Showing 33001 words to 36000 words out of 142577 words
Chapter 12 - TAWA TA SAME NI BOOK 1 COMPLETE DOCUMENT by Halima Abdullahi k. Mashi .txt
Abba yace.
"Farouq ku tafi dare yanayi."
"toh" yace sannan suka rekosu harabar gidan Usman ne ya bud'e musu mota bayan sunyi saida
safe sannan Hamma Umar yaja motar suka tafi.
Tunda suka shiga motar ummul taci gaba da kukan ta,
shi kuwa Hamma Umar tuk'in kawai yakeyi hankalin shi na kan titi haka sukayi tafiyar tasu
Ummul daga Potiaskum har cikin Damaturu kuka take batayi shiru ba,
suna isa k'ofar gidan ba tare d'aya shiga cikin gidan ba yayi parking sannan ba tare d'aya
kalleta ba ya fito gefen da take ya zagayo marfin motar ya bud'e sannan ya jawo hannun ta,
ita kuwa sai fizge hannun take tana k'ok'arin kwancewa,
shiko sai matse hannun yayi da k'arfi cikin sanyi ya jata zuwa bak'in gate d'in juyawa yayi ya
kalleta cikin bada umurni yace.
"Ki nitsu kisan abinda kikeyi karki kuskura ki shigar min gida da k'afar hagu ,
sannan kiyi Addu'a kafin ki shigar min gida, dan na lura akwai shaid'anu a tsakiyar kanki,
so ki watsar dasu anan kan titi karki kuskura ki shigar min gidana da su."
kai ta sunkuyar cikin zubda k'ollah dan ta tuno Nenne tama ta horeta da tayi addu'ar kafin ta
shiga gidan,
k'ollah ta zubda sannan a hankali ta d'aga k'afar ta dama wanda kusan a tare suka d'aga
k'afafun nasu,
a hankali sukayi addu'ar shiga gida sannan suka shiga cikin gidan.
A gida kuwa bayan Hamma Umar yaja motar sun tafi,
Usman ne ya dafe k'ahon zuciyar shi da sauri jin yadda zuciyar shi ke bugawa da sauri-sauri
idon shi ya rumtse da k'arfi lokaci d'aya yaga wani irin duhu cikin k'arfin hali ya juyo ya kalli
Nenne sai yayi murmushi ya bud'e baki a hankali yace ,
"Shike nan yau kam ni kad'ai zan kwana ba Hamma Umar,
da safe kuma ba Ummul wazan tsokana?."
Dariya su Ammi sukayi mishi sannan suka juya zasuyi cikin gida kenan a dai-dai lokacin Usman
yayi wani irin numfashi tare da dafe k'irjin shi yayi taggal-taggal ya fad'i kan kujerun jiki ba.....
By
*GARKUWAR FULANI*
ν ½ν³ν Όν½ν Όν½ν Όν½ν Όν½ν Όν½ν Όν½ν Όν½ν Όν½
*RUBUTACCEN AL,AMARI*
Page 1β£4β£
*NA*
*AYSHA ALI GARKUWA*
ν Όν½ν Όν½ν Όν½ν Όν½ν Όν½ν Όν½ν Όν½ν Όν½ν Όν½
*Y'an uwa abokai k'awaye yayu k'anne yara manya maza da mata masoya na da sab'anin haka
writers da reedars dan Allah don soyeyyar mu da Annabi ina barar addu'arku ga mahaifiyata
bata da lafiya dan Allah kusa min ita a addu'arku da bakunanku masu albarka Allah ya bata
lafiya rabbi ya tashi kafad'an ta Allah yasa zakkan jiki ne a wanan gab'ar kuma zan shaida muku
ba tabbas kuci gaba da samun posting nan kullum in nasamu nayi fani'imal in ban yiba la'basa
nasan zaku min uzuri, DEDDE Am Allah ya baki lafiya ν ½νΈν ½ν±ν ΌνΏ»*
*A baya nace Usman Accounter ne so na batane Usman Lecturer ne a Yobe state university so
daga yanzu a lecturer sa zamu tafi dan shine aikin sa na gaskiya*
*B*a numfashi ya konta kan kujarar ba inda yake motsi a jikin shi, gaba d'aya su Nenne da
Abba dasu Hajjajo a tare suka juyo kanshi ya Adam ne yayi sauri ya tallabo shi jikin shi cikin
tsananin firgici ya rink'a juya kanshi yana d'an tab'a fuskar shi cikin d'imuwa yana .
"Usman ! Usman ! Usmaaaaaaan! ka tashi ka tashi Usman , Abba Daddy ku gani Usman baya
numfashi."
Sai kuma ya k'ara rugumoshi jikin shi cikin rawan jiki,
Abba ne yasa hannu ya jawo Usman d'in jikin shi cikin k'arfin hali irin na manya ya cewa
Daddy.
"Hussaini kawo wuruwa."
jiki na rawa Daddy ya shiga cikin gidan,
Ammi kuwa tunda Usman ya fad'i gaba d'aya sai jikin ta ya fara rawa kar-kar ko ina na jikin ta ya
sake k'afafun ta suka k'asa d'aukar nauyin ta zuciyar ta sai bugawa take tara-tara cikin wani irin
rashin kuzari ta zame a wurin ta zauna ta jingina da kujaran da Usman yake kai cikin sanyi baki
na rawa take cewa. "Ya Allah ka rufa min asiri Allah ka dub'eni da idon rahama Allah ka hanani ganin mugun abu
Allah ka jinkirtawa wannan bawa naka kabashi lafiya Usman Allah ya hanani ganin gawarka
ganin na mahaifinku ma har yau bai bar idanuna ba."
Inna ce ta dafa ta cikin sanyi tace.
"Kiyi mishi Addu'a Amina addu'arki gare shi ba hijabi insha Allah karb'ebb'iya ce ."
jin haka sai zuciyar Ammi ta kara karaya cikin sanyi ta kontar da kanta a cin yar Innarta ta kamo
hannun Usman ta rink'a wani irin kuka mai cike da fargabar faruwar wani abu,
Hajjajo ma sai kukan takeyi ya Sadip da Aliyu ma gaba d'aya sun k'asa saida hawaye su Anty
Halima kuwa cikin gida ta shiga tana kuka cur-cur,
Daddy kuwa yana zuwa ya d'auko goran ruwan mai sanyi ya dawo Abba ya mik'a wa,
yana karb'a ya b'alle marfin gorar sannan ya tuttulo ruwan sanyin a tafin hannun shi da k'arfi ya
watsa a fuskar Usman d'in,
a take sai yayi wani irin ajiyan zuciya mai k'arfi sai kuma yayi shiru numfashi sa na harbaqa ,
cikin kuka Ammi ta rik'o hannun shi tana.
"Usman ! Usman! Usmaaaan!." sai kuma ta fashe da kuka,
Shi kuwa can sama-sama yake jin sautin kukan mahaifiyar shi da sauran yan uwa,
cikin tsananin mutuwa jiki ya bud'e idanun shi kuma sai ya lumshe su ganin baya ganin su sosai
,
su kuwa ganin haka yasa Ya Adam ya zaro woyarshi da sauri yace.
"Abba bari in kira Hamma Umar yazo ya duba shi."
jin hakan yasa Usman d'in ya k'ara bud'e idanun shi cikin rawan. Murya yace.
"Ah,Ah a a Adam kar ka gayawa Hamma Umar komai ka barshi ,
naji sauk'i."
meda woyar Adama yayi cikin jin dad'i ya kamashi ya rugume murya na rawa yace.
"Usman meyasa kake wasa da lafiyar ka me kake tunawa me damuwarka a duniyar nan
Usman?."
cikin k'arfin hali ya d'an ture Adam sannan ya d'an jingina da jikin kujerar ya kamo hannun
Ammin shi ya kalli Hajjajo da inna dake ta zubda k'ollah yace.
"Kai da Allah ni ku dena min kuka lafiyata lau ji tsoffin nan fa aini ras na ke sai namu rakiya kafin
nima a min rakiya zuwa gidana na gaskiya,
Abba kace su dena kuka ni na worke."
Sai kuma ya kalli Ammin shi cikin sanyi yace.
"Ammi shi komai da kika gani a duniyar nan toh Rubutaccen al'amari ne so karki damu ki sawa
ranki dangana insha Allah ba zakiyi kuka ba matukar Hamma Umar na yana raye,
karki damu shi d'aya ne tamkar da mu biyu kinji ko Ammi na."
kanshi ta shafa cikin rawan murya tace.
"Ku duk ina fatan ku rayu har bayan rayuwa ta."
dariya ya d'an yi sannan ya kalli Abba da Daddy dake binshi da ido cikin fidda numfashi mai
nauyi yace .
"Dan Allah Abba kar a gayawa Hamma na kunga kar hankalin shi ya tashi."
Nenne ce ta kalleshi a hankali tace,
"Kasha maganin ka yau?."
Kai ya gyad'a mata sannan yace.
"Hamma Umar ya bani kafin ya tafi."
so haka yayi ta basu k'arfin guiwa ya kuwa hanasu su gayawa Umar,
a haka sukayi ta mishi nasiha kan shan maganin shi, sannan Abba yace daga yau shi da Adam
zasuke kwana tare,
haka kuwa akayi,
shi kuwa Usman,
suna shiga d'akin nasu ya zame ya shiga toilet k'ofar ya maida ya rufe cikin tarin takaici dajin
haushin kanshi da zuciyar shi ya kife kanshi jikin gini ya rink'a wani irin kuka maicin rai kuka
yake yana d'an dukan saitin kahon zuciyar shi cikin kukan yake cewa.
"Kai tona da Wannan zuciya tawa mai zuwa hurumin daba nataba."
haka yasha kuka har saida yaji kamar numfashi sa zai yanke sannan yayi al'wala ya fito ya
shimfid'a sallaya ya fuskanci gabar,
Adam ne ya kalleshi cikin kula yace.
"Usman zaka iya tsayuwa ? ka konta mana ka d'an huta."
Murmushi yayi cin juya fuskar sa dan baya son Adam yaga idanuwan shi da sukayi jazir suka
kumbura,
cikin yanayin wasa yace.
"Kai nafa fika lafiya kuma zanyi wa Hamma na da Ummul addu'ar Allah ya basu zaman lafiya
dakuma 'yan biyu."
dariya Adam yayi tare da cewa.
"A a yan ukune ba yan biyu ba."
Toh hakafa rayuwa tayi ta juyawa Usman kullum yakan b'uya yasha kuka har sai yayi gyatsa ya
kuma ji numfashi sa na carkewa sannan ya fito,
ba kuma wanda yasan halin da yake ciki.
*Gidan Hamma Umar da Ummul kuwa*
Bayan sun shiga cikin gida Hamma Umar na rik'e da Hannun Ummul d'in a haka ya jata har
bak'in k'ofar shiga cikin asalin gidan bak'in k'ofar parlour ya tsaya key ya zaro a haljihun shi
sannan ya bud'e k'ofar cikin bada umurni yace.
"Kiyi Addu'a ki kuma shiga da k'afar dama."
bata kulashi ba sai k'ollah da take zubda wa sannan tayi yadda yacen,
suna shiga cikin Parlour Ummul tayi fizge hannun ta cikin kallon yadda Abban ta ya binne mata
dukiya a parlour fuska cike da k'ollah tayi cikin bedroom da gudu tana zuwa shiga ta maida
kamar ta rufe kan gado ta fad'a cikin disashewar murya taci gaba da sana'arta,
shi kuwa Hamma Umar shiru yayi a parlour ya tsurawa k'ofar d'akin ido yana jin sautin kukan
can k'asa-k'asa kai ya juya ya fito kai tsaye motar shi ya shigar cikin gida ya ajiye ta a harabar
gidan sannan ya bud'e bayan motar ya d'auko lodojin da ya ciko da abubuwan cin da sha,
kai tsaye parlour ya shigo kan dinning table ya ajiye ledojin sannan ya bi d'an corridor dake
gefen d'akin da Ummul ta shigan nan ma wani d'aki ne babba wanda yasha gyara da shimfid'u
daga dukan alamu dama nanne d'akin da yake rayuwa in yazo Damaturun daga can d'aya
b'arin kuma nan ma akwai wani bedroom d'in dan gidane mai yalwar d'akuna parlour ne guda
d'aya babba wanda ke d'auke da dinning area mai girma da tsarina sai daga gefen shi wani d'an
corridor ne da zai sadaka da kitchen sai sito dake manner a gefen shi,
ta bayan kitchen din kuwa d'an k'aramin wurine mai cike da tsirrai masu kyau ,
cikin parlour kuwa yana d'auke da 3 bedroom,
so yana shiga d'akin sa wonka yayi sannan ya fito yayi shirin baccin sa,
parlour ya fito cikin nitsuwa yana taku mai cike da haiba a hankali ya jawo kujara ya zauna a
dinning table d'in kanshi ya jingina jikin kujerar sannan ya d'ora k'afafun shi kan table d'in yana
d'an kad'a su a hankali ida nunshi ya lumshe tare da kamo lips d'in shi ya matse yana jin yadda
Ummul ke yin kuka cikin sauti mai cike da rauni da wahala da alamun gajiya daga kuma jin
sautin kukan da alamun zazzab'i a jikin ta,
ido ya k'ara rumtsewa dan yana jin kukan nata na ratsashi dan window d'akin ta yana ta saitin
dinning area d'in,
cikin sanyi ya mik'e a hankali yaje bak'in k'ofar, cikin murya mai cike da tausayawa yace.
"Khairi kiyi hak'uri ki dena kukan nan ya isa kizo ki bud'e k'ofar kinji kibar kukan kar ya saki
zazzab'i ki fito kici abinci kinji ko Khairi?."
kukan Ummul ta kuma k'ara yi cikin dishewar muryar tace.
"Bazan fito ba,
ka barni nayi kukana in banyi kukaba me zanyi ? bazanci abincin ba inya so yunwar ta kasheni
kowa ya huta tunda dama ba,a sona."
Shiru yayi sannan ya d'an yi ajiyan zuciya tare da cewa.
"Khairi baki da lafiya fa ki bud'e kizo kici abinci kisha maganin inyaso kyaci gaba da kukan tunda
shi kikeso ."
bata kuma kula shi ba haka tayi ta kukan ta yayi ta lallashin ta a banza,
haka ya hakura ya barta ya koma bedroom d'in shi ba tare da yaci abincin ba,
ita kuwa haka ta kwana kuka har Allah ya wayi gari.
Bayan Hamma Umar d'in ya dawo masallaci ne ya zauna a parlour tare da kunna TV ya kama
tashar manara idan ya samu sun saka sautin karatu k'ura'ani tare da muryar Ahmad Sulaiman
volume ya k'ara ta yadda sautin ya rink'a ratsa cikin gidan baki d'aya kan kujera ya konta ya
lumshe ido yana bin sautin karatu hannun shi kuma rik'e da carbi, itako Ummul tunda tayi salla ta konta kan sallayar cikin jin zazzab'i ga ciwon kai kuma ta k'asa
barin kukan,
a haka tana kukan har bacci ya saceta,
shi kuwa bai bar parlour ba sai 9:00 am ya mik'e ya shige kitchen nasu gas ya kunna tare da
d'an tafa musu ruwan tea sannan ya sake d'uma kajin daya seyo ajiyan ya had'a musu komai
yazo ya ajiye kan dinning d'in ,
d'akin shi ya shige wonka yayi sannan ya shirya cikin kananan kayan ya fito ras sai k'amshi
yake zubawa,
kai tsaye k'ofar d'akin ta yazo ya tsaya cikin sanyi yace.
"Khairi ! Khairi ! tashi kizo kiyi breakfast."
tana jinshi tayi shiru kamar bata jinshi ,
sai mik'e wa tayi ta zauna ta jingina jikin gado tana jin yadda yake kiranta tayi cib kamar bata
d'akin,
shi kuwa sai komawa yayi ta jikin window ta ya bud'e glass d'in sannan yasa hannun ya bud'e
labulen ido ya zuba bata,
itama idon ta zuba mishi cikin nuna kiyayyarsa a fili,
kai ya jinjina cikin jin tausayin ta yace.
"Khairi taso kizo kinji ko."
"Bazan zoba bazan cin abince ba,
Na mutuwa mane me ruwan ka?."
Kai ya juya tare da cewa.
"Meyasa bazaki ciba."
a kufule tace .
"Sabida na tsane kaa! bana son ka! bana son ganin ka! bana son ko jin muryar ka!."
ido ya zuba mata cikin tsananin mamaki da al'ajabi bai tab'a zaton k'iyayyar da Ummul take
Mashi yakai matsayin da zata kalleshi ido da ido tace mishi bata sonshi bata k'aunar shiba,
muryar tace ta kuma katsemai tunani tana cewa .
"Na tsane ka tunda ko yaushe a sana dinka nake azabtuwa."
Kallon ta ya kumayi sannan a hankali yace.
"Kina son kanki ai?."
"Sosai ma dama ina son kaina kam mana."
murmushi ya d'an yi sannan yace.
"Toh ki fito kici abinci dan ki kula da kanki ni kuma nagode da k'iyayyarki gareni."
"Bazan ciba ! ba kuma zan fito ba!."
Haka Hamma Umar yake ta fama da Ummul Amman sam tak'i fitowa ,
zuwa yanzu kuwa kukan har ya gaji da ita dan ba itace ta gaji da kukan ba kukanne ya gaji da
ita sai dai tayi ta diri ba hawaye shi kuwa duk kula da tattali yana had'a mata Amman ko fitowa
tak'i tayi bataci komai sai ruwan da take sha da fari bata jin yuwar Amman zuwa yau da tayi
kwana biyu a hakan sai take jin yunwar kamar zata kasheta inta tsaya sai jiri , tayi wonka kuwa yafi sau 3 wai duk ko zataji k'arfi Amman abin yaci tura a deren kwana na 3 ne
ta k'asa bacci dan yunwar dake kwak'ularta.
Shi kuwa Hamma Umar gaba d'aya kewar d'an uwanshi ya cika mar jiki da zuciya haka yasa
kullum sai sunyi magana a woya a kalla sau 5 zuwa sau 6 duk lokacin shan maganin Usman in
yayi sai Umar ya kirashi yace mishi kasha maganin a b'aggaren Ummul kuwa yana damuwa da
halin da take ciki.
A al'adun shuwa'arab d'in kuwa suna yin wata al'adarsu duk lokacin da akayi Aure aka kai
Amariya gidan ta washe gari y'an uwanta zasuje karb'ar tukuici a gun aggo kuma Wannan
tukuici ba'a badashi sai aggo ya kusanci matarshi so haka yasa wasu basa zuwa washe garin
randa aka kai Amariya sukan bari sai randa tayi kwana 3 ko 7 kuma Wannan tukuici ba'a ba
dashi ga amariyar da bata kai budurcin ta gidan mijin taba,
so Hamma Umar kuwa yasan da wannan al'dartasu,
so yau ya tashi da wuri ya kimtsa ko ina na gidan dan yana tsammanin y'an uwan Ummul zasu
zo yau d'in tunda yau kwanan ta uku da zuwa gidan,
bayan ya gama komai yayi wonkan shi fes ya fito ya shirya cikin
wagamri mai kalar sararin samaniya ya fito ras sai k'amshi yakeyi.
kamar kullum yazo bak'in k'ofar d'akin nata cikin sanyi yace.
"Khairi ki zo ki bud'e k'ofar nan zakiyi bak'i su Anty Shuwa na zuwa."
A hankali cikin wahala da jiri ta mik'e tazo bak'in k'ofar ta bud'e sai kuma ta juya ta koma ta
zauna gefen gado tana ta haki hannun ta rik'e da cikin ta,
shi kuwa Hamma Umar yana ganin haka ya koma parlour dinning area ya nufa yana zuwa,
ya d'auki cup tea ya had'a mata mai kauri sannan ya juyo ya dawo cikin d'akin yana shiga kiran
Usman na shiga woyar shi gefen ta yaje ya zauna sannan ya mik'a mata cup d'in cikin kula
yace.
"Karb'i kisha tea zakiji k'arfi."
kai ta juya tare da matse ido ta samu ta zubda k'ollah,
shi kuwa woyarshi ya zaro ya amsa kiran yana kallon fuskar ta,
gaisawa sukayi da Usman sannan yace .
"Kashe maganin ko?."
"Eh nasha tun d'azun ma."
sai kuma yayi shiru... can kuma yace .
"Hamma Umar Ummul fa?."
"Gata nan tana ta kuka tak'i cin komai kuma bata da lafiya ,
gata bari in bata woyar."
"Toh" yace sannan yayi shiru yana jin Hamma Umar d'in yana cewa.
"Ga Usman yana magana."
Karb'ar woyar tayi cikin rawan jiki murya na rawa tace.
"Hello ya Usman."
A hankali cikin sanyi yace.
"Na'ammmm Ummul."
Tana jin muryar shi sai kuma ta fashe da