Showing 9001 words to 12000 words out of 23399 words
Chapter 4 - Darajar Yayana Book 3 compelet writing by Halima Abdullahi K Mashi .txt
ma yaya usman din nan, to bari
in latsa shi.Na ce, ya Usman ka ce masa yayi
hakuri kawai dan na riga na tsaida mijin aure
wanda nike so.Ya Usman ya ce, kin kai shi gida
ne?Na ce, gobe ne iyayan sa zasu shigo gidan
mu.Usman ya ce, in har zan baki shawara ki
yarda zan so ki dakatar da su domin kowa zaki
aura na tabbata bai kai Aliyu ba, samunsa sai an
tona, ko na ce irinsa.In kika sameshi a matsayin
miji tabbas zakiyi alfahari samun muji kamarshi,
mata da yawa suna sonsa, kila sun fahimci
nagartarsa, amma ba matsi in baki sonshi zan
koma in fada masa cewa baki sonshi da aure.Na
kalleshi bance bana sonshi ba, saboda duk
abinda iya ta haifa dole ne in soshi, kai ko wani
ne can ba danta ba in dai ya mutunta ta to zan
soshi bare dan cikinta, na riga na zabi wani
ne.Usman yayi shiru, ya zaci da yayi mun
magana zan amsa da murna, can ya ce, to yanxu
mai zanje in ce masa?
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Na ce, ka fada masa zanyi tunani zuwa gobe. Ya
ce, shi kenan, zan kiraki amma kiyi shawara da
kawarki wadda ta sanshi, na san zata fada maki
qualitie din Aliyu. Na ce, ba damuwa. Ya ce, shi
kenan gobe zanzo naji. In kin shiga kicewa Abida
su fito mu tafi daman na sallami iya. Na ce, to.
Bayan tafiyar su iya tashiga yi mun fada wai ai
gashi nan saboda bai daukeni da muhimmanci ba
abokinsa ya turo min, ta san jikina yana bari na
ce na yarda. Na vata fuska tamkar zan saki kuka
na ce, ni fa iya banyi fa rawar jiki ba, ce masa
kawai nayi zanyi shawara zuwa gobe. Ta ce, ato
in kin kimanta kanki yaga darajarki in kuma kinki
ni dai na fada maki babu zuwa a kawo mun kara.
A waya Aliyu yaji duk yanda mukayi, mamaki ya
dinga yi wai wanan yarinyar ce zata ce sai tayi
shawara, dawa zata yi? Kuma ita ce wa? Usman
ya ce ita ce mace. Aliyu ya ce, shi yasa kaga ba
zan iya kai kaina ba ga wata ya in ce ina son ta
ba, bare tayi mun yauki, nidan oya-oya ne.
Usman ya ce ka barni da itakawai na san jan
ajine zamuyi nasara cikin jin haushi Aliyu ya ce,
in taki ka kyaleta kawai, yarinya sai kace wata ta
gold sai ga ruwa nake yi a kanta. Ya ja tsaki nan
ya kashe wayar ba tare da ya sake jin mai
Usman zai ce ba. Kwana Aliyu yayi da zullumin
halin da zai tsinci kanshi, in yarinya taki
amincewa da shi. Da safe ina shara ya fito daga
dakinsa ban san me ke sani faduwar gaba a duk
lokacin da na ganshi ba.Na gaida shi ya amsa
cikin isa, kuma a ta kaice kamar yanda ya saba.
Sanan bai ko kalleni ba sai dai nice na bishi da
kallo. Namiji ne sosai ko tafiyarshi ta shaida
haka, daga ganinshi baka ga rago ba, dama abin
da ya dace dashi kenan jami'in dan sanda. Iya
daga daki ashe tana kallona ta ce, in kin gama
kallonshi sai ki ci gaba da sharar ko? Cikin kunya
da shauki na ci gaba da sharata. Da rana naje
gidansu Aisha kawata nake bata labari duk yanda
muke ciki, tace, tabbas! Sadiya idan zan fada
maki gaskiya ki amince kawai, kada ma ki tsaya
wani jan aji,sau nawa nake fada maki Aliyunku
unique ne?Allah in kika yi sake kin tsaya yauki
kya zo kina na dama, kin san shi da zuciya ya ce
yafasa.Kash!Ina ma nice ya ce yana so?Jin haka
yasa na kagu dare yayi.Har na debe tsammanin
xuwansa dan tara ta kusa, duk na tsure kar dai
ya Aliyu ya hakura da gaske.Can sai na tsinkayi
muryar wani yaro yana sallama ni ina cikin daki a
kwance kan kujera.Iya ce ta amsa salamar don
tana tsakar gidan, ya ce an ce sadiya ta zo inji
wani a waje.Ka fin ya rufe baki na mike, zaraf na
suri mayafi na fita.Iya ta ce, kai jama'a!Kai
jama'a!!Ni wanan yarinya ko dai zaki kai kanki
ne?Na ce ban fa san ko wane ne ba, ma ai
iya.Cikin gatse iya ta ce, ina zaki sani, shiyasa
kike ta sintiri tun daxu kin kosa ko wanene maya
zo?Na ce, sai na dawo.Ta ce, kada ma ki dawo ki
kwana can.Usman yana tseye a gurin da muka
tsaya jiya, na sameshi da sallama, muka gaisa ya
ce to kanwata nazo jin me kika yanke?Na danyi
shiru kamar mai nazari, ya ce, kada ki damu in
har baki sonshi ya ce babu komai.Na ce, ai ba
zan iya cewa bana sonshi ba ko dan iya, don
haka ka ce masa na amince.Usman ya ce,
Alhamdulillah, sai kin ji mu.Ranar nayi farinciki
har nafila nayi don godiya ga Allah, iya ta ce yau
kuma ibadar ce ta motsa har da nafilar dare?Ni
dai ban tanka mata ba, ta ci gaba, Allah ya sa a
dore, ina ta samun gadanga ce akayina san daga
yau shi kenan.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Washe gari yaje ya samu yaya zakari da yaya
Sulaiman yayi musu bayani, su kuma suka sami
dan uwan mahaifinsu dake nan layin kasuwa, a
nan unguwar mu'azu.Nan dai suka sa ranar zuwa
zariya gurin mahaifina don jin zance, Aliyu da
zasu tafi ya bada dubu hamsin ya ce har sadaki
duk yanda ta kaya shi kenan.Mahaifina yayi
murna har yana cewa wannan abu ai da ba sai
anxo ba, ita iya Sadiya tata ce, Aliyu ma nata ne,
da ba shi kenan ba sai dai muzo a yan
gayyata.Kawu ya ce, a a kun wuce haka, kuma
dole abaku hakkinku.Baba yayi ta godiya kafin
daga bisani ya ce bari ya kira dan uwansa.Sun
yanke sadaki dubu talatin sanan aka basu na
gaisuwa goma, sai dai suna dawowa suka fadawa
iya duk yanda akayi.Iya ta ce sam yarta tafi
talatin, su kawo goman nan hamsin ne sadakin
yarta, sanan gadanga ya ciko goma kudin
gaisuwa.Da kyar suka shawo kanta ta amshi
goman, sadaki arba'in kenan.Aliyu dai yana
zaune yana jin su yana kallonsu amma bai ce ko
mai ba.Suka ce an tsaida rana watan tara sha
biyar da shi, lokacin kuma ana watan shida.Aliyu
ya ce yaya Sulaiman lokacin nan bai yi tsawo ba
kuwa?Anawa ra'ayin nafi son wata biyu, iya ta ce,
har ka gama shiri ne zaka ce wata uku yayi maka
kadan?Aliyu ya ce, wane shiri ne mai zafi?Ba lefe
bane ko meye ne kuke cewa ya rage ba?Ta ce,
kana da gurin zama kenan ko nan zaka gyara mu
zauna?Ya ce, a haba dai, zan nemi gurin zama
duk a cikin wanan lokacin.Ta kalli Sulaiman ni fa
in nayi auran nan zataci gaba da karatunta ku
shaida wanan, in ya ce a a za a jimu.Aliyu ya ce,
na sani iya, nima ina son ta ci gaba da
karatun.Ta ce, to batun aure a barshi wata ukun,
sai kaga lokacin ya zama ba ka kammala da wani
abun ba har kake raina lokacin.Ya ce Allah ya
kaimu.Ina zaune cikin ajinmu bayan mun gama
zana paper din mu ta karshe, ina kallon yanda
yaran ajinmu suke ta jin dadi da murna tun da
muka baro hall din.Ta gumi na zabga ina
mamakin irin halin ya Aliyu, yau kusan sati hudu
da sa muna rana amma ko sau daya bai taba
kirana ba, haka nan kuma ko cikin gida ya shigo
ban isheshi kallo ba.Nima fa yanxu na soma
sarewa, anya kuwa mutumin nan yana sona?
Kullum iya sai tayi min gori, yau kam zanje in
nemi ya Usman.Bayan nan na cewa Anty Abida in
yadawo tace ya zo, ina son magana da shi, ta ce
to zata fada masa na ce ina su Ummulkhairi?Ta
ce suna makaranta.Da daddare kuwa sai gashi
ana sallama dani, na mike har ina tum tube.Iya
ta ce, sai karaftu kike sai kace a dakin Ajantina,
na san dai ba wanda kike son gani bane, dan
nasan shi ya fi karfin ya kiraki.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Nace, iya to ai ina so ne na ga ko wanene.Ta ce,
oho ke dai kika sani.Ina fita yaya Usman ne
kamar yanda nayi tsamani bayan mun gaisa ya
ce, Abida ta ce kin zo nema na.Na ce, eh.Na
sunkuyar da kaina ina wasa da yatsuna, na ce
dama nazo ne a kan maganar mu ne da ya Aliyu,
in abin ba zai yuwu ba gara mu hakura tun
yanzu.Ya gyara tsayuwa wani abu ne ya faru?Na
ce to ya Usman a haka ne za mu fahimci juna in
san abinda baya so yasan abinda bana so?Na ci
ga ba, bai taba kirana da sunan muyi zance dashi
ba, ko gida ya shigo ban ko isheshi kallo ba, shi
bashi da wani lokaci ne sai na aikin shi?Usman
yace ba wai zan goyi bayan shi bane amma
ninasan kina ranshi,ki fahimce shi, shi mutum ne
mai kishin kasarsa da aikin sa, shi yasa baya
samun lokacin kansa.Amma da zarar kin zama a
gidansa na san dole ya baki dukan lokacinki.Nayi
shiru kamar maganar ta shigeni, ammada na
tuna ko kallo na bayayi na ce, yaya Usman ka
san Allah ba dan aikin shi bane, ko kallo fa ban
isheshi ba.Usman ya ce, to bari zanyi mashi
magana.Na ce, don Allah kada ka ce nayi maka
magana, kada yayi tsammanin na damu da shi
ne.Usman ya ce, zanyi masa maga na da ma ai,
ba zan ce kece kika sani ba.Kusan sha dayan
dare Usman ya daga wayar Aliyu tare da yin
sallama, bayan sun gaisa Usman ya ce aboki
dazun ina ta kira baka daga ba.Aliyu ya ce, bari
kawai aboki, lokacin ina tsakiyar wani case ne
abin nan yana matukar daga hankalina tare da
bani mamaki.Ka san wani mutum dan kimanin
shekara arba'in aka kama yayi wa yar shekara
hudu fyade.Usman ya zabga salati tare da cewa,
wai aboki wanan wace irin masifa ce?Ko dai wani
tsafi ne?Aliyu ya ce, wa ya sani?Wannan fyaden
na kananan yara yayi yawa.Kullum sai mun sami
wanan case din wlh yanda abin nan ke mun zafi
a raina zan iya kashe irin wadannan mutanen,
don mugaye ne.Idan mata ne su je mana ga
karuwai nan,Usman ya ce, to Allah ya shirye su,
ya tsare mana daukacin musulmi.Aliyu ya ce,
amin aboki to kaji halin da nake ciki, lokacin da
ka kirani lafiya lau dai ko?Lafiya lau dama zance
ne ya kamata mu shirya muje muyi hira da
yarinyar nan ko?Aliyu ya ce, wace yarinya ke
nan?Usman ya ce, sai karinka yi kamar baka san
da zancen ba bayan nasan tana ranka.Aliyu ya
ce, tsakani da Allah sai ka tuna min.Usman ya ce,
ok, tunda yanxu iya ta yarda dole ka manta.Aliyu
ya ce subuhanalla? Dama wai Sadiya kake
magana?To wacce hira kuma zamuyi tun da na
rigaya an gama magana, sai jiran lokaci.Usman ya
ce, ai duk da haka za aje ayi hira ta san abinda
baka so don a samu zaman lafiya.Aliyu yayi yar
dariya.To ni ba haka tsarina ya ke ba, ina zaton
in har zanje gurin budurwa zan jene don ina
tallata kaina in in samu shiga,tonina riga na
samu shiga babu dalilin da zan matsawa
kaina.Usman ya ja tsaki kai dai bahago ne wlh, to
sai ka sai mata waya ko ta waya kunyi
magana.Aliyu ya ce, to yan zu dai kaine sarkin
yakinta ko?Suka sa dariya.Usman ya ce, da gaske
nikeyi, akwai wata waya da ake saidawa mai kyau
nan kusa daoffice din mu (MTN OFFICE) ya ke
aiki.Aliyu ya ce, ka suyo mata in kazo sai na baka
kudin, sanan kai zaka bata don har karshen satin
nan ban san lokacin dawowata, kafin ita ta tashi
na fita.Usman ya ce shi kenan.Washegari da
daddare ya usman yazo ya kawo mun waya wai
iji yaya Aliyu, inyi hakuriza mu rinka waya aikine
yayi masa yawa.Bani da zabi dole na hakura
tunda ga waya har da layin (MTN) ko da na nuwa
wa iya baki ta tabe sanan ta ce Allah ya sa
alheri.Tun da na karbi wayar ko flashing ba a
taba yi mun ba, ga dai lambarshi a ciki ya usman
ya samun duk da cewa har da kudi a layin nawa
nima cewa nayi ba zan kira shi ba.Sai dai in ta
kiran kawaye da yan uwa wadanda nake da
number su.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Wata rana da dadare naji Iya tana yi masa fada
cewa yana zaton haka za ayi auren ba lefe, biki
saura wata daya da kwanaki, amma ba a ga yana
motsi ba.Ya ce, abin ne ya shige masa, amma
gobe zai je ya sami matar ya sulaiman.Ita da
matar Usman Anty Abida sukai ta zaryar zuwa
kasuwa, saura sati biyu lefe ya kammala da dinki
da komai.Iya ta ce ya Aliyu ya bada kudin mota a
kaisu zariya, ni kuma nan kawaye na sun matsa
da batun anko, lokaci yana tafiya gashi ba zan iya
yi mashi magana ba.Aisha ta ce, kiyi wa iya
magana.Na ce, iya kwana biyu bata sana'a , bata
da kudin anko?Tab! Ba zai yuwu ba.Wayata na
dauka inyi kamar zan kira shi in fasa, Aisha ta
amsa na ce kada ki kira shi dan bai taba kira na
ba, ba wani kiranshi da nima zanyi Allah aisha ni
auren nan tuni ya fitan min daga rai.Ace kai kafi
karfin kazo sai dai abokinka?Aisha ta ce, Allah sai
na rubuta masa tex.Ina kallonta ta rubuta
masa.SALAM.INA FATAN KANA LAFIYA?KAYI
HAKURI KILA YANXU KANA CIKIN AIKI NA TSAIDA
KA, DA MA NAYI MAKA WANAN MESSAGE DIN NE
DON NA TAMBAYEKA A KAN MAGANAR ANKO,
DONKAWAYENA SUN DAMU SABODA LOKACI YANA
KAREWA.NA GODE, KA HUTA LAFIYA.Tana gama
rubutawa ta tura masa, maji amsa-maji amsa
shiru, nace kin gani ko?Ke ayi biki haka bani kara
masa batun anko.Aisha ta ce, niko yanda yake
nashi salon birge ni yake, na ce, au!Wulakancin
da yake min din ne yake burgeki?Tayi dariya, ai
ba wulakanci bane rayuwar sa ce haka.
Lokacin yana office din commissiner ya je a kan
nemansa da yayi tsam ya kame kamar yanda
yake al'adar yan sanda, sanan ya soma magana
cikin natsuwa ranka ya dade an ce kana nema
na.Commissioner ya dube shi cikin natsuwa
sanan ya ce da ma na kira ka ne a kan maganar
barawon shanu din nan da aka ce kaki yarda a
bada belinshi.Aliyu ya sunkuyar da kai don
girmamawa, yace ranka ya dade haka ne, naki
bada belinshine saboda bincike ya nuna shi din
ba karamin mai laifi bane.Daji suke shiga da
motoci suna kora shanayen fulani suna kwashewa
su kai kudu su saida, wanan kamawar ita ce ta
goma sha uku amma ba a taba mikashi kotu ba,
azzalumine na gaske,Commisioner yayi dan
murmushi sannan yazo ya dafa kafadar Aliyu ya
bubbuga alamun jinjina, san nan ya ce, Dan
Sanda mai kishi, lallai kasan aikin ka da ka tsaya
binciko wannan files din, ka tattarosu ka miko
min nan, ni nasan yanda zan kawo karshen
lamarinsa.Zan shigo gurinku anjima kaje.Aliyu ya
sara masa, sanan ya fito.Gaskiya in son samu ne
case din nan ya tsaya a hannunsa dan kam zaiyi
gogaiya da zalunci.Shigarshi office din sa kenan
sako ya shigo wayarsa, sai da ya zauna sanan ya
duba.Murmushi yayi bayan ya karanta, a fili
kumaya ce, ko me nene anko?(hahaha,kunjifa
dan rainin hankali inji,shin kuna ganin zai yuwu
ace baisan Ankoba,ai dai kayan yansanama
Ankone,kuma kala biyu, wasu su sa baki
kawai,wasu kuma baki da light blue ko? Cewar
ANaM Dorayi)
Ya kira layin Usman bayan sun gaisa ya tambaye
shi ko menene Anko? Usman yayi murmushi wato
kai dai in kaje ka shige caji ofis dinku shi ke nan
baka tuna meye a cikin garin.Aliyu ya ce, aboki
mu kuwa dake wanan ofishin mu muke da
labarin abunda ke cikin garin, amma ba wanda
ya shafi biki ba.Usman ya ce zaka bata kudi ne
kurum ta shiga kasuwa da kawayenta su zabo,
haka su ke yi.Aliyu ya ce, gashi ni kuma bana son
yawo bare kuma xuwa kasuwa, in dai zani ne in
zan je gidan zan tsaya nan wani super market in
sayan masu, guda nawa ake siya?Usman ya ce,
da ka basu kudin.Aliyu ya ce, ba zata kasuwa ba,
wanan shine ra'ayi na, zan siyo musu zani.Usman
ya ce shi kenan, sai ka suyo musu mai kyau.Aliyu
ya ce ina ruwa na da zabe, ni dai kawai in dau
zani.Don haushi Usman ko sallama babu ya
kashe wayar.Aliyu ko da wuri ya bar office din ya
bi ta kasuwa ya sai zaunnuwa kala uku ko
wanneguda bibbiyu ya nufi gida.Iya tana zaune
tana yankan kubewa ni kuma ina daga kicin ina
kwashe tuwo ina mulmulawa a leda ina sakawa a
kula ya Aliyu ya shigo da sallama.
Kusan kwana hudu ban sashi a ido na ba , da ya
zauna yana gaisheta.Ta amsa ya ce, ga zaunnuwa
anko ne suka ce ko menene ma?Ta dauki ledar
tana cirowa ta re da fadin kaine ka siyo ankon
gadanda da kanka?Ya ce, to duk ba zani bane,
shi nan sai su zaba.Ina kallo daga ciki kuma ina
jin su, tun kafin in fito zaunuwan suka tafi
dani.Ya ce, naki ne da nata.Iya ta ce, to mun
gode, da ma ina so inyi maka zancen gidan ne, a
ina kasamu?Ya ce, to ni dai nafi so a can kasan
layinku, gefen makabarta din nan, to ba a samu
ba sai na dawo neman na siyarwa, kudina
dakekasa yanxu za su iya semin gida, amma
albashin wanan watan da na wancan watan hada
mana za ayi.To ganin kurewar lokacin sai kurum
na barshi yanxun anjima zamuje mu ga wani gida
da yaya Sani da Usman wai ciki da falo sai kichin
da ban daki dubu dari da hamsin.Iya tayi shiru
tana nazari, can ta ce ina nufin kasan gidan su
babba ne?Ya ce ciki uku ne da kicin da ban daki
sanan ga filin da mutum zai iya fakin din mota
har biyu.Iya ta ce kuma nawa?Da sauri ya ce wai
miliyan daya da dari takwas.Ta ce, ina ganin zaifi
ka siya gidan in yaso sai a daga bikin.Ya dubi iya,
ai saboda bana son dagawar shiyasa na hakura
da siyan gidan.Iya ta ce siyan xai fi maka sauki
ka huta da biyan haya, auran kurum za a daga
ba.Ya ce ba dagawa za'ayi ba, abinda ya sa in an
daga za ayi asara da yawa.Abokaina sun kashe
kudi gurin kati mai tsada tare da wasu abubuwan
abokan aikina suma sun kashe kudi gurin shirya
bukin.Iya ta ce to, kana ji ko, yanda za ayi kawai
a daura auren da buki, sai ta zauna gida kafin a
gama gyara tunda dai nan a gida ne ba a dawa
ba, bana so ka rasa gidan nan ne muhalli a bariki
ba karamin rufin asari bane
Aliyu ya ce, shi ke nan sai ayi haka din bari zan
kira yaya Sani sai muje dake ki ga gidan sai a
biya.Lumshe ido nayi cikin jin dadin an fasa daga
bikin, kai naso in tare a gida na ranar amma baji,
buri na dai a daura auren, amma da iya ta so
kwafsawa wai a daga.Ya mike ya juya da nufin
fita ida nunsa sukasauka a kichin a inda nake, da
sauri na ce ina yini?Sai da ya dauke kai sanan ya
ce, lafiya.Har ya fita ina kallonshi.Iya ta katse ni
da cewa, wata rana sai kin gaji da kallon shi.Na
sunkuyar da kai kunya ta rufe ni, ban santana
kallona ba sa karya, in dai gadanga ne gaki ga shi
nan.
Pink din muka zaba ni da Aisha, sai dai muna
zuwa kasuwa aka ce dubu uku ce gashi kudin
aisha bai kai ba.Sai muka dawo gida da kyar
mamanta ta cika mata muka koma muka
siyo.Muka roki mai shagon ya ajiye mana da mu
siya da yawa.Yamma tai mana a kasuwa gashi
ana wahalar mota.Muna tsaye a kan titin kano
Road, na ce