Showing 18001 words to 21000 words out of 21779 words
wa juhud wayar tace
'' ungo bana son wannan shashancin..,
amsar wayar ta tayi tana dariya walwalar mama ce ta tsaya kasa cin abincin dake gabanta tayi ta tashi tace
'' juhud kwashe kayan nan na koshi...,
Mama bakyaci abin da fa kika fi so nayi miki
idanuwanta ne suka ƙada sukai ja tace
'' nace miki bana so na koshi idan papa ya dawo kice mai nace kar a tashe ni kaina na ciwo..,
cikin sauri ta hau staircase hawaye na bin kunci ta rasa inda za ta saka kanta tayi duniyar tayi mata zafi kamar sa ta gani a fuskar yarinyar nan da sauri ta tura kofar bedroom dinta ta murza mata key kwanciya tayi hawaye na bin kuncinta..
________nigeria
Dan ladi na sidi quarters***
sosai iska ke kadawa cikin lambon yayi da bishiyoyi sukai koraye shar da su gyara zama tayi ta ɗora kafa ɗaya kan ɗaya ta ci gaba da danna wayarta cikin kwanciyar hankali kai kace bata da wata damuwa jin karar taku tayi da sauri ta juyowa tayi da sauri ta tashi zata bar gurin kafa ya saka mata tayi tangal tangal zata wadi ya taro ta hankade shi tayi idanuwanta suka kada sukai ja tace
'' mene darin gamina da kai ina ruwanka da ni..,
tamkar da dutsai take fisge hannun ta tayi daga rikon da yayi mata tace
'' abu kaɗan kacewa mutum dan iska kai yanzu ai tarbiyya ce ta saka ka riƙe ni..,
cire baƙin glasses dinsa yayi yace
'' of course me zanji in na riƙe hannun ki dubuna sun rike kashe din da nazo nayi miki ki buɗe kunnuwanki ki jini kar na ƙara ganin nayi baki, kin zo kina wuce su idan kuwa kika ƙi wallahi na lahira sai ya fiki jin dadi ce miki akai abokai na irin halin mazan da suke tare da ke ne ko zaki samu kasuwa Allah ya temaka zuciyar su ba irin wacce kika sani bace..,
Ya altab tun ina ƙarama kake jifana da mugayen kalamai to wallahi Allah dan sauran mutuncin da nake ganin ka dashi zan cire me ruwanka da rayuwa wallahi wata ran sai kai takaicin wannan kalmar da ka faɗa lokacin dama ta kure maka
dariya yayi yace
'' yarinya ke dai zaki dana sani ki bi a hankali wallahi na aure ki na gasa miki aya a hannu ki dawo kan hanya...,
dariya tayi ta cire farin glasses da tasaka tace
'' au Allah dan girman Allah kai baka ji kunyar wannan kalaman naka na kayi amai ka lashe kenan abin da zan faɗa maka shi ne kaje ka fara gyara gida kafin kazo ka gyara ni..,
shafa sajensa yayi yace
'' ai kece gidan ke zan fara gyarawa kaf cikin ahalin me tangaran wa kika ji yana aikata makamancin abin da kike aikatawa...,
dariya tayi ta wuce shi tace
'' ja bincika kaji na wata ma yafi nawa munu sai dai kuma akwai na sarari akwai na boye wani da kuɗin sa ya saka ya auri na boye sai lokacin da bai zata ba asiri zai tonu..,
da sauri ya kalleta har ta kulewa ganin sa me kenan take nufi turkashi akwai fa lauje cikin nadi dole ya nemo koma mene juyawa yayi ya bar gurin shashin hajiyar sa ya shiga tana zaune sai girgiza kafa take luban Aisha na gefenta Assalama yayi suka amsa gaishe su sukai ya amsa yana gaishe da Hajiya
cikin fara'a ta amsa tace
'' barka dai ya gida...,
Alhamdulilah
yauwa daman ina so na faɗa maka kaja kunnan matar ka akan ya'yana jiya tayi musu diban albarka to wallahi bazan amince ba
da sauri ya ɗago abin ya bashi mamaki kwana ɗaya har an fara kawo mai kara kai halin Hajiya da yaran nan sai Allah yace
''insha Allahu zan faɗa mata wallahi ban san haka abin ya faru ba...,
owo dai na faɗa maka idan zaka dauki mataki ka dauka dan wallahi bazan lamunta ba kai kaɗai ne babban dana ace ƙananan ka basu da iko da gidan ka ai tama lami din na kirawo ta nace taja kunnen yarya idan ban da na dage yar ta ta zata aure ka wallahi ba zan lamunci yarda take juya uban rufaida ba su juya min kai haka kurum
shiru yayi yana bin zanan kasan carpet din dakin da ido yace
'' Allah ya wuce zuciyar ki..,
amin yauwa ba ruwanka da shiga sabgar wannan shegiyar yarinyar kasan fa duk inda shege yake dan sunna ya rabe shi zai ga ba dai-dai ba nidai na faɗa maka yanzu nace wa yaran nan indai suka ganta to su matsa daga hanyar ina zamab zamana ba za su sani yawan karbo magani ba garin biye biye mutum ya kauce hanya be sani ba
tashi yayi yana cewa to hajiya sai anjima
to Allah ya tsare ya kare ka yaushe kuma zaka koma gun aikin naka
dan jim yayi yace '' sai nan da ƙarshen watan nan ...,
okay Allah ya kai mu
amin ya Allah ya fada yana futa kai tsaye yana fita be biya ko ina ba ya hau motar sa ya wuce gida parking ya daidaita ya fito kai tsaye hanyar da zata sada shi da shashin rufaida ya nufa sallama yayi da sauri ta amsa batare da ta ɗago ba idanuwanta nakan wayar ta abin mamaki parlour yayi kaca kaca kai kace anyi wata ba a gyara ba kallo ya shiga bin ko ina ga rubar lemo da ruwa yadda kasan kana kasuwar sai da robobi ka kuntun cake da donut ga ledojin biscuit cikin bacin rai yace
'' rufaida kinsan ni fa bana son kazanta wannan wanne irin abu ne tun safe da kikai shara baki ƙara yi ba...,
ɗagowa tayi tace
'' ni wallahi tsiyata da kai kenan ka dinga fadan da ba dalili ina ni ina sharar katon parlour nan ai sai kuguna ya karye Wallahi bazan iya ba a dazun ma turare kawai na saka sai yanzu nake charting da aunty take ce min nayi maka magana ka samomin yar aiki..,
da sauri ya kalleta yace
'' yar aiki kuma a ina ance miki ina da burin ajiye yar aiki to wallahi tun wuri tunanin nan ya bar zuciyar ki idan har zaki kanzanta wallahi ba xakiji daɗin zama dani ba rufaida tun wuri ki ɗauki tsintsiya ki gyara dakin nan tun kafin ranki ya ɓaci..,
da sauri ta ajiye wayar ta tace
'' haba altab ka tausaya min ina ni ina share wannan dakin kalli fa kagani ni wallahi a gidan mu ban saba ko tea ban iya dafawa ba idan kuma kaga zaka iya jigilar siya mana take away bisimillah..,
tun da yake be taɓa jin rainin hankali irin wannan ba anya kuwa rufaida lafiyar ta qalau lallai zai gyara mata zama soja ba wasa ba dole ta nutsu idan kuwa ta ƙi zata sha wuya..yace
'' ki kawo min abinci bedroom dina..,
tashi tsaye tayi tana zuba uwar miƙa tun kayan dazu ne da safe da tasaka suke a jikin ta wato kawai kyale dan adam idan ba zama da shi kayi ba baza ka iya fahimtar wane shi ba duk uban barar da turaren da rufaida ke yi yau babu ko kamshi a dakin da take ko jikinta ma banda wari ba abin da take baya jin ko wankan tsarki tayi domin wannan wari da walakin
hausa suka ce goro amiya 😂😂 ba ruwan oum yasmeen kowa ya debo da zafi bakin sa
Sauran page biyu free ya ƙare domin yin payment zaku biya ta wannan account din
8141785374
Amina alhasan Muhammad opay
ku turo da shedar biya ta wannan account din
09061890481
ƁAƘIN SHAFI
Oumyasmeen
Daga wannan page wannan page din freee ya kare ku daure ku siya ku karanta halalin ku duk wanda ya karanta min littafina ba tare da ya biya ni ba yaje shi da Allah..
masu fitar min da book ku kuma kuje dan kan ku sai ka gama wahala rana tsaya mutum ɗaya ya fitar maka da book..
domin biyan kudi zaku biya ta wannan account ɗin 8141785374 Amina alhasan Muhammad opay ku turo da shedar biya ta wannan hanyar 09061890481
₦500
yan niger zaku iya turo da katin moov ko sahel fcfa 300 ku ɗauke shi gaba da baya ku turo ta wannan number 09061890481
Cameroon Ghana chadi zaku turo da katin VTU ta wannan number 09061890481
Complete document 1000
yan aljanna ku nuna min one love
EPISODE 9-10
Bedroom dinsa ya shiga ransa a ɓace yana shiga ya cire takalminsa ta ajiye zama yayi akan armchair rasa ma me zai yi shi mutum ne da baya son ƙazatan ta amma yarinuar nan ya lura ba ƙaramar ƙazama bace kwana ɗaya har tafara nuna halinta to wallahi ba zai dauki wannan kazantar ba kamar an waɗo ta haka ta shigo tana sosa kai zanin zata a ɓantare tace
'' beb Wallahi tun safe nake cin snack na gaji ko za kai mana take away...?,
kansa ya ɗago da yake sara mai yayi mata wani irin kallo sannan ya ɗauke ƙansa abin da ya lura idan ya ci gaba da zama a gidan nan rufaida bata gyara halinta ba wallahi a kwai matsala tashi yayi ya shiga bathroom,
Cire kayansa yayi ya jefe cikin Landry basket sakarwa kansa shower yayi domin ji yayi kansa har turiri yake saboda tsabar ɓacin rai,
cikin daki kuwa ko da ya tafi ya barta ko a jikin ta sai ma taɓe baki da tayi ta fice daga dakin tana cewa bara na samawa kaina mafita yunwa ba kanwar uwarka bace zama ka sauko kan hanya wayar tace tayi ringing da sauri ta ɗaga ta fashe da kuka tace
'' aunty ni wallahi bazan iya ba dawowa gida zanyi yanzu naya dawowa ya rufe ni da faɗa ba irin kulawar nan da nuna tarairaya kinga dazu ma da ya fita sallar asuba wallahi be dawowa ba sai wajejen ɗaya Sannan abokanansa suka zo ya kara wanka ya fice bayan ba haka ake ba da suka tafi yawa wani kwaɗo ya kara wanka ya fice shi ko mura baya gudu yanzu ma gashi nan wankan yake ... wai kuma bazai samo min yar aiki ba idan zanyi inyi da kaina wallahi rana ɗaya dan baki ga yadda na firgice ba kuma ji kamar ba zan yi raina amma..,
da sauri aunty ta katsaita tace
'' ke tsaya bana son shashanci wannan ai zakanin kine da mijin ki bana son jin wannan zance wai yaushe rufaida zaki hankali kwata kwata bakya iya rufawa kanki asiri zancen kuma aikin wannan tabkeken gidan wallahi ba zata saɓu ba tun da nake dake kin taɓa yi min shara ne ai yasan gidan da yaje ya dauki ki dan haka anan ma ko tsintsiya ban yarda ki dauka ba kinga share hawayen ki autata..,
share hawaye tayi tace
'' to na share...,
yauwa abin da ya saka na bugu nayi miki magana a charting baki buɗa ba ya gane ko kuma shirin mu yayi aiki kinsan daman dayan biyu ne idan ya gane a canza wani shirin
kallo kofar dakinsa tayi da sauri ta shiga nata dakin tace
'' hmmm aunty Allah ya rufa mana asiri be gane ba amma kuwa idan ma ya gane to yana cikin ko kwanto ...,
aunty tace
'' dan kuka me jawa uwar shi jifa yanzu da ace ban sani ba da shikkenan kin zubar mana da martabar gidab mu ni ban ga abin so a wannan shegen yaron ba Allah yayi miki kafiya duk da ma lokacin da na sani abubuwa su ƙure da wallahi karya yake ya sani sai dai in kuma shima yana yi...,
dariya ta saki tace
'' shi yasa ka nake alfahari da ke aunty sai an jima ga shi nan...,
da sauri ta kashe wayar ta saka akan gado budewa tayi cikin haɗe rai kamar lokacin da ta fara haɗuwa da shi ba annuri ko ɗaya a fuskarsa yace
'' wato tun yanzu rufaida ban isa na faɗa miki kiji ba ...? , ba zaki share gidan nan ba kitchen ma gashi nan kaca kaca..dakin duk wari yake
wallahi Allah bani na ɓata kitchen ba su Maryam ne da sara suka dafa mana indomi zancen kuma kace daki na wari to ai da sauki tun da bani nake ba dazu da safe na saka turaren wuta
Rufaida ta faɗa tana ɗaga hammatar ta tana shin shi nawa..
wata kan idan kana da rai zaka sha kallo bin ta yayi da ido ya ma kasa magana dole ya nema wa kansa mafita yace
'' kafin na dawo wallahi Allah ki gyara gun nan idan kuma ba haka ba zaki ga abin da zai faru..,
zama tayi a kan gado tana cire daurin ta ashe a jiyan hular gashi ta saka tamanta da yanzu ma bata saka ba ta ture daurin kanta sai gashi yan mutsi mutsin kalba irin wacce ake wa yara da sabulu ta fito kasa tantance me yake gani, kamar fa kan jariri yake gani jar uban can haka ya ambata a zuciyar sa zuciya da hange hange sai ta hango mai dazu lokacin da suke tara da nasreen a lambo da sauri ya kawar da tunanin nan daman ya dade da shafe wannan babun a ransa duk da shi kansa yasan karya yake wa kansa ba zai iya ba..,
afusa ce ya fice domin a halin da yake ciki idan yayi magana to kalma mara dadi ce zata fito daga bakin sa da harara ta bi bayansa da ita sai a lokacin ta lura da kanta tsaki ta ja tace
'' koma mene ai an riga da an daura kome zai biyu da baya me sauki ne..,
kwanciya tayi a binta a nan bacci ya ɗauke ta tayi rashi rashe bakin nan a buɗe miyun bacci na zuba har akai sallar isha tana wannan baccin na asara kamar da ga sama taji an buga mata pillow a gigice ta tashi tana zab ga ihu ganin shi ne ta mustsuka idanuwanta tace
'' kai innalillahi ashe daman haka auren sojan yake haba altab abin da kake ba baya kyautawa ka dena cin zali wallahi..,
wata uwar harara ya gallamata yace
'' idan na rantsai bazan yi kaffara ba akai magariba kina kwance akai isha kina kwance duk baki tashi kin yi ba sannan aikin da nasaka ki baki ba...,
wani uban salati ta saki tana tashi tace
'' haba sweet na ga addinin nan dan sauki ne dan girman Allah idan kai kake amsar sallar nan idan nayi dawo min da a bata naga tun da kata shi da safe baka irin tarairaye ni ba haka kayi sauri ka tafi kayi sallar asuba sai wani cewa kayi,
beb tashi kiyi wanka kiyi sallah tsakani da Allah ya dace ban taɓa shan azaba irin ta yau ba kuma da ace mazan waje ne har toilet suke raka mace
da sauri ya kalleta yace
'' ke ina kika san ana yin haka..,
da sauri ta rufe bakin ta tace
'' kar ka ne mi ga zarge ni nima faɗa min ake yadda yake yi shi ya saka na kwanta ina jiran ka dawo to shiru shiru baka dawo ba kuma ga yanayin sanyi na shigowa garin nan gudun mura sai kawai nayi kwaskwarima idan rana ta danyi na yi wanka na haɗa sallar nayi to da rana tayi na duba zan kunna heater switch din yaƙi kunnuwa kawai sai na hakura idan ka dawo ka haɗa min ruwan wankan nayi
tamkar wani mata laka haka ya zauna dafe da kai yace
'' yanzu dai asuba ahazar la'asar magariba isha duk baki ba..?,
cikin da confidence ta ɗaga mai kai domin ita bata ga abin laifi ba addnin nan dan sauki ne kuma Ubangiji yaga zuciyar ta
tsawa ya daka mata da sauri ta takure guri ɗaya tana zare idanuwa yace
'' wallahi rana ɗaya nasan na gamu da ƙaddara domin ke wallahi kaddara ce da ranki da lafiyar ki har ki dinga haɗa sallar saboda baki da tunani wallahi idan zaki ci gaba da haka wata ran bazan san lokacin da zan karkaryaki ba kin san kuwa mece sallah kinsan kuwa wanne mahimmanci Ubangiji ya bata...itace fa marabar arne da musulmi sannan kuma itace idan mutum ya tsayar da ita zata zo ta dinga tash zaman kabari..,
zunburo baki tayi ta tashi tana karka da mai zani ta shiga toilet fita yayi dakinsa ya kwanta wayarsa ya ɗago duk ƙarfin zuciya irin tasa a yanzu zuciyar sa tayi rauni yasan ba zai taɓa samun muradin sa limshe ido yayi ya buɗe a lokaci ɗaya ka ƙurawa screen din wayar sa ido itama kamar shi din take kallo ajiye wayar yayi..
ya kurawa suspender ido yawa me shirin gano wani abu idan ya furta zai zama barazana da farin cikin wasu har da nasa idan ya furta yasan baƙin cikin da mahaifiyar sa zata shiga ba ƙarami bane gwara ya bar shi a ransa idan ya mutu ajalinsa ne wayar sace tayi ringing da sauri ya ɗaga ganin me kiran cikin girmamawa ya yi mai sallama tare da gaishe shi
amsawa me kiran yayi yace
'' ya kowa da kowa dafatan kowa yana lafiya..?,
Altab yace
'' lafiya qalau alhamdulilah ya su ni'ima..?,
Suna lafiya qalau alhamdulilah kowa lafiya dan Allah ka ƙara riƙe min amanata ina gab da dawowa
tashi zaune yayi yace
'' Allah ya dawo da kai lafiya...insha Allahu baka da wata matsala.,
godiya yayi mai sukai sallama ya kashe wayar sa
_______________ BOMPAI
jazz ka tabbatar wannan zancen gaskiya kake faɗa min cewar nasreen da ta dora kafa ɗaya kan ɗaya acikin mota shi kuma jazz yana tsaye da kan sa yawa abarba saboda tara gashin da ya yi yayi tsaibebe a ka yace
'' na taɓa kawo miki rawo tan karya ne..?, da kunnuwana naji suna maganar..,
cije lips dinta tayi ta duki staring wheel tace
'' kasan me jazz wallahi tara matar nan nake akwai ranar da zan kamata naci ubanta..,
Sai wacce rana kenan kawao hajiya ta ki baza yanayin ki kema
ɗagowa tayi tace
'' ban gane ba nayi mai kaga duk wata harkar haram kai ne a sahun gaba nidai barni a nan rabon bawa da arziki mutuwa baruna yanzu ba wannan ce a gabana ba da sauri ta ɗago jin karar parking din mota baffa ne driver sa ya fito ta buɗe mai idanuwansa ne lokaci ɗaya suka canza launi tun daga sama har ƙasa ya kalli...