Showing 18001 words to 21000 words out of 23305 words

Chapter 7 - KARYA DA GASKIYA ORG.txt littafin Yaki writing by Mansur Usman Sufi

wani na cewa sarki Lamsarul-Azlam ya buƙaci a sake tura nashi ƙarin dakarun yaƙi, kaga kenan babu tabbacin ga lokacin da zai dawo tun da bai yi nasara ba. Kuma zamu dami damar yin GABA DA GABA da duk wata barazana, domin matuƙar yawan fursunonin dake kurkukun nan ya isa ya sanya mu cimma nasara, domin masu iya magana na cewa SARKIN YAWA yafi SARKIN KARFI, kuma tabbas hannu da yawa maganin ƙazamar miya ne";
Koda jin wannan batu daga bakin bawa Amral sai gaba ɗaya fursunonin dake wajen suka zurfafa izuwa kogin tunani domin samun mafita.
Tsawon daƙiƙa ɗari ana cikin wannan hali sai daga bisani wani daga cikin su ya yi gyaran murya ya ce "gaskiya ni shawara ta ina ganin mu tsaya a batun samun 'yancinmu mu ajiye batun JUYIN SARAUTA domin sanin kanku ne cewa karo da sarki Lamsarul-Azlam tamkar tunkarar ANNOBA DARI ne".
Da jin wannan batu sai sadauki Ukaiza ya yi caraf! Ya tari numfashin shi ya ce "ba za mu taɓa janye juyin mulki ba domin koda ba mu yunƙurin hakan ba. Ƙarshe dai mutuwa ce makomar mu. Shin yanzu ina amfanin baɗi babu rai, ka sani cewa har abada matsoraci ba ya zama gwani.
Koda jin wannan batu daga bakin Ukaiza sai kowa ya yi na'am da batun.
Ukaiza ya ci gaba da cewa "muhimman abubuwan da zamu yi sune. Samun haɗin kan dukkan fursunonin dake cikin kurkukun nan cikin sirri ba tare wani bare ya sani ba.
Na biyu kuwa muna buƙatar haƙa rami da ya kai tsawon kamu ɗari, sannan mu cika shi da itace, za mu yi wannan aiki ne a tsakiyar dare lokacin da dakarun ke sharar barci.
A cikin daren zamu tattare a waje guda tun daga mata yara da tsofaffi nesa kaɗan da inda ramin yaje. Wasu a cikin mu sai su kaure da faɗa da hayaniya ta yadda dakaru su zasu kawo ɗauki, wajen kawo agajin za su afka cikin wannan rami, sai mu jefa wuta izuwa cikin rami dakarun su ƙone ƙurmus ba tare da an zubar da jinin kowa ba. Hatta sauran dakarun da za su farmake mu za mu jefa su cikin ramin.
Hikimar yin hakan shine babu wasu dakaru da za su kawo ɗauki domin sai an samu ƙarar takubba za a yi zaton akwai abun ya faru.
Lokacin da alfijir zai keto za mu tunkari masarauta zamu yi amfani da dawakai da makaman yaƙin dakarun kurkuku ne.
Amma ya zama wajibi mu sanya yara da mata a tsakiya a lokacin da muke tunkarar abokan gaba.
Ya ku yana 'yan uwana fursunoni kuyi sani cewa matsawar ba ku sauka daga kan wannan tsari da na kawo ba haƙiƙa babu abin da zai tsare mu daga kawo KARSHEN ZALUNCI a wannan masarauta da nahiyar mu baki ɗaya;
Sa'adda Sadauki Ukaiza yazo nan a jawabin shi sai kowa ya cika da matuƙar farin ciki maral-musaltuwa, cikin hanzari kowa ya watse domin yaɗa shirin bazato ga sauran fursunoni.




Al'amarin shugaban 'yan fashin duniya Sadauki Fitinatul-amir da yan majalisar shi, sa'adda suka luluƙa cikin gajimare suna tsala gudu akan wannan mikiya, bayan sun kammala fafata artabu da su jaruma Rusayyat.
Tafiyar rabin sa'a kacal suka yi suka iso gida. Lokacin da suka sauka sai Fitinatul-amir ya huce kai tsaye izuwa fadarshi. Har A wannan lokacin fadar cike take maƙil da jama'a, bayan ya haye bisa karagar mulki sai ya yi umarni ga MAGAYAKI ya tara dukkan dakarun yaƙi.
A wannan lokaci duk wanda ya ɗaga idanunshi ya kalli Fitinatul-amir sai kaga ya sunkuyar da kanshi bisa ganin yadda yake tsananin fushi.
Al'amarin Hairat 'yar uwar yaro Usaiba mai hatimin takobi kuwa, tun sa'adda Fitinatul-amir ya fita farautar yaro Usaiba da uwar gidansu Rusayyat. Sai ta kasance a hannun waɗansu kuyangi na musamman ba su bari ta fita koda waje. Duk da cewar Hairat ba ta san abin da ya wakana da yayanta da ummunsu ba amma ta ji hankalinta a tashe yake.


***
Kamar yadda sadauki Ukaiza ya tsara haka al'amarin yakasance a cikin kurkukun, bayan an sanar da dukkan bayi abubuwan da aka tsara, wato an kammala ginin wannan ƙaton rami mai ɗauej itace, a daren kwana na biyu sai dukkan jama'a maza da mata suka taru a waje guda, kawai sai samari majiya ƙarfi suka kaure da artabu tsakanin su ta hanyar kaiwa juna naushi da bugu nan take waje ya kaure da ifice-ifice.
Koda jin hakan sai dakarun su ka ɗimauce suka, domin a tunanin su FARMAKIN BAZATO aka kawo masu.
Kash! Haƙiƙa rashin sani yafi dare duhu, da yake a wannan lokaci gaba ɗaya fitilun kurkukun a kashe suke sai dakarun suka dinga afkawa izuwa cikin wannan rami suna masu tsandara ihu, kuma wani abin mamaki da al'ajabi shine da zarar sauran dakarun sun daina jiyo motsin 'yan uwansu sai su kunno kai wajen, lokacin da su Ukaiza suka tabbatar cewa dukkan dakarun sun afka izuwa cikin ramin sai nan take zaratan samarin suka kunna fitilun ice gami da jefa izuwa cikin wannan rami, nan take wuta ta kama jikkunan dakarun suna ihu da kururuwar neman taimako wasu lokutan sai dai ka ji randan cikin su tana bindiga suna fashewa.
Koda kammala samun wannan nasara sai aka shiga aikin mayar da ƙasar da aka tono cikin matuƙar farin ciki suna masu kiɗe-kiɗe da raye-raye.
Daga nan sai aka shiga fir-fito da fursunonin dake kunne a ɗakunan duhu, aka ɗebi makaman yaƙi aka buɗe ƙofar kurkukun aka kunna kai izuwa gari kamar yadda aka tsara.
Tun kafin a iso izuwa fada aka fara gwabza artabu da dakaru, nan fa ƙarar karafniyar ƙarafa da ihun mazaje ya cika dodon kunne, jama'a suka kaure da guje-guje gami da ifice-ifice.
Kasancewar masu iya magana na cewa SARKIN YAWA yafi SARKIN KARFI sai ya zamana cewa an murƙushe dakarun ta hanyar saukar masu da azabar KAIFIN TAKOBI.
Sa'adda al'ummar birnin suka hango cewa fursunoni ke yin YAƘIN YANCIN BAYI sai suka dinga ɗebo makaman su suna yin shirin yaƙi suna shiga cikin ayarin, domin suma sun gaji da zama a KANGIN BAUTA na sarki Lamsarul-Azlam, wasu kuma farin ciki ne ya cika zukatansu bisa saduwa da masoya da 'yan uwansu da suka shafe tsawon shekaru a kurkuku suna cikin azabar sarki Lamsarul-Azlam.
Kafin shuɗewar daƙiƙa ashirin birnin ya cika da mayaƙa babu masaka tsinke,
Nan fa birnin ya ƙara yamutsewa da azababban yaƙi mai matuƙar muni da daban tsoro, a wasu lokutan sai kaga badakare ya cika wandonshi da iska, amma sai kaga jama'a sun yi tara-tara sun rafke shi ya faɗi ƙasa matacce ko shurawa bai yi ba.
Nan fa JINI DA KASA suka cakuɗu waje guda, sassan jikkunan bil'adama suka dinga shawagi a sama suna zubowa ƙasa, ƙura ta turnuƙe sararin samaniya saboda yadda kofatun dawakai ke kartar ƙasa suna turmutsutsu.
Kaico! Haƙiƙa yaƙi abin tsoro ne da tashin hankali ga dukkan wata halitta a doran ƙasa, domin wata musiba bata kai yaƙi ba, shi ne ke haifar da rasa rayuka, dukiya, mutunci da daraja kuma mayar da yara marayu mata ta zamo bazawara, yaƙi maishar da 'yan maza mataye kuma ya haddasa yunwa, fari da cutuka.
Wannan shi ne abin da ya wakana a ƙasar Darul-Ashmar a lokacin da fursunonin kurkuku suka yi yunƙurin JUYIN MULKI a lokacin da sarki da sarki Lamsarul-Azlam ya kai FARMAKI birnin Madinatul-Afnan.


Sa'adda boka kaddad ya rikiɗa izuwa mucijiya mai kawuna arba'in ya kanannaɗe jarumi Muhassin domin ta kafta mashi sara da kawunan arba'in, a bisa saman tekun Baharul-saljir.
Kwatsam! Bazato babu tsammani sai gimbiya Aslaima ta dako wawan tsalle tamkar an harbo ta daga cikin baka ta sauka akan mucijiyar ta ƙwala kabbara da ƙarfi gami da dunƙule hannayenta biyu ta gabzawa wuyan mucijiyar ɗaya wawan naushi ji kake ruƙus! Ƙas kan ya kare. Kafin cikar daƙiƙa ashirin Aslaima ta ƙarya kawuna ashirin na mucijiyar.
Wohoho haƙiƙa JARUMTAKA baiwa ce daga Ubangiji, babu abin da zai burge mutum face idan ya ga yadda Aslaima ke ƙarya wuyan mucijiyar tamkar tana ƙarya siraran busassun ƙirare. Wani abun al'ajabi ma shine yadda Aslaima ke iya zillewa hare-haren mucijiyar.
Sa'adda mucijiyar ta ji TSANANI DA UKUBA sun tsananta gare ta sai ta saki jarumi Muhassin ya faɗo ƙasa ba tare da ya nutse cikin tekun ba yana mai fitar da numfashi sama-sama,
Duk wannnan abu da yake wakana aljani Ramsisul-Ayyam yana tsaye a gefe inda gawar wannan kada yake yana kallo sai ya cika da matuƙar mamaki bisa ganin irin bajintar da Aslaima ke yi ya ce a cikin ran shi "haƙiƙa Ubangijin jarumi Muhassin buwayi ne gagara misali domin ga shi ya bawa Aslaima JARUMTAKA wacce ba ta daɗe da yin imani da shi ba, amma ya aka yi gimbiya ta kasance jaruma bayan cewa a wannan tafiya koda sauro bata iya kashe wa, amma tana iya yiwu wa saboda makauniya ce ya sanya bajintar ta bata bayyana ba. Amsar tambayoyin da Ramsisul-Ayyam ya kasa bawa kansa kenan kawai ya yi shiru yana mai zuba idanu.
Koda gimbiya ta samu nasara sare kawunan mucijiyar baki ɗaya sai ta sake dako wawan tsalle cikin gwaninta tana mai taka tekun da ƙafafuwanta tamkar tana tsaye a turba.
Take mucijiyar ta rikiɗa izuwa boka kaddad an yi mashi yankan rago jininshi ya kwaranya a kan tekun, fuskarshi ta yi baƙi wuluk! Idanuwanshi da harshen sun zazzago, kaico! Tir da mutuwar fasiƙi maƙiyin Allah da Manzonshi, inda ace yana tsaye a wannan waje zai ga yadda boka kaddad ya yi mutuwar wulakanci, dole ne ya ji tsoron Ubangiji ya kama shi, domin babu wani abun halitta da ya gagare shi hukunci.
Cikin matuƙar farin ciki Muhassin ya sakarwa Aslaima wani kyakkyawan murmushi, take ta mayar mashi da martani cikin annuri, sannan ya juya ya dubi Ramsisul-Ayyam ta ce "ya kai wannan aljani shin za ka bayar da gaskiya da ubangijin halitta ko kuwa ka zaɓi ka yi mutuwar hasara tamkar yadda mai gidanka ya yi";
Koda jin wannan batu daga bakin Muhassin sai Ramsisul-Ayyam ya ce cikin ladabi "ya shugabana ai tuni na imani da ubangijinka tsoron ubangidana ne ya hana ni bayyana wa, yanzu a shirye nake na shiga addinin ka".
Koda jin hakan nan take Muhassin ya karanta KALMAR SHAHADA Ramsisul-Ayyam ya maimaita.
Faruwar hakan ke da wuya nan take duk wani gashi dake jikinshi da ya sanya mashi muni ya ɓace ɓat! Kuma ya ji wani ƙarfi da nutsuwar zuciya ta musamman ta same shi.
Muhassin ya ci-gaba da cewa "ya kai wannan aljani ka yi sani cewa sunan da ake kiran ka da shi baya da wata ma'ana a Musulunci yanzu zan canja maka shi izuwa ABU-AYUB, sannan yanzu sai ka ɗauke mu daga nan izuwa birnin su gimbiya Aslaima";
Abu-Ayub ya risina ya ce "an gama ya shugabana, amma a shawara ta a ciro ALLON TSAFI daga cikin wannan kada domin kar wani ya mallake shi ya cutar al'umma".
Muhassin ya ce "kwarai kuwa haƙiƙa ka kawo shawara mai kyau, nan take ya karanta Ayatul-kursiyyu da falaƙi da nasi ya tofawa kadan, nan take ya kama da wuta ya ƙone ƙurmus!
Kawai sai Abu-Ayub ya shimfiɗe gadon bayanshi jarumi Muhassin da gimbiya Aslaima suka hau bisa kan shi suna yin bisimilla, sannan ya yunƙura yana tashi zuwa sama ya na mai kaɗa fuka-fukanshi ya ɓace ɓat! Cikin gajimare.
Sa'adda aljani Abu-Ayub ya wanzu yana keta gajimare cikin matuƙar sauri tamkar giftawar tauraruwa mai wutsiya, sai aka tsawon sa'a ɗaya ana tafiya babu sassauci.
Ana cikin wannan hali ne gimbiya Aslaima ta buɗi baki sannan ta yi gyaran murya ta ce "ya masoyina abin alfaharina ka yi sani cewa a halin yanzu ƙaunar da nake yi maka ba zan iya misalta taba, ina jin zan iya rasa rayuwata idan babu kai, ka zamto tamkar gudan jini dake kewaya wa a zuciyata, soyayyar ka ta zamto tamkar bugun numfashi na, ina godiya ga Ubangiji da ya bani abin ƙauna ma'abocin kwarjini, SADAUKANTAKA da DAUKAKA DA BAIWA".
koda jin waɗannnan daɗaɗan kalamai daga bakin Aslaima sai 'yar ƙaramar dariya ta suɓucewa Muhassin har kunci shi suka loma fararen haƙoranshi suka bayyana cikin tattausar murya ya ce "ya abar bege na a dare da rana ki yi sani cewa ni ina sonki ne tsawan rayuwa, dukkan wani abu da ya shafi rayuwar mu addini ya tsara mana shi, Ubangiji ya umarce mu mu ƙaunaci ababan ƙaunar mu da Allah, domin idan saboda da kyawu, kuɗi ko mulki ne wata rana za su gushe;
Inda ace kin taɓa karanta hikayar littafin JARUMAN DUNIYA za ki ji yadda yarima Muzaifar da ya kamu da soyyyar almajira Sharilat yar tsoho Kuhairu da za ki tabbatar da cewa soyyya ta gaskiya babu ruwan ta da dukiya, mulki ko nasaba";
Da jin wannan batu sai gimbiya Aslaima ta gyaɗa kai cikin annurin fuska ta ce "haƙiƙa wannan bayani ya sanya na ƙara ƙaunar Ubangiji domin bai bar wani abu mai muhimmanci na rayuwar mu ba face ya tsara mana yadda za mu yi, kuma bayan an ɗaura mana aure sai na karanta littafin JARUMAN DUNIYA domin jin irin darussan dake cikin shi.
Koda gimbiya ta zo nan a zancen ta sai su duka biyun suka bushe da dariyar farin.
Daga bisani jarumi Muhassin ya dubi Abu-Ayub ya ce "akwai buƙatar mu yada zango anan domin mu yi sallah mu samu abun kalaci tun da guzurin mu ya ƙare"
Koda jin wannan umarni sai Aljani Abu-Ayub ya risina cikin ladabi ya ce "an gama ya shugabana;
Yana gama faɗin hakan ya saki fuka-fukanshi ya yi ƙasa luuuh! Ya sauka a turba.
Inda aka sauka ya kasance daji mai ɗauke da bishiyoyu, duwatsu tsilli-tsilli gami ƙoramu, kuma dajin ya yi tsit tamkar babu wata halitta mai numfashi a cikin shi.
Al'amarin da ya bawa kowa mamaki kenan. Cikin hanzari Muhassin ya yunƙura ya sakko daga kan aljani Abu-Ayub gimbiya Aslaima tayi koyi da shi, suka durfafi wata ƙorama Abu-Ayub na biye da su, ya yin da suka isa sai suka tsafta ce jinin dake jikin tufafin su suka suka ɗaura alwala, sannan Muhassin ya shige gaba ya tayar da iƙama ya tayar da sallah.
Bayan an kammala ne Muhassin ya yi gyaran murya dubi abokan tafiyar shi ya ce "ya ku abokan tafiyata ina ganin bai kamata mu yada zango anan ba akwai buƙatar mu ƙara yar tafiya kaɗan.
Koda gama faɗin hakan sai Muhassin ya miƙe tsaye ya shige gaba gimbiya Aslaima da aljani Abu-Ayub suka mara mashi baya a ka ci gaba da tafiya.
Ana cikin wannan tafiya ne aka hango wani gida guda jal da aka yi ginin shi da zallar duwatsun wuta masu ƙwarin gaske a wannan lokaci ƙofar gidan a buɗe take alamun dake nuna akwai halitta a ciki,
Sa'adda aka yi arba da gidan sai kowa ya cika da matuƙar mamaki, Abu-Ayub ya dubi Muhassin ya yi gyaran murya cikin ladabi ya ce "ya shugabana shin zamu shiga cikin wannan gida ne domin mu ga abin da ke ciki ko kuwa zamu ƙetare?
Koda jin wannan tambaya sai Muhassin ya yi shiru yana mai zurfafa cikin kogin tunani daga basani ya dube shi ya ce "akwai buƙatar mu duba ɗin sai dai ina so kar ku shagala da addu'a domin kariya daga dukkan abin cutarwa;
Da jin wannan batu sai dukkannin su suka gyaɗa kai alamar gamsuwa. sannan aka durfafi gidan aka shiga izuwa cikin shi, sai da aka yi tafiya mai tsawo a cikin zaure sannan aka iso farfajiya, daga ciki gidan ya kasance ƙasaitacce mai matuƙar ƙawatuwa yana ɗauke da ɗakuna biyar.
Nan fa aka dinga shiga ɗakunan amma wayam! Babu komai, lokacin da aka shiga ɗaki na biyar ne aka ga wani abun mamaki.
Bakomai aka gani ba face kayan tsubbe-tsubbe nau'i dabam-daban, babu kyawun gani a tsakiyar ɗakin an ajiye wani dogon teburi na azurfa, bisa kan teburin wani kyakkyawan yaro ne mai kimanin shekaru sha uku an ɗaure hannayen shi da waɗansu irin sarƙoƙin tsafi, hawaye na zuba daga idanuwanshi.
Koda ganin halin da yaron ke ciki sai kowa dake wajen ya kamu da matuƙar tausayin shi, kawai sai Muhassin ya matsa daf da yaron ya karanta Ayatul-kursiyyu da falaƙi da nasi ya tofa a jikin sarƙoƙin take suka narke suka zamo ruwa suka ɗige a ƙasa.
Cikin farin ciki yaron ya yunƙura ya sakko daga kan teburin,
Har Muhassin ya buɗe baki da nufin ya ce wani abu, kawai sai aka ga wani dubu ya mamaye ɗakin ta yadda ko tafin sannu mutum ba zai iya gani ba.
Sannu a hankali duhun ya dinga curewa waje guda ya rikiɗa izuwa wata mummunan tsohuwar aljana,
Tana shirye gagarumar shigar yaƙi mai matuƙar kwarjini da ban tsoro, a hannayenta tana ɗauke da zaratan takubba masu KAIFI DA TSINI fuskantarta a murtuke babu annuri tamkar an aiko mata da WASIKAR MUTUWA.
Duk da dakewar zuciyar su jarumi Muhassin sai da suka ji hantar cikinsu ta kaɗa,
Aljanar ta taƙarƙare ta daka masu wata tsawa da ta haddasa raurawar ɗakin, daga bisani ta haɗe ta buɗi baki cikin kakkausar murya mai kama da haniniyar doki ta ce "ya ku waɗannan bil'adama ku yi sani cewa haƙiƙa tafka babban kuskure da kuka shiga gona ta, ina mai tabbatar maku da cewa ɗayan ku ba zai fice daga wannan gida a raye ba";
Kafin aljanar ta gama rufe bakinta Muhassin ya yi ƙarfin hali ya tari numfashinta yana mai cewa "ƙaryar ki ta sha ƙarya yake wannan la'ananniya kuma tsohon AZZALUMA ba za ki taɓa samun nasara akan mu ba da yardar Annabi Rahma, zaɓi biyu zan ba ki ki ɗauki ɗaya, ko dai ki miƙa wuya zuwa ga addinin Allah ki daina shirka da tsafi ki dawo bisa TAFARKIN TSIRA, ko kuma ki yi mutuwar wulakanci".
Koda jin wannan batu daga bakin Muhassin sai aljanar ta fusata ainun ta sake daka masu tsawa a karo na biyu ta ce "na rantse da gemun kakana boka Zanzamul-Auƙat sai na yi maku kisa mafi muni ta hanyar gididdiba naman jikkunanku

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login