Showing 6001 words to 9000 words out of 33825 words

Chapter 3 - INDO A BIRNI BOOK COMPLETE 2020 by Rasheedat Usman.txt

20 Jan 2025

8589

Ni, domin ke ɗin shugaba ce dake Adalci ga duk na ƙasa dake, Allah ya barmu tare Aunty nah.






*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________




*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________


*P* 5️⃣ ➡️ 6️⃣


Taɓa bakin ta indo tayi tace.


" Oh wannan Azzalumin ne ya Tanimu, yamin haka da baki, Kuma wlh na rantse da Allah sai na bawa tumakin sa maganin ɓera sunci sun mutu, badai shi azzalumi ba.
Wlh saiya gwammace bai taɓa ni ba.


Zaro idon sa, Mustapha yayi, Yace.


" Ke mahaukaciya, ke yanzu idan aka barki sai ki kashe masa tumaki, dake kema tinkiyar ce, hankalin ku ɗaya da tumakin, amma dai Allah ya Kawo Miki shiriya, dan wlh iyayen ki suna fama da ɓakin cikin ki, sai dai Allah ya basu hkrn zama dake, iya gama faɗin haka ya buɗe motar sa da niyar shiga, indo tayi carap tace.


" Dan Allah ya Mustapha karka tafi wlh ban gaji da ganin ka ba.


Tsuka Mustapha yaja tare da shigewa motar sa, yaja da ƙarfi, duk ya bule Indo da ƙura, bin motar Indo tayi da gudu tana.


" Ya Mustapha ka tsaya dan Allah na manta bance maka, *kifiyar Sonka ta soke ni a ƙirji na, Wlh ina Sonka sosai har cikin ƙahon Zuciyata*.


Shi kam Mustapha baima san tana yiba, dan tuni yayi gaba Abinsa, juyawa Indo tayi Ranta a haɗe, cikin takaicin tafiyar Mustapha, gashi wannan zuwan da yayi basu wani haɗu sosai ba, dawa Allah zai haɗa Indo idan ba Zainabu ba, can ta hango Zainabu tsaye ita da, Hansai suna zance, lallaɓawa Indo tayi yanda Zainabu baxata ganta ba, bare ta gudu, ita ko Zainabu sam bata wani lura da Indo ba sai ji tayi an tsakomo ta.
Ware idonta Hansai tayi cikin jin tausayin Zainabu.


" Uban waye na kama dan kutumar ubanki, ƴar durun uwa, da kin zata kin tsokaneni a banxa ne, to wlh yau na lahira saiya fiki jin daɗi.


Ƙoƙarin kwacewa Zainabu take hanun Indo sai dai ina Indo tafi ƙarfin ta, dukan Zainabu Indo take tsakanin ta da Allah, yayin da ta wurgar ta kasa, ta ɗane ruwan cikin ta, sai dukan bakin ta take tana cewa.


" Dan ubanki akanki zan huce haushi na yau, gobe Uwar ki Hali zata ƙara zuwa gidan mu kai ƙarata, na kuma ƙara tareki naci ubanki, karku fasa karna fasa, muga nida ku waye zai gaji.
Sannan ta sauƙa da ruwan cikin Zainabu.

Harara ta zabgawa Hansai tace.


" Ke kuma matsa ki bani waje, kema kinyi Sa'a, Wlh da Mai Gari ya kama Baba na, da kema naci naki uban.


Ita dai Hansai bata kula Indo, ba har tayi tafiyar ta.


Hansai ce tace


" Ki tashi kiyi hkr, kema Zainabu meya kaiki tsokanar Indo, kinsan dai Indo tafi ƙarfin ki, maza ma yaya suka ƙare da ita bare kuma ke.


Kuka Zainabu tasa, cikin jin haushin dukan da Indo tayi mata,
Rabuwa sukayi da Hansai kowa ya kama hanyar gidan su.


Da kuka Zainabu ta ƙarasa wajen Goggo Hali.


" Lfy Zainabu meya same ki, zaki shigo min gida da kuka, cewar goggo Hali.


" Ba Inda bace, ta kama ni da duka, wai gobe ma ki ƙara kai ƙaranta gidan su, itama ta ƙara kamani da duka.


Sallallami Goggo Hali ta ɗauka, sannan tace.


" Kinga Zainabu ki haƙura ki bar Indo da Allah domin kuwa Indo shaiɗaniya ce, Babu mai iyawa da ita sai ALLAH.


Tura baki Zainabu tayi tace.


" To Allah ya isa na Wlh.


" Shikenan zai kuma isar Miki.




Misalin ƙarfe Uku na Rana Mustapha ya shigo cikin dutse, Shango Estate na gani Rubuce a mashigar Inda zai shigan, gidaje ne da yawa cikin Estate ɗin, wani gida mai shegen kyau naga Mustapha ya shiga, yara biyu ya samu a compaunt ɗin gidan suna ƙwallo, da gudu yaran suka taho wajen sa, suna Oyoyo yaya Mustapha, parking ɗinsa ya gyara, sannan ya fito yana dariya, ɗaya bayan ɗaya Mustapha ya ɗaga su yana cewa.


" Autan Momy, yau Babu islamiyya ne, na ganku a gida.


Sharif ne yace.


" Babu yaya, malamin namu baban sa ya mutu, wai sai anyi Uku mu dawo.


" Ayya Allah ya jiƙansa da rahama, ina Momy?


Ishaq ne yace,


" Tana ciki yaya, Aunty *RAUDA* ma taxo jiya take tambayan ka, Momy tace, ka tafi ƙauye wajen *Hajiya Innah*.


" Sannun ta da zuwa to,
Tare suka ƙarasa makeken falon, wanda ya tsaru da Adon pink da purple, falon yayi kyau sosai, idan ka ɗaga kanka sama kuma, tozali zakayi da wani ƙaton Elagement, Kama ce tsantsan tsakanin su kamar a raba ruwa biyu, haka suke, basu da wani banbanci, koda ta yatsa ne, gefe ɗaya anyi Rubutu da manyan baƙi, *MUHAMMAD MUSTAPHA AND MUHAMMAD HABEEB*, sai kuma gefe duka Family ɗin gidan, wata kyakkyawar mata na gani fara sol daga ganin ta kasan bafulatanar Asali ce, sai wani Dattijo shima kyakkyawa wankan tarwaɗa, sai kuma wata yarinya ƙarama, da kuma ƴan biyun ta Hudu Habeeb Mustapha sai Sharif da Ishaq.
Muryar Momy yaji a bayan sa tana cewa.


" Mustapha yaushe ka shigo.


Murmurshi yayi yace.


" Yanxun nan shigowa ta, na same ku lfy.


" Lfy lau yasu Hajiyan ka barta.


" Tana lfy sai darun tsufa ni wlh Momy na gaji da zuwa wannan ƙauyen gaskiya, Daddy ya daina tura ni, kullum naje ƙauyen nan da ciwon kai nake dawowa.


Murmurshi Momy tayi tace.


" Mustapha idan bakaje ba waye zaije, kasan dai *Sharifa* baxata iya zuwa ita kaɗai, haka kuma Sharif da Ishaq sunyi ƙanƙanta, Habeeb kuma baya ƙasar ma gaba ɗaya, tunda kaine babba, ai dole kuma kaje ka.


*RAUDA* ce ta fito daga kitchen ɗin Momy hanun ta riƙe da cooler, dariya tayi tare da cewa yaya Mustapha sannu da dawowa, Haɗa Ransa Mustapha yayi, yace


" Yawwa sannu, tare da kawar da kansa gefe.


Jikin *RAUDA* ne yayi sanyi ganin irin amsar da Mustapha ya bata cikin hadewar fuska, gashi ita kuma Allah ya ɗaura mata jarabawar soyayyar sa, amma sam Mustapha baya sake mata fiska Asali ma idan tana waje bai cika zama ba, ta rasa Meye aibun ta da Mustapha ke gudun ta.


Shigewa tayi, daining ta ajiye, foodplast ɗin dake hanun ta, ta ƙara komawa kitchen ɗin domin kwaso sauran Abincin.


Shigewa ɗakin sa yayi, ba tare daya ƙara wata magana ba.


Ran Momy sam baiyi daɗi ba, domin kuwa bata jin daɗin abunda Mustapha ke yiwa RAUDA, gashi ita kuma tana da burin ganin sun haɗa kansu kodan ƙudirin dake ranta na Son haɗa su, Aure.


RAUDA jikin ta a sanyaye tace Momy na haɗa komai a daining bari na shiga ɗakin ya Mustapha, na share masa.


To Momy tace mata sannan ta haura sama ita kuma RAUDA tayi ɗakin Mustapha.


Fitowar shi kenan daga tollet, ɗaure da towel, a ƙugun sa, yaga mutum Zaune gefen gadon sa, ta ƙurawa pic ɗinsu shida Habeeb ido.
Tsuka yaja mai ƙarfi wanda ya dawo da RAUDA cikin hankalin ta.


" Me kike nema a nan? ya jefo mata tambaya.


" Babu komai, daman ɗakin zan gyara maka sannan na sanar da kai, Food is ready.


" Na gode to, amma sharar bana buƙata, abinci kuma na ƙoshi, kina iya tafiya.


" But amma ya Mustapha.


Da katar da ita Mustapha yayi ta hanyar cewa, sorry Please leave me alone, kaina ciwo yake ina buƙatar hutu.


Cikowa idon RAUDA yayi da hawaye Cikin tausayin kanta na *Son Maso wani*








🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻
Afwan Fan's wlh yau na wuni a makaranta ban samu na muku typing mai yawa ba, ku biyo ni next page gobe.




*Yawan comments yawan typing*




*Share*
*And*
*Comment*


*Alƙalamin Rasheedat Usman✍🏻*


*(Ummu Nasmah)*
[1/5, 2:39 PM] MAKAMAR KAINUWA 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻: 💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻


*I͓̽N͓̽D͓̽O͓̽ A͓̽ B͓̽I͓̽R͓̽N͓̽I͓̽*
💅🏻💅🏻💅🏻💅🏻




*Na*


*r̸a̸s̸h̸e̸e̸d̸a̸t̸ u̸s̸m̸a̸n̸*


*(մʍʍմ ηαςʍα)*






👸🏻 *mᎪKᎪmᎪᏒ ᏦᎪᎥᏁuᎳᎪ*👸🏻




*Marubuciyar*


*Sauyin Rayuwa*
*Nasmah ko Nasirah*
*Sara da Sassaka*



*D̸͟͞E̸͟͞D̸͟͞I̸͟͞C̸͟͞A̸͟͞T̸͟͞E̸͟͞D̸͟͞ T̸͟͞o̸͟͞*


*Ä̤ṳ̈n̤̈ẗ̤ÿ̤ F̤̈ä̤ṳ̈z̤̈ä̤ ÿ̤ä̤r̤̈ ä̤m̤̈ä̤n̤̈ä̤*


ṳ̈ẅ̤ä̤ m̤̈ä̤b̤̈ä̤d̤̈ä̤ m̤̈ä̤m̤̈ä̤
k̤̈ä̤ṳ̈n̤̈ä̤r̤̈ k̤̈ï̤ d̤̈ä̤b̤̈ä̤n̤̈ ẗ̤ä̤k̤̈ë̤ g̤̈ä̤r̤̈ë̤n̤̈ï̤, d̤̈ö̤m̤̈ï̤n̤̈ k̤̈ë̤d̤̈ï̤n̤̈ s̤̈ḧ̤ṳ̈g̤̈ä̤b̤̈ä̤ c̤̈ë̤ d̤̈ä̤k̤̈ë̤ ä̤d̤̈ä̤l̤̈c̤̈ï̤ g̤̈ä̤ d̤̈ṳ̈k̤̈ n̤̈ä̤ k̤̈ä̤s̤̈ä̤ d̤̈ä̤k̤̈ë̤.




*S͢p͢e͢c͢i͢a͢l͢ G͢i͢f͢t͢ t͢o͢*


Aunty Hauwa Maman Uswan, ina roƙar Ubangiji daya Albarkaci Rayuwar zuri'ar ki baki ɗaya🙏🏻




*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________




*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________


*Godiya*
Gareku masoyana, a gaskiya banda bakin da zan muku godiya domin kuwa kun nunawa wannan book ɗin nawa ƙauna fiye da tunani na.
Allah ya bar ƙauna, ina muku godiya a duk inda kuke, da wanda nasan su da wanda bansan suba.




*P* 7️⃣ to 8️⃣


Mai ya shafawa jikin sa, sannan ya zura jallabiya, wayar sa ya ɗaga, ganin kiran ɗan uwan sa, Habeeb.


" Mutanen India, kwana biyu kun manta da mu fah.


Dariya Habeeb yayi cikin zolaya yace.


Ni waye na isa da mantawa da ɗan uwana na haihuwa, kasan dai kaima hakan baxata kasance ba, rai ya mata da rai.


" Ba wani nan cika min baki kake yi kwana biyu ka jini shuru ai zaka neme ni meya faru.


" Nafa nemi layin ka naji unable to connection, na kira Momy take cemin, ai ka tafi ƙauyen dasina, wajen *Tsohuwa mai Ran Ƙarfe Hajiya Innah*, Gaskiya nayi missing ɗin tsohuwar nan, kasan rabo na da ita, 8yrs.


" Ƙauyen Dasina ko ƙauyen masifa, kullum naje wannan ƙauye sai na dawo da ciwon kan wannan mahaukaciyar Aljanar yarinyar.


Dariya mai sauti, Habeeb yayi, yace.


" Gaskiya zanso ganin wannan, Aljanar taka, da kullum nake shan labarin ta, *umm Waya ga Musty Angon Aljana INDO* zanso ganin Ranar da zaka cewa INDO *I love You*


" Amma dai Allah ya isa tsakanina da kai Habeeb, ashe kuwa zaka mutu baka ga wannan Ranar ba, Allah ya kiyashe ni, ɗiban yayi, kaga ma sai Anjuma naga Alamu, yau da baƙar Fata ka tashi, kafin bakin ka yayi tasiri kaina gara na kashe waya ta.




Dariya ce sosai Habeeb yake tun yana kan kujera saida ya sauƙo ƙasa, yanda Mustapha ya hasala kai kace, ance gobe za'a ɗaura masa Aure da INDO, duba wayan yayi yaga harma ya kashe wayar.


" Mustapha Sarkin Zafin Zuciya, gaskiya duk matar da ta Aure ka, zata sha wahala kafin ta gane halin ka, domin sanin Halin ka sai wanda yayi dogon Zama da kai.


Tashi yayi daga ma daidaicin falon da yake ya shige bedroom ɗinsa tare da turawa Mustapha saƙo kamar haka 👇🏻


Allah ya huci Zuciyar ka ɗan uwana, sannan ka shirya tarbata gobe ina hanya insha Allah, zanzo hutu.




Murmurshi mustapha yayi bayan ya karanta saƙon Habeeb, tura masa yayi da cewa.


Kai amma gaskiya naji daɗi sosai Allah ya kaimu goben da rai da lafiya, bari ma naje na fara yiwa Momy Albishir.





*DASINA*


Kwanan Mustapha Uku da tafiya, Indo dai tsiyar tata da sauƙi, domin kuwa yau har ruwa Mama ta samu Indo ta jido mata, Bayan ta gama ɗibawa mahaifiyar tata Ruwan ne, cikin girma da Arziki tace Mama na tafi gidan Innah.


A dawo lfy Mama ta mata, sannan Indo ta fice daga gidan zuwa na Innah, a hanya ta gamu da Baffah mahaifin, Hansai, har ƙasa Indo ta sunkuya ta gaishe shi, mamaki ne ya cika, Baffah ganin Indo a nutse, har mutuncin gaisuwa ya samu, Amsawa yayi ta shige, abunta gidan Innah.


Baffah ne yace,
" Allah dai yasa *ba nutsuwar kwantan ɓauna tayi ba*


Indo ta samu Innah sai shan Baccin ta takeyi hankali kwance, bata tashe ta ba, saima tsintsiya da ta ɗauka ta sharewa Innah gidan ta tsaf, tare da wanke mata kwanukan ta, sannan ta hura wuta, ta dafa taliyar ta, sanda taci ta ƙoshi tayi gyatsa sannan tace


" Alhamdulillah, to bari na lissafa aikin ladan da nayi yau, na farko dai, nayiwa Mama ɗiban ruwa, na gaishe da Baba, na kuma gaishe da Baffah, yawwa sai yanzu da nayiwa Hajiya Innah aiki, wataƙil zan iya samun, lada, guda *ɗari da tamanin* ko haka na tsaya a cikin satin nan na samu, yawwa to yanzu bari na tashi Innah ta bani Naira hamsin na tafi shagon ɗan tasi na sayo maganin ɓera, dariya tayi tace, ya Tanimu nida kai shege ka fasa cikin wannan ƙauyen, tashi Innah ta hau yi, da salati a bakin ta, Innah ta farka, washe baki Innah tayi tace.


" Kaji ƴar Albarka ina mafarkin ki, sai kuma gaki.


Naɗe kafar ta Indo tayi tace dan Allah Innah gaya min me kika ganni inayi cikin mafarkin.


Dariya Innah tayi tace,


" Ganin ki nayi, a Makeken gidan da Muhammadu Mustapha ya gina, kina zaune hakince, komai sai dai kisa amiki, ga kayan ciye ciye kala kala, ke harda fah ƴarinya na ganki wai harkin haihuwa.


Rufe idon ta Indo tayi wai ita a dole taji kunya, ance an ganta da yarinya ta haihu, cigaba da cewa Innah tayi.


" Kinga wasu maka makan kujeru dake cikin ɗakin ki, harda wani ƙaton tebi.


Dariya Indo tasa tace.


" *Wayyo Allah, Allah ya Kai damo ga harawa ko baici ba yayi ɓarna chap Innah waya ga INDO A BIRNI, za'a ga tsiya Aradun Allah, dan zan tsula ciyata son Raina, kinsan Innah, nifa Idan na Auri ya Mustapha ya daina fita kenan, karma wata shegiya ta gansa tace tana sonsa*.


dariya Innah tayi tace.


" Idan kin hanasa fita naga shegen da zai nemo muku abinci kuci, bare ma kekam mai cin tsiya, nifah nama fi sonki da Habibu, domin kuwa yafi wannan mai zafin ran tsiya, sauƙin kai.


Tura baki Indo tayi tace.


"Kinga Innah Idan kina son mu zauna lfy ki daina zagin ya Mustapha, waye ma habibu, sunan ma ko daɗi Babu, wai *HABIBU* nidai ya Mustapha nake so.


Kama bakin ta Innah tayi, tace


" Ikon Allah, wai damma ba kyale ki yake yiba kullum yana cikin Hantarar ki, da tsangwama.


" Naji nidai yanxu bani Hamsin, tunda sharar da nayi miki ma baxaki gode min ba, sai ki bani ladar shara na da wanke wanke, dan nayi ne domin ki biyani.


Sai lokacin Innah ta lura da sharar da Indo tayi mata, fes ta share gidan ya fita, dariya Innah tayi, tace.


" Sannu ƴar Arziki Irin Albarka, ai ɗari ma zan baki ba hamsin ba, laritarta Innah ta buɗe ta ɗauko gudan Ɗari ta bawa Indo.


Aiko kuɗin nan na shiga Hanun Indo ta tashi a guje, sai shagon ɗan tasi, maganin ɓera tace ya bata na hamsin, karɓar kuɗin ɗan tasi yayi, tare da danƙa mata maganin ɓerar.


A hankali Indo ta shigo cikin gidan nasu tana leƙen, gidan domin bata son kowa yasan ta shigo gidan, cikin Sa'a kuwa Babu kowa tsakar gidan, ɗakin tumakin ta shiga, suna ɗaure sunfi goma, dusar dake gaban su ta zazzagewa maganin ɓerar, sannan ta dama shi sosai, kallon tumakin tayi tace.


" Kuyi hkr fah tumaki ba da son raina ba zaku mutu, wanda ya ɗaure ku shine ya jawo muku dan haka sai ku ɗauki hkr, wuf tayi ta fice tabar gidan kafin kowa ya ganta, a dakalin ƙofar gidan nasu ta zauna, zuwa azhar kafin ta shiga cikin gidan nasu.


Fitowar Mama daga ɗakin ta, zatayi madafi ne, sai taji tumaki na wani irin gurnani, leƙa ɗakin tayi, sai tagan su gabaki ɗaya kwance, bakin su kuwa sai fitar da kunfa yakeyi, zaro ido Mama tayi, da sauri tayi ɗakin Tanimu ta kira sa tare suka fito duka harda Baba, Salati Baba ya ɗauka, cikin mamaki yake cewa


" ikon Allah dobbobi kamar wanda suka ci guba, maxa Tanimu, tafi ka kira idi mahauci yaxo ya siyi dabbobin nan dan Wlh mutuwa zasu yi.


Da gudu Tanimu ya fice daga gidan, a gigice, INDO dake zaune taga ficewar Tanimu, Dariya tayi, tace.


" Lallai magani ya fara aikin sa.


Tare Tanimu suka dawo da idi mahauci, ko Kafin su iso ma tuni tumaki kam sun mutu, gaba ɗaya ko ɗaya bai tsira ba, shuru Tanimu yayi tare da zamewa ya zauna a ƙasa, sai Kuma hawaye ya fara bin idanun sa, Mama ma taji tausayin sa ainun, domin kuwa ko wani rago ɗaya zaiyi dubu Arba'in, Baba kuwa, Haƙuri ya fara bawa Tanimu da cewa ya ɗauki ƙaddara.


INDO da ta shigo cikin gidan ne, ta samu Tanimu na zaune sai famar kuka yake, salati ta ɗauka tare da cewa.


" *Subhanallah me zan gani haka, GARDI da kuka, sai kuma tasa dariya, Allah sarki daɗi na da gobe saurin zuwa, haka Nima jiya iwar haka, ka Sani kuka, sai gashi nima yanxu Allah ya saka min.*


Jin furucin INDO yasa Mama, zargin kodai Indo ce tasawa dabbobin nan wani Abu suka mutu.


" Zo nan Indo cewar Mama.


" Naxo kuma Mama me zanyi ni Kuma?


" Kixo nace ko, idan kuma baxaki zoba, sai ki faɗa min.


Tahowa Indo tayi, kusa da mama, tace


" Gani nan tana tura baki tayi maganar.


" INDO kece kika kashe dabbobin nan koh?


Saurin ɗago kansa Tanimu yayi jin abinda Mama ke furtawa.


Cikin rashin tsoro, Indo tace.


" Ni

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login