Showing 6001 words to 9000 words out of 20453 words
Chapter 3 - MUTUWARE GIDAN GAWA Complete By Mrs Sadauki .txt
da Momah ke ɓoye min sai dai ban san shi ba.
Kamar wacce take karantar zuciyata na ji saukar furucinta “Ayodele ban ɓoye miki tarihin ki ba don wani abu ba,sai don kiyaye ki daga mumunar ƙaddarar da mahaifin ki ke son ɗora ki a kai”
Da sauri na yunƙura na tashi zaune na ce “Momah don Allah ki faɗa min wane ne mahaifina? Sannan ya na raye?”
“Da ransa duk da na fi shekara ashirin da baro ƙasarmu ta gado,amma ina ji a jikina bai mutu ba”
“Mine ne dalilin ki na guduwa to?”
“Zan faɗa miki sai ranar da kika cika shekara ashirin da biyu cicif”
“Nan da wata biyu kenan?” na faɗa don birthday ɗina ya kusa.Ta jinjina min kai alamar tabbatar wa,cike da farin ciki na kwana.
Washegari da zan tafi makaranta Momah ta jadadda min kan cewa na mayar da Kunkurun nan inda na ɗauko shi “to” kawai na ce mata ba wai don ina da niyyar yin haka ba.
Da na fito waje a ƙofar gida na yi rame daidai inda ruwa ke kwanta wa na saka Kambun Kunkuru na mayar da ƙasa,ina ganin yadda yake kallona da manyan idonsa amma Allah na gani ba zan barsa ba ya cutar da mutane.
Ko da na isa asibiti na tarar ana ta ɗaga ankon bikin A'isha ,ban ware kaina ba na shiga duba wa tare da tambayar inda suka fiddota.
Muna tsaka da aiki A'isha ta zo kusa da ni ta ce “Ayodele kin tuna mutumen da ya mutu jiya?” duk da na fahimci wanda take nufi bai hana ni neman ƙarin haske ba “wane fa?”
“Wanda kafin mu sauka ya mutu,gadonsa kusa da na yaron nan mai cutar sikila”
“Oh! Na gane shi”
“Hum! In faɗa miki an sake maido shi asibiti”
“Bai mutu ba?” na tambayeta da sauri,har sai da ta min wani kallo bisanin ta ce “ya mutu! ”
Na sauke ajiyar zuciya,ita kuma ta ci gaba da cewa “sai dai fa gawarsa ta ƙi shiga kabari ” A'ishah ta faɗa cikin wani yanayi.
Dukkan nutsuwata na bata tare da tambayarta “ban gane ba? To ya su ka yi da gawar?”
“Sun maido ta mana! Ta na can MUTUWARE cikin sanyi”ta ban amsa.
“Can shi ya sani! Mugun halinsa ne yasa Ubangiji ya nuna masa ishara” na faɗa zan ci gaba da aikin cika takardu don mun ɗan tsaya hutu ne .
“Amma Ayodele na tambaye ki mana”
“Ina jin ki” na faɗa ba tare da na dube ta ba.
Ta ce “mine ne haɗin ki da shi?” na ɗago na zuba mata na mujiya sai na ga ta ɗan rikice da sauri ta ce “ah! Ina nufin mi ya haɗa ku,jiya da ina ƙoƙarin taimakonsa na ji ya na cewa ki yi masa rai kar ki muzanta ni ban shirya zuwa ɓoyayyar duniya ba”
“Sai kuma ya ce miki da ni yake?”
“Sunan ki na ji ya faɗa”
“To ki je ki tambayesa” na faɗa cikin fushi tare da tashi na barta ma wurin.
Wunin ranar haka muka yi aiki sam babu walwala har Fatimah sai da ta lura kamar mun samu saɓani.Ta yi tambayar duk muka ce mata ba komai,wurin cin abinci ma haka A'isha ke ta min kallon ƙasa-ƙasa ban san mi take zargi a kaina ba har mu ka zo kwanciya.
Addu'o'i na ga ta na ta yi na neman tsari,sannan alamu sun nuna a tsorace take don motsi kaɗan sai ta zabura.Kasa haƙuri na yi na ce “ A'ishah ina son yin magana da ke”
Fatimah ta kalla wacce ta sharar bacci bisanin ta ce min “to”
Na saki wani murmushi sannan na ce “ki na tunanin ko wani na gani zai cutar da ke zan bari ballantana ni da kaina na cuce ki? Ban san zargin mi kike yi a kaina ba,amma ki sani ruhin Ayodele tsarkake ne .Burinsa kullum ya kawar da mugunta da masu yin ta,na san abin da ya faru a unguwarmu da kuma na mutumen nan sun saka miki shakku a kaina”
Ta ja wani dogon numfashi sannan ta ce “wallahi ni lamarin ki ne ya fara bani tsoro,abubuwa kike kamar ƴar autar aljan.Idonki fa har canza kala suke,kuma ba zan ɓoye miki ba wallahi na fara jin tsoron ki”
Na ƙyalƙyace da dariya na ce “wallahi ba muguwa ba ce ni ! Kuma ban san mike faruwa da ni ba.Abu guda nake so ki saka a ran ki shi ne Ayodele amanar A'isha ce”
Wani gamsashen murmushi ta sakar min ta ce “har na ji zuciyata wasai,yanzu kam zan yi bacci cikin aminci”
Sai da mu ka ɗan yi hira bisanin ta ɓingire bacci,na dube su cike da so da ƙauna irin ta jini.
Ina shirin yin kwanciya na ji an kira sunana “Ayodele?” na waiga ban ga kowa ba,sai na yi tunanin ko kunnena ne bai ji min daidai ba.Sai dai da mamakina haka aka sake kira a karo na biyu,kawai sai na fito.
Ci gaba da kiran sunan nawa aka yi,inda sautin ke fito wa na dinga bin direction ina ta tafiya har na ɓullo wata kwana.Nan na yi kiciɓis da allon sanarwa,sunan *GIDAN GAWA* ne ɓaro-ɓaro da manyan baƙi,a ƙasa kuma hoton gawa ne naɗe cikin farin likafani.
Waige-waige na fara ,har zan koma na ƙara jin sautin sunana,muryar ya ta namiji ce ba mace ba.Ɗakunan da aka tanada don ajiyar gawa na nufi na mazan,ƙofar da kanta ta buɗe hakan yasa na kutsa kai.
Ƙyalƙyal ! Aka kece da dariya,da sauri na fara dube-dube don tantance shin cikin wane akwatin ne ake dariya.
“Ga ni nan” na ji ya faɗa a bayana,na juya na yi tozali da mutumen da A'ishah ke ban labari an maido gawarsa.
Ido cikin ido muke kallon juna da shi,bisanin na ce “lafiya ka kira ni izuwa nan?”
“Kambuna nake so ki ban”
“Ba zan bayar ba doli ka mutu kamar sauran da ka kashe”
“Ki bani cikin lalama ko kuma na gayyato miki shugabanmu”
“Au! Har shugaba gare ku? Na tambaye ka mi yasa kuke son yin mugunta? Don me ba za ku zauna cikin duniya normal ba kamar kowa?”
“Saboda duniyar ɓoye ta matsafa ta fi daɗi,za ka sha jini ka yi ta siddabaru ka na tsoratar da mutane cike da nishaɗi ”
Hira ya fara yi min ta yadda suke kama kurwar mutum da kuma yadda suke yi in su na son bai wa mutum tsoro,hakan ya shagaltar da ni sosai sam ban fargaba sai mugayen esprit na ga duk sun cika ɗakin.
Ruhika ne na maras imani,wasu ma daga maƙabarta suka zo nan don taimakon ɗan uwansu.Kewaye ni suka yi,ba na ganin fuskokinsu.Wasunsu tamkar innuwa,wasu kamar dunƙulalen baƙin hayaƙi,wasu kuma cikin siffar fatalwa ne da farin likafaninsu.
“Auwushhh tangarrsinn,mahulujaaa.An yarhihum khaaaaa!” shi ne furicin da na samu bakina ya na furta wa,duk a tsorace suka ja ba shi kuwa tuni ya koma cikin akwatinsa.Idona na rufe na ci gaba da yin wani Yare ina yarfa hannu,a take wani haske duk ya game ɗakin wanda rufe wa idona bai hana ni ganin halin da suke ciki ba.
Tuni duk suka tsere suka bar ni da shi,akwatin da yake ciki na ɗora hannuna akai ya fara ihu ya na “cewa ki yi haƙuri zan tafi wallahi na yi miki alƙawari gobe zan bar gidan gawar nan zan je na kwanta kabar....” bai ida kai furucinsa ba wani haske ya fito daga bakina ya daki goshinsa tsit ya mutu a yanzu kuma na tabbata ko fatalwar ba zai iya yi ba.
Kaina yayi mugun sarawa,na dawo garas da sauri na fito waje sai kuma na ci karo da mai gadin wurin.“Wace ce ke?” ya jefo min tambaya,murya na ɗan rawa na ce “dama... Dama!”
Sai ya saki murmushi ya ce “yi tafiyar ki” ban san dalilin shi na yin haka ba amma sosai na ji,domin muddin maganar ta yi nisa ya tara min mutane dole a ɗora min Ayar tambayar mi ya kawo ni gidan gawa a wannan tsohon daren.
Ko da na koma ɗaki sai da na yi tunani bisanin bacci ɓarawo ya ɗauke ni.
Washegari bayan duk mun kimtsa na ga A'isha sai murna take,ban yi ƙasa da gwiwa ba na tambaye ta “wai farin cikin na mine?”
“Mansur zai zo ɗaukata,kin ga daga nan sai mu aje ki gida” ta ban amsa.
“Au haba? Fatimah ba ta zo da babur ba?”
“Ya samu matsala a jiya hanyar mu ta fiddo anko sai ta barsa wurin mai gyara”
Mu na tsaka da hira aka kirata,cike da murmushi ta ɗauka bisanin ta aje wayar ta ce “har ma ya iso mu je”
Sai da muka fito ne muka haɗe da Fatimah wacce ke zaune ta na shan love.Bakin ƙofar asibitin muka fita ,idona ya sauka kan wata ƙatuwar mota baƙa wuluk mai taya a baya.
A'isha ta buɗe mana gidan baya muka shiga ni da Fatimah yayin da ita kuma ta shiga gidan gaba.
“Baby ga ƙawayena da nake baka labari ka rage masu hanya” cewar A'isha .
“A gaishe ku fatan duk ku na lafiya?” ya faɗa cikin muryarsa irin ta siraran maza ,duk muka amsa da lafiya lau.
Ya dubi A'isha ya ce “ya maganar zuwa gidan abinci kenan?”
“Mu je mana ai su ma za su ji daɗi,ko ya kuka ce ƙawayena?”
Fatimah kawai ta amsa mata,ni kuwa na lula duniyar tunanin ta yaya ya samu kuɗi har haka cikin ƙanƙanen lokaci in dai yadda A'isha ta bamu labari ne Lagos ne ya je to tabbas akwai lauje cikin naɗi.
Ina cikin wannan tunanin har muka isa , restaurant ce ta sai wane da wane don ni ban ma san da zamanta ba.
Yadda aka tarbe mu kawai ya isa mu gane Mansur sananne ne a wurin.
Shi ya zaɓi abin da za a kawo ma A'ishah yayin da ya nemi mu zaɓa da kanmu,amma sai A'ishar ta nuna masa ko wurin aiki cikin plate ɗaya muke cin abinci don haka nan ɗin ma ba za a ware mu ba.
Shiru yayi ya na ɗan tunani,bisanin ya bai wa serveur ɗin umarni kan yayi yadda ta ce.Lafiyayen abinci ne,haka muka fara ci hankali kwance ba tare da wani tunani ba shi kuwa Mansur duk ya zama wani iri.
Tamkar wacce aka sa ƙugiya ana ƙoƙarin zaƙulo hanjin cikinta haka na fara ji cikina na min ciwo,da sauri na fidda hannuna na ce na ƙoshi.
Na tashi tare da tambayar masu kula da wurin ina ne toilet,aka nuna min na shiga.Amai na ta kwarara wa kamar raina zai fita,tsabar azaba har wata zufa ke tsatsafo min ina buɗe ƙofar toilet na yi kiciɓis da saurayin A'ishah....
[31/10 à 11:05] MRS SADAUKI 💫: *MUTUWARE ...*🧟♀️
GIDAN GAWA🧞♀️🌬️
Love
and
Horror story
```MRS SADAUKI💫✍🏻```
Dedicted to Ameera Adam
FCWA ☀️
_________________________
Page 5
Na yi tunanin ko banɗakin zai shiga hakan yasa na ɗan yi saurin ja baya na basa wuri.Amma da mamakina sai na ga yayi tsaye ƙiƙam hakan yasa na ɗago na dube shi.
Kamar mai son tantance wani abu haka yake kallona bisanin ya ce min “fatan dai lafiya?”
“Alhamdullah!” na amsa masa a takaice “okay!” ya faɗa tare da koma wa baya yayi tafiyar shi.Na bi shi da kallon mamaki bisanin na take masa baya,ina zuwa sai na tarar ya zauna kujerata wacce na tashi kawai sai na yi tsaye.
“Ki zauna mana” ya faɗa cike da kulawa,ban sani ba ko bai lura ba ne ya zauna a nan ɗin oho amma dai haka kawai na ji ban ra'ayin zama inda ya tashi .
“Ke ma ki zauna mana ga kujera nan,ki yi tsaye kamar wata soja?”cewar A'ishah,ganin haka yasa na zagaya zan zauna kan kujerarsa ba don na so ba don haka kawai nake jin akwai makircin da ya shirya,cikin ikon Allah wayata ta ɗau ringing,ina duba wa sai na ga sunan Momah .
Ina ɗaga wa ta ce “a ina kika tsaya har yanzu ba ki zo gida ba?”
“Momah gani nan zuwa yanzun nan” na faɗa cikin rawar murya.
“Ki na ina na ce?”
“Tare da su A'isha Momah ” na faɗa tare da mayar da wayar a hand free ta yadda za su ji abin da Momar za ta ce sai kuma na yi masu alama da su yi magana,sai dai kafin su kai ga yi Momah ta ce “ki dai yi sauri ki dawo gida sam jikina na bani babu hairan a ind....” ban bari ta kai Aya ba na kashe kiran ina muzurai “zan tafi sai gobe in mun haɗe”shi ne abin da na iya furta wa bisanin na yi tafiyata ba tare da na jira cewar su ba.
Bayan na fito daga restaurant ɗin sai na yi tsaye turus,don rasa ta ina zan bi na yi.Tamkar an sauya hanyar, lokacin da muna cikin mota lafiyayyar kwalta ce saɓanin yanzu da na tsinci kaina cikin jeji.
Wurin babu gida ko ɗaya sai ciyayi,da na waiga ma hatta restaurant ɗin babu ta ɓace ma ganina.A nan take na fara jin tsoro duk da ni ɗin ba ma'abuciyarsa ba ce,tafiya na fara ba tare da na san inda nake jefa ƙafata ba har na isa wurin da hanya ta tsage ta rabu biyu.Wata irin ƙishirwa nake ji a cikin mintin da bai gaza goma ba,maƙoshina ya bushe ƙamas.
Idona suka fara ɗaukar caji,na lumshe su a hankali kuma bakina ya fara fitar da sautin wani Yare.Ban buɗe idona ba sai da na ji ƙarar motoci da zantukan mutane.
A bakin titi na tsinci kaina, Allah ya taimake ni na hangi wani gu ana sayar da ruwan leda na tsallaka na sayi leda huɗu a nan tsaye na shanye su.Na ja ajiyar zuciya kamar wacce aka dawo ma da ruhi haka na ji,daga nan na tari taxi sai gida.
A can restaurant kuwa sosai hankalin Mansur ya tashi,muryar Momah tamkar busar sarewa haka ta ratsa dodon kunnen shi.Ya so ya tsayar da Ayodele saboda hatsarin da ke da wurin,amma da ya tuna zuciyarsa ba ta aminta da lamarinta ba sai ya ƙyaleta tare da yaƙinin sai dai a yi labarin wata amma ba dai ita ba.
Bayan sun gama cin abinci ya ɗauki su a mota,sai da ya fara ajiye Fatimah sannan ya kai A'ishah.
“Wai wace ce ita? Wato abinci mai magani ba zai taɓa zama a cikinta ba shi yasa ta amayar da shi.Na tsane ki! Ita kuma uwarta ta wace ce? Ya aka yi har ta san na shirya plan akan ɗiyarta?” ya jero ma kansa tambayoyin ya na mai bugun sitiyarin mota a haka har ya isa tankaɗeɗen gidansa wanda ya ji komai na more rayuwa.Sai da yayi wanka ya sha madara mai sanyi sannan ya kira A'isha suka yi ta hirar soyayya a ƙarshe ya tambaye ta “ya labarin ƙawar ki?”
“Wace daga ciki?”
“Wannan mai siffar Inyamurai” ya bata amsa,ta yi dariya ta ce “don dai ta na da jar fata ne sosai amma ai ba ta kama da Inyamure ”
“Fatan ta je gida lafiya?”
“Wallahi ba mu yi waya ba”
“To ki kira ta mana,sam ban yi kirki ba da ban bata ko da kuɗin taxi ba ne”
“Jira na kirata to” cewar A'isha ta na mai kashe kiran,Mansur ya lumshe ido ya na jin zuciyarsa na ɗan dokawa burinsa guda A'isha ta kira ta ce masa ta mutu.
AYODELE
Ina isa gida Momah ta wani jawo ni a jikinta ta rungume bisanin ta fara duduba ni kamar wacce ke neman ko na samu wata illa ne.
“Daga yau kar na sake jin kin tafi yawo kin ji ko? ”
“To Momah ” na amsa.
“Ayodele ke ɗin ta daban ce,dole ki dinga taka tsantsan duk da ina da yaƙinin ababen bauta ba su taɓa bari a cutar da ke ba,domin su na tare da ke a ko ina amma ki dinga kulawa ba ko ina ba ne ake zuwa” Momah ta sake faɗa ta na mai kallona cikin ido.Kai kawai na jinjina mata bisanin na wuce ɗaki,kaya na cire na yi ɗaurin ƙirji na je na yi wanka .
Ina tsaka da cin dambun shinkafa da Moma ta girka kiran A'ishah ya shigo,gabana sai da ya faɗi a take duk abin da ya faru da ni ya dawo kaina,hakan yasa har kiran ya katse ban ɗauka ba . Lokacin da na biyu ya shigo kuma a daidai nan maƙociyarmu Asabe ta shigo ta na rangaɗa sallama.
Na amsa mu na gaisa wa,Momah ma ta fito .Godiya ta zo ta na ta faɗa mana yadda lamarin ya kasance da Zeinab nan muka yi ta hira kan Mayu da illolinsu.Sai bayan ta fita ne na duba wayata ,har zan maida kira kuma sai na fasa na tsunduma zancen zuci ‘tabbas da walakin goro cikin miya! In babu rame mi ya kawo zancen shi? Mine ne na biyana har toilet? Babu shakka akwai abin da ya saka a abincinmu,to shi kuma restaurant ɗin da ya zama kamar ɓatan wata? Hummm! Zan nutsu,na ankare komai sai na gano gaskiyar lamarin’
Abincin ma sai ya fita raina,tashi na yi na fiddo fararen rigunan da nake saka wa na likitanci na wanke su tasss bisanin na kwanta ina yin bacci don jiya mun sha aiki sosai.
Tamkar a mafarki na ga wasu mutane masu fararen kaya sun zagaye ni,idona sun min nauyin da ba zan iya ware su duka ba amma tabbas ina iya ganin abin da ke gabana.Kaina na ji an fara shafa wa yayin da sauran kuma ke yin hira cikin wani Yare wanda in ba zan manta ba shi ne na taɓa ji Momah ta yi.Cikin wannan yanayi na lula duniyar mafarki,yau ma kamar kullum sanye yake cikin kayan ƴaƴan sarakuna ya saka kayan yaƙi,daidai ƙugunsa kubai ne mai ɗauke da takobinsa.Gefensa kuma masu tsaron lafiyarsa ne a tsaye cikin shirin yaƙi akan duk wanda ya kawo masu farmaki.Murmushi yake sakar min ya na kallona daga nesa, cikin izzar da ban san yaushe na same ta ba na fara takawa izuwa inda yake muna facing juna.Da sauri na lumshe ido sa'ilin da ya tsaka ɗan yatsansa manuni ya dangwala min jininsa a goshi a nan take wani sanyi ya luluɓe ni yayin da kuma nake jin shigar wasu lamurran da ba zan iya fassara su ba su na ratsa ɓargo da tsokar jikina.
“Ayodele? Ayo....” a kasalance na buɗe idona na zube su kan Momah wacce ke faman jijigata da kiran sunana.
Ta