Showing 18001 words to 21000 words out of 23399 words
Chapter 7 - Darajar Yayana Book 3 compelet writing by Halima Abdullahi K Mashi .txt
don ya
barni.Kuma ko ba dan iya ba ina tsoro, tunda
ban san yanda abubuwan suke ba.Na makele fulo
ina tunanin ko a wane hali yake ciki yanzun, na
jima kafin bacci ya tafi dani.Nayi mafarki kala
kala masu dadi wai muna ta shawagi a cikin wata
duniya ni da ya Ali.Ku ziyarci blog dinmu domin
karanta Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Da safe kuwa fuskarshi a murtike, don ko amsa
gaisuwata baiyi ba, lokacin da yazo gaida Iya ina
gai da shi,hakan bai yi min dadi ba, na kunna
waya ta na tura masa sakon ban hakuri tare da
ce masa jiya naso inzo Iya ce bata bari na fito
ba.Ko ya gani ko bai gani ba oho, bai dai bani
amsa ba, na dafa ruwan tea na kai mai na same
shi ya gama shirin fita yana daura ta kalmi.Na
shiga da sallama ciki ciki ya amsa, ina shiga ya
dubeni fuska daure ya ce, lfy?Cikin wata murya
irin ta a salin jarumin maza.Jiki na ya dauki bari
na ce, dama....dama tea ne.Ya ce fitan min da
shi ina azumi, fargaba na ya karu, iya ce jiya ta
fash....Ke!Ya katse ni, fita a nan dan Allah.Na fita
da sauri, zugun na zauna ina tunanin yanda ya
Ali yake canza launi tamkar hawainiya...
Kimanin kwanaki uku kenan yayi mun dif, inna
gaida shi baya amsawa, haka nan in abinci na kai
mai ko yaushe sai ya ce yana azumi.In iya tayi
mashi magana ke nan, in nice ma na kai mishi ni
abu sai ya koro ni, ina girki a kicin iya ta fita
lokacin sai ga Aisha kawata.Naji dadin zuwanta ta
tayani,muna fira na bata lbr duk halin da nike
ciki na kara da cewa, ya Aliyu gaba yake dani, iya
ta sa ido sosai dan ganin ban bada kai ga miji na
ba, ba tare da mun tare ba.Don Allah Aisha ki
bani shawara, ta ce, ni dainawa ganin in har zan
fada maki gaskiya kibi mijinki, daga lokacin da
aka daura muku aure da shi dukkannin hakkokin
shi sun hau kanki.Nayi ajiyar zuciya tace, nasan
kin san komai ma kina yi ne kamar baki sani ba
nace Aisha nasani,Iya fa idonta yana kanmu.Ko
daki na shiga sai kiga tana kai kawo, in na fito
kuma tayi ta yi mun kallon tuhuma, to ki bashi
shawarar ku fita wani wurin mana.Nace tap nice
ma zan bashi shawarar?To an ce maki iya za ta
barni in fita ne?Aisha ta ce, yanda kika gani,
amma in nice zan bi miji nane.Rayuwar nan ta
yanxu mata suna bin maza har inda suke,
balantana mijinki dan kwas irin wanda basu da
yawa a cikin jama'a?Ku ziyarci blog dinmu domin
karanta Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Na ce nima ina tuna haka, shiyasa wlh ban so ba
da ban tare ba, kamar yarda ko wace Amarya
take tarewa a dakinta. Ki tayani da adu'a don sun
sani a tsakiya ita tana kallo na a mai rawar kai
na shige masa,shi yana kallo na mara
biyayya.Aisha ta ce, abu ne fa mai sauki ke ce
kika dauke shi da zafi, in kin bi mijinki kinga dole
ta barku.Na dubi Aisha ta ce, fa ba zai dubi
mutuncina ba, Aisha ta ce, in bai sameki a
mutuncenba ba?Kin bi maza ne?Na kai mata
duka, kinji ki da wani zance, in na bi tare muka
bi kenan.Ta ce ke ce da wani shirme, in kin ga
namiji yaga rashin mutuncinki ya sameki kin bi
wasu....(Biri fa kuma yayi kama da
mutum,watakila irin haka tafaru da yar uwarki da
Zaria,shiyasa mijin yayi inkarin kasancewarvcinkin
a matsayin nasa,hartakai ga saki ANaM Dorayi)
Kalu bale ga masu saida mutuncinsu a banxa.
Aliyu tukur ya tsaya a gaban shugaban shashin su
na binciken manyan laifuka, mataimakin
Commissioner.Ya ce ASP Aliyu zanfi so idan kana
tsayawa a kan aikinka, ina nufin ka rinka
dakatawa a madakatarka.Sanan ka rage kishin ka,
domin kasar mu a yau in kace haka zakayi lallai
ba zaka kai ko ina ba.Ina yi maka magana ne a
kan barawon shanu din nan, mutumin mai girma
commissioner ne, na tabbata da yana gari baza
ka kamashi ba bare tsarewa.Inma kayi nasara ka
kama shi, ba zaiyi minti talatin a tsare ba kai ba
a taba kama shi ba, yaranshi kurum ake
kamawa.Da sunyi waya da commissioner zaisa a
sake su, nayi mamakin ma da commissioner bai
tsawatar maka ba, ya ce kawai ka bar case din a
hannunsa.Ran Aliyu ya baci, shi da ya shiga aikin
dan sanda kishin kasarshi da kawo gyara, sai
kuma su rinka ganin barna suna kauda kai?Ya ce,
yallabai ina rantsuwar da mukayi da alkur'ni
cewa zamuyi aiki tukuru bisa amana da gaskiya,
idan dannanda bai zama mai kishi da gaskiya me
za a kirashi?Idan dan sanda zai rinka amsar cin
hanci yana hulda da manyan azzalumai yana
daurewa barayi gindi suna zalunci, za a kirashi
mai tsaron lafiya al'umma.AC ya dagawa aliyu
hannu, dakata ASP, wannan tambayoyin zasu fi
dacewa kayiwa CP su, ni shawara na baka.Da
akwai mutane irinka da yawa wadanda suka
nuna kishi, wasu anyi musu canjin gurin aiki zuwa
wasu garuruwan da ba zasu sami irin wanan
barnar ba bare suyi gyara.Wasu anyi musu sharri
an koresu, kai wasu sun mutu yayin da wasu da
yawa suka ajiye hularsu.Ban hanaka yin kishi da
gaskiya tare da kin karbar cin hanci ba, sai dai
ina mai baka shawara ka dinga tsayawa ga
kananan masu laifi, jeka abinka.
Aliyu yana zaune a office din shi, kansa ya dauki
zafi yana tuno sa'insa da sukayi da Barawon
shanun, inda barawon yace, kai yaro wanan ba
wani bakon abu bane satar shanun da muke
yi.Haka nan mu nan Headquarter gidan mu ne
kaine mutum na farko da na taba bawa cin hanci
ya maido mini.Nafi tunanin kana daga cikin
mutanen da basu da rabo, amma kai bako ne
ko?Aliyu ya ce, ba jin tarihi ko maganar cin hanci
na xo ba, nazo nan ne dan in kama ka,a
matsayinka na mai laifi, ni kuma na hukuma.Duk
wadan nan baya nan zasu biyo baya in munje
office, yaranka muka kama kuma suka ja
sunanka.Barawon ya zaro ido tare da daga murya
ya ce, kai bako ne shiyasa baka sanni ba amma
muje.Aliyu ya ce nasan ko ban sanka ba, bako ne
ni bako ne wannan ba damuwata ba ce.Ku ziyarci
blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Sun san Aliyu bai san wanene wanan barawon
ba, shi kanshi barawon cewa yayi zakayi da
nasanin kamani.Aliyu bai ce kala ba, ya nufi
Office din sa zuciyarshi cike da son nunawa
wanan baron cewa hukuma bai bar
kowaba.Amma me? daidai lokacin da yake bada
ummarnin ashigar da kara ne shugaban shashin
su AC ya ce, kajira tukunna sai an sami ummurni
daga commissioner.Dafawar da akayi mashi itace
ta dawo dashi daga dogon tunaninsa.Ya dago
kai.Insperctor kamal kaita ne ya ce Sir, ka daina
damuwa da irin wadan nan matsalolin, sanan ka
ci gaba da yanda kake, Allah zai kawo maka
dauki dan yana tare da irinku.Sai dai dama baku
cika farin jini ba a cikin yan sanda, saboda kowa
yana ganin cewa zaku toshe masa kafar
samu.Shawarata ka bar batun Barawon nan ko
ba komai kayi namiji tunda ka kamo shi, ka kuma
tsare shi.Sanan Allah ya doraka a kan CP bai
dauki zafi a kanka ba.Aliyu ya mike tsaye, na
shigo aikin dansanda cike da kishi da buri, gami
da kwazo.Manufata insamu waddanda zasu
fahimci niyyata don mu kawo gyara cikin
hukumar yan sanda.Na tabbata ko cikin
headquarter din nan akwai masu kishi da yawa
wadanda suke jin irin abinda nake ji yanxu a
zuciyata. Inspector ya ce, hada dani, sai dai ina
mai bakin cikin sanar da kai cewa ba zamu kai
labari ba, tunda daga sama a ake tadiye mana
kafa.Aliyu yace inko haka ne zaya ci gaba da
faruwa, watarana zan iya ajiye hulana.Inspector
ya ce, ranka ya dade kada kasaka haka a ranka
tun yanxun, kaji a cikin xuciyarka cewa burinka ya
cika, Allah yana tare da mai gaskiya.Ranka ya
dade ka duba tashin farko bin diddiginka yasa
sashinmu na bincike suke shakkarka, ina son
mutum irinka.Aliyu ya lumshe ido tare da cewa
zantukanka sunyi mun allura inspector, zan kara
kaimi.Da wanan ya cigaba da aikin sa.Daf da zai
tashine aka shigo da wani da ake zargi, ya kalle
gobjejen mutumin sanan ya dubi yan sandan.Me
yayi shi kuma wanan? Sajan Ado ya ce, ranka ya
dade, kato kamar wanan aka kama yayiwa yar
shekara takwas fyde,ran Aliyu ya tunxura, ya
runtse ido cikin takaici, ya ware ido ya kalli
mutumin cikin tsana ya ce, wai wane irin
zaluncine wanan kuke yiwa jikokinku?Cikin rawar
murya mutumin ya ce ranka ya dade na rantse
maka ba ni bane, sharri sukayi min, na rantse
maka.Aliyu ya harareshi, ba kowa bane yake
amsa laifinsa da sauri.Ya kalli yan sandan suwaye
suka kama shi?Sajan ya ce ranka ya dade ga
mutanen da suka kawoshi can, sune suka
kamashi da yarinyar a shagon shi tana ihu.Yace
ina yarinyar yanxu?Sukace an tafi kaita Asibiti.Ya
kalli mutumin yaja tsaki ya ce, ya ce ku rufe shi,
yanxu ba wani sausauci ga irin mutanen nan
masu cutar da kananan yara ta ta hanyar fyade
Ya koma office din sa cikin ta kaicin fyadan nan,
kullum sai sun samu irin wanan case din da yar
da jarirai yafi yawa, amma yanzun yanaga zasu
xo daidai.Ya kira sajan ya ce, ya kawo masa
takardar tuhumar (statement) da ya duba tsaki
yaja, ya dubi sajan.Kullum dai abin iri daya ne.Ya
tabe baki, sanan ya dubi a gogonsa, yau shida
zan bar nan, duk wanda ya nemeni
saidasafe.Sajan ya sake kamewa tare da fadin
yes sir!Sai kuma wanan mutumin yaya za ayi da
shi?Aliyu ya ce, ba maganar beli ko wani ya zo
zuwa gobe za a hada bincike a turashi kotu.Sajan
ya sara masa sanan ya fito.Da dunbin wanan
damuwar ya iso gida, daga ganinshi kasan akwai
abin da yake damun shi, kan katifarshi ya zube
rigingine bata re da ya cire koda ta kalmi
ba.Lokacin da ya shigo ina zaune a kan kujera a
kofar daki ina karatun wani littafi (SIRRIN BOYE)
na Anty Bilkisu.Ga al'adarshi in ya shigo dakin Iya
yake fara shiga kafin ya dawo dakinsa, ya cire
kaya in sun gaisa.Ya shiga wanka.Amma yanxu
tunda ya shigo shiru, iya ta fitodaga bayi (ban
daki) na dubeta na ce, yaya fa?Ya dawo yanayin
shi kamar na mara lafiya, ko baya jin dadi ne?Ta
ce, ba wani ke dai kina sonzuwa gurin mijinki ne,
kuma ba zan hanaki ba.Na hade fuska, Allah iya
nifa ba wai zanje bane fa.Ta ce, kije ki duba ko
lfy,naki tashi, dan dama ina tsoron inje yayi mun
wulakancin shi, ya ce nafita shiyasa naki
zuwa.Ganin da iya tayi tabbas ba zan shiga ba
kuma tabbas bai fito ba sai ta shiga dakin. Yan
da ta ganshi warwas a katifa batare da ya cire ko
takalmi ba, sai abin ya bata tsoro.Cikin saurin
muyar ta ce, Gadanga!Ya dago kai da kyar ya
dubeta, wani matsanancin ciwon kai ke damun
sa.Ya ce na'am Iya sannu.Ya tashi zaune,
ciwonkai ne ya hanani shigowa ciki.Ta ce,
matarka nema ni take ce mun ka shigo cikin wani
yanayi, bari a kawo maka magani ka sha.Yace
zanje Asibiti in anjima bayan magariba.Duk
kwanakin nan da haka nake ta yawo da ciwon
kan nan.
Ta ce, to kasha maganin yan xu sai kayi sallar da
dan karfin jikinka, kaje asibitin da dan kwari.Ya
ce, to.Ta kwala min kira Sadiya.Na amsa ta ce,
dauko min magani panadol kizo da ruwa.Naje har
gabanshi na ajiye da ruwan ina yi mashi sannu
yaya, ya jikin?Ko kallo na baiyi ba bare ya amsa,
mamakin yanda naga iya tan gutsi gutsi da
maganin, ta dubeni dauko mun cokali.Na dauko
ta jika ta bashi a baki tare da fadin, shiyasa nake
fargaban ciwonka gadanga.Duk da dai ba yawan
ciwon kake ba, amma kin maganinka shi ke
wahalar da kai a ciwo dai dai yake da na yaron
goye.Shi yasa duk lokacin da katashi ciwo bama
jita dadi.Ya sha ya koma ya kwanta, dai dai
lokacin aka kwada kiran magariba.Ta dube ni,
bari inje inyi sallah, nima na biyo bayanta.Ta
dakatar dani da cewa, jira tukunna muga yanda
jikin zaiyi.A raina na raya cewa dan ta ga ina
fashin sallah, shi kuma bashi da lfy.Shi kam yana
kwance, na isa gurinsa gabana yana ta faduwa,
duk da ina zaton zai daka min tsawa ban fasa yin
abin da nayi niyya ba.Gabansa na tsugunna ina
kwance masa takalmi, na cire su na aje gyafe,
sanan na kwashi kafafunsa na zubasu a kan
katifar.Har lokacin idanunsa biyu amma suna
lumshe, haka nan hannunsa yana dafe da
kai.Kusan minti shabyar ina zaune can gefe, ya
tashi zaune yana kici kicin cire rigarsa, na taso na
balle masa boturan, sanan na sabule rigar sai
farar singiletin, ita ma ya kama ya cire.Na kalli
kirjinshi gashi ne kwance na kauda kai don sai da
naji wani iri.Ya sabule wandonshi, sai gajere na
ciki, shima na kwashe su na zaba su a cikin
kwandon da yake zubawa.Naga yana kokarin
tashi nace mai zaka dauko in dauko maka?Ka
zauna kawai.Ya ce, bani jallabiyata.Na bashi fara
kal mai dogon hannu, ya mike zai fita, na ce ina
zaka je?Ya ce masallaci.Yana fita na shiga gyaran
dakin, ban taba yi masa gyaran daki ba sai
yau.Ko yaushe da kansa yake yin gyaran dakinsa,
nayi zaton zanga mujallun da na taba gani da, sai
kuma ban gani ba, har na gama.Iya ta idar da
sallah, ta sake lekowa ko ya tashi, na ce ya je yin
sallah, shiru shiru ashe daga can ya tafi
asibiti.Har kusan tara gashi bai fita da waya
ba.Iya da kanta ta fita har masallaci layin mu,
wanda suke sallah tana nemanshi.Duk wanda ta
tambaya sai su ce mata tare dai suka idar da
sallar isha'i.Da ta dawo sai na ce mata ko dai
yatafi Asibintin da ya ambata ne?Ta ce zata iya
yuwuwa ya tafin, tun da ya ambata.Nan dai
muka zauna zaman jiran tsammani,mun kasa ko
cin abinci.Sai sha dayan dare da yan mintuna
dan acaba ya sauke shi, ni da iya har rige rigen
fita muka yi, shi ne muka yi masa sannu ya
amsa, iya ta ce, muna ta neman ka.Ya ce, natafi
Asibiti ne shi yasa ciwon kai ya matsa min da
yawa.Amma na sami allura da magunguna, kuma
na kwanta canne kamar yanda likitan ya ce in
dan huta, Alhamdulillahi kai yayi sauki.Ta ce to
me zakaci yanzun?Ya ce, nasha tea a can kafin
ayi min allura, muka shiga dakin shi ya zauna
bakin gado.Iya ta fita nima na mike zan fita, sai
ta ce ki dan tsaya ke saboda dare ko?Na koma
na zauna ya kwanta tare da lumshe ido.
Wayarshi tayi ringign, ya daga ya kalla sannan
yaja tsaki, bari na kashe wayar nan ina so in dan
huta.Har zai kashe sai ga ma bari yayi anfani da
wanan damar ya nunawa sadiya anafa ribibin shi
har da take masa yan ga.Don haka sai ya daga ni
dai naji yana fadin yaya mati na me ya faru ne?
Ban zaci jin muryarta ba, ashe ya saka
hanfree.Sai kurum naji ta ce, lafiya lau sir, ban
gankaba ne an ce ka tashi tun six, ya ce akwai
wata matsala ne matina?Ta ce babu, naso in
ganka kawai, kayi hakuri kasan ganinka kawai
yana cire min damuwa dayawa, dayawa, amma
sir sai kanayi kamar baka san haka ba.Yace
matina yanzu bani da lafiya ne, ban dade da
dawowa daga Asibiti ba in nafito da safe zamuyi
maganar.Ta ce to Sir, nagode Allah ya kawo
sauki.Raina yayi mugun baci, a gabana yake
magana da wata arniya har take ce masa ganin
shi yana sata sukunni da kwanciyar hankali?Yana
ajiye wayar ya kalleni, na hada rai matuka na
mike ya ce, ina zaki?Nace zanje in ci abinci ne, da
kyar nake magana.Ya ce, au dama baki ci abinci
ba?Kamar in kai masa duka don ta kaici.Mutumin
da yayi nasa guri bai fada muna ba muka yi tsuru
tsuru cikin damuwa.Shine zai ce dama ban ci
abinci, ya mai maita tambayar nace um, ya ce
kina ciwon baki ne?Nayi shiru yace in kin ci ki
dawo, tunda Allah yasa yau naji da kunnena ba
iya ce take hanaki zuwa wurina ba, karya kike yi
mata.Ban tanka shi ba na wuce, a raina na ce ba
zan dawo baCan kusan daya saura ina ta tubka
da warwara na kasa bacci, ni nasan kaina ina da
mugun kishi, sai ga sako ya shigo cikin wayata
cewa ba zaki dawo bane?Na tura masa amsa da
cewa eh, ka kira Matina.Yana ganin haka yayi ta
dariya, sakonshi ya kai ke nan, don haka shima
kurum sai ya kashe wayarsa ya kwnta.Da Asubahi
iya taje dubashi ta sake shiga dan duba shi, sai
ta samu jiki yayi sauki, har ma ya tafi
masallaci.Don ya Aliyu ba rago bane namiji ne, ga
juriya da izza, matsalarsa daya in yana ciwo kin
magani,yayi tawa iya shagwaba sai kace karamin
yaro, shi a dole auta.Nikam har gari yayi haske
ban tashi daga makwanci na ba, tunda ina fashin
Sallah ba wai ina bacci bane kurum takaici ne ya
hanani tashi.Jiya ko baccin kirki banyi ba, saboda
takaicin ya Aliyu.Iya ta shigo, ke ba zaki tashi kije
ki gano mijinki ba?Ko da nafito kin xuwa nayi na
debi ruwa na shiga wanka.Ina fitowa nayi zaman
shafa mai duk ina jan lokaci ne don yayi abinda
zaiyi ya kama gabanshi.Bana ma ko son ganinshi,
lokacin da na shirya na nufi kicin a tsammanina
ya fita.Ina tsakiyar kunna risho sai naga mutum a
kofar kicin tsaye.Na rasa dalili in zan ga ya Aliyu
sai gabana ya fadi.Na kalli fuskarshi, gaskiya har
ya dan rame na ce ina yini?Ya ce ban yini ba, ni
yanxu zafiya ce, sanan ba zan amsa ba tunda
baki san hanyar daki na da bazakije ki gaida ni
ba.A raina na ce ina matina?Ita batazo ta duba
ka ba?Ya katse tunanin da cewa,ruwan zafi nake
so zanyi wanka.Na kalleshi, ban taba ganin yayi
wanka da ruwan zafi ba, nace to bari in dora
yanzun, bai ce, kala ba ya koma daki.Da yayi zafi
na sirka na kai masa ban daki, sai naje na ce
masa ga ruwa can.Lokacin yana waya, da hannu
yayi min alamar cewa in je yaji.Na tsargu da wa
yake waya, don haka da nasaki labule sai na
tsaya.Ji nayi yana cewa, kada ki damu, yanzu
zanfito.Jikina yayi sauki, ai da tunaninki na kwana
araina.Na girgiza kai tare da yin kwafa.Tabbas da
matina yake yin waya, nayi kicin ina yin magana
ni kadai, na ce to ita wanan shegiyar matinar me
ke tsakaninsu?Nemanta yake yi ko me?Wata
zuciyar ta katseni da cewa, ba kina gudunsa ba?
Ai ga Matina zata maye gurbinki. Jikina ya sake
mutuwa, na shiga tambayar kaina mafita.Wunin
ranar sukuku nayi shi, na kasa tuna yanda zan
bullowa abin.Duk jin su iya nake ko da can da
suke cewa ba ruwanshi da mata, ni nasan da
ruwanshi tunda ni naga mujallun batsa a dakin
shi.Wanda baruwanshi da da mata me ya
ruwanshi da irin kallon tsiraici?Dole ke nan inyi
yakin rabashi da matan banza.Wata zuciyar tace
haka ba zata yuwu ba, sai in zakiyi aikinki a
matsayin matarsa, lallai saikin mika kanki a fili na
ce ya na iya?Ku ziyarci blog dinmu domin karanta
Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Muna zaune a falo da iya washe gari da safe,
yazo yiwa iya sallama zai fita, nima na bude
baki da nufin ce masa sai ka dawo.Amma da
yake matina ce a raina sai kurum naji na ce
masa ka gaishe mun da matina.Har ya juya sai
naga ya tsaya cak, sanan ya waiwayo fiskarsa
dauke da murmushi ya furta cewa zataji in sha
Allahu.Ya juya ya tafi, ni kam kamewa nayi
tamkar gunki, a zuciyata tambayar kaina nake
dama mutun na iya kuskuren magana ya furta
abinda ke son zuciyarshi ya bar na saman leben
shi?Kash!Ban so nayi zarar bunun nan ba, abin
takaici harda murmushi na ambaci sunan
masoyiyarshi.
Kwana uku suka shude ina cikin damuwa,na san
Iya ta lura banza kawai tayi mun,narasa abinda
ke yi min dadi, ni ba fita nake ko ina