Showing 6001 words to 9000 words out of 17169 words

Chapter 3 - KAWAICI Book Free Pages By Zahra Royal Star.txt

Advertisement

kin san babu yadda za'ai idan har bai ɗaukar mata kuɗi ta ce shine ko?, ai kinfi kowa sanin dai halinsa ne dama a aje ya ɗauka".

"To faɗi ba'a tabbayeki ba d.....

Ismail ne ya katseta da cewa.

"Na rantse da rabbil samawati Inna idan ban ɓarar da wata mata a yau ace shege nake, kar nayi abu azo ana wallahi tallahi".

"Kai dalla can gafara nan, harka isa wuyanka ya isa yanka kace wai zaka ɓarar dani, tsabar dama ku ƴan ɗakinku a lokacin da ake raba tarbiyya ma bacci kuke, saboda baku da rabo a duniya, to Bismillah baga ni ba?, zo ka ɓarar dani ɗin naga ƙarewa rashin kunya a wajanka".

Asiya ce ta ɗaga labule ta fito tana fitowa ta wani nuna Isma'il da yatsa tana faɗin.

"Kul wallahi ahir ɗinka ka taɓa min uwa, nanfa ɗaya".

Amina ce ta shigo gidan tana riƙe da wata baƙar leda cike da mamakin sha'anin gidan nasu da basa gajiya da rigima da gutsiri tsoma ta ce.

"Wai dan Allah Umma wai ku baku gajiya da magana ne?, mu kenan kullum makwafta ke ji ana surutun gidan nan, sai kace a gidan nan Shaiɗan ke zaune haba".

Hindatu ce tayi sallama itama taci uban wanka, idan ka kalleta saika rantse da Allah ƴar gidan wani shugaban ƙasa ce, riƙe take da wata faskekiyar waya a hannunta sai wata Jaka dake hannunta, ganin Isma'il a gidan yau yasa ta ƙara damƙe wayarta da Jakarta, danta sanshi, a ɓangaren sata dai shine lamba ɗaya, sadda zai yashe ka ma baka sani ba.

"Miye kuma yake faruwa a nan?".

Ta faɗa tana ƙarasa shigowa.

Ismail tsabar ɓaci rai waje zai nufa domin ficewa daga gidan dama abunda ya kawosa kenan ya samu baida ko sisi, shine wannan ƴar iskar yarinyar take son kunno masa ruwa.

Shan gabansa Falmata ta sake yi bata daddara ba, jikinta na rawar tsoro, ganin yadda ya ware ido yana sake dubanta da mamaki.

Riƙe baki yayi bai san lokacin daya ɗaga hannu ya yarɓar da ita ƙasa ba, sai gata rashe-rashe a ƙasa yasa ƙafa ya haurar mata ruwan ciki, yana ɗan ƙara mata wani uban zagi, ya kuma tsallaketa wuce ya barta da sakin ihu.

Mama ce ta fito ita ɗaya danta hana Shamsiyya fitowa kwata-kwata, Shamsiyya harda matse hawaye an hanata fita ana kuma cin zalin Aunty Falmata.

Nunata da yatsa Mama tayi cike da kakkausar murya ta ce.

"Dan ubanki zo ki wuce ɗaki, yau dai karna ƙara ganinki a tsakar gidan nan, idan ba haka ba wallahi ranki idan yayi dubu saina ɓata miki shi".

"Wai minene yake faruwa ne kunmin shiru?"

Hindatu ta ƙara faɗa.

"Yo mifa yake faruwa kuɗinta ya ɗauka mana, shine ta tsareshi sai ya biyata su".

Umma ta faɗa tana nuna hanyar waje.

Inna zatai magana domin ta gaji da irin shigar sauri da Ummar ke mata akan lamarin ƴaƴanta.

Hindatu ta rigata cewa.

"To ai da alama ya ɗaukar mata ne, ke tashi Falmata ga ɗari biyar nan, kin riga kin san dai tunda ya ɗauka ba dawo da ita zaiyi ba, koda gidan nan zai tashi dan bala'i".

Ta ƙare maganar tana fiddo ɗari biyar zata miƙama Falmata, ai ko Inna tayi tsalle ta ɗari ta wafce ɗari biyar ɗin tana nuna Hindatu da yatsa ta ce.

"To sannu na ce marar kishin ɗan uwanta, ai wallahi ita da kuɗin nan har abada sun tafi, wannan ma ai tozarci ne da rashin kunya ta tari gabansa tana wani cewa ya bata kuɗin daya satar mata, ai ana barin halak kodan kunya, tunda a girme ya bata shekaru masu yawa, duk bata duba wannan ba".

"Wuce nace".

Mama ta faɗa domin tsayuwar jin maganganun Inna da saurin jama'ar wajan ya fara hawa kan Mamar, tana da hakurii amma aka kaita ƙarshe tofa bata iya magana mai daɗi ba itama, domin idan ta ce zata tanka to kuwa za'a ci gaba da faɗan nan ƙila har sai mai gidan ya dawo a kuma ɗora da wani, tunda dama basa jin maganar mai gidan ba kuma tsoronsa suke ji ba.

Tashi Falmata tayi tana gunguni haɗe da ɓata fuska tana jin wani irin ɗaci a zuciyarta, sosai taci alwashin Ya Ismail ɗin yau saiya bata kuɗinta, tunda ai ba nashi bane, kuma lokacin da tasha wahalar samo su ai baya ma gidan, bai san yadda akai ta samo kuɗin ba, kawai ya gansu daga sama ne ya ɗauka.

"Haba Inna amma dai kin san Ya Ismail yana ɗaukar abu idan har an aje ya gansa, bare ma wadda zai saida ko ya sami kuɗi ko?, hatta kayanki ba bari yayi bafaa".

"Ke dalla shashasha gama kwance mana zani a kasuwa nace kinji?, kuna ɗaki ɗaya amma kike jefansa da irin wannan lafazi a gaban maƙiya da mahassada".

Juyowa kawai Hindatu tayi tana cire gyalen dake kanta ta shige ɗakin nasu tana sake jin Inna na faɗin.

"Ban taɓa ganin wacce bata kashin ƴan uwantaa irinki ba Hindatu, yanzu da Zahariyyar ce ko Ma'u da yanzu sun shige masa gaba wajan kwato masa ƴancinsa".

"Su ai da yake basa son gaskiya ba".

"Hansatu wallahi ki kiyayi shiga abunda bai shafe ki ba".

Inna ta faɗa tana nuna Umma da hannu.

Wani guntun tsaki Amina ta saki tana janye Umma daga wajan suka shige ɗaki.

Sai Asiya dake tsaye a wajan, samun dakalin ƙofar ɗakinsu tayi ta zauna tana wake-wakenta, Inna kuma ta saki tsaki itama tana yin hanyar kitchen ɗinsu.

"Wallahi nasu yayi miki dukan da zaki kasa moruwa yau".

Faɗin Mama tana kallon Falmata dake zaune ƙasa tana share hawayen baƙin cikin bata ci nasara ba.

Mama cike da ɓacin rai ta sake cewa.

"Bazaki taɓa sauya hali ba Falmata, ina gudar miki wata rana ki tsinci kanki a inda wannan rashin haƙurin naki zai iya janyo miki wata masifar wallahi ki sauya tun kan waje ya ƙure miki".

"Mama dan Allah ki daina mata wannan fatan, Mama kinga fa suma suna da laifi gidan nan, sai idan anyi abu kaɗan kiga sun tarar maka, dama kamar jiranmu suke".

"To koda da laifinsu ai nata yanzu yafi yawa, mi yasa da taga babu kuɗin a inda ta aje ba tayi hakuri tabarsu ba?".

"Toni Mama bada idona na gansa yana ƙoƙarin zurata a aljihunsa ba, nafa ganta a hannunsa wallahi".

"Ni rufe min baki, ke baki san idan baka iya kama ɓarowa ba shi sai ya kamaka ba?, ke da yake shashasha ce ke haka aka gaya miki ana yi ne?, kawai ki tari mutum wai bani kuɗin daka ɗauka, tsabar baki da hankali da tunani?, wallahi ki kiyayi kanki fa, ke kenan kullum cikin sani magana kike da ɓaɓatu?, Allah yau dai na sake ganinki a tsakar gidan can Allah saina ɓata miki rai".

"To Mama idan zanje Ban ɗaki fa".

"Sai dai kiyisa a wando koma miye, naga ta tsiya wajanki yau, idan ba alwala zaki je kiyo ba ko wani abun mai mahimmanci baki ƙara fita wallahi, tunda ke kin zama kamar wakiliyar Shaiɗan........

*KAWAICI*


*©Zahra Royal Star*


*ROYAL STAR WRITER'S ASSO.......*


PAGE 5


*Sabuwar Abuja Kankia LGA, Katsina state Nigeria*


A nutse ta fito kamar wata mutuniyar kirki tana taku ɗaya baya ɗaya, kallon inda Amna take tayi tana wani taɓe baki kallon takalmin data aje tun ɗazu tayi, cike da mamaki take duban takalmin,
kamin ta juyo da wani irin fushi akan fuskarta tazo inda Amna take zaune tana ƴan surutanta.

"Kan uba, wai ke mi kika taka ne yau iye?".

Shiru Amna tayi dan ko ɗaga kai batai ba bare ta tanka mata, hasalima kamar bata ga kowa a inda take ba, tayi kunnan uwar shegu da ita.

"Waike ba dake nake ba ne?".

Nanma shiru tayi tana sake duban wani wajan daban, kallonta sosai Siya keyi da mamakin rainin wayo irin na Amnar data tashi dashi yau ɗin.

Hannunta tasa tana dungure mata kai tana cewa.

"Ke dalla can banza dai-daifa nake dake wallahi, nafiki iya wulakanci idanma shine kike ji yau, wai ba tun ɗazu na ce miki ga takalman da zan fita dasu bane ki goge min su iye?".

"Sai kuma aka ce miki ni baiwarki ce ko kuma ƴar aikin da kika aje ce?".

"Ni kike gaya ma haka?".

"Na faɗa ki ɗauki mataki".

"Waike mi kika taka ne yau?, naga sai wani cika kike kina batsewa dalla Mlm".

"Abunda kike ji shi nake ji Siya".
Ta faɗa tana miƙewa daga inda take, da wani irin sauri Siya tasa hannunta ta jawo Amna baya, har Amna na shirin kifewa ƙasa da sauri ta tsaya da ƙafafunta tana sake kallon Siya da mamaki itama, kamar yadda Siya ɗin ke kallonta itama da mamakin rashin kunyar da take mata a yau ɗin.

"Ke mike faruwa a nan?".

Umma ta faɗa bayan ta fito daga Part nata tana dubansu gaba ɗaya, ganin Amna na cika tana wani hura hanci yasa Umma nunata da yatsa tana faɗin.

"Hala keda wannan marar kunyar?".

"Waifa Umma ce mata nayi ta goge min takalmin da zan fita dashi yanzu, shine take gaggaya min magana harda su zagina".

"Ahh gaskiya ne Amna wuyanki harya isa yanka wato?, a girme ai Siya ta girme ki nake ganin ko?, tsabar baki da kunya ta saki abu kiƙi mata".

Wani kalar kallo Amna ke jifan Umma dashi tana mamakin wai Siya ta girme ta?, a ina ta girme matan?, duka bai wuce koda tama girme ta bai wuce na watanni, ƙilama bata bata watannin ba, tunda kusan shekarunsu ɗaya.

"Ke ni daina kallona da idonki masu kama dana mayu, kina kallona da idonki na rashin kunya, ko nima rashin kunyar zaki min ne?".

Amna bata ce komai ba, saima ƙoƙarin wucewa da take yi, da sauri Siya ta taɓe baki tana cewa.

"Umma kice ta goge min".

"Keee Amna dawo nan".

Umma ta faɗa tana nunama Amna inda take tsaye.

Dawowa da baya kaɗan tayi tana tsayawa ta harɗe hannunta a ƙirjinta tana duban Umma.

"Duƙa yanzu ki goge mata su na ce".

Murmurshi kaɗan Amna ta saki tana wani basarwa ta ɗauki lokaci batai magana ba, har sai da Umma ta sake cewa.

"Ko baza kiyi bane?, nima rashin kunyar zaki nuna min?".

"Zan goge mana Umma, amma ta sani idan har nina goge mata takalmin nan tasa ta fita to duk abunda ya faru da ita, itace tajama kanta da kanta, kar a sake ayi kuka dani".

"Kin daɗe baki yi duk abinda zakiyi ba, shegiyar yarinya sai mugun fatan tsiya, anya baki da Shaiɗani a saman kanki kuwa Amna?".

Umma ta faɗa tana tafa hannuwanta.

Amna zata sake magana Ummi ta fito daga Toilet ɗin tsakar gidan nasu, tun ɗazu take sauri ta fito gudun kar Amna tayi wata maganar da zai jaza masu wata maganar daban a ƙara fassarata.

"Ke wai bance karna sake ji kina irin wannan maganganun naki marassa kan gado ba?, idan har ba fatan arziƙi zakiyi ma mutum ba, to kul ɗinki ki ƙara faɗin mugun abu akan waninki na gaya miki, maza duƙa ki goge mata takalmin".

Turo baki tayi tana jin haushi sosai tana kallon Siya da wani mugun kallo ta ɗuka ƙasa ta goge mata takalmin tana gamawa ta tura mata su a gabanta tana miƙewa ta shige ɗakinsu kamar zata tashi sama...


*MA'U POV*

"Gaskiya bana yin ƙunshin sama dana dubu biyar".

Ma'u ta faɗa tana duban matar data kwaso ƴaƴanta wai za'a masu ƙushi.

"Haba baiwar Allah ki taimaka kiyi masu na dubu biyu-biyu dan Allah".

Wani kallon uku saura kwata Ma'u tayima matar tana cewa.

"Nifa baiwar Allah banma yima ƙananun Yara ƙunshi gaskiya".

"Taimakawa zakiyi dai".

"Haba ke kam Aunty Ma'u ki daure kiyi masu man".

"Mtsww to na sako kine ciki ke kuma?, kizo kiyi masu mana idan abun yinsa mai sauƙi ne".

Ta faɗa tana hararar Shamsiyya datai mata magana fitowarta ɗaki kenan ta tsinci maganar da matar keyi da magiyar da take ma Ma'un.

"Hmm Allah ya baki hakuri daga magana Aunty Ma'u?".

"To bana son shishshigi ai kin sani a cikin sana'ata".

"Ke kuma baccin neman magana ina ruwanki da ita, jeki kiyi abunda ke gabanki, ai ita ce zatayi ma kanta, wata rana zata nemi masu zuwanma ta rasa, mudun mutum shi ɗan wulaƙanci ne".

"To da uban waye kike Falmata?".

Ma'u ta faɗa tana nuna Falmata dake zancan.

Taɓe baki Falmata tayi tana ma Ma'u kallon banza ta saki wani tsaki tana cewa.

"To Aunty Ma'u ai gaskiya na faɗa, ya kamata ki rinƙa sassauta ma masu son ƙunshinki bare ma ƴan unguwar nan".

"To dole ne na ce sai wani yazo a unguwar nan ne?, dama ni ƴan gayu masu naira nake ma ƙunshina, dama ina ni ina wahalar da kaina akan yima ƴan unguwar nan ƙunshi?, ai wahalar da kaine, ga inda zaka yi ƙunshi a ɗauki naira dubu Hamsin a baka ko dubu ɗari, ai nan ya kamata ka saki jiki kayi".

"Ai shikenan a juri zuwa rafi dai".

Falmata ta faɗa tana juyowa ta koma ɗakinsu, tana jawo hannun Shamsiyya dan idan suka ce zasu tsaya to abun zai zama rigima ne.
Matar dai tana tsaye bata ƙara cewa komai ba.

Sai da Ma'u ta daɗe bata ce komai ba, kamin zatai magana wata hamshaƙiyar Mata tayo sallama.

"A'a a'a Teemah kune tafe a gidanmu? lale-lale"

"Ai ko dai wallahi Oga ne zai dawo jibi shine fa na ce bari nazo wajanki ƙunshi, domin a cikin masu ƙunshi ma ke ɗin daban ce, shi yasa tun daga unguwar mu na tako har nan".

"Ai ko kinzo a dai-dai Teemah ai kawai zama zakiyi mu fara, zan kuwa ɗanɗasa miki mai shegen kyau, ta yadda Oga zai yaba wata ƙilama ya bani kyautar ƙunshin dana tsarama Madam ɗinsa".

Dariya suka sake a tare, kwata-kwata Ma'u tama manta da ƴaƴan matar dake zaune sai Matar dake tsaye har lokacin tana kallon ikon Allah, yanzu dai rayuwar nan mai kuɗi kawai ake ganin darajarsa.

"Na ce ƴaƴan nan zasu samu ƙunshin nan Ma'u?".

Kallonta ta ɗanyi kamin ta ce.

"Zasu samu man, amma sai sun ɗan jira, idan aka gama zasu taho".

Amsawa tayi da to, tana miƙa mata dubu biyar kuɗin ƙunsin yaran.

Amsar kuɗin tayi kamar ta amshi kashi tana taɓe baki Matar bata ce komai ba ya juya tana ma yaran magana kamin ta fice daga gidan.

"Ni ko Ma'u yaushe kika fara ma Yara ƙunshi ne?, ni dai a sanina ai bakiyi ma yara ƙunshi".

"Hmm kedai bari Teemah yau ɗin ma danta tsareni da magiya ne shi yasa zan masu, amma bana Yara har yanzu".

Wajan zama ta bata tana zama dandanan aka fara mata ƙunshi mai kyan gaske tana yi tana santin ƙunshin, idan Ma'u ta zana ƙunshi kamar wacce Aljanu kema wahayi da iya ƙunshi, yadda kasan ba mutum ke zana shi ba.

Sai da ta gamama Teemah harta wanke zata tafi ta gwangwajeta da Naira dubu talatin kash an kari, ai ko har ƙofar gida ta rakota suna dariya da shewa, domin ba ƙaramin daɗi Teemar taji ba da ganin yadda kullum Ma'u ke sake kwarewa ta fannin ƙunshi.

Yaran tana dawowa ta zauna tayi masu, taso tayi masu dai-dai marar kyau kuma, amma sai dai bazata iya ba, mai ɗan karen kyau tayi masu wadda baida yawa sosai, amma yayi masifar kyau, su kansu Yaran sai murmurshi suke suna kallon ƙunshin nasu, koda uwar tazo ɗaukarsu itama tayi mamakin ƙunshin, taita godiya kamar zata ari baki, sai cewa take.

"Gaskiya Ma'u dole kice baki ƙunshi sama dana dubu biyar, ai Allah ya baki baiwar iya ƙunshi gaskiya".

Ma'u dai bata ce komai har matar ta kama yaran nata suka fice bayan ta gama santin ƙunshin.......

*KAWAICI*


*©Zahra Royal Star*


*ROYAL STAR WRITER'S ASSO.......*


PAGE 6


*ASIYA POV*


A hankali ta gyara tsayuwarta tana dubansa kamin ta ɗan ɗaga masa hannu tana masa wani kallon uku saura kwata.

"Kai kaga bawan Allah duk naji da abunda kazo dashi, amma banda buƙatar soyayya da irinku ni yanzu, dan haka sai anjima Mlm".

"Haba dai Asiya ai ya kamata ki amsheni hannu biyu-biyu, saboda babu mai ƙarfin halin zuwa wannan gidan naku da baida maraba da gidan kazo nazo, waye zai iya auranku idan ba irinmu ɗin ba?".

Bata san lokacin data ja birki tana yuyowa ta dawo baya ba, wani kalar kallo take masa na tsantsar takaici tana nunasa da yatsa ta ce.

"Ya isheka haka Mlm, bazaka zo har ƙofar gidan nan ba ka ce zaka ci ma gidanmu mutumci na kyaleka ka tafi a salin alin ba, dan haka tun kan wani yaji cikin ƴan gidanmu kama gabanka ka ƙara gaba Mlm".

Wani haushi ne ya kamashi yana sake kallonta ya ce.

"Ai gaskiya na faɗa ko ƙarya nayi?, wane mai hankali da tunani ne zai zo neman auren ƴan gidanku?, idanma bazaki amshi soyayyata ba ai kece kikaima kanki wallahi, ni ai taimakon ki nayi".

"Zaka bar ƙofar gidan nan ne ko sai na ɗauki waya na kira Ya Shamsu yazo duk inda yake yayi min maganinka?".

Zaro ido waje yayi ya fara tafiya baya-baya yana faɗin.

"Wa ni?, ni ɗin banza ai tafiya zanyi mana, basai kin kira wannan mai kama da Fir'auna ba, ai kaji irinta nima tsautsayi yasa nazo gida irin wannan wai neman matar aure".

Har ya ɓace ma ganinta tana tsaye wajan takaici ya rufeta, da kyar ta iya ɗaga ƙafafunta tayi cikin gidan nasu.

Gidan cike yake damƙam da ƴan mata a zaune wasu ana masu ƙunshi, wasu kuma na gefen ɗakinsu Falmata tana masu ƙitso, saboda bukukuwan mutane da ake yawanyi a wannan watan da suke ciki, shi yasa gidan kullum yake cike.

Tsallake su tayi tana ji suna maganganunsu haɗe da gulmar Majensu wasu harda sakin shewa.

"Ai wallahi ƙawata nake gaya miki, ni Mijina shi ya kira ni ma ya bani kuɗin ƙunshin nan naira dubu ɗari gata nan, wai naje ƙunshi, ai ni mai gida na baya wasa da duk wani gayu nawa, kuɗi yake narka min na fitar hankali".

"Ah gaskiya ne Shuhuda kina baza Capacity a gidanki, yo ni ai ko sisinsa baya bani, ke ƙunshin ma ba so yake yi ba, da kyar ya barni na fito yau, amma bai san ma ƙunshi nazo ba, saina koma muyita ta ƙare, ai halin Maza wani lokacin sai su wallahi".

"Tabɗi jam ke kuwa Mmn Anam miya kaiki tahowa ba tare da sanin Miji ba?, ai kinyi kuskure nake ganin".

Ma'u ce ta amshe maganar da cewa.

"Ke bafa wani kuskure da tayi, haka kawai saita zauna a kaca-kaca ba gyara?, duk dan badanshi take yi ba?, ai da sauƙi ma tunda ba kuɗi ya bata ba, kuma ba ajewa yayi ta ɗauka ba, kuɗinta ne ta cire tazo dasu ƙunshin, nifa shi yasa bazan iya jure ciwon kan ɗa Namiji ba wallahi, ko zan aureka sai munyita da wajewa, bana son

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login