Showing 21001 words to 23399 words out of 23399 words

Chapter 8 - Darajar Yayana Book 3 compelet writing by Halima Abdullahi K Mashi .txt

ba, ba TV
Garemu ba bare nayi kallo, ta lalace ni kuma ba
ma abociyar radiyo ba.Wani kayan haushi ko
littafi na dauka da sunan karantawa sai in kasa
fahimtar komai.Na san kaina ina da shegen kishi
na ban mamaki, ko saurayina naga suna yawan
gaisawa da wata budurwa hankalina kan tashi,
bare a ce miji na.Tabbas da Ya Aliyu ya skar min
fuska da tuni na same shi munyi ta, amma ya
Aliyu ya wuce haka.Ku ziyarci blog dinmu domin
karanta Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Cikin sauri sauri ya Aliyu ya shiga shashin su, ya
kalli sajan Ado ina barawon?Suka kaishi ya
shiga.Ya tsura mutumin ido, aransshi ya ya ce
kai wanan mutumin baiyi kama da barawo
ba.Ya kalli Sajan, kawo abin zama, sai da ya
zauna sanan ya kalli mutumin.Kaine barawon fili
ko?Hawaye suka soma kwarara daga idanun
tsohon, don bakin cikin sunan da aka kirashi.Ya
ce cikin rawar murya, ranka ya dade ni ba
barawo bane, ban taba sata ba.Aliyu ya juya
kulkin dake hannunshi ya dan jefashi, sanan ya
cafke.To baba ya akayi har ka mallaki filin da
kake gini?Ya ce, ran ka ya dade filin nan na
gajeshi ne a gurin mahaifiyata, don mahaifinta
manomine.To ina zaune a gidan haya ga iyali,
ina da mace daya ga yaya takwas.Yan samarin
yara na a makota na roka sunakwana, ganin
kullum nauyi na karuwa, sai nayake shawarar
gina fili na ko da daki biyu ne rak.Na soma gini
ni da yaya na, dan sana'ar mu ke nan ta
leburanci da yaran.Mun soma ginin kawai sai
ganin yan sanda nayi sun xo kamani, ban san
abinda nayi ba.Aliyu ya ce, to baba naga
takardar bayanin laifinka, naga cewa ana
zarginka da laifin yingini a filin da ba naka ba,
filin tsohon jami'in dan sanda ne.Tsoho ya ce,
dana wlh wanan filin nawa ne, kowa ya sani a
unguwar mu ina da takarduna ina da
sheduna.Kuma ni da aka kawoni nan ba a
tambayeni ankawoni nan aka jehoni ne
kawai.Babu wanda yaji ta bakina.Aliyu ya ce ka
tabbata kana da takardu da shedu?Tsoho ya ce
ina dasu ranka ya dade.Aliyu yace zamu mikaka
kotu kuma in sha Allah zan tsaya maka sai kayi
nasara.Cikin izza ya nufi wajensu Sajan Ado,
yace sajan, yace Sir, bayan ya kame.Aliyu yace
waye ya kawo wanan mutumin?Sajan ya ce,
barawon fili?Aliyu ya ce, eh shi.Sajan ya ce CP
ne yasa a kamo shi.CP da kanshi?Ya tambaya
cikin mamaki.Yace shi, amma AC ne ya tura.Kan
Aliyu ya daure, ina takardar bayanan da kuka
bani dazu?Sajan ya sake daukota, Aliyu ya kalla
ya sake karantawa, wanan rubutun kofur bala
ne ai, sajan ya ce, eh, Aliyu ya ce kira min
shi.Ya juyya ya koma office din shi.Ya tsare
kofur da idanun shi waddanda basadaukar raini,
kainne ka rubuta wanan takardar ko?Ya kame,
eh, nine Sir, ya juyya mishi baya, amma ai baka
tambaye shi ba ka rubuta da yawun shi.Ko
menene dalilinka?Kofur cikin daburcewa ya
ce,Sir ai nima AC ne ya ce na rubuta haka, sabo
da raini mutumin yake so ya kawo wa tsohon
mataimakin IG.Aliyu ya daga hannu da nufin
dakatar dashi, tsaya min kowa ya cuta sai a ari
bakinsa a ci mai albasa?Ya ninke takardar ya
zura cikin aljuhunsa, yace dauko wata kazo muje
ka sake rubuta ainihin bayanin da yake daga
bakinsa, mu masu kare Al'umma ne da
rayukansu ba masu danne masu hakkin ba ne
da kuma kashe su.Kofur dake biye dashi ya ce,
sir, wanan tsohon mataimakin IG yana yawan
kawo mana matsalolinshi a nan, kullum
maganarshi bata wuce an cuceshi.Ku ziyarci blog
dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Aliyu ya ce dan ya taba zama jami'in dan sanda
bazaiyi anfani da wanan damar ba, sanan yayi
anfani da mu.Alkawari na daukarwa kaina ba
zan bar zalunci ba, matsawar naganshi zanyi
yaki dashi.Aliyu ya tsananta bincike kuma cikin
kwanaki kadan yagano cutar tsoho wanan
jami'in ke son yi, don hakka ya tattara dukkan
bayanai ya turasu zuwa kotu.Gobe da safe ya
tabbata in anje can tsohon zai sami hakkinsa,
saboda bayanai da hujjojin da Aliyu ya
hada.Yana tsaye a bakin titi zai hau a caba zuwa
gida Inspector Kamal ya sameshi a gurin, ya ce
ranka ya dade zuwa yanzu yakamata a ce ka
mallaki abin hawa ko da mashin, amma in san
samu ne a ce kana da mota.Aliyu yayi
murmushi, kada kadamu, ko mai lokaci ne, ya
ce in dauko maka na aiki mana ba sai ka sha
mai ba?Aliyu ya ce, a a na aiki anyi shi ne dan
aiki kawai.Ispector ya ce, kana birgeni Sir, komai
kana barinsa a muhallinsa.Lokacin da aka raba
mana mashina baka zoba.Aliyu ya ce, ko ina
nan ba zan amsa ba, don bana son bashi.Ya
karasa zancen tare da tare dan acaba.Wayyarshi
ta dauki tsiwa, ya cirota cikin hanzari ya daga
saboda ganin sunan AC, hakuri ya baiwa dan
acaban, sanan ya komaciki kamar yanda AC ya
bukata a cikin officeya same shi, kai kawo yake
ransa a bace ya dubi Aliyu.Me yasa ba bada
damar a kai barawon filin nan kotu?Aliyu ya ce,
angama bincike ne sir, sanan doka ta hana a
tsare mutum tsawan lokaci ba tare da an kaishi
kotu ba.AC ya ce, na san dai na rigaka sa kaki
ko?Bai jira amsa ba ya ci gaba da cewa, don
haka kasan na rigaka sanin doka.Ya koma
kujerarshi ya zauna.Wanene ya hada binciken?
Kai kasan ma da wa yake rigimar?Kasan filin
wayake son kwacewa?Aliyu ya ce, nine da kaina
nayi binciken sanan nasan rigimarsu shi da
tsohon IG ne, kuma CP ne ya sa a kawoshi.AC
ya ce, gud, to zan sake mai maita maka, in an
kawo mai laifi da umurnin CP dan Allah ba
ruwanka da shi, in zaya shekara.Ran Aliyu ya
baci, ya ce, Sir, amma ba akan haka mukayi
rantsuwa ba.AC ya daga masa hannu ban ce
maka inason tunatarwa ba, sai dai ina son
kasani ka kusan kai CP bango, dan kana son
shiga cikin lamarinsa.Sanan kayi hanzarin cire
kanka daga cikin lamarin tsohon, ka barsa yayi
nashi binciken.Shiru Aliyu yayi, amma ji yake
tamkar ya kama da wuta don zuciya.AC ya ce,
ka iya tafiya.Aliyu ya fice da kunan rai.Matina ta
hangoshi cikin sauri ta bishi, yana tsayawa a
bakin titi tana tsayawa, ta ce barka da warhaka
yallabai.Ya furzar da wani huci mai zafi, sanan
ya ce barka dai.Tace ina tuni yallabai ya runtse
ido don yanason saita zafin da zuciyarshi ke
yi.Baya so ta fahimci yana cikin damuwa, sanan
ya budesu sun kada sunyi ja, sanan ya ce
matina zanfiso mu zauna a matsayin abokai, na
fada maki bani da sha'awar auran mata
biyu.Ina yi maki adu'ar samun mijin da ya
fini.Ta ce, samun kamarka ne yallabai sai an
tona, kunyi karanci a cikin al'umma.Ba duka
namiji mace kamata zata bashi kanta ya kauda
kai, har yanxu ina tuna ranar, ranar da na fada
maka ni da kai muyi soyayya koda bamuyi aure
ba.Ku ziyarci blog dinmu domin karanta
Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Na fada maka cewa wata gara basa da zan
maka shi ne, zaka iya yin duk yadda kake
sodani na mallaka maka kaina, amma sai kayi
mun nasiha ka kuma nuna min cewa addininka
ya yi hani da hakan.Na sami kaina da sonka
tare da son addininka, sanan cikin aikinka kowa
yasan kana kwatanta gaskiya da amana.Ina
tsoron in auri wani cikin masu addininku ya sake
ni, dan ku hausawa ance kuna da sakin aure
amma kai nasan ba zakayi haka ba.Aliyu ya
kasa kallonta dan ta daureshi da jijiyoyin
jikinsa.Ya ce, Matina ki amshi addinina da zuciya
daya, sanan kisa a ranki zaki sami mijin da ya
fini, nima zan tayaki da adu'a.Ta gyara tsayuwa
kada ka damu, ni zan ci gaba da zaman samun
irinka, alfarma daya nake roko in zaiyuwu, in na
kiraka ka daga wayata.Sanan in kazo nan muke
rinka gaisawa.Ya ce dan mun hadu mun gaisa
ba damuwa,abin da zaiyi dan wuya ki rinka
kirana ina da mata, nasan bazata so hakan
ba.Ta rausayar da kai gefe, cikin raunaniyar
murya ta ce, na gode,ka fadiwa matarka cewa
ta rikeka da kyau, dan tana cikin matan da
sukayi sa'ar zuwa duniya.Murmushi yayi duk
lokacin da kuka hadu saiki fada mata da kanki,
na barki lfy.Yana kan mashin yana tunani ko me
yasa yake samun irin wanan matsalar?Mata suyi
ta sonshi suna binshi, amma shi bai damu da
su ba.Matina yana kulata ne saboda musulantar
da take sha'awar yi, ya san in yazama sanadiyya
zai sami ladan hakan.Daga nan tunanin sa ya
koma kan matsalarshi ta office, in dai da irinsu
AC da PC anya kasar nan zata gyaru?Lallai
kasarsa Nageria tana cikin wani hali, kullum
burin nasama ya danne na kasa, sam ba a son
gaskiya.In ka tsayawa halas dinka sai mutane su
rinka yi maka kallon dan kauye.Ya girgiza kai
sakamakon tuno tsohon nan da yayi, shi da
gaskiyarshi da filin sa da komai ba a tausaya
masa ba, kasancewarshi mai rauni ana neman a
zalunce shi.Mai dama yana anfani da damarsa
gurin cutar mai rauni, yasan in ba wani ikon
Allah ba tsohon nan ya rasa filinsa kenan, in
yasamu ya fita da ransa kenan.Duk lokacin da
irin wanan ta faru sai yaji tamkar ya bar aikin
dansanda, amma da ya tuna kudirinshi na kawo
canji da gyara, sai ya hakura, da wanan sake
saken ya isa gida.
Niko tun lokacin da na furta masa cewa ka
gaishe da matina cikin kuskure, ban sake yarda
mun hadu dashi ba.Kusan kwana uku wasan
buya muke yi har iya ta fahimci cewa na guje
masa, amma bata nemi jin ba'asi ba, yi tayi ma
kamar bata san me ni ke yi ba.Sam ban zaci
dawowarshi a wanan lokacin ba, domin cikin
kwanakin nan sai dare yake dawowa.Ni kadaice
a gidan,Iya tun bayan la'asar sun tafi Asibitin
dutse duba wata makociyarmu da bata da
lafiya.Sun tafine da ma da sauran
makotanmu.Na wanke hijabaina da na Iya ina
shanyawa,daga ni sai best, zanina kuma iyarshi
kugu.Ina shanya ina mitar cewa iya sunje sunyi
zamansu, nasansu da son tafiyar kafa, yanzu
haka ma da kafa suka tako.Banji sallamarshi ba
sai dai naji ya ce ina suka tafi?Na waywaya na
kalle shi, da gudu na shige daki dan kirji na duk
a waje yake.Dan murmushi yayi sanan ya shige
dakinsa.Ina zaune bakin gado ina kallon jikina
sai ganin shi nayi tsaye a gaba na har uwar
daki.Ku ziyarci blog dinmu domin karanta
Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Naja hijabina, ya ce ina tambayar iya kina gudu?
Ya hade fuska tamkar bai taba dariya ba.Tsoro
ya darsu a raina, cikin in ina na ce,Asibiti suka
tafi.Ya ce, dan kada ki bani amsa shine kika
kwasa da gudu?Nayi shiru, ya ce kin min
banza.Nace yi hakuri dama zan dauko dan kwali
nein daura.Ya ce, ok, ni zaki boye min gashin
kanki?To ajiye hijabin in ga gashin tunda halas
dina ne.Gabana ya soma faduwa, na zame
Hijabina ya ce ashe ma ba wani gashi kike dashi
ba, cire hijabin daga jikinki in gani.Na kalleshi da
sauri ya kauda fuska yana yatsina baki, sai kace
zai ga abin kyama.Na cire hijabin na ajiye cikin
sauri kuma na sa hannuna na rufe kirjina.Ya ce
cire hannunki.Na cire tare da runtse idanuna.Sai
kurum naji yasa hannu ya turani baya, na fadi
rigingine na bude idanuna da sauri ina tsoro,
yasa hannu ya janyo best din sai ta yage, kirjina
ya bayyana.Tsayawa yayi yana kare mun kallo,
ya tabe baki, dama best din taki rubabiya ce?
Sallamar iya ta tsakar gida ce ta sani tashi
zumbur, na dauki hijabi saka.Cikin tsoro mai
tsanani na ce ga iya nan.Shi kam ko a jikinshi.Ya
tabe baki tare da daga gira sai me?A zato na bai
fahimci nufina ba, don haka sai nayi nufin
fahimtar da shi katafi da sauri kada ta ganka a
nan tayi zaton ko wani abu ne.Sai naga kurum
ya zauna bakin gado, na zaro ido dai dai lokacin
da ta shigo falo tana cewa Sadiya ina kika shige
ne?Kin ganmu sai ynzu?Da sauri na fito cikin in
ina na ce gani nan, kun...kun dawo?Eh, lafiya
na ganki a hargitse?Ta ce ba ko mai.Na yi
waje.Ita kuma ta nufi uwar daki, gabana yana
faduwa.Tana shiga ta ganshi zaune bakin gado
yanawaya, ta ce au, ka dawo?Ya ce, eh, na
dawo tun dazu, waye babu lafiya kika tafi
asibiti?Tace matar mai besfa ce a asibiti mukaje
duba ta.Ya ce, Allah ya bata lafiya.Ya mike bari
in karasa masallaci.Sai tin kunne na naji
maganar shi, a hankali yace sarkin tsoro.
Sam ya kasa bacci abin da ya kalla daga
yarinyar kurum yake tunanowa, juyi yayi har
gari ya waye sai ya dauki waya da nufin kiranta
dan yana togon cewa ita din halas dinsa ce.Sai
kuma ya tuna cewa yarinyar ba zatazoba, sanan
ga iya, kai!Shi fa ba zai iya jira sai sun tare
ba.Da safe naje kai masa abin kari, lokacin ya
gama shirin fita kawai zaiyi, ya amshi kofin daga
hannuna ya kurba.Sanan ya kalleni kin kawo a
latti, kin san da wuri nake fita. Na ce, a
shanarmu ce ta jike shi yasa, sai da masu shago
suka bude iya ta fita ta siyo.Ya ce my choice.Na
kalleshi zan sunkuyar da kai, ya ce a a kada ki
sunkuyar da kai, kalli cikin idona, bana son
wanan sunkuyar taki tana cutar dani.Na kalli
idon shi, ya ce yau ina bukatarki, na gaji ina da
mata kullum nine cikin azumi.Nayi kwalkwal zan
soma kuka, ya tsareni da idonshi, ya kuma
hanani sukuyar da kai.Cikin raunaniyar murya
na ce, kasan dai iya ba zata bari ba.Ya ce daina
karya da iya, na gano ma ba ita take hana ki ba
tun da ranar nan in an ji ta ce ki zauna da ni,
lokacin bani da lafiya.Ya mika min kofin tare da
cewa, zan fada mata, jeki abinki.Na tafi ina
mamakin shi, musanman da naji ya ce zai
fadawa iya zanso inji ko me zai ce mata na kasa
karyawa don zullumi, ina ta juya biredin dake
gaba na, kamshin turarenshi ne yasa gabana
faduwa.
Ya ce, iya na tafi.Ta ce to auta na, Allah ya
tsare.Ya ce, amin.Yana wucewa na sauke a jiyar
zuciya.Cikin jin dadi na gutsire biredi, na dago
kofin shayi na kurba sai naji takun sawunsa ya
dawo, take naji shayin ya sane.Ya ce au, na
manta iya.Ta ce, na'am iya za a zo a dauketa
taje ta gaida matar oga, ko bani ba wani zaizo
daukarta. Na kalli iya, shi dama vai jira amsaba
ya tafi, ganin kallon da take min sai na tsargu,
na taihashashen baki muka hada.Don haka na
ce, iya ke ce masa ba zanje ba,Allah ni bana son
xuwa.Ta harareni, bakya son zuwa ne kika bari
ya tafi baki ce ba zaki ba, sai nice zance karki
je? Bayan kun kitsa abinku?Ta taba baki haba
yayan nan, na fa rigaku zuwa duniyar har da
kuke son maidani wata sakara. Na ce iyya Allah
ba haka bane, ba mu kitsa komai ba, ni bansan
ko mai akai ba, ban san da wata magana ba sai
da yayi yanxun. Ta ce kwaji da shi, nifa bance
kada kije ba, ke da mijinki zan hana ki?Ta fada
cikin gatse sanan tayi tsakar gida tabarni zaune
cikin damuwa.Da naga har la'asar babu wanda
yazo nemana, kuma shi bai dawo ba, sai naji
dadi kuma na dan saki jikina. Cikin haka wayata
ta fara ruri, na daga a raina ina adu'ar Allah
yasa ya ce an fasa.Sai naji ya ce ki shirya
Usman zaizo ku taho.Sai da na daga murya
yanda iya zata jiyo, sanan na ce, yaya, Allah iya
ta ce bazanje ba. Iya daga inda take ta ce, a a
ba ruwa na ni Sa'adatu, ban hanaki ba ni ko
baku hada baki ba ni yar bada shawara ce.Yace
to najiyo abinda iya ta fada, don haka na baki
minti talatin ki shirya.Sai ya kashe wayarshi.Na
ce na bani yanxu yaya zanyi?Don Allah ku bani
shawara, inbi mijina ko in nunawa iya
harshashenta ba haka bane?
Taku Halima K/Mashi kemuku godiya. Awanna
gabarma Kanwarku Sadiya tana neman shawarar
ku, Saimun hadu a cikin littafi na biyu.Ku ziyarci
blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347


Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100

6
7
8

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login