Showing 15001 words to 18000 words out of 23399 words

Chapter 6 - Darajar Yayana Book 3 compelet writing by Halima Abdullahi K Mashi .txt

kaina, shi wanan ya canza daga jin
kan ne?Koko isa ce tasa shi yin haka?Wata zuciya
ta ce koma me nene mijinki ne a yanzu.Tsayuwar
motar ne yasa ni bude ida nuna.A zatona in zai
fita dole ya sakar min hannu,amma har muka fito
hannuwan mu sarke, a haka yayi ta daga waya
na kalli gurin da muka zo, an rubuta Cristal
Garden da wani rubutu mai yi kala kala na
wuta.Usman ya shiga ciki ya fito sanan muka
shiga tare.Dam gurin ya cika da mutane an
wadata ko ina da kayan ciye ciye da na shaye
shaye, naga muta ne manyan mutane da banyi
tsammani ba.
Anci ansha kuma anyi wasa da kudi, sai dai duk
yanda abokan ya Aliyu suka so muyirawa yaki ko
mikewa tsaye.Dan haka duk wanda ya matsu da
ya yi mana liki sai dai ya ishe mu a kan kujerar
mu, abokan shi da kawaye na sun sha rawa.Sai
kusan sha daya a ka tashi, mu kam sai sha biyu
sanan muka tafi don sai da aka kwashe kowa.A
kofar gidan mu motar ta tsaya, na yunkura zan
fita, sai naji ya dafa hannuna, wato ya dora
hannunshi a kan nawa.Na kalleshi shima ya kalle
ni, dai dai lokacin Usman ya fita, da ma mun
sauke Abida a gida.Aliyu ya ciro wayarshi ya
haska fiska ta, ya cire hannunshi da ke kan
nawa, ya dora a kan kuma tuna ya shafa har
zuwa dokin wuya na.Sannan ya juya bayan
hannunshi ya shafi haba ta, dole na lumshe
idanuna abin sai kace a mafarki.Ya tsansa dan
manuni ya saka ya gewaye lebuna na, na bude
ido ina kallonshi, murya kasa kasa ya ce, ki bar
wayarki a kunne zan kira ki.A jiyar zuciya na
sauke, sanan na amsa a kasalance to.Tsakar
gidan mu cike da mutane duk sunyi shinfida sun
kwanta, kasancewar lokacin damina ne amma
anyi kwana biyu ba ayi ruwa ba.Don haka gari
duk ya dauki zafi.Na nufi uwar daka, nanma duk
jama'a ne kwance, gado na dai ba kowa.Na cire
kayan jikina nai daurin kirji sanan na fada kan
gado.Iya can na varo ta a falo tana yin sallar
nafila, a rai na na ce iya koda biki ba a daga
kafa.Filo na dauka na rumgume ina tuno
abubuwan da suka faru yau, tamkar almara ji
nake yau na zama mace sosai.Karar ringing din
waya ta shi ne ya dawo dani cikin hankali na, na
dauka cikin faduwargaba na ce salamu a
laikum.Muryarshi can kasa kasa ya amsa sanan
yace ke da waye ne a nan?Na runtse ido dan
yanda muyarshi take ratsa dodon kunnena, na ce
ni da mutane amman sunyi bacci sunyi shinfida
ne a kasani a gado nike, ya ce ok, kin san me
yasa na kira ki?Na ce a a ya ce, saboda mu
fahimci juna...
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347.
A raina na ce abin da ya kamata a ce shine a
farko ya koma karshe.Tamkar ya shiga raina.Ya
ce kila kiga abun babu tsari ko?Kafin na bashi
amsa ya ci gaba.Ni irin nawa tsarin kenan, kina
jina?Na ce eh.Yace to yanxu sai ki fada mun
dokokinki kafin kiji nawa.Da sauri na ce ya Aliyu
ai bani da wata doka sama da ta Allah da
manzonsa, wada suka tsara ita ce abin bina doka
ta ni kadai in bika.Gud to me kike so me bakya
so?Zan so in soma jin naka yaya, tunda kaine
babba.Ya ce, to da farko dai bana son kazanta,
duk inda zan shiga a gidan bana so in shaki wani
wari.Kuma bana so in ganki babu tsafta ko in
shaki wani wari daga jikinki, sannan ina son
komai a kan lokaci.Na san kin fi kowa sanin ni
dan oya oya ne, komai cikin hanzari bani son
kasala, bana son musu ko gaddama.Abu na kusa
da karshe bana son duk wani abu da zai shiga
lokacin aiki na, ina fata kin fahimta?Na ce eh.Ya
ce yan zu sai inji naki.Na ce, ni dai bai wuce uku
ba, duka da zagi ne bana so.Sai nayi shiru.Ya ce,
ina jinki, saura daya.Na ce imm.... Bashi kawai
ma.Ya ce a a, ki fada in nayi maki cikin rashin
sani fa?Bana son mu munafunci juna,fadamin
duk abinda ke ranki da xuciya daya.nace
amm...dama kishiya ce bana so dai,kuma bamuyi
sabo daxan fada maka ba.shi kanshi shiru
yayi,nasan yana mamaki ne don bai zaci jin haka
ba,a zuciyarshi shi kamshiru yayi saidai bai ji
wani mamaki ba saboda yasha samun case din
mata akan kishiya.ganin kishiya ce abu na karshe
da mata suka tsana.nima shiru nayi gabana yana
ta faduwa,tsai din dana ji araina na raya cewa
magana xai dankaramin mara dadi,can yace ba
xan yi miki alkawari ba in na duba cewa komai
na rayuwata rubutaccene tun fil'axal kamar
yanda yake ga kowa.kifahimta,baxan taba yi miki
karya ba,don kawai kiji dadi.sai dai shawara daya
xan baki,kiyi kokarin tsare duk hakkokina,ta yiwu
in kinyi hakan bazaki rage gurbin wata ba
Kuma kila baxan ji sha'awar karawa ba.(Lallai
yaya kazama abokona,muna da ra'ayi daya
dakai, dan haka me sona nima namiki nasiha
makamanciyar ta Yaya Aliyyu,kiyi kokarin
kyautatawa,tayanda zaki rufe idanuna daga ganin
dukkanin wata mace da matsayi irin na soyayya
bayan ke. ANaM Dorayi)
Nayishiru tabbas nasan gsky yafada,amma kishi
ne daninasan wanan tundaga ranar da kunnena
yaji ya Aliyu ya furta yana son aurena.can kasan
xuciyata tunani ne kada wata rana yace xai so
wata har ma ya aureta.duk sauran samarina da
duk wanda yaxo da niyyar aurena nakan fada
mishi koda na aure ka banason kishiya fa.Toh shi
xakin nawa ina naha fuskar fada masa,shine sai
yanxun...ya katse tunanina da cewa,nasan baki
fahimce ni ba akan batun kishiya,don haka a aje
zancan gefe muyi mai amfani.nima naji abinda
bakiso zan kuma kiyaye insha Allahu.kiyi baccinki
sai dasafe kar ki manta gobe akwai ranar yan
sanda.bikin da suka shirya mana,ina fatan zakiyi
shiri?muryata sarke nace Allah yakaimu goben.
shine ya katse wayar sannan nakashe tawa na
kwanta,kalamansa ne ke yawo cikin kaina na
damu da bai min alkawari cewa baxai min
kishaya ba har bacci yayi gaba dani.(kabwata duk
lokacin da saurayi yace bazaimiki kishiyaba to
kisani hakan mafificiyar karyace a hasashena,pls
kabwata karkisa saurayin yayimiki wannan
alkawari kawai dan gudun bacin ranki,ANaM)
Ya aliyu ya iya magana cikin natsuwa,kai inason
gayen sosai.
Dasafe kin fitowa nayi ina yin sallah asuba dama
komawa nayi nacigaba da bacci. da Iya ta tashe
ni sai na langabe nace mata kaina ciwo yake yi
nan ko banason tashine in ta aiki ga mutane. sai
kusan sha biyu sannan na tashi nayi wanka na
karya.Aisha taxo muka sha hira anan ma muka
xabi kawayanmu da zamu je bikin anjima
dasu.yau kam shigar Green da Golding nayi
nawani leshi mai kyan gaske,abinka da farar
mace kayan sun dauke ni duk da cewa wai farin
ne yacece injiwasu
Duk yau ban sa shi a idona ba sai yanzun da za
mu tafi., yau kam gadanga kusar yaki kakinsa
yasha na yansanda, ya iya aje hularsa a kai
tamkar sai da ya yi course din sata,wani dan
sanda ne ya jamu zuwa wajen, guri yayi
guri,Usman shi ya taho da sauran kawayena,
Police band sai tashi take ga wasu yan sanda
suna ta bin kida fareti. gurin zamanmu na
musamman muka nufa înda masu kidan suka
dafo bazanmu da kida. ya Ali da abokansa da
fareti suka yi tafiyar har zuwa gurin zaman har
wani yana cewa yakamata matar dan dan sanda
ta îya fareti itama . sun yi wasa kala kala har
wani wasan su wai lokacin suna makaranta suna
cin garin kwaki,anci ansha anyi rabon
abubuwa.sai bayan magriba muka dawo
gida.karfe sha biyun dare dai dai wayata ta soma
ruri da sauri natashi nadaga yace xo mana
natashi xaune na kalli shashin da Iya take, tadan
rumtsa kafin lokacin sallarta ya karato,Na tashi
sadaf-sadaf tamakar munafuka nafita, a kofar
daki nayi sallama, ya amsa na shiga.Kwance
rigingine na same shi yana danna wayarshi,
jikinsa sanye da farar singileti tareda gajeran
wandonta.Nayi saurin dauke kaina don kunnyar
ganinshi a haka.Na rusuna kaina a kasa ga ni
yaya ba tare da ya dube ni ba ya ce, tun cake
din da kika bani a baki dazu gurin party nan ne a
ciki na,yun wa nake ji.Na dube shi me zaka ci?
Shima sai lokacin ya dube ni, me kika ga ya dace
in ci?Na ce, ko za ka fara shan ruwan zafi tun da
ka jima baka ci abinci ba, saboda cikin ka
yawarware?Ya ce to yaya za ayi, na samu ruwan
zafin?Na ce sai na dafa maka, na mike tare da
ajiye wayata a gefe na nufi kicin, ina kunna risho
naji takun tafiya, sai ga iya tsaye a kaina ta ce,
na farka ban ganki ba lfy kika kunna risho?Na ce,
yaya ne ya kirani a waya wai yana jin yunwa shi
ne zan dafa mashi ruwan zafi , ta ce, hum!Ki dai
kiyayi kanki, kuma ri rage wanan barin jikin,
sanan kiyi maza ki dawo daki na ce, to.Ina
komawa dakin dauke da dan flaks dinsa na
ruwan zafin na same shi yana danne danne cikin
waya ta, na juyo na jawo kofi zan zuba masa ya
dube ni baki da numbata a she?Na ce ina da ita
mana.Ya ce in gani.Ya ciro number ya miko min
wayar, na amsa na danno sunansa inda na sa ya
Ali, ya ce ok, bani ruwan zafin, na zuba a kofi na
hada masa sanan na mika masa.Sai da ya amsa
ya kurba sanan ya ce, amma na zaci cewa na
wuce wanan matsayin na yaya.Na kalle shi eh
haka ne.Ya dauko wayarshi ya danna ya nunu
min numbata a wayarshi.Yayi saving dinta da
suna my choice, a fili nafurta my choice, ya ce
nima sai a canja min suna ko?Muka kalli juna
cikin ido sannan na soma danna wayata, ya ce
zauna sosai mana, sai kace ba dakin mijinki ba?
Na zauna sannan na soma rubutawa na sa
honey, sai na goge na sa darling, shima na goge
sai kuma na rubuta sweet Aly.Zan goge yayi zaraf
ya amshe wayar ta re da cewa in gani me kike
rubutawa kina gogewa?A fili ya ce sweet Aly.Yayi
dadi ki barshi haka.Ni kuma tuni na sunne kaina
cikin cinya ta don kunya.
Ya ce ai babu wani sauran kunya tsakanin mu,
kinyi alkawarin za ki rinka kirana sweet dinki har
gaban kowa?Na dubeshi cikin kunya sanan na
sunkuyar da kai ina wasa da gefen hijabina na ce
ba dai ga ban muta ne ba, yace to ni gaban kowa
zan ce maki my choice, sunan ya da ce?Na saka
yatsa a bakina ina dan wasa da shi,na ce me
yasa ka zabi ka sanya min zabin ka?Ya dan kara
matsowa, dan duk duniya ke kurum zuciyata ta
zaba har mamakin ki tai lokacin da muka taya
wai saida kikaimana yanga kafin ki amsa.Na
yunkura bari inje in kwanta, ya ajeye kofi bakya
jin dadin firar tamu ko?Ya ci gaba, kiyi hakuri
dani ban taba fira da mace ba shi yasa, na dube
shi tare da dan zare ido ya ce baki yarda ba ko?
Nace naga kana dan sanda ka ce baka taba fira
da mace ba?Amma ba wai ban yarda bane yayi
dariya gaskiya bana yi, tsakanina da mace sai dai
in matsalar da ta shafi aikina ne ta hada ko har
yanzu baki yarda ba?Na ce na yarda na mike
tsaye ya ce, firata ba dadi ko?Na ce, da dadi
mana.Ya ce to shi yasa kike so ki gudu? Iya ta ce
kar na dade,yace ta manta ni mijinki ne ya ce ok
sai da safe?Na ce tam, har na kai bakin kofa
yace, gaki dai baki son kishiya sai ina ganin ba
zaki iya kula dani ba.Ina tsoron kada hakan ya ja
maki kiashiya. Cak!Na tsaya cikin wata murya
wacce ban san ina da ita ba na ce, sweet Aly,
Allah zan iya kula da kai fa ka ji?Kasa amsa ni
yayi don jin irin muryar da nayi anfani da ita.Na
ruga da gudu cikin kunya shi kam shiru yayi yana
mama kin mata.Lallai mata abokan nishadi ne,
dubi yar hirar nan da yayi da yarinyar nan ya
shagaltar dashi ya koma kamar sakarai, yayi
murmushi sanan ya kwanta.Nima kwanciya nayi
ina tuno abin da ya faru tsakaninmu duk da
kallon da Iya ta bini da shi, da na shigo sai dai yi
nayi kamar ban lura ta ji haushin dadewar da
nayi a wurin yayan ba.Washegari ban tashi da
wuri ba sai wajen tara lokacin baki suna ta shirin
tafiya gida jen su.Sha biyu kowa ya kama gaban
shi, sai mu munata aikin gyaran gida ni da
iya.Kusan karfe uku na yamma ya kirani wai a
kwai fura ko?Don anzowa iya da fura da nono
lokacin biki, na ce masa nono yayi tsami, sai dai
in ya siyo yogot ya shigo da shi ya ce to.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Tunda na idar da la'asar na zauna zaman zabar
kayan da zan saka iya dai tana kallo na na sauke
akwatuna na zabo atamfa cikin kayan aure na.Da
na idar da sallar isha'i kuwa na shiga zabga
kwalliya ina ta feshe jikina da turaruka.Iya ta
shigo ta zauna bakin gado ta tsareni da idanunta
ko da bata fada ba nasan abinda kallon nata
yake nufi.,don haka nakoma nima bakin gado na
zauna tare da ajiye dan kwalin da na dauko zan
daura.Ta ce sadiya ni ba wai ina hanaki ki lura
da mijinki bane ko ki shige masa a ana fi so ki
bari sai kin tare, shi fa namiji babu ruwan sa da
zancen kunya, in baki ji nauyi na a matsayin
mahaifiyar Aliyu ba ai kyaji kunya na a matsayina
na uwarki.Saboda iya shege ko watsewa yan biki
basu tafi ba kin tafi dakin miji kin raba dare
saboda rashin kunya?Na sunkuyar da kaina rai
bace a zuciya ta na ce, har ga Allah shi yasa na
so in tare a daki na, ta ce daina bata rai, daraja
nike nemamaki da kima in kin tsare kanki har sai
kin tare kifi kima a idonsa, ga dai misali a gidan
ku.Kiji tsoron abinda ya faru da yar uwarki ta
zariya Harira ya faru dake, kan ta tare tayi ciki a
gidan mijin nata ya shiga yi mata wulakanci.Kin
manta banda ubanku tsayaye ne ai cewa zaiyi
cikin ba nasa bane, shi yasa in andaura aure ba
a tare ba mace ta mika kanta ba karamin so
mijin keyi mata ba za ya daraja ta.Wani dama
sha'awa ce ta kawosa gurin mace da ya biya zaiji
baya sonta, amma in tana gidansa fa?Ai yasan da
kunya ya ce yayi aure sati daya ya kori
matar.Jikina yayi sanyi, tabbas babu ja a batun
iya,kuma haka ne batun Harira, tayi goyon ciki a
gida ta haihu a gida ba ta tare ba.Kuma ya
saketa da kyar ya amshi cikin amma har yanzu
dan yana hannun uwarta agidan mu ita kuma
tayi aure a Hunkuyi.Na saka kaya a sanyaye na
zauna ina kara nazarin abubuwa.Har dakin iya ya
shigo suka gaisa ya ce, ina yarinyar nan?Ta ce,
tana ciki.Kamar daga sama sai naji ya ce, my
choice.Na fito da sauri tare da amsawa, duk da
nasan iya bata san me yake nufi ba.Amma tana
da saurin dago abu, zata san cewa suna ne na
musanman ya sa min, na amsa sannu tare da
gaishe shi.Ya miko min yoghot din in kin gama ki
kawo min.Na ce to,ya dubi iya bari nayi wanka.
.Na shiga da sallama, yana zaune kan sallaya da
alama salla ya idar, na ce baka sami jam'i bane?
Yace, shafa'i da wutiri nayi.Zan tsugunna ya ce
zauna a bakin katifa mana.Kina yi ya ce, sai kace
ba dakin mijinki ba.Ya gyara zama kan sallayar,
sanan ya dauko wata laide dake gefe ya bude ya
ciro kunshin takarda ya warware yana fadin.Kin
ganni da son kilishi shi yasa na saimuku
Balango.Ya dauki daya ya saka a bakin shi, zo in
baki a baki. Nace na koshi ni na ci abinci tun
dazu.Yace wanda kika ci da ban nawa nama ne,
matso kiji.Na dan sunkuyo ban sauka daga kan
katifarba, shima ya matso ya miko nannu ya sa
min abaki, na amsa tare da rufe fuskata cikin
tafukan hannaye na.Ya ce fada min gaskiyarki, ni
dake yanzu ba wani batun jin kunya. Kin kosa ko?
Na daga kai alamun eh, yayi yar dariya kinyi kyau
da wanan kwalliyar ta wace?Nasake makale kaina
cikin cinyoyi na, na ce eh.
Ya matso sai kurum naji ya kama ka fada ta, ya
saka dan yatsansa yana bin zanen fulawar, jikina
ya dauki bari don ji nake tamkar susa yake
min.Shima nasan yaji abin da naji don naji
muryarshi ta dan sarke.Ya ce wata gwana ce ta
zana maki wanan fulawar?Na ce wata yarinya
ce.Ya ce, yayi kyau.Ina son farar mace na dan
ware ido ina duban shi.Me yasa?Ya saki kafada ta
Ra'ayi nane kawai ba dan komai ba, ke fa?Na
sun kuyar da ka, kalar ka nafi so a cikin
maza.Yayi yar dariya, wace iri ce kala ta?Na ce,
wankan tar wada baka cikin farare kuma fara
cikin bakake.Ya tashi daga mazaunin shi ya dawo
kusa dani kan katifar.Kina nufin duk mun dace da
zabin mu?Ban iya amsawa ba saboda yanda ya
kusance ni, jiki na da na shi har suna haduwa.Ya
saka hannun shi a kafada ta ya manno nijikin sa,
fada mini gaskiya can dama kina sona?Duk da
halin da nake ciki na faduwar ga ba sabo da irin
yanda ya makale ni, bai hana ni tunanin wanan
mutimin ya cika tam baya.Ko yana zaton nima
mai laifin ce?Ya dago fuska ta, kalli cikin ido na ki
fada mun. Zan gane in kinyi karya kwa yar idonki
xata nuna mun.Naji mamakina lokacin da nake
furta can dama ina son ka kai fa kana sona?Cikin
wata ma yaudariyar murya nayi maganar.Kurum
sai na fuskanci le bunan shi a kan nawa yana yi
mun sumba, lamarin ya zo min sabo, ko na ce
bako.Ya dinga yi mun wasu abubuwa masu
firgitani har na zama bani da karfi.Tsoro na daya
kada ya gota daga haka, saboda ina tsoron
Iya.....zandakata Anan,muhadu a lokaci nagaba
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347




Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100






Darajar Yayana1-04
Posted by ANaM Dorayi on 10:48 PM, 16-Mar-16
Under: DARAJAR 'YA'YANA
_______________NA
_____HALIMA K MASHI
Nayi karfin halin zame jiki na daga na shi,
yakwanta rigingine na mike sai da safe.Ya miko
hannu ya riko nawa hannun, cikin wata rikitaciyar
murya ya ce, ki zo nan mu kwana.Da sau ri na
ce, tab Iya ba zata yarda ba.Ya ce, ina ruwanta,
ni ba mijinki bane?Na ce to ai ban tare ba.Ya saki
hannu na.Da sauri na fice.Na tabbata in na shiga
daki haka iya zata fahimci wani abu, don duk
kwalliyar fiskata ya goge min.Don haka sai na
bige da sabar buta na nufi bandaki, na zo nayi
alawala.Ina shiga uwar daki ta bini da kallo tana
kwance kan gadonta.Na cire kayan jiki na dauko
rigar sallata nayi shafa'i da wutiri.Ta tabe baki
bata dai ce min komai ba ko takula duk na
tsargune?Oho.Da kyar na samu bacci ya soma
dauka ta sabo da tunanin abubuwan da suka
faru tsakani na da shi.Shigowar sakonshi dan
sautin ya farkar dani, na bude na duba cewa
yayi, kin hanani bacci my choice kixo ki taima ka
min please.A raina na ce mai zanyi maka sweey
Aly, ka dan bani lokaci mu tare, kiranshi ne ya
katse tunanina,sa sauri na farka dan ina tsoron
kada ringing din ya farkar da iya, duk da cewa na
san tana jina don bata da nauyin bacci.Can kasan
makoshi na nayi sallama ya amsa muryarsa a
raunane, har mamakinsa nake ina girman kan?
Ina isa da jin kan?A she dai mace dai ita ce
namiji.In ba mace rayuwar namiji ragaggiya ce.Ya
katse mamaki na da cewa, kizo kinji?Ba zan iya
bacci ba ki taimake ni.Nace iya fa tana jinmu ka
bari sai tayi bacci.Ya ce dagaske zakixo in jira ki?
Na ce eh.Sai ya yanke niko gaba daya ma sai na
kashewayar, na amsa masa cewa zan xo ne
kurum amma ba dan zan je din ba, sai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login