka ce akwai wannan kwalbar ba zamu yarda ba,amma tunda da idanun mu muka gani dole mu gasgata."
Kafin wani daga cikin su boka jinshan yace wani abu sai suka ga anyi musu ƙwawanya.
Wasu mutanen garin ne cikin shigar mayaƙa kimanin su dubu bisa jemagun nan.
Ko sillan kara babu a hannunsu,amma kuma bakunan su sun fi na sauran mutanen garin tsawo da faɗi.
Kafin su aljani Durmazalu suyi wani yunƙuri tuni an cafkosu da bakuna ɗaiɗai an ɗora su akan jemagun an cilla da su da gudu a cikin sararin samaniya ba tare da ɗayansu ya iya ƙoƙarin gudu ba.
********************
Aljani Durmazalu ya dubi girman halittar jikinsa mai ɗauke da fukafukai miliyan ɗaya yaga cewa girman sa bai amfane shi da komai ba,tunda ga ƙananan halittu sun kama shi