Showing 3001 words to 6000 words out of 12075 words

Chapter 2 - BINTA YAR JAGALIYA COMPLETE oum yasmeen.txt

motsa labɓansa yana bi a hankali har suka iso ƙasar limon a hankali yake tattaka stairs case ɗin jirgin yayin da brief case ɗin na hannu zan wata kyakkyawar motar baƙa har ta glass ɗin baƙi ne yar gidan Benz ta tsaya a gaban sa


security ɗin sa suka tare shi saboda irin ciƙar da akai a waje tarbar sa sosai ya shiga mamaki saboda shi be sanar wa kowa zai zo garin ba tuni security suka shiga tare hanyar shiga cikin sauri ya shiga mota driver da Hajiya ta turomai ya ja shi yana fita sosai mutane suka rufe shi hannu ya ɗin ga ɗaga musu ganin irin soyayyar da suka nuna mai


ya ciro kudi wanda shima besan a dadin su ba ya ɗin ga watsa musu har ya samu hanya jilibal j.r.a ya nufa da shi unguwar wance da wane duk wanda kagan shi a unguwar to yaci ya tada kai anan zone 1 nan faɗar shugaban ƙasa take shi kuma yana zone 2 a gaskiya iya tsaruwa limon ta tsaru yawa a ƙasar waje kake jami'an tsaron sai yawo suke da bindigu tsayar da su Ku kai katin shi ya ɗauko na shedar shi ɗan cikin gun ne yasa suka barshi ya shiga amma ko tsutsune ba su yarda da motsin shi ba sai sun harbe shi da yake ba sabo kullum da irin wa'yanda za'a kawo




gaban wani tamƙameman gida suka tsaya sojojin dake tsaron gidan suka buɗe mai suna sara mai da yake mahaifin shi babban soja ne lokacin mulkin soja ya ruƙe kasar na shekara bakwai bayan ya sauka farar hula ta ƙarɓi mulki tun da lokacin soja be ƙara ƙar ɓa ba har kawo i yau gidan girma gare shi ga an ƙawata shi




Kai kace wata ɗaulal ƙasar larabawa kake parking space suka nufa yana dai dai ta tsayuwar motar sa ya fito a cikin nutsuwa yake tafiya har ya isa ɓangaran hajiya Turai tsayawa a kwatanta ƙyan gun ɓata baki ne sallama yayi




cikin fari'a yar shekara sittin taci doguwar riga ta tsadar diyyar atamfa tayi dauri irin maryam a bacha


hannayan ta tayi jan kunshi wata budurwa ce a kusa da ita ƴar kimanin shekaru goma sha tara taci fitted gown ta wani material baƙi an mai adon flower golding colour hannun ta ruƙe da tamfatsi tsiyar waya tana video a tiktok ganin sa yasa ta ƙasai cikin ƙissa tace


"Your welcome back my big brother,


ɗur ƙusawa yayi ya zauna a lallausan carpet cikin girmamawa da ƙaunar mahaifiyar sa yace


"Barka da dare hajiya da fatan na same ki lafiya ,


Tace


"Lafiya qalau alhmdllh da baka dawo ba na sami sauki kwana biyu na ci gishiri ne shi yasa hawan jina ya tashi ,


Allah ya ƙara sauki


"Ameen azzam baka ga yusrah ba ?"


Cikin nuna tsananin biyayya ga mahaifiyar sa yace


"daman bata koma ba?,


Eh ta dawo nan saboda zama ni kaɗe ba dadi ga kai kaƙi aure balle in Sami jikokin da zan ɗin ga gani suna ɗebe min kewa su ramlat suna nan zuwa suma


Shiru yayi domin beji dadi ganin Hajiya Turai tayi zance auran sa a gaban yusrah


Ga abincin ka a dining room ko sai kayi wanka ne


''eh ga magarib an kusan kirawo wa ,


Okay a fito lafiya


Ameen ya ce ya tashi ya nufi wata ƙofa inda ta nan ne zai isa shashin sa yana shiga bedroom ya nufa ya cire kayan sa ya shiga toilet wanka yayi ya fito ya shirya cikin jallabiya brown colour ya feshe jikin sa da tsadaddun turarurruka masu kyau da tsada tuni yake fidda ƙamshi me dadi counter din sa ya ɗauka ya fito a hankali yake motsa baƙin sa yana tasbiyi sai ka kula sosai sannan zaka gane baƙin sa na motsi central mosque ya nufa


masallacin fadar shugaban ƙasa da yake an kusa kiran sallah da yake ba jami'yar su bace ke mulki sun gaisa da abokan hamayya sun gaisa cikin mutunta juna


(Wani abun sai mu talakawa in mutum baya jam'iyyar da kake ka dau gaba da shi kenan har abada wani har jafa'i kake jamai mu dena yarda masu mulki suna gwara kanmu alhalin su nasu a haɗe yake siyasa daman ita mugun wasa ne)


Sai bayan sallar Isha'i ya dawo gida kai tsaye dining room ya nufa abinci ne sunfi kala goma ajere da sauri yusrah ta taso ta cire rigar dake jikin ta yan zu doguwar riga ce me roba duk ta bi jikin ta ga uban farce da tasa yawa me shirin shan jini tace


"Bara inyi zuba maka ,


Da sauri ya ɗaga mata hannu ya nuna mata hanya


Wasu kwallace ne suka toro a idon ta ga yahun bakin ta da ya ƙafe jiki a sanyaye ta juya tana juya ɗuwawu


taɓe baki yayi domin ko a jikin sa shi yana mamakin yan matan yaxu su dinga yiwa maza tallan kan su lemon kwakwa ya zuba ƙadan sai farfesun hanta wanda yaji albasa da kayan ƙamshi ya zuba kanda ya fara ci




bayan ya gama ya ɗauki tissue ya goge bakin sa ya nufi bedroom ɗin Hajiya Turai domin yi mata sallama akan daduma ya yatarar da ita tana addu'a zama yayi a ƙasa suka shafa tare yace


"Hajiya sai dai safe,


Cire hijab ɗin ta tayi tace


"Har ka gama ?"


Eh zan je in ƙwanta gobe zan je store ne saboda a ƙwai sababbin kayan da nayi order to sun zo tun waccan satin ina so in rabawa yan kasuwa ne be dace in roƙe Kaya ba bacin ana nema




Hakane Allah yayi albarka ka


Ameen baffa yace ki fito da kuɗi kimanin biliyan hudu


"To, kawe tace mai


Tashi yayi ya nufi shashin sa shirin kwanciya yayi kasan bacci yasan ya kashe lamp ya mai da dum light yayi addu'a ya kwanta ya ja blanket ɗin sa ɗaya wayar shi ya ɗauko ya buɗe tiktok ya nemo sunan ta duk wani video nata iya fusƙarta kawe take nunawa tsaki yayi yace


Allah ka rabamu da fitinar zamani ka mar a mafarki yaga yusrah ita da wani namiji suna kiss ɗin juna sosai hankalin sa ya tashi


Wannan kenan. 10:30 pm


Zabga ƙamahi take kai kace ɓarin turare tayi a kayanta abaya ce baƙa yar Turkiyya sai taunar chengum ta ke ba kwalliya a fuskar ta amma tayi kyau mayafin a bayar ta sashi a kanta kashin kanta ya sha gyara kowa sabgar gaban sa yake a gun masu shaye shaye nayi masu soyayyar shan minti nayi masu rawa nayi masu shan shisha hayaƙi ta ja ta fisar tace




"Wallahi Binta kina ban mamaki ya kamata ki amince da muƙatar Alhaji kin san kuɗi ba matsalal shi bace ,


Dena danna wayar ta tayi tayiwa ƙawarta ta banzan kallo tace


"Rufy bani da wata daraja da ƙima sai wannan mutuncin nawa ba zan rabawa kadangarun bariki ba insha'Allahu sai na kai shi gidan mijina yar da zai kalleni da mutunci sannin kanki ne kinsan mumsa kanmu a wahala duk wani mutumin arziki baya kallon yar tiktok a matsayin me mutunci wasu ma kallon mushurukai suke mana dan haka


Wallahi ƙar ki ƙara yimin wannan zanca balle ni da duniya ke kallo na karuwa ga shi wannan najadun tsohon ya ƙara zubar min da mutunci yau Wallahi su nusi sun shiga ukku we harni zasu yiwa kahu video yana Bara sun sa yace ni yar sa ce bana bashi komai shi yasa yake bara shi yasa yau ko Kabo na ban bayar ba sun bashi kuɗi dan su cimin mutunci,






Gaskiya basu kyauta ba


Hango su tayi da sauri ta tashi ta nufi tabirin giya ta fasa ɗaya ta nufi kansu tuni komai ya tsaya aka kashe kiɗan saboda ƙar fasa ƙwalba da a kaji wayan da suka dade basu zo club ɗin ba yau sun zo domin sun san a kwai drama tun har neman magana yasa su nusi suka taɓo yar gaban goshin gwamna.........


*




Bourn page




Cikin sauri rufy ta kamo ta cikin Muryar wanda ta sha tayi manƙas tace




"Haba sister wannan ba girman ki bane kina da yara kisa suci uban su me akai akayi su nusi ko followers 1k basu da shi sun taɓo kine dan ki kula su suyi suna ,


A jiyar zuciya ta sauke ta yar da ƙwalbar a ƙasa ta ɗauki jaƙar ta rataya ta dubi nusi tace




"Za mu haɗu ko ba a nan ba kin san bana barin bashi ƙaramar arniya ki bari sai kin kai sannan sai ki taɓo ni ƙanne mata ido ɗaya tayi ƙas da hannu,


Wani irin ihu gun ya ɗauka suka ci gaba da rawar su


Ita kuwa fita tayi ranta a ɓaci jin horn tayi da sauri ta juyo


Wani matashi ne ya ci asƙin nan na yan isa ya leƙo da kansa yace


"Hey Beb how you doing ?,




Cikin ɓacin rai ta buɗe gidan gaba ta shi ga ta saki a jiyar zuciya ta biyu tace


Jazzz kai ni gida raina a ɓace yake




Wata ƙwalba ya ɗauko yace


Kullum ina faɗa miki in kina shan wannan ba ke ba ɓacin rai


Cikin I don't care manner tace


"Jazzzzzzz Please ai sai ɗauƙar hakki yayi yawa ƙarshe in shaye shaye yayi min yawa in hauka ce ko ? to ba haka nake ba nasan mutuncin kai na ,


Murmushi yayi yasa


waƙar simi me taken love don't care ya saki ya fara tafiya a hankali yana bin waƙar juyowa yayi yace


Okay Alhaji datti yace min
yau 12:00 ki same shi a government house


Ɗa gowa tayi tace


"I don't have any time,


Da katawa yayi da bin waƙar yace


"Why not?,


Banyi niya ba kasan we yana so in ƙarɓi ƙwangilal ɓata wannan pro 'azzam Bilal mu'azzam kura


Kina tsoron sa ne


Dariya tayi tace


"Ko ɗaya sai de ina tsoron Allah kasan fa sharri zan mai ,


Dariya yayi har da ruƙe ciki sai da ya gama sannan yace


"Beb tsoron Allah fa kika ce ai Wallahi da gani har ke ba batun tsoron Allah a rayuwar mu kin san kafin izo nan daga ina nake hmm Allah ya kyauta na birni ya cuci na ƙauye ,


ai kasan duk iskancin mutum akwai wan da ya fi shi wata ƙila kai kafi ni


Hmmmm kee uhmm ai Wallahi ko bokan daji haka ya ganki ya ƙƴale


Wani kallo ta yi mai tace




Uhmm haka kake gani ni Yanzu so nake in zub da makaman yaƙi na gaji Wallahi




"Ya kamata in karatu ne in roƙe kalaman ki sau nawa kike faɗar haka,




Rufe sexy eyes ɗinta tayi tace


"A kwana kin nan Wallahi ina yawan yan mafarkai ko da na tashi bana gane komai ina tsoron wani abu ya faru fa bana ganina a wannan duniya a wata daban nake gani na fa ga wani mutum bana iya ganin fusƙar sa sai de bayan sa ,




"Hhhhhhhhh ko suruki na ne?,


Hmmmm ka dena daukan magana ta wasa jazz


"To Allah ya kawo mafita,


"Ameen,




zo muyi video yau in rikita fans ɗina kin san wasu cewa suke we bakƴa video da namiji


Hmmmm kawe ta ce


Iphone 15 ya ɗauko ya shiga tiktok yace


Hey fans gani ga Princess bintu


Murmushi tayi tace


Hey fans yau gani ga jazzzzzzz nan yasa musu waƙar salim smart me taken labarina baya zama nawa inhar bake tariyi na sukai bi waƙar dai dai gidan su ya tsaya yace


''beb gobe in dawo ?'


Ba zan fita gobe ba


Okay bye


Bye fito wa tayi tsaki ta ja ganin yan zaman sha isaka da yake zafi ake suna zaune suna hira da munafurci canza taku tayi tafiyar ta tayi sai ƙas ƙas taƙalmin ta keyi


Wani daga ciki ne yace




Allah ka shirya mana zuri'a




Juyowa tayi ta ɗage glass ɗin ta sama tace


"Amin dan karuwa uban ka yasa kwabashu me huta ,


Tuni sauran sukai shiru domin sun san tsaf zata zage su


shiga soron gidan su ta shi ga ta ƙunna fitilar wayar ta da yake ba huta da sauri ta tsaya ganin meragaje da saurayinta ɗantala suna manne da juna cikin ƙunar rai tace


Dan uwar ka a she baka da hankali tunda har ka iya zuwa gidan mu kana nema ka lallata meragaje rayuwa


Jikinsa rawa ya fara yace


Dan girman Allah ki haƙuri


Uhmmm ke kuma shiga gida ko inyi kasa kasa dake kai kuma zamu haɗu a way zanyi maganin ka


Ki yi hakuri


Baza tayi mai


Meragaje ta shiga gida da gudo tana kuka


Cikin sauri uwani ta fito tace


Meragaje lafiya kike kuka


Koroni tayi muna tare da ɗantala we zai lallatani


Kan uban can ita daga ina take ke gwara kina gida ita fa


"Daga gidan uban ki ,


Hantar cikin uwani ce ta kaɗa batayi zatan zata jiba ta zata ta tsaya suyi tujara da ta saba ashe ta shigo


cikin sauri ta kama hannun Meragaje suka shiga ɗaki




Kama ƙugu tayi jin alamar ringing a jaƙar ta da sauri ta ɗauka ganin sunan yasa ta ja ƙaramin tsaki ta ɗaga tayi shiru


"Haba Binta kin sa fa dake muka do gara na tabbata in ki kayi wannan aikin Wallahi za mu sami kujera kin san fa ni zan fito ta karar gwamna nayi miki alkawarin biliyan shidda har da mota wacce ba kowa ke hawan ta ba,


Shiru tayi ta shiga tunani anya kuwa za ta bar kuɗin nan tana da buƙatar nemo mahaifin ta saboda rashin kuɗi


bata sami zuwa Saudiyya ba domin mamanta har address ɗin sa ta bata kawar da wannan tunanin tayi tace


Amma Alhaji datti baka ganin duniya zata zage ni sannan taya zan kulla mai sharri har a yarda


Wata irin shu'umar dariya yayi yace




Wannan ba matsala bane domin kinsan na iya kulla sharri da maƙirci zamu kulla mai gadar zare kuma keee zaki je zan baki karamar camera ki sa a jikin ki tunda Allah yayi miki halitta da zaki ɗauki hankalin duk wani ɗana miji in de me lafiya ne




Samin gu tayi ta zauna tace




"Alhaji tsiraici na zaku nuna wa duniya akan mulki tab Wallahi da na san Wannan banzar maganar zaku zomin da ita Wallahi da tuni na daɗe da dena harka da ku kai hmmmm,


Kin daka ta kiji mana ko fusƙarki ba wanda za a nuna sannan kuma za'a rufe jikin ki kawe hugging ɗin sa zaki yi kin fahimta sannan sai kinyi taka tsantsan muna sakin video nan zaki dawo gidan gwamnati da zama




Okay na yar da




Yauwa ko ke fa kashe wayar tayi ruwa ta ɗiba ta zuba a buta ta nufi bayi bayan ta fito ta tora ƙofar ɗakin ta da sauri ta kunna fitilar wayar ta wa zata gani cikin baƙin ciki tace




"Kut melesi jajar uban can Wallahi yau kowa ba zai bacci ba jajar uban can lalle ,


Iya da take sharar bacci bata san wacce wainar Binta ke toyawa ba


A fusace ta fito ta fara dukan ƙofar ɗakin kahu labahani


Cikin magagin bacci yace


Wane mara neman albarka ne yake tashi na tun asuba da na fita nema ban dawo ba sai hudu


Wata da bara ce ta haɗo mata ta maƙe murya tace


"Fatalwa ce ,


Cikin ɗaki kuwa tuni wani irin tashin hankali ya ruske shi Oni labahani a haka mutuwa ta zo ban cika burina ko ɗaya ba a duniya ashe a fili yake




Gyara tsayuwa tayi tace




"Ai kuwa yau zaka baƙunci lahira domin mun gani ana ta'asa a gidan ,




Dan girman Allah fatalwa kiyi min rai Wallahi ban sani ba cikin yar da bara ya sa ƙafa ya doka a wa uwani domin Wallahi ba zai fuskanci tashin hankalil nan shi ka ɗe ba yace


"Uwani tashi daman ance in da rai zaka sha kallo yau ga fatalwar gimbiya nan ta dawo kan mu,


Aikuwa cikin masifa ta ɗauko tasar da taci abinci ɗazu ta buga mai tace




"Zan fasa maka kai kafin ni ka fasamin fatsarmama in ban da ka mai dani mara hankali fatalwar gimbiya ce za tazo gidan nan?"




*Ya ku yan adam har kuna da lokacin yin faɗa alhalin yau zaku mutu*




Innalilahi dan girman Allah ai bansan gaskiya yake faɗa ba kaimin rai Wallahi bacci nake ya ta sheni


Ai kuwa yau zaku yi kwanan barzahu


Tuni uwani ta saki gudawa a zaune yayin da numfashin labahani da ƙƴar yake fita saboda ta shin hankalin da yake ciki ko mutsi ba yaso yayi ƙoƙari yake ya tuno addu'a amma ina ya kasa sai mun jaye nu'ara kulya li'ilafi yake mai mai tawa tun yanayi ahankali har ya dawo da ƙarfi.........…..✍🏼




*BINTA YAR JA GALIYA*








free page






Dariya ce ta kusan kuɓucce mata ta danne tace


"zan baku zaɓi ku zaɓa in kuna so in barku da ranku sai kun hana saurayin meragaje zuwa gidan nan in da gaske yake ya fito ya aure ta


ko in hana ku ba haya na tsawan shekara ɗari ko in saƙar maka gudawa ta tsawan shekara tamanin ,






zaro ido yayi tuni wata gudawa ta kuɓucce mai ji kake tsuuuuuu yawa an saki fanfo taɓa ƙasan shi yayi ga wani irin wari da ya game ɗakin a zuciyar shi yace




"anxu gun har an fara saƙar min tawa yasan wataran ba gudawa zaiyi ba sai de ya kashayar da ƴa'yan hanjin sa ,






duban uwani yake amma a baɗini wasu taurari yake gani sun za gaye shi yau yasan ƙar shan sa ya zo shekara ɗari ba kashi ko ƙwana ɗaya mutum beba yake ji balle mutum yayi shekara ɗari


futsari ne ya biyo baya jin har da gudawa yo rana daya mutum yayi gudawa yake fita hayyacin sa balle shekara tamanin ai kawe mutuwar tsaye zaiyi da kƴar ya iya buɗe baki yace






Innalillahi fatalwar gimbiya ku yimin min rai dan allah wallahi ba laifina bane laifin uwani ne na matsani yaron nan ita ta dage sai ya zo gun mairo


Zuface ta ƙaryowa uwani tace


Wallahi sharri yake mun kullum sai ya bashi kuɗi ko mero




MERO da ta fita hayyacin ta tayi dana sanin shigowar ta ɗakin nan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login