Showing 27001 words to 30000 words out of 36944 words

Chapter 10 - Karayar Arziki Complele Book Writing by Billyn Abdull .txt

Advertisement

22 Feb 2025

5972

ba rainawa kayiba.
Mik'ewa ya Umar yayi yana dariya, ni na' Isa?, aii sadai nace ALLAH yasaka da alkairi yabar zuminci kawai.
To Ameen.
Yana fita saddiqa tashiga hidimar bama Asma'u abinci, saiga Rafi'a da ya Umar ya kar6eta ya ce, "tashigo gida.
Atare suka gyara gidan tsaf, bayan Asma'u taci abinci Saddiqa tasakata tayi wanka tasha magani, sanda tafito angyara d'akin tsaf, saikawai tasaka wasu kayan takuma kwanciya sai barci.


Saida suka gama komai sannan Maman Faisal tawuce gida, Rafi'a kam saida tamusu abincin dare takuma gyara gidan tsaf sannan tawuce gida Dan tanaso taje islamiyya.
Ya Umar yanata zagayata danyaga yajikin, amma har yamma bata farkaba.
Sai bayan isha'i daya shigo yataradda ta tashi.
Kintashi?.
Kanta tad'aga masa, har yanzun tana cikin bargo. To yajikinnaki?, da sauk'i amma har yanzu inajin sanyi wlhy.
Zai daina shima, tashi kiyi sallah ko?.
Nanma kanta ta jinjina sannan ta yatsina fuska, yaya dama akwai ruwan zafi sainayi dashi, bazan iya da ruwan sanyiba. OK bara naduba ko Rafi'a tazuba a filas.
Rafi'a tawucene?.
Eh tun d'azun tawuce, tanason zuwa islamiyya tace.
Batace komaiba, shima yafita yakawo mata ruwan zafin, dakansa ya taimaka mata zuwa bayi, tsayawa yayi kanta yak'i fita.
Tajuyo tana kallonsa kamar zatayi kuka, kafita to.
Gira yad'age sama tareda d'an langa6e kansa gefe, bazaki iyayi agabana baneba?.
Gyad'a kanta tayi cikeda shagwa6a.
Murmushi yayi, ya jingina da bango harda hard'e hannu ak'irjinsa yana kallonta. Ta marairaice murya tana k'ank'ame jikinta, yaya sanyi nakeji wlhy, kuma zanyi fitsarin atsaye...
d'an zaro idonsa yayi waje, ya CE, "da gsk?."
ALLAH kuwa.
Murmushi yayi mata sannan yafice batareda yace komaiba.


Tana idar da sallan takuma zuwa zata kwanta, rik'o hannunta yayi yana fad'in no zauna ki huta.
Wayyo ya sanyi fa.
Toni wannan sanyi namiyene? Dayak'i tafiya. Bara nakira doctor namasa bayani......
Kafin Asma'u ta ce, wani Abu saiga Faisal (babban yaron Muktar), rissinawa yayi ya gaidasu, yayma Asma'u sannu, sanan ya ce, "uncle Abba ya ce, "kakawo key d'in shop yazauna, kaikuma kazauna wajen aunty.
To yarona ALLAH yayimaku albarka kaji, gashi kacemasa ngd.
Rissinawa yayi yakar6a yafita.
Shikuma yashiga kiran doctor. Bayan sun gaisa yaymasa bayanin harfa yanzu Asma'u tanajin sanyi.
'Yar dariya doctor yayi, ya ce, "wanan aikinkane Alhaji, indai babu zazza6in to Alhmdllh, maganar sanyi kam tana buk'atar d'umin jikinkane kawai.
Da sauri Asma'u da ya Umar suka kalli juna Dan yasaka wayarne a Hans Free.
taja bargo ta kwanta, shikuma yad'auke idonsa daga kanta yamaida hankalinsa akan maganar doctor.
Okey doctor babu damuwa ngd sosai, saida safe.
ALLAH yakaimu Alhaji, agaidamin da madam.
Okey zataji, agaida iyali.
Koda ya Umar ya kammala wayan baikalli Asma'u ba yatashi yafice, itako tak'ara k'udundune kanta a bargo, tamkar wadda ake shirin sacewa.


Waje yaje wajen Muktar, saida sukad'anyi magana ta mintuna sannan yadawo gidan.
Kaitsaye d'akinsa yanufa, yay wanka tareda shirin barci tsaf sannan yakoma d'akin Asma'u.
Harma tafara barci ita.
Yad'an dad'e akanta yana k'are mata kallo cikeda tunani kala-kala tamkar bayason abinda yay niyyar yi agareta na bata taimakon da doctor yabashi shawarar.
Tsawon mintuna sannan yazauna abakin katifar tareda d'aga bargon yashiga ahankali.
Jawota yayi ya manna da jikinsa, wata sassanyar ajiyar zuciya ya sauke tareda rinmtse idanunsa. Itakam sai kawai tagyara kwanciyarta danjinta cikin wani lallausan jiki, gawani d'umin mai dad'i da k'amshi. Barcin yaci k'arfinta shiyyasa ko farkawama batayiba.
Amma ga mutumin naku ba haka baneba, jinsa yakeyi tamkar bashiba, tuni yasan shi mutumne mai yawan buk'ata shiyyasa yake tausayin fara kusantar Asma'u, amma yazaiyi? Zuciyarsa takasa daurewa, akwana biyunnan hak'uri kawai yakeyi. Yanason kasancewa da matarsa amma yana gudun karkuma ta rainashi. Yakuma k'ank'ame ta sosai tamkar za'a kwaceta daga gareshi, jin anrik'eta tamau yasakata motsawa, shima saiya sassauta mata.
Addu'a yamusu ta barci, tanata barcinta amma shi yagagara yin nasa saboda kwad'ayin kasancewa da ita................








*_"ngd duknaga sak'on gaisuwarku, harma damasu kirana, harma wad'anda basu sami damaba, dukna gode ALLAH yabar zuminci, nama warke, ammafa ina jiran kazarπŸ˜‹πŸ˜‹πŸ€·πŸ½β€β™€πŸ˜„"_*.
Luv you allπŸ’‹πŸ’―














*_Luv you all_*
*_(((S))).......2017_*


πŸ‘©πŸ»β€πŸ’».........






πŸ’Ž *_KARAYAR ARZEEK'I!!_*πŸ’Ž




*_NA_*
*_Bilyn Abdul_*




*_Sadaukarwa_*
_miss Xoxo na_
_Zarah Bukar_
_Ayusher Muh'd_


*_NIKA'DAIπŸ‘ŒπŸΌ WRITER ASSO........😜_*


*_page→35-36_*


.......Haka yayta zagaye d'akin yana surutai, saida yagaji Dan kansa sanan yashirya cikin wankan k'ananun kaya yafito sai baza k'amshi yakeyi. Idan kaga ya Umar saika d'auka irin matashin saurayinnan ne dabai wuce 26 ba, yanada tsafta Da son k'amshi sosai.
Atsakar gidan Yakuma tarar da su Asma'u, wadda tun d'azun tadawo wajen Maman Faisal.
Saina dawo yafad'a yana k'ok'arin ficewa.
Adawo lafiya sukafad'a suduka, shikuma yafice.
Yana fita Maman Faisal tashiga yima Asma'u fad'a (Dan ta girmeta gsky, zata iya zama sa'ar Anty saratu ma). Haba Asma'u yanzunan mijinki zai fita bazaki masa rakkiyaba? Idanfa kika saka wasa wata zatazo ta kwace miki miji. Nakula kinada sakaci sosai. Hakamafa d'azun abirkice kika fito, kamar wadda taje wajen dodo. Kodai akwai matsalane?.
Girgiza kai Asma'u tayi, Dan aganinta baikamata tabama Anty Saddiqa labarin abinda yafaru itada ya Umar ba.
Maman Faisal tacigaba da fad'in to gsky ki gyara kinjiko. maza sunason ana kula dasu tamkar kwai a cokali. Indai kinama namiji haka to tabbas zai koma miki tamkar jinjiri wlhy.
Hakane anty amma wlhy ya Umar daban yake, yacika tauri dayawa. Wani lokacinma dolene kiji matuk'ar tsoronsa.
Hummm Asma'u kenan, duk taurin namiji mace saita sakashi laushi. Shawarar dazan baki ki fara karatun Hausa Novels, insha ALLAH zaki k'aru matuk'a da ilimin zama da miji. (Musamman idan kin had'u da buk d'in marubutan dasuka san Kansu) akwai wasu buks dana karanta na bilyn Abdul, na tabbata zaki k'aru acikinsu.
To a ina zan samu?.
Bak'yayin charting?.
Inayi da, amma yanzu banayi.
Tom Indai ba mijinki ya hanakiba kikoma yi zan baki no. d'inta.
To Anty ngd sosai.
Maman Faisal tamik'e dak'yar saboda tsohon ciki datakedashi, haihuwa yau ko gobe, bara naje gida, nasan sunacan sunamin 6arna tunda sukak'i dawowa.
To Anty ngd.....






..................................
Su Lubna anata hidimar biki, shiri sukeyi na garari Dan bikin namasu akwaine babu k'arya.
Komai awadace yake tafiya, party kam aii anshirya yafi kala 10, su Lubna sune amarori k'irjin biki.
Yau kamu Dan haka sukaci uwar kwalliya nawani sky blue d'in less itada Suhaima, sai walk'iya sukeyi, idan kagansu kai kace sune amaren, bakowa zaiga Lubna ya ce, "ta ta6a aureba bareba harda yara biyu.
Harabar gidan suka fito inda abokan Ameer suke birjik, duk sunci wankan bak'in wando da yellow d'in Riga, wanan shine kwalliyar kamu na maza.
Matankuwa yellow d'in wando da bak'ar riga. Sudai su Lubna basu sakaba.
Wani abokin Ameer ya ce, " kai yarinyar canfa tawuce dani wlhy, wai k'anwar Amee CE?.
Inaganin k'anwarsace, ammafa in k'aramar tafimin k'yau, kasanni ko aure zanyi banason yar 20+ gsky. Nafison daga 16 zuwa k'asa.
Dariya abokin yayi, ya ce, "humm aikai mugunta kakeji.......
Wucewarsu Luban tagabansu tahanasu cigaba da hirar. Sukam basusan sunayiba, sun wuce sun barsu da k'amshinsu.
Mota suka shiga, Lubna tajasu suka bar gidan.
Kaitsaye hall d'in daza'ayi kamu suka nufa. Dangin amarya Suma sunyi shirinsu sosai, amarya tad'auki k'yau, naira tayi kuka agidannan. Su Lubna sai nan nan akeyi dasu, sukuma suna fankama da Nuna isa, su adole dangin miji.
Babu dad'ewa su Ameer suka iso. Ba awani tsaya 6ata lokaciba aka fara gudanar da kamu Wanda yak'ayatar.
Sai wajen 9pm aka tashi, ansha casu kam babu k'arya. Idan kuga yanda Lubna tadage tana rawa saikusha mamaki......






____________________
Tunda Anty Saddiqa tafad'a mata idan tana sakaci wata zata kwace mata miji tashiga damuwa, tana matuk'ar son mijinta, tanajin ya Umar yafi sauran maza awajenta, idan akace wata zata iya kwaceshi agareta takanji tamkar an soki zuciyarta da mashi.
Wasu zafafan hawaye suka gangaro bisa kumarunta. Bata sharesuba, saima cigaba da matso wasu datayi.
Duvanta takai ga agogon d'akin, karfe 9:23pm amma har yanzu ya Umar bai dawo gidanba, tun fitar d'azu da yamma. Tana mamakin ina yajene har zuwa wannan time d'in?.
(Zuciyarta ta ce, ''yaje tad'i.") Rushewa tayi dawani kuka mara dalili....


Ni dariyama tabani araduπŸ˜‚.


Tana nan tana kukanta saitaji motsin bud'e k'ofa, da sauri tad'ago tana kallonsa. Ya Umar ne sanye cikin kayan barci, da'alama ma yadad'e da dawowa gidan.
Shima kallonta kawai yakeyi amma fuskarsa ko kad'an babu walwala. Cikin d'akin yak'araso, yaja tum-tum yazauna har yanzu idanunsa akanta. Itadai nata na k'asa, ga hawaye sha6e- sha6e a fuskarta.
Ahankali ya firzo huci daga bakinsa yana mai kauda kansa daga gareta. Ko kad'an bayaso yaga mace na kuka. Shi mutumne mai tausayi sosai musamman akan mata.
Yakuma dawo da kallonsa gareta, kukan mikikeyine? Ko har yanzu bakida lafiyar?.
Shiru tamasa, bata d'agoba, bakumata tanka masaba. Dan zuciyarta wani irin zafi takeji, gani takeyi kamar da gsk daga tad'in yake.
Cikin d'an fad'a-fad'a ya ce, "wai bakijinane!!?.
Da sauri tad'ago takalleshi, ganin yanda yakuma tur6une fuska sai tsoronsa yakuma kamata. Bakinta na rawa ta ce, "bakaine kaje tad'iba."
Tad'i!?. β€˜ya Umar yafad'a cikin sigar tambaya da mamaki.’
Itama kanta tad'a tana wani kumbura baki.
Siririn tsaki yayi, amma batajiba. Ya ce, "kewaye yagaya miki naje tad'i?.
Gabantane yafad'i, dan kuwa dai zuciyartace ta sak'a mata, bawanine yafad'a mataba.
Shima ganin haka sai kawai ya girgiza kai. Yakuma yin k'aramin tsaki tareda fad'in kinga ni bar wannan banzan shirmen naki gefe, magana nazo muyi. Tashi kije ki wanke fuskarki kidawo.
Ahankali tamik'e kamar wadda kwai yafashema aciki tashiga bayi. Fes tawanke fuskarta sanan tadawo gareshi.
Saida sukaja wasu 'yan mintuna sannan yay gyaran murya:- inaso kibani hankalinki nan muyi magana. Kanta ta jinjina masa alamar to.
_d'azu fitar danayi naje office d'in su muktar ne, dama tun kwana hud'u daya wuce munyi magana, ya ce, " nabada takarduna zai kaima ogansu yanemamin aiki. Dafarko ban aminceba Dan narigada na fidda raina ga aikin. Amma saiya nace sosai da magiya da kawomin hujjoji akan fa'idar Neman aikin harna amince.
Jiya yakai takardun, yaukuma ogan nasu saiya buk'aci ganina. Shine Muktar yakirani ina shago yasanarmin. Wanna dalilin yasa nashirya naje.
Tom saidai kuma abinda yagirgizani shine ogan su muktar abokine ga dad (mahaifin Lubna) akwai dangantaka mai k'arfi a tsakaninsu ta kasuwanci gsky, Dan sanda ina k'arkashinsa yasha aikena awajensa.
Abu na biyu kuma shine Alhaji Ahmad mai kano yad'aukeni aiki ak'ark'ashin kamfanin nasa, ya ce, "kuma yana buk'atar bayani daga gareni akan abinda yasa muka rabu da mahaifin Lubna.
Yabani dama daga nan zuwa gobe, idan nafad'a masa yace zuwa Monday zan fara aiki.
Yakika gani nafad'a masa gsky?, kokuwa na hak'ura da aikin kawai?. Ban fad'ama kowa maganarnanba saike, koshi Muktar baisan yanda mukayiba.
Asma'u tasauke ajiyar zuciya sanan ta gyara zama. Yaya nidai abinda nake gani kafad'a masa kawai, Dan ALLAH yagani bacin amana ko cutarwace taravaku da mahaifin anty Lubnar ba, yanzu kuma aiki za'a d'aukeka idan kayi kuma za'a biyaka, kaga kuwa guminka zakaci bawai a k'ark'ashin wani zaka zaunaba.
Kuma ina ganin koda kafara aiki tom nikuma saina cigaba da lura da shagon harmuga abinda ALLAH zaiyi.
Sosai ya Umar yagamsu da bayaninta Dan haka ya jinjina mata kai alamar gamsuwa, gawata k'aunarta na ratsashi, wani lokacin idan tayi Abu tamkar wata babba. Idan shirmen yamotsa kuma sai an sauke masa cikin tirelaπŸ˜‚.
Asma'u tayi murmushi mai kwantar da zuciya, ya Fharuk natayaka Murna, ALLAH yabada nasara da sa'a.
Ameen Husna ngd.
Filo yajawo ya kwanta.
Gaban Asma'u ne yafad'i, karfa asake irin ta ranar.
Kamar yasan tunanun datakeyi saiya mik'e zaune yana fad'in yau baza'a bani abinci bane?.
Da sauri Asma'u tamik'e, Dan danan tacika gabansa da kulolin abinci, tashi yayi zaune tazuba masa komai.
Yanzukam babu laifi yad'an saki fuskarsa, Dan yanacin abinci yana satar kallonta. Sukan had'a ido lokaci-likaci, ganin haka ya Umar yad'auke idonsa gaba d'aya daga kanta yamaida ahankali kan cin abincinsa.
Kamar daga sama yaji Asma'u ta ce, "ya Fharuk inada tambaya?."
Idanunsa masu haske yad'ago yana kallonta, saida ya had'iye abincin bakinsa sannan ya ce, ''ina saurarenki?."
Shiru nawani lokaci tanata juya maganar a zuciyarta, kamar tayi kamar kartayi, can wata zuciyarta na angizata akan ta tambayesa da ace tazauna cikin duhu.
Jin tayi shiru yace yadai? Kokin fasane?.
A'a. Dama inason tambayarka minene maganin mata?.
Sosai ya ware idanunsa akanta. Aransa yace mike damun kan yarinyarnan?. (Inhar bai mantaba Lubna ta ta6a fad'a masa kayan k'arin ni'ima sune ake kira Maganin mata. Dan yata6a rutsata tana sha saiya tambayeta maganin minene wannan?. Dayake Lubna macece da batada kunyar Abu kai tsaye, musamman ga mijinta, sai takecemasa maganin k'arin ni'imane)..........
Ganin yayi shiru yadaina cin abincin, kuma gashi ya tsura mata idan ko k'yaftawa bayayi saitasha jinin jikinta. ad'arare ta ce, "ya Fharuk akwai matsalane?.
Girgiza mata kai kawai yayi yacigaba dacin abincinsa, Dan aganinsa dawata manufa daban tamasa tambayar, ashema k'aryar gudunsa takeyi, tasan komai, tana raina masa hankaline kawai.
Wani d'an murmushin gefen baki yayi, shikad'ai yasan miya kitsa wa zuciyarsa.
Asma'u kam tayi gum, Dan sosai tasha jinin jikinta akan tambayar.
Harya kammala cin abincin babu maicewa da d'an uwansa k'ala.
Bayan ta gyara wajen ta kwashe kwanikan tadawo d'akin. Inda tabarsa anan ta iskesa.
Ya ce, " kinason amsar tambayarki?.
Kanta ta jinjina da sauri.
Yalumshe idanunsa yana wani murmushi na musamman Wanda Asma'u bata ta6a gani daga gareshiba.
Zan baki amsar tambayarki amma nima zan tambayeki Abu biyune, idan kinsani bazan amsa mikiba. Idan baki saniba zan had'a duka nabaki amsa, amma bayauba, zan baki amsar Abu d'aya a daren yau, biyun kuma saida safe.
Bata kawo komai arantaba ta ce, "to ina saurarenka.
Mizakiyi da maganin mata?. Na biyu:- miyasa kika tambayeni.
Gefen wuyanta ta Sosa Dan batasan amsar dazata bashiba.
Ganin haka ya ce, "shikenan, tashi kiyo alwala zan baki amsar farko dakika tambayeni...............








_kuyi hak'uri danifa, yanzu bakwajina yanda ya kamata, wlhy nayi matuk'ar busy ne kawai, kutayani da addu'ar samun nasara kawai._
*l Love you all*😍












*_((S)).....2017_*
*_luv you all_*


πŸ‘©πŸ»β€πŸ’».........






πŸ’Ž *_KARAYAR ARZEEK'I!!_*πŸ’Ž




*_NA_*
*_Bilyn Abdul_*




*_Sadaukarwa_*
_miss Xoxo na_
_Zarah Bukar_
_Ayusher Muh'd_




*_NIKA'DAIπŸ‘ŒπŸΌ WRITER ASSO........😜_*


*_page→37-38_*




..........Bata kawo komai arantaba tatashi zuwa Bathroom, babu dad'ewa tafito d'aureda alwala.
Ya Umar baya d'akin, da alama shima yaje d'auro Alwalane.
K'ok'arin canja zanin sallah tafara, saigashi yashigo. Babu Wanda yace da d'an uwansa k'ala. Ya Umar yad'auki sallaya ya shimfid'a musu guda biyu.
Sallah suka gabatar raka'a biyu. Ya Umar yadafa kanta yay addu'a kamar yanda addinin islama ya koyar mana. Sai ayanzu wani tunani yazo zuciyar Asma'u. Gabanta yashiga fad'uwa da dukan tara-tara. Duk addu'oin dayaketa kwararawa bata fahimtar komai, kawaidai tad'aga hannunta samane. amma ko ameen tagagara furtawa. Nashiga uku ni Asma'u! Shin mi ya Fharuk yake nufine? Nidai nasan wannan sallace da MAZON ALLAH (SAW) yakoyar damu muyi aranar da aka kawo mace amatsayin amarya. To amma shi ya Fharuk miye tasa manufar?. β€˜wani ras gabanta yafad'i yayinda zuciyarta tabata wata bahaguwar amsa.’
Bata dawo hayyacintaba taji ya Fharuk na girgizata. "K!. Tunanin mi kikeyine haka?.
Firgigit tadawo hayyacinta, sai mazurai takeyi da idanu. Murya na rawa ta ce, " ya Fharuk mizai farune?."
Kallonta yayi kamar zaiyi magana, saikuma yafasa ya mik'e, saida yazauna abakin katifar sannan ya ce, "mizai faru, kamarya?.
Shiru tayi Dan gane kato6arar datasoyi. Baikamata ta nuna masa tama fahimci wani abuba, tunda yamaidata k'aramar yarinya. Itama bara zata nuna masa tanada wayo fa.
Bai kuma cewa da ita komaiba taga yad'auki keys d'in shago yafita. Ta k'ofar cikin gida yabud'e, mintuna kad'an yadawo hannunsa d'aukeda yogot mai sanyi.

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login