Showing 6001 words to 8267 words out of 8267 words

Chapter 3 - TSATSUBA BOOK 5 Complete by Madakin Gini .pdf

zuba a jikina amma kuma ya kasa
kafa min hakoransa a jikina

lokacin da jiri ya fara dibana na tabbatar da cewar ina daf
da halaka sai zuciyata ta kufulo cikin tsananin
zafin nama na suri zakin na dokashi akan wani
katon dutse nan take kan zakin ya dagwargwaje ya
zama gawa
A sannan ne na yanke jiki na fadi kasa cikin mugun yanayi
da kyar na iya bude jakar guzurina na fiddo magani
na shafa akan raunikan jikin nawa da hannu daya
wadansu raunikan ma dake gadon baya na in da
hannuna ba zai kai ba ban sami damar sa musu
maganin ba
a sannan ne na dauko battar ruwana na bude nash
Sai da na dan huta naji karfin jikina sannan na mike
tsaye na dauki gawar zakin na saba a kafadata
amatsayin abincinmu na rana itama barewara
sai na barta a jikin mashin nawa naci gaba da tafiya
na nufi inda zamu hadu da matata zalina
hakika SADAUKANTAKA tana da rana tabbas in ba don
na kasance sadauki ba da babu yadda za ayi na iya daukar
wannan katon zaki har na sabashi a kafadata da
hannu daya kuma naci gaba da tafiya alhalin ina
rike da barewa bisa mashina, haka dai naci gaba da
tafiya har na iso inda zan hadu da zalina matata
tun daga nesa kuwa na hango zalina zaune akan
wannan dutse tana hange hange da waige waige
ko zata gano ni, har ma ta zaku tana mikewa tsaye
akan dutsen
ai kuwa tana hangoni dauke da zakin da kuma barewa
sai ta cika da tsananin mamaki, cikin tsananin
murna ta duro kasa daga kan wannan dutse ta farfalo
da gudu izuwa gareni ta rungumeni koda taji
raunika a jikina sai ta janye jikinta daga cikin nawa
da sauri ta dubi sauran raunikan na jikina, take
hawaye ya kwararo daga cikin idanuwanta ta
dubeni cikin alamun tausayi tace yakai mijina me yasa
ka sai da rayuwarka don kawai ka cika wannan ka ida
ta al adarmu
Sa adda naji wannan tambaya sai na bushe da dariya
nace
yake matata kiyi sani cewa ko a tamu al adar namiji
baya samun matar aure a cikin sauki har sai ya
sha bakar gwagwarmaya ta hanyar gasa a neman
auren,

kuma gasa ce mai hadarin gaske wacce mutum ma
zai iya rasa rayuwarsa gaba daya, nan dai muka juya
da baya muka nufi hanyar gida, muna cikin
tafiya ne na dubi zalina na bushe da dariya, Al amarin
da yai matukar bata mamakikenan
ta dubeni tace yakai mijina kai kuwa menene dalilin
yin wannan dariya taka, kawai sai nayi ajiyar numfashi
nace gani nayi nidake mun shafe sama da sa a biyu
a cikin nan muna farauta amma ke ko fiffiken dan
tsako baki samo ba, dajin wannan batu sai itama ta
kyalkyale da dariya tace ni kaina na yi matukar mamakin
yadda ko tsuntsu guda ban iya harbowa ba daga sama
alhalin ga su nan birjik suna ta kaiwa da komowa
a sararin samaniya sai dana yi asarar kibiyoyina
sama da guda talatin, kai bama tsuntsaye ba hatta
kananan dabbobin daji sai dana kasa tsere da wajan
guda bakwai amma da zarar sun shiga cikin duhuwa
saina nemesu sama ko kasa na rasa su
koda jin haka sai nayi dariya nace ai kin san cewa komai
sa a ne da rabo
haka dai muka ci gaba da hira har ya rage saura tafiya
kadan mu iso gida
kwatsam muna cikin tafiya sai zalina tayi tuntube ta fadi a lokacin da zuciyarta
ta fara bugawa da karfi, cikin sauri na ajiye mashina
mai cake da barewa na tasheta zaune na dubeta
cikin kaduwa ina mai dudduba jikinta nace lafiya
kuwa menene ya sameki, zalina tayi ajiyar zuciya
ta dubeni cikin alanun firgici kawai sai naga hawaye
ya zubo mata take ta fashe da kuka tana mai cewa
naji a jikina cewa mahaifina yayi kaura, koda jin haka sai
nima hankalina ya tashi na dubeta cikin kwarin guiwa
nace ke haba ! Tashi mu karasa gida mahaifinki na
nan raye
kawai dai zuciyarki ce take raya miki hakan
nan dai na tasheta muka mike tsaye har zuwa wannan
lokacin ina dauke da wannan katon zakin a kafadata
ga kuma barewa a jikin mashina
haka dai muka
cigaba da tafiya harmuka
Iso gida
tun daga nisa muka hango Abul zalina kishingide
a jikin dutsen kogon da muke kwana ya dora
kafarsa daya akan daya yana barci, kuma ga sanda

a hannunsa in ba don dora kafarsa da yayi ba daya bisa
daya da kuma sandar da ya rike a hannunsa da dole ne
ace ya mutu
Al amarin zalina kuwa lokacin da ta hango mahaifinta
a cikin wannan hali tun daga nesa sai jikinta yayi sanyi
Al amin Ahmed Misau Nake Guyson Ko A square
zuciyarta ta karaya kawai sai ta yarda bakan dake
hannunta ta falfala da gudu izuwa gareshi tana
isa gabansa sai ta kura masa idanu koda taga
idanunsa a kafe suke ko kiftawa basa yi kuma babu
inda yake motsi daga cikin gabobin jikinsa sai ta
fada kansa ta rungumeshi tana mai tsandara uban
ihu sannan kuma ta fashe da kuka
koda ganin abin da
ya faru sai nima na rugo da gudu ina dogara sandata
ina isowa na warbar da wannan zaki na kafadata
kuma nayi jifa da sandata da mashin da barewar
ke tsire akai
kawai sai na tsugunna kasa bisa guiwoyina na fara
kuka aka rasa
wanda zai rarrashi wani tsakanina da zalin
nikaina Al amin Na tausaya musu gaskiya
da wannan gagarumin rashin mahaifin ta da sukayi
sai da muka shafe kusan sa a guda muna kuka sannan na
mike tsaye naje na kama kafadar zalina na
tasheta tsaye na shiga rarrashinat, sai da ta dawo cikin
hayyacinta sannan muka fara shirye shiryen
binne gawar mahaifin nata, tun daga wannan rana
muka bar wannan daji ba tare da fatan komawa cikinsa
ba
ko don ziyara ga kabarin mahaifin nata wanda ke cikin
wannan kogon dutse
haka dai mukaci gaba da tafiya a cikin daji mu
kwana nan mu tashi can ba tare da sanin inda muka
dosa ba muna neman inda yake da ni ima mu zauna
muci gaba da rayuwarmu, sai da muka shafe watanni
shida cur muna tafiya sannan muka iso wani daji dake
cikin nan kasarka ta Askandariyya, A nan ne muka zauna
muka ci gaba da rayuwa nida matata zalina inda
muka gina wata yar bukka a gefen wani tsauni
inda muke kwana har ma muka kafa wani garken dabbobin
gida muna kiwo bamu da wata sana a face farauta
kuma mu kan kai fatun dabbobi cikin birnika mu siyar

mu siyo abin da muke bukata da silallan da muka
sayar da fatan dabbobin dajin sannan mu dawo
dajin da muke da zama ba tare da mun taba sha awar
yin rayuwa ba a cikin gari har muka samu rabon
haihuwar Yata SIYAMA
tun siyama tana da shekara biyar a duniya na fara bata
horon yaki har ta cika shekara tara kuma duk irin horon da za a baiwa
babban mutum shi nake bata
hakika siyama tasha bakar wahala sosai a wajen
horon yaki kamar zata rasa ranta kuma sau tari sai
uwarta tayi ta
kuka idan taga tana shan wahalar taji kamar ta
hanani bata horon amma idan ta tuno da irin
kisan gillar da sarki shardas yayiwa kabilarsu da
zuri arsu da tawa sai ta hakura, haka dai siyama taci
gaba da koyon yaki har ya zamana cewa nima
ta fini jarumtaka juriya da naci, a bangaren iya farauta kuwa
ni kaina sai da na cika da mamaki bisa ganin irin
abubuwan al ajabin da take yi a daji da kuma irin
kwarewar da ta samu ta iya harbin kibiya fiye
da mahaifiyarta
bamuyi shawarar sanya siyama a cikin gasar jarumtaka
ba don komai sai saboda mu jarraba karfin
damtsenta da kuma iyakar jarumtakarta kuma
burinmu shine taci gaba da baiwa kanta horo gami da
tanadin daukar fansa akan sarki shardas, ina mai tabbatar
maka da cewa
yanzu haka ko sunan sarki shardas siyama taji
an ambata sai zuciyarta ta kama tafarfasa kamar zata
kone saboda irin kiyayyar da muka cusa mata
kuma a kullum bata da burin da yafi na mu kyaleta
ta tafi zuwa birnin shardas ita kadai ta shiga har
cikin fadarsa ta kashe shi amma na gaya mata cewa
ba zata taba samun nasara ba a kansa a yanzu face
idan ta mallaki wata Hula da ake kira HULAR LAMSARA
koda Hailur yazo nan a labarinsa sai idanun sarki
hulbasu
suka zazzari ya kamu da tsananin tsoro gami da
mamaki saboda rabonsa da yaji an ambashi sunan
wannan hula ta LAMSARA tun yana yaro karami sai kuma
yanzu da yaji a bakin hailur, tabbas ya sami labarin
hular lamsara a wajan kakansa wato wanda ya haifi ubansa amma bai kara jin
labarinta ba kawo i yanzu

sai da sarki Hulbasu ya baza fatake jarumai da
mayaka izuwa sassan duniya domin su nemo
masa wannan hula ta lamsara amma ba a samu wanda ya jiyo labarin inda
hular take bama
sarki hulbasu yayi gyaran murya sannan ya dubi
hailur a natse yace hakika jikina ya bani cewa lallai
akwai wani babban sirri a tsakanin shardila matar sarki shardas
kuma ina mai tabbatar maka da cewa idan sarki shardas ya gano cewa kana nan
a raye kuma anan cikin yankin kasata tobama kai ba
ko iyalinka hatta nida kaina bz an zauna lafiya ba
don zai iya zuwa ya yakeni ya kawai da mulkina
koda jin haka sai hailur ya dubi sarki Hulbasu yace
yakai wannan sarki mai Karamci me yasa ka taimakeni
Alhalin ka san cewa yin hakan hadarine ga rayuwarka
da mulkinka
koda jin haka sai sarki hulbasu yayi gyaran murya
gami da ajiyar zuciya sannan yace A rayuwata
babu abinda na tsana sama da zalunci kuma mahaifina
kafin ya gushe ya bar mini wasiyya akan cewa
idan har ina son nayi nisan kwana akan karagar mulina to
dole ne
Na guji aikata zalunci ga talakawa na dama duk
wadanda suke karkashina ko kasa dani kuma na
kwatanta adalci a tsakaninsu gwargwadon iyawata
ina so ka sani cewa har yanzu sarki shardas bai san
komai ba dangane da wanzuwarka ko baiyanarka a cikin aksata kuma
dolene kaci gaba da boye kanka har izuwa lokacin da
zaka iya fuskantarsa, duk da cewa yanzu kaga matarka
shadila da kuma danka yarima Hulkasa
amma dole ne ka hakura da mallakarsu har sai nan
da zuwa lokacin da ya dace, idan ba haka ba kuwa zaka
rasa su ne gaba daya kuma kai kanka ma zaka rasa kanka
ba zan hanaka ka gana da shadila ba amma kada ku
kuskura ku bari wannan yaro hulkas ya san cewa
kaine mahaifinsa kuma kada ku bari ya san duk abinda
ya faru a baya
hakan ba zai haifar muku da komai ba face rugujewar dukkanin burikanmu
gaba daya da kuma salwantar rayukanmu
yayinda sarki Hulbasu yazo nan a zancensa sai hankalin
hailur ya dugunzuma ainun fiye da ko yaushe har hawaye ya zubo masa kuma
zuciyarsa ta kama tafarfasa kamar zata kone saboda
fishi
ya dubi sarki hulbasu yace yanzu kana nufin kace dani

inaji ina gani zan hakura da matata wadda aka
rabani da ita a daren angwancinmu da ita na farko kuma na hakura da
dana wanda tun yana ciki bai san cewa nine ubansa ba
gashi har ya cika shekara bakwai a duniya, ka sani cewa har kwnaan gobe zuciyata bata
bayar da soyayyarta ta gaskiya ba ga kowa face shadila
ina son shadila fiye da yadda nake son kaina
Al amin ahmed Misau Nake Shin tayaya kake tunanin
zan
yarda ta sake kubuce min a karo na biyu al halin ban taba
zaton cewa zamu sake hadu wa ba a cikin wannan
duniya
koda hailur ya zo nana a zancensa sai hawaye ya zubowa
sarki Hulbasu al amarin da yai matukar girgiza
hailur kenan kuma yai matukar bashi mamaki
ya dubeshi yace yakai abokina inda dalikin zubar
wannan hawaye naka mai tsada koda jin wannan
tambaya sai sarki hulbasu yaja dogon numfashi
sannan ya sa hannu ya goge hawayansa ya dubi
hailur cikin alamun karayar zuciya yace yakai abokina
kayi mini tambayar da ta fama min tsohon ciwon dake cikin
zuciyata ne kuma shine asalinsanadin da yaja
mummunar kiyayya tsakanina da sarki shardas inaso
ka sani cewa duk irin kiyayyar dakake yiwa sarki
shardas bata kai koda rabin wacce nake yi masa ba
domin duk ladabin da nake yi masa a yanzu na
dole ne saboda yafi karfina kuma bana son abinda zai
taba kasata da jama'ata, ka sani cewa bakincikin
sarki shardas ne ya kashe mahaifina kuma sarki
shardas ne sanadin dana rasa dana na fari YARIMA
HUZEIN
Cikin alamun tsananin mamaki da kaduwa hailur ya
dubi sarki hulbasu yace tayaya mahaifinka da danka
huzein suka gushe
koda jin wannan tambaya sai hawaye ya sake zubowa
sarki hulbasu ya dubi hailur cikin nutsuwa yace
yakai abokina ka saurari labarin da zan baka yanzu
dukkanin amsar tambayar da kayi min yanzu tana
cikinsa......
.
JARUMA SIYAMA DA MAHAIFINTA HAILUR SUNA CIKA
BURINSU NA DAUKAR FANSA AKAN SARKI SHARDAS ?.
.
MAI ZAI FARU IDAN SARKI HULBASU YA GAMA BAIWA HAILUR

LABARIN MUTUWAR DANSA DA MAHAIFINSA ?
.
A WANNE HALI SHADILA TAKE CIKI BAYAN TAYI ARBA DA TSOHON MIJINTA HAILUR ?
.
YAUSHE YARIMA HULKAS ZAI SAN CEWA HAILUR SHINE
MAHAIFINSA NA GASKIYA
.
Marubucin littafin Wato Abdul aziz sani M/ Gini yace
mu hadu a Littafin Tsatsuba na (6) Don jin
cigaban wannan kayataccen kasaitaccen labari
mai dumbin darasi fadakarwa da nishadantarwa
Mai debe muku kewa a kullum da ko yaushe.
Suleiman Zidane Kd 09064179602:

1
2
3

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login