Showing 3001 words to 6000 words out of 46005 words

Chapter 2 - SHIN SO DAYA NE BOOK COMPLETE BY HAFSAT ALMUSTAPHA.doc

14 Sep 2025

2406

ce ta rad'a min magana akunne,cewa tayi"Ki shiga da kafar damarki tare da bismillah,haka kuma xakiyi idan aka maidaki can gidanki.... "



Daga mata kai nayi alamar naji jawabin nata,daga haka naji wasu mata su wurin uku suma sun rungumeni kamar zasu kada ni akasa suna min sannu da xuwa har muka shige gidan.



Wani daki aka saukemu aciki wanda muka ji wani daddad'ar kamshin turaren wuta ya mana maraba da xuwa,gaskia ba laifi suma kanawa akwai son kamshi.Maganar gaskia ba k'aramin karramamu akai ba,nima sae naji na d'an saki jikina amma har xuwa wannan lokacin ban yaye mayafin kaina ba,ina nan lullub'e aciki kamar wata munafuka,lokaci xuwa lokaci nake dago kai na d'an saci kallon mutane.



Cikin k'ank'anin lokaci muka ga an cika mana gaba da kayan ciye-ciye da shaye-shaye.Mama Sadiya ne suka dan taba amma babu yadda basuyi dani ba amma naki ci.Ce musu nayi ak'oshe nake.Ak'arshe dai ruwa kawai na d'an sha.



Mama Jamila ce tace"Yarinya idan zaki mah saki jiki toh tun wuri ki saki don anan zamu barki,gobe idan Allah ya kaimu komawa gida abinmu xamuyi..."



Juyawa tayi ga Mama Sadiya tace"Sadiya hanzarta ki gama cin abincin ki min rakiya xuwa gidan wata k'awata dake nan jambulo,bazamu jima ba..... "



"Toh Addah... "acewar Mama Sadiya don Mama Jamila na gaba da ita.



Ni kuwa wani sabbin hawaye naji sun ziraro min saman k'unci,tayaya xan soma rayuwa agidan wasu bayan na sab'a da namu?taya mah xan soma had'a shimfid'a daya da wani k'aton gardi amatsayin mijina?



Yaye min mayafi naji anyi ana fad'in"Ai kya bari muga fuskartaki muga ko kin fini kyau koh? "



Ji nayi an fashe da dariya,ni kuwa gabana ne naji ya yanke ya fad'i,dakyar na iya d'ago kai ina duban wacce ta yaye min mayafina,ido hudu nayi da wata tsohuwa wacce kana ganinta kasan ta dad'e ana cin sallar idi da ita.Sae dai ba'a wani gane tsufanta don jikinta meh k'yau ne.



Tace"Masha Allah!.. Ashe dai megidan nawa balarabiya ya zab'o mana shiyasa yake ta rawar kafa da dokin auranta..... "



Aka sake fashewa da dariya akaro na biyu,ni kuwa d'an murmushin leb'en baki ne kawai ya sub'uce min,atake anan na gane cewar wannan tsohuwar kakarsu ce.



Tace"Amarya share hawayenki,don ni dake xamuyi zaman lafiya idan da hakan kika zo,idan kuwa da akasinta kika zo,toh nima nan uwargida ashirye nake...... "



wasu 'yan mata ne naji sunce"sae kakus! Kakaaa rigima.... " aka fashe da dariya.



Haka dai tayi ta mana barkwanci da wasannin wanda atake anan naji kawai tsohuwar ta shiga raina.Su Mama Jamila kuwa suna gama ciye-ciyensu suka sa kai suka fice xuwa unguwar da suka ce xasu,muka rage daga ni,Ash,Zuwairah sae kuma Anty Hajaar wacce ga dukkan alamu jininta ya hadu dana Kaka rigima,don sae hira suke ta xubawa.



Ba'a wani jima ba muka ji an soma k'iraye-kirayen sallar magrib,daya bayan daya muke shiga bandaki muna dauro alwala.



***

Itama Suhaima anata b'angaren an musu tarban mutunci,sosae aka karramasu.Reedah itace wacce ta soma rungumota,ta rad'a mata magana akunne"Oyoyo sahibata,barka da xuwa,yau Allah ya cika muku burinku ta mallakar junanku,Suhaima dear welcome home as matar yayanah...... "



Ita kuwa Suhaimar murmushi kawai tayi abinta tana meh jin wani irin farin ciki mara misaltuwa na ratsa xuciyarta.



Leedar da Engr. bazan iya kamanta muku irin tsananin farin cikin da suka tsinci kansu aciki ba na ganin ayau sun mallaki 'the women of their dreams'.Bama kamar Mahmood wanda jinsa yake kamar Zaynab d'insa ce ta dawo.



***

"Anty Fadima inji Yaya Mahmood wai na kawo miki wa'ennan kayan ki saka wai xuwa qarfe takwas za'a taho ah daukeku xuwa reception...... "



Hafeezah 'yar baba Mu'azzam ne ke yiwa Fadima wannan maganar wacce take kusan sa'ar su Suhaima.



Kokarin magana nake sae naji Ash ta rigani,cewa tayi"K'anwata zubasu saman gado yanzu xata shirya kinji? "



"Toh.. " kawai tace sannan ta zubasu saman gadon dakin ta fice.



Ina gama ganin ficewarta na dubi inda Ash ke xaune nace"Sannu sarkin felek'e da iyayi,ina fatar da kika amshi wannan kayan ke zaki sakasu kuma ki bisu donni yadda kika ganni nan babu inda zani.... "



Zuwairah ce tayi saurin taran numfashina"Haba babe ya kike neman kwafsa mana ne?"



"Ke dai Zuzu banni da ita da meyi take yi,yanzun nan kuwa xamu hau sama mu fad'o don bazan tab'a bata goyon baya wajen wulaqanta sirikai ba..... "



"Toya isheki hakanan tunda de ba surukan naki bane,don haka babu ruwanki idan mah zaginsu nayi.... " acewata.



Ita kuwa Ash cewa tayi"Wallahi hadaki xanyi da Anty Hajaar ai kin san halinta sarai.... " tasa kai ta fice daga d'akin da nufin xuwa gun Anty Hajaar din wacce take dakin Kaka rigima suna shan fira.



Dama ashe taku ce tai wa Fadimar,babu kai kararta da xatayi gun Anty Hajaar,taku ce kawai tayi,nemo Hafeezah tayi tace mata"Don Allah k'anwata lambar yayan naki xaki ban,wayar amarya ta mutu balle akirashi da ita,ni kuma xancen gaskia bani da lambarsa.... "



Ta fad'a tare da mik'a mata wayar,murmushi kawai Hafeezah tayi tare da k'arban wayar ta latsa mata harufofin layinsa don tasanshi aka,lambarsa babu wuyar rik'ewa.



"Nagode my chuchu... " ta fad'a ah sa'ilin da Hafeezah ta mik'o mata wayar.



Babu b'ata lokaci ta sanya k'iransa,sae daya d'an jaah aji kafin ya d'aga.



"Hello!! pls who's on the line? " ya fad'a cike da k'asaitarsa.



Saukar da ajiyar xuciya Ash tayi,kana tace"It's the bride's best lady Aysha...... "



Tabbas ya ganeta! Sahibar matarsa ce,adakile yace"How may I help you? "



Tace"Gaskia fa kun mana laifi babba,meyasa ba'a fad'a mana cewar akwai reception agidan ango ba sae akurarren lokaci? "



Shi kansa yasan tabbas ko kadan basu k'yauta ba,kuma shi yama so afasa batun wata reception,amma kuma abokansa ne suka nace wai sae anyi don baza suyi asarar kudadensu ah iska ba sabida tun asali sune suka shirya masa wannan reception din.Sam be shirya fuskantar tashin hankali daga Fadima ba,amma kuma yaya ya iya? yasan kila Ash ta tsegunta mata zancensa don haka y xama dole yaje suyi ta ta k'are kowa ya huta,kuma yasan komin haukarta babu abinda xata iya yi don an riga an daurasu kuma igiyoyin auren ahannunsa take.Da wannan tunanin ya sami salama acikin xuciyarsa.



Ahankali yace"Pls we are very sorry tabbas munyi laifi babba amma agafarcemu..... "



Da sauri ta tari numfashinsa"Ni abar wannan xancen mah,yanxu gashi nayi nayi da ita ta tashi ta shirya amma fir tace bazata ko'ina ba,don haka sae kazo ka lallashi abarka ko kuma afasa..... "



Da sauri yace"Am on my way.... "

Ya fadi hakan da rawar murya tare da yanke call din.Dama acikin mota suke,suna kan hanyar xuwa daukarsu ne,abayansu wasu extra five cars ne ke biye dasu wanda za'a kwashi mutanen da keda ra'ayin xuwa agidan.



"Khaleed drive the car fast..... " acewarsa,ai kuwa kamar jira Khaleed yake abashi umarni,nan da nan kuwa sae gashi sun iso. Sai dirin motoci kakeji ah layin.



Ita kuwa Ash tana jin dirin motocin,da sauri tayi ciki,inda tabar Fadima hakanan kuma ta dawo ta sameta,wato lazimi take saman sallaya.



"Oya maza ki gyara ga ango nan shigowa,ke kuma Zuzu fito mu basu wuri.... "



Ta fadi hakan tare da janyo hannun Zuwairah suka bar dakin,Zuzu sae dariya take tana cewa"Kai Ash gaskia baki da dama,wato yanxu sae da kika kirashi shi yazo ya saka mata kayan kenan ko? "



Ash tace"Ai rabu da ita,dani take zancen,idan tasan wata ai bata san wata ba,dole gyad'a tayi mai,idan taki kuwa tasha matsa......... "



Ni kuwa binsu nayi da ido da baki bud'e kamar wata shashasha har suka fice,kafin na tsaya wani dogon tunani naji an doko sallama wanda nake tunanin babu tantama ango nawa ne.



Tuni gabana ya hau dukan uku-uku,rud'ewa nayi nama rasa abinda xanyi da kuma inda xan saka kaina. Mik'ewa tsaye nayi tare da gyara saman hijab dina wacce ta Anty Hajaar ce na ara.



Sae dana baiwa kofa baya sannan na k'arba masa sallamarsa,kai tsaye naji ya shigo yana furta"Amincin Allah da albarkarsa su tabbata agareki amaryar Mahmood..... "



Kunnuwana ne suka dauki kuwwar maganarsa,ji nake kamar na tab'a jin wannan muryar awani wuri,dakyar na danne wannan tunanin nawa tare da furta"Gareka kaima wanda ya yakice farin cikina har yaci nasara aka aura masa ni..... "



Ina gama fad'ar hakan naji wasu hawaye masu dumi sun ziraro min saman kunci har ina ji suna diga ak'asa.Shi kuwa sautin murmushinsa kawai naji,kana yace"Subhanallah! ah ina kika tab'a jin wani masoyi meh matuk'ar qaunar masoyiyarsa ya rabata da farin cikinta? A'ah sae de mah dada tsundumata cikinsa da zeyi..... "



K'ok'arin magana nake,sae kawai naji yayi saurin taran numfashina"Gimbiya pls safe the discussion for later,yanxu zuwa nayi na rokeki da pls ki rufamin asiri nasan sam bamu k'yauta muku da bamu sanar daku xancen reception da wuri ba sae akurarren lokaci,don Allah amaryata amana afuwa,ki taimaka ki rufa wa angon naki asiri ki halarci reception din nan,pls kada kisa naji k'unya agun abokaina don su suka shirya abin......... "



Afusace nace"Nasan tabbas an fad'a maka cewar bana jindadi,kuma yanxu ka nuna min cewar baka damu da rashin lafiyar matarka ba,ta k'unyar abokanka kake right? toh bari kaji,agaskia babu inda zani naje na kwaso sanyi abanza na janyowa kaina farawa daga square one ta rashin lafiyar ba......... "



"Fadima Zahra banfa sanki da Kafiya da taurin kai ba,haka kuma ban sanki da tsiwa da rashin kunya ba,infact ko bah kece da laifi ba,kina da saurin bada haquri,then why all diz all of a sudden changes? "



Gabana ne ya tsananta faduwar gaba,ah iya tsawon rayuwata nasan mutum d'aya ne ke gaya min wannan kalaman da bawan Allahn nan ya fad'a kuma shine *ENGR.MAHMOOD*.



Yana yawan cewa"Kai sister inlaw ni dai halayyarki sun mugun min,sam baki da hayaniya,baki da girman kai,komanki da sanyi kike yinsa,abinda yafi birgeni dake shine saurin bada haquri koda kuwa ba kece keda laifi ba.... "



For the very first time na samu kaina da son yin ido hudu da *Mijin Kaddarata* (another name for the novel).



Sannu ahankali na juyo da kaina xuwa gareshi.Fes! na sauke rinannun idanuwana akan fuskarsa.Hasken lanta din dakin ne ya bani damar k'arewa handsome face dinsa kallo.



Shock!startled!astonished!Amazed!.... and any other type of surprise mood u could think of,duk na shigesu alokaci daya ah sa'ilin da idanuwana da nashi suka gauraye cikin na juna.....



Kun san wah nake gani agabana??.......... ??Qd



A/N

Hahaha! amaryar Nakowa maida wuk'ar,duk mun riga da mun sani kece kurum aka bari cikin duhu,yanxu tambayar itace "Taya zamar auranku ze kasance? " mun fa k'osa mu gani.



*Hey! Hafnan's freaking fans! wai atunaninku family house za'a sauketa?? Haba its too early to start separating fight mana,atleast biko let dem enjoy their first night tukun Koya kukace? Lol



Pls ur comments & votes are getting down,I need like 100votes before I move on,lol juz kidding amma nasan inda zan kamaku ai.....!!



*IT'S YOUR LADY HAFNAN*??c

*??
cSHIN SO DAYA NE???c*



*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION*



*{Onward together}*

*{ we give the reader's of ours the best out of the best's,, our inks are melodious And dropping a kinda light's to reader's}*

'''THE PEN OF LOVE ???i HEART TOUCHING B??? TEARS OF SORROWS ???i CURDLES ???i GIGGLES ???i AND MARRIAGE THINK ???b'''

*JUST GIVE US FOLLOW.....*A???



*MALLAKAR:HAFSAT ALMUSTAPHA*



*WATPADD:HAFNANCY??c*



*IG:Hafsy___mustee*



A?"1jnA???



_*Jinjina gareku my slay queens,my surporters,I started diz novel kamar wasa,na fara first babi sae kuma na dakata naki cigabawa,wa'ennan qawayen nawa sune suka bani gwarin gwiwan cigabawa wanda har muka Kai inda muke ayau,gashi ayau na kammala littafin *SHIN SO DAYA NE?*tare da taimakon abokan arziki masu son cigabana,don haka gabaki daya wannan littafin na sadaukar dashi agareku my lovely squad*_



_**Ayusher Shafi'i???b*_

_**Zatifah,marubuciyar 'Neelam'*_

_**Nafisatouh unique???a*_

_**Sorphiyyerh Sorphie???a*_

_**Maryam 'yar fillo???b*_

_**Fatymerh Zahra??^*_

_**Queen deeyana??kd*_



_*Thank you all for your support,I love you all so very much irin sosan nan,am assuring you all dat ana mugun tare har abada juz lyk magnet da qarfeA??\Hq??*_



??c??c



*KASHI NA BIYU:RIKICIN K'ARSHE*



*??2\BABIN K'ARSHE??2\*



*??Ke??Ke??Ke??Ke??Ke???a*



Bayan Mahmood ya kammala waya da Momi,cike da tashin hankali ya dubi Fadima wacce tayi matashi da kanta asaman cinyarsa,itama hankalinta tashe ganin yanayin mijinta ya sauya ah sa'ilin da yake waya.



"Dear nah what happened? Wani ne ya mutu?" na fada cike da fargabar amsar da ze biyo baya.



Murmushin leb'en baki kawai yayi yace"Momi ce ta k'irani take fada min cewar Mubarak ya dawo don haka mu hanzarta xuwa kano yanxun nan kuwa,so Zahmood tashi muje ayita ta kare da zazzafin nama........"



Ya fadi hakan tare da mikar da kanta,ya tashi tsaye.Ni kuwa duk wani na'ura meh aiki ajikina ya tsaya cak!,alokaci daya naji duk wani kuzari dake jikina ya kau,idan ka kasa kunnuwa kuma kana iya jiyo yadda xuciyata ke bugawa da sauri da sauri non-stop.



Har ya kusa shiga dakinsa sae jikinsa ya bashi cewar bata biye dashi,da sauri ya waigo,tana nan de inda ya barta,sae binsa take da kallo,kwayar idanuwan nan nata dauke suke da tsantsar tashin hankali.Jikinsa ne yayi sanyi qalau,Sam baya son ganinsu cikin tashin hankali haka,amma kuma toya ya iya?dolene dama su fuskanceta koba jima koba dade,kuma insha Allahu daga yau za'ayi ta ta k'are don ba tsoron Mubarak din yake ba.



Sannu ahankali ya taka xuwa gareta,ya tsugunna tare da dafe gwiwowinta don zaune take saman kujera.



"Zahmood dear nah...... " ya fadi hakan cikin wani irin siga ta salon soyayya.



Ni kuwa kamar dama jira nake ya fadi hakan,sae kawai na rusa masa kuka meh daga hankali.beyi yunkurin hanata ba,seda tayi meh isarta don kanta tayi shiru ta koma 'yar shesshek'a.Can ya janyota ta fado jikinsa,ya lalubo lips dinta ya shiga tsotsarsa don kawai ya dan rage mata damuwar data shiga ciki.



Nima din biye masa nayi cuz I can't hold it back,bazan iya jurewa ba.saida yayi meh isarsa sannan ya cikani,ya riko hannuna tare da mik'ewa yana fadin"Oya let's go..... "



Kokarin magana nake sae naga yayi saurin sanya 'yar yatsarsa saman lips dina,yace"Shhhhhh! Zahmood don't say anything again,Idan har kina sona then ki taho mu tafi muje ayita ta kare yau...... "



Runtse idanuwa nayi ba tare da furta komai ba,banyi aune ba kawai naji ya kinkimeni yayi daki dani,shida kansa ya saka min kaya,don ada daga ni sae wata yar shimi da bone shot ce,shi kuwa threequarter da kuma singlet.ya dan shirya mana wasu kayan acikin wata 'yar karamar akwati wai zamuyi weekend gaba daya ne acan,dayake yau jumma'a ce.??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????Nide jinsa kawai nake da kuma binsa da kallo don gabaki daya hankalina baya jikina.Cikin kankanin lokaci muka kama hanya bayan na k'ira Umma nace mata mun tafi weekend kano,fatar alheri kawai ta mana.



***

_*A??!ANOA???*_



Mubeen da Usee,sae kuma Hanan ne kadai xaune afalo,sunyi shiru kamar wasu kurame,Hanan ce kurum ke 'yar shesshekarta.Daya da daya matan ke shigowa ahargitse cikin kuma tashin hankali,kowacce Idan ta shigo sama-sama take gayar dashi sannan ta nufi dakin Momi.Ganin kowacce na shigowa fuska sam babu annuri akai yasa hankalin Mubeen tashiwa.'Yar wasar da suke da yayarsa Meema akodayaushe yau babu ita,hasalima sama-sama ta gaishesa kana ta wuce dakin uwarta da sauri-sauri.



Akalla yanxu an shafe kusan mintuna talatin kenan da zamarsa anan wurin yana jiran momi,amma shiru-shiru taki fitowa suyi maganar datace zasuyi,sae ganin yan'uwansa mata dake ta shigowa yake wanda hakan ya bashi tabbacin lallai an buga an sanar musu da dawowarsa ne shine suka taso suka zo,kuma yanayinsu ya tabbatar masa da cewar lallai babu lafiya,dakwai abinda ke kasa wanda suke tsoron gaya masa Kai tsaye.ya yanke shawarar k'ara mata wasu mintuna talatin din,wanda ze kama 1hr kenan,Idan har kuwa 1hr din ya cika kuma bata fito ba,toh kuwa shi zeje ya sameta ta gaya masa abinda ke faruwa.



shesshek'ar da Hanan keyi sosae ya soma isarsa,afusace ya dubi inda take yace"Wai zaki yiwa mutane shiru ne ko kuwa? Kin de san arayuwata na tsani kananan koke-koken banza ba tare da dalili bako?tukunna mah de meh aka miki kike kuka? Huh gaya man? "



At once ta tsaida shesshek'ar,ta shiga jifarsa da kallon mamakin wannan sauyawarsa daga dawowa wai kuma duk akan Fadima wacce bema san cewar wansa ya aureta ba,yanxu muddin ya sani kuwa toh abin ze ninka wannan ninkin ba ninkin kuwa,wani dan marayan kuka ne taji yana nemar kubce mata don ita arayuwarta ta tsani ganin Mijinta cikin tashin hankali.



Murmushin leb'en baki kurum ya sakar mata ganin tana shirin sakin wani kukan,shi kansa yasan he's harsh on her wanda har ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login