Showing 69001 words to 72000 words out of 163596 words
 a matukar fusace yana duban sudais "kai kuma k'aramin D'an iska bawan mata ai kagama had'in husumar data kawoka ko ,sai ka kama gabanka tun ban had'uku tare ba ,"kodayake  da alamun kmr kana sonta ne ko ?
"bawani yana sona ,kai dai gidan ne bakason zama sai kuma  ka zauna gida ko kaki kokaso you will stay at home. 
Cike da rawar jiki da murya sudais yace " wata irin mgn ce hk fu'ad?" wallahi ba abinda kake expecting bane karka manta da .....
Fuad Yayi saurin katseshi da cewar  "no  karka damu kai dai  kajira na saketa sai ka aurenta..
Momy tayi saurin had'e hannuwa guri "Dan girman kabar zance sakin nan , wani irin mgn kake gayawa abokinka  da babu dadin ji..?
" momy bakiji duk maganganunsa ba ,saboda shi soko ne a gidansa  juyasa akeyi tunda sonta yake ni kuma zan saketa so that shi sai ya aureta ..
"Oooooooo let me tell you  another good news fu'ad..ko ka sakeni bazan ta'ba sakuwa ba ,matsawar  akan wannan matsalar wallahi bazan sakuba you are my husband for life bazan saku ba mutu kara ba.... 
"Ke da wa kike wannan mgnr ?
 "ke ai ba matar mutu karaba bace saboda ke ba  matar arziki ce...
"Kina ji kina gani zan sakeki kuma nayi aurena , kuma idan kin zauna kula da nasreen uwarki da ubanki zina sukayi suka haifeki, ai  idan na sakeki  dole kowa yakama gabansa  ,ki sa ido kiyi kallo this time around I will surprise you yakarasa mgnr yana kokarin juyawa ..
Mmn sudais ce💗💗💗💗💗💗
       'YAN CINKI
      💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
             ~NA~
 *AYSHA  A BAGUDO*
~DEDICATED TO~
      MRS ADAM
( YAR MUTAN KAGARA)
page 69 to 70
........sudais ne yayi saurin kamo hannunsa cikin kid'ima "dan girman  Allah fu'ad kayi hakuri ,karka yanke hukunci cikin fushi, ba'ason mutun yayi saki alhalin yana cikin fushi, idan sakinta zakayi kabari ka natsu, hankalinka ya dawo jikinka  amman ba acikin wannan halin da kake ciki ba.. ...
A matukar tsawace me'ad tace "meye haka ne sudais ..?
"kana hauka ne ko ka fara shaye shaye ne bansani ba,da har  na d'add,akoka cikin maganata? 
"wani irin maganar banza  ne yake fitowa daga cikin wannan banzar  bakin naka irin na marasa hankali da tunani kuma 'yan shaye shaye?"saki ko me ..ko me naji  kake maimaitawa ,?
" wayace maka sakina fu'ad zaiyi da kake wani shirmen hauka anan .? 
"wai naga kmr... "short up there  ......."kaga kmr me ai idan ma 'kwa'kwaluwarka na hasasho maka  saki tsakanina da fu'ad maza kayi saurin cirewa domin tsakanina dashi babu wannan kalmar har abada, mutu karaba  tare zamu qarasa rayuwarmu dashi har tsufa his my husband for life.... dan ko ya sakeni bazan ta'ba sakuwa ba, kuma babu inda zani, zama daram sai dai nida shi muyi zaman daduro ,amman wallahi bazan saku ba agurinsa zama daram agidansa no going anywhere.... Dan hk kazo ka wuce ka bar gidan yanzu bana bukatar sake ganin wannan fuskartaka fool kawai ....
a matukar harzuke fu'ad yace "dan ubanki idan na sakeki karki tafi ,ki zauna zaki ganewa idanunki kowaye Asalin fu'ad, zan sakeki.. sai dai idan na sakeki ki fad'i ki mutu amman sai kin d'and'ani radadin da zafin saki arayuwarki ,"kuma karkiyi tunani idan na sakeki zan dawo dake wallahi wallahi me'ad matsawar na furta na sakeki ,na barki kenan har abada sai dai idan mutuwa zakiyi kiyi shashar banza shashar wofi kawai da batason ciwon kanta ba ,"nayi danasani nayi danasani aurenki arayuwata, ban san haka zaki zamemin ba, wallahil azim da ban  aureki na gur'bata zur'iata ba, domin aurenki bashi da wani faida da amfani agurina facce tarin bakinciki da nadama," a gaban mahaifiyarki gaban abokina kike  bayyana sirrin da Allah ya  boye, tur da masu hali irin naki ...."Amman babu komai da sannu zaki gane kuranki Dan komai yazo karshe atsakaninmu... ya sake juyawa fuuuuuuuu... daidai lokacin da sudais  ya isa  bakin kofar barin parlour'n yana kokarin fecewa.... 
"fu'ad yayi taku daya biyu ya jiyo sautin muryar momy cikin kunnenshi wanda yasa take ya  tsaya cak agurin , zuciyarsa na wani irin harbawa da sauri sauri, tsayuwa yacigaba dayi agurin batare daya juyo ya fuskanceta ba har sanda  ,
 momy ta sake kiransa  " fu'ad ka dawo ka zauna dan girman allah ba dan ni ba  .......
runtse idanunsa yayi gam saboda yadda zuciyarsa ke tafarfasa ,domin  ahalin bakin cikin dayake ciki Allah Allah yake yak'arasa d'akinsa ya aiwatar da niyyarsa gareta, ko zai samawar zuciyarsa sukuni, amman yadda momy tayi masa magana bazai iya wulakantata ya wuce  ba,ko babu komai tana da wata daraja da kima agurinsa, dan hk ya juyo ahankali ya zauna yana huci tmkr mayunwacin zaki.
 momy ta numfasa ta koma ta zauna tana fuskantarsa sosai cikin mayunwacin hali da ita kad'ai tasan halin tashin hankali datake ciki , sannan tasoma magana atsanake cikin tausasshiyar murya "kayi hakuri fu'ad, wanda aka cuta shi ake bawa hkr, kayi hkr dan girman allah ba dan na kasance suruka ko mahaifiyar matar gareka ba , dan wannan yar iskar yarinyar bata bani wannan girman da matsayin ba, kayi hkr saboda girman allah da kuma girman da Allah yabani dan nasan a haife na haifi kmr ka in dakace nayi haihuwar wuri.
"bazan hanaka sakin me'ad ba har idan kaji bazaka iya cigaba da zama daita ba saboda tayi  maka abinda ya cancanci saki agurinka, sannan bazan hanaka cigaba da zama daita ba saboda nasan har yanxu kuna matsananci son junanku, iya shekarun aurenku ban ta'ba jin kanku ba sai a wannan lokacin, yanxu tunda abun yazo da haka ni adawo da NASREEN  gurina nacigaba da  kulawa da lafiyarta tunda ni zaune nake yanzu bana aikin komai ko kuma nasa akawo muku kanwar ummi tsohuwar mai aikina tazo ta dinga kula da nasreen, yarinyar na da natsuwa da hankali sosai .... amman me kagani akan NASREEN ta dawo gidana ko kuma nasa akawo najma........ ?
naunayen ajiyar zuciya ya sauke tare da numfashi da karfi, ba zai iya rabuwa da NASREEN ba ballatana har ya kaita gidan makinyinsa da bai sonsa da kaunarsa sannan  bai kaunar jininsa, duk duniya agurinsa bashi da wani  makiya sama da mahaifin matarsa, tun daga haihuwar NASREEN har kawowa rashin lafiyarta bai ta'ba jin surukin nasa ya bud'e bakinsa da sunan yi musu ya jikin yarinyarsu ba, idan zatayi  ciwo sau dari sai dai momy ko suhailat suzo dubata amman banda shi, dan haka bai ga haukan da zai kaishi wannan kasadar ba ,wasu zafafan hawaye ne  suka cicciko idanunsa "duk fa rashin gata da galihu ne yajawo masa wanan tozarcin da kaskanci "Allah sarki inna.........
" ina ma tana raye dayasan abubuwa bazasu yi masa tsanani haka ba, ahankali kalamanta na karshe garesa suka dinga zuwa masa daya byn daya "fu'ad ka kasance mai tsananin hakuri arayuwarka ,da kuma rayuwa tare da me'ad ,kayi hakuri kayi hakuri daita  dan Allah  ta maimaita kalmar  hakuri tafi sau ba'adadi ,kayi  hakuri daita domin tayi maka hallaci arayuwa ,duk runtse duk wuya karka yarda ka rabu daita saboda furucin mahaifinta gareta, wannan alfarmace  da zan nema agurinka ba dole zan maka ba saboda rayuwa komai Kan iya canzawa D'an adam, Amman  nasan zaka  min wannan alfarmar  ,Allah ya albarkaci rayuwarka data zuriarka .......
 saurin danne hawayen dake makale acikin kwarnin idanunsa yayi zuciyarsa na  wani irin harbawa kmr zata buga ta fito  daga cikin kirjinsa.
 "wayyo inna kmr kinsan wannan tashin hankali zai faru byn babu ke a duniya ..." "Allah nagode maka da banyi saurin zautar da hukuncina akanta ba,  bugu da k'ari ma tace kona saketa bata saku ba sai dai ayi zaman daduro, shi abinda bazai so faruwarsa kenan ba "amman wallahi ko bai saketa ba sai ya d'auki 'kwa'kwaran mataki akanta ta yadda zata dawo haiyacinta.
tsawon lokaci yana zaune agurinsa dafe da ha'barsa yana tunanin rayuwa gbdy ya kasa cewa komai har sanda momy ta sake kiran sunansa "fu'ad bazan maka dole ba, sai dai akwai dalilin dayasa kaji na kawo wannan shawarar bazan so ku rabu da junanku ba duk da bansani ba ko me'ad ta ta'ba gaya maka gargadin mahaifinta gareta da sharudd'ansa akan aurenku , amman zabi yarage naka ka saketa ko kuma nasa akawo muku najma... .......
"dan ko agabana ka saki wannan jairar yarinyar mai shegen taurin Kan  ba zai min ciwo ba ,saboda ita ta jawa kanta, son abun duniyarta ne ke neman rufe mata ido har take kok'arin manta abinda ya faru daita abaya.. ..
tunda momy tasoma magana nadama da danasani sukayi mata diran makiya wani irin mahaukacin bugu kirjinta keyi, yayinda tsoro da matsanancin fargaba suka mamaye ilahirin jikinta, hawaye ne suka shiga gangarowa  daga cikin kwarnin idanunta zuwa bisa kuncinta tana gogewa wasu na sake biyo kuncinta "meyasa tayi abinda tayi a yanzu ?
"meyasa idan zuciyarta ta hau sama idanunta ke rufewa ta dinga aikata ba daidai ba......? "Why why why!!! Mead why did you do this to ur husband..?
"Ya Allah ka taimakeni kar ya sakeni, idan ya sakeni yaya zanyi da rayuwata ,ga kuma  tarin kaunar danake masa ..?
"Allah na tuba, Allah ka ceceni ka sanyaya zuciyarsa kar ya sakeni, dan ina son mijina banason abinda zai rabumu....numfashi ta sauke da karfi kana muryarta cike da  kuka tace "momy ki daina cewa son abun duniya ke damuna duk wannan wahalar fa danake saboda wa nakeyinta....? 
" I think saboda shine da yarinyarmu nakeyi , kaso d'ari acikin albashina agidansa da yarinyarsa suke tafiya, nifa nasan abinda nakeyi momy kuma kema kinsani idan na zauna abgida rayuwa  zata mana tsauri dayawa,yanxu idan wata matsalar  ta taso ba fata nakeyi  ba   wa zai taimaka mana? 
"momy bamu da mataimaki fa sai Allah, kinsani nasani momy shima kansa yasan da haka , babu wanda zai taimaka mana , da d'awainiyyar rashin  lfyr nasreen ma kawai akabarmu ya ishemu fama "nawa muke siyan maganinta  ?
"Magani daya akwai wanda muke siya more than 100k ban da sauran magunguna "yaya yake son nayi da rayuwata idan dai ba kasheni yake son yi ba?
" wannan aikin nawa shine rufin asirinmu ........ tak'arasa mgnr tana zubda hawayen nadamar abinda tayi masa... 
Momy dake fuskantarta ta gyara zamanta kana tace "nasan da haka me'ad amman ai baki biyo ta tsarin daya dace ba sam, yanzu dai kiyi  shiru muji ta bakinsa" fu'ad me kace akan shawarata? 
runtse idanunsa ya sakeyi zuciyarsa na wani irin mahaukacin bugu da kyar yasamu  ya iya bud'e bakinsa "shikenan momy azo da mai aikin kawai dan gsky bazan iya rayuwa babu yarinyarta a kusa dani  ba......
 "nagode nagode !! da mutuntaka fuad Allah yayi muku albarka ,ka girmamani kuma gani kai mai  Allah  yasa ayi maka fiyye da yadda kamin "ameen momy. 
nan momy ta juya  tashiga yiwa me'ad fad'a ta inda take shiga batan take fita ba, fad'a sosai tayi mata, hawaye sosai me'ad take daga karshe momy tace "kije ki durkusa gaban mijinki ki rokesa gafarar abinda kikayi masa ,idan kina bukatar rayuwarki ta daidaita, wani irin kuka mead  ta fashe dashi  sannan ta durkusa kasa tashiga Jan gwiwowinta domin   isa garesa, yayi saurin  dakatar  daita da  hannunsa"no momy ba sai ta bani hakuri........
"Karkace haka  fu'ad ,kuskure ne tarigada tayi kayi hakuri ka yafe mata" ki karasa garesa kibashi hakuri shashar banza kawai mara mayo da tunani,da sauri ta k'arasa zata rike kafafunsa yayi saurin janyewa yana watsa mata uwar  harara , tana kuka tace " kayi hkr honey  na tuba bazan sake ba .......
batare dayace mata uffan ba  ya mike tsam  ya fice abunsa yana Jan tsaki Dan yasan da wuya ta canza halinta .....
bayan fitarsa fad'a dai momy tacigaba dayi mata, akan ta rike mijinta gam gam akwai mata akan titi suna neman irinsa basu samu ba ,sannan  a wannan duniyartamu  babu nmj irinsa ,  dan da wani nmj ne da yanzu zance ya sha bambam, "yanzu yarinyar nan da za'a kawo miki , kiyi kokari ki zauna lfy daita karki  Mata  mugun Dan nasan  halinki,ko  ki  koreta idan kika  koreta i don't have any option sai dai kinsa yadda zakiyi da rayuwarki dan bazan bari matsalarki ta kasheni ba...
Har bakin mota me'ad ta raka  momy still fad'a take mata da Jan kunne  ,tana tsaye har sai data ga tashin motarta sannan ta juya zuwa  cikin gida kai tsaye d'akinta tashiga tayi showel ta fito ta canza kaya zuwa riga up shoulder iya gwiwa, wacce aka tsaga gabanta har zuwa gwiwan kafarta ,ta  nufi d'akin nasreen har lokacin bacci take ,dayake cikin magungunanta akwai wanda ke sata bacci sosai , kwanciyarta  ta gyara mata ta sake lullu'beta tare da yi mata kiss a goshinta ta fito ta shiga kitchen domin girka musu  abincin dare ,abinda tasan yafi so shi ta fara prepare din  d'orawa  ,wato doya Wanda zata sarrafa shi zuwa pounded yam ,da miyar egusi ,da busashen kifi da naman kaza, tana cikin aikin taji sautin k'arar  wayarta  dake ajiye  agefe daya ta karad'e ilahirin kitchen din , ahankali ta bar abinda take  tana duba screen din wayar, sunan data gani ne yasata d'aukar wayar ta manna a kunne  "hello kawata ykk ,ya kwana biyu ?
 Bangaren sajida tace "komai lfy ya mai jiki kuma?
"Da sauki kawata yau dai in gaya miki yakin karshe  akayi agidan nan .
 
"Allah kawata me ya faru  kinje aiki kenan inji cewar sajida?
"Me zai hana kuwa, ai zuwa aiki a yazama Dan ada, it most be dole  ,naje bayan an gama bura'uba ba takarasa mgnr tana murmushin daya zame mata jiki.....
Sajida ta kyalkyale da wata uwar dariya kana tace "da kyau  kawa, shiyasa nake mugun sonki wallahi akwai saurin  d'aukar action akan Abu ,wallahi karki sake ki yarda ,duk borouban da za'ayi kiyi Amman karki yardar masa ,ta yaya ma yake expecting ki ajiye aiki ki zauna agida, nifa kina ganina babu aikin da zan iya bari akan wani miji  saboda ba duniyarsa nazo...
"Haka ne wallahi kawata yanzu dai mai aiki za'a kawo mana ,nan tashiga labarta mata komai, sajida nagama jin bayaninta tace "kash ni kuwa   banso kin sake d'auki yar aiki ba wallahi.."to ya zanyi sajida ni kaina banaso daukar masu aiki saboda tsaro duk I trust my husband bazai ta'ba yin abinda bai dace ba ,amman dole na d'auka ko dan momy data tashigo cikin zance ,ni kuwa sajida ina son yi miki wata magana so very important." Ina jinki kawata"
"A gsky ya dace ace zuwa yanzu kinyi aure zaman ya isa hk getting to 11 yrs now kina zaune without married ga emran har yayi yara uku Amman  ke kina zaune "me yasa bazaki samu wani ki aura ba tunda nasan barasa masoya kikayi ba ...
"Ai mijinki ya kanainaye koina acikin zuciyata bazan iya auran wani ba ..ta fad'i hk a zuciyarta.."kina jina sajida ?
Naunayen ajiyar zuciya sajida ta sauke sannan tace "ina jinki kawa mazan ne sai a slow duk Wanda yazo ba maganar aure ke kawosa ba, wani abu suke nema ni kuma bazan iya raba  gindi ba ,acikin mazan duniya mutun daya nagani me nagarta, shiyasa  nake addua a kullun  in samu miji kmr naki..dip me'ad ta d'auke wuta tare da tsaida aikin datake tayi shiru zuciyarta na wani irin beating fastly, mgnr sajida tayi matukar bugar mata da zuciya "wai meyasa take kwad'ayin son  auren miji kmr nata ?
abun na maseefar taba zuciyarta da gangar jikinta. 
"Me ma maganarta take nufi da  guda daya tagani me nagarta shiyasa take adduar samun miji kmr nata......
 "hello hello.."ina jinki, sajida "wai  me yasa kike kwad'ayin mijina ko kina son shi ne .....?
Tayi mata tmbyr muryarta na rawa. 
"Uhmmmmm ammm ko daya ,ina dai son me nagartarsa ne kawai bawai ina.."dakata dakata !!sajida for the last warning banason muna magana kina nuna kwad'ayinki akan mijina, idan babu dama mu daina zancensa dake plz Dan maganganunki akwai rainin sense ciki, haba da zarar anyi mgn sai kece kina adduar samun miji kmr nawa ....idan kina sonshi ki fito ki gaya min than I will know what do ..
"no no ki fahimci me'ad  "babu abinda zan fahimta acikin mgnrki baya ga tsabagen rainin hankali takarasa fadar hk tana me katse kiran gbdy ta  ciza lips dinta da karfi zuciyarta nacigaba da bugawa, ahankali tashiga  jujjuya wayar hannunta, tunanin tashiga yi "anya kuwa babu ayar tambaya akan zantukan sajida ..? 
"Kai da wuya wannan abun yakasance ,Sam wannan lamari  ba me yiwu bane "ta yaya sajida zata so mijinta?" kawai sha'awar me irin halinsa take  bawai nufinta tasoshi ba ..
da wannan tunani tacigaba da aikinta atsanake har  ta gama  taje tashirya dining ,ta sake fad'awa wanka wanda  zuwa lokacin tuni nasreen ta tashi, bayan ta fito ta shirya cikin wasu had'add'u kanan kaya riga da siket ,sai bakin hular tauban data sanya akanta, ta nufi d'akin nasreen,inda ta isketa  zaune fitowarta kenan daga bayi, tana hango momynta ta shagwa'be fuska alamun fushi , me'ad takaraso da sauri ta rungumeta ajikinta  tana shafa sumar kanta "har kin tashi baby nah?
" I really miss just for same hours"
"Nasreen tayi mata banza Dan haushinta take ji har acikin zuciyarta saboda ta fita aiki tabarta tare da dadynta alhalin ita tafi son kasancewa tare daita , kuma tayi mata alkwarin karya,na Cewar  zata dawo da wuri su  kalli tv tare suna cin popcorn gashi  duk babu wanda sukayi aciki. 
Zaunar daita tayi a









