Showing 12001 words to 13265 words out of 13265 words
Chapter 5 - Barauniya Amarya by sadnaf and Mrs fawwaz-1-1.txt
????♀
N??
*SADNAF*????
*&*
*ʍʀs ʄaաաaʐ*??
®PURE MOMENT OF LIFE WRITERS
P.M.L
Dedicated to all Readers of B'??R??UNIY??R ??M??RY??
Page 60-70
??
"Zoben waye wanan Kausar " ?
Khalid yace ransa a mutukar b'ace yana nufarta,
Kausar d'ora hannu tayi aka tana ja da baya dan da akwai yanda zata iya hak'a rami ta binne kanta da ta binne kanta wanan abun kunya da mai yayi kama,
"Tambayarki nake kibani amsa kafin na k'wada miki mari" Khalid yace a tsawace,
Kausar durkusawa tayi agabansa tace,
"Khalid kayi hak'uri wlh ba halina bane sharrin shaidan ne narasa yanda zanyi nasamu kud'i na biya basukan dake kaina dan Allah ka rufa min asiri" wani wulak'antacen kallo ya ringa mata can yafara magana,
"Kausar dama Ashe ke B'??R??UNIY?? ce bansani ba?,Kausar kinsan yanda na tsani mai halin b'era kuwa? namiji ma ya yak'are ballantana mace, mai kika nema kika rasa Kausar in badan rashin godiyar Allah irin naki ba,wane irin bashi kika ci da bazaki gayamin inbaki kud'i ki biya koda banida shi ko ranta ne Kausar sai nayi da ki kunyatani agaban abokaina yanzu dawane ido kike san suringa kallona,sun San kece kika d'au zoben,gaskiyar Aunty zulaihat datace ke kika d'auke mata zobe Ashe shiyasa kika bi kika rud'e dakikaji zata zo, , kafin ki mata kikayi a saloon Kausar wanan wane irin masifa ne ahaka in aka ganki kamar bazaki aikata ba,nagode wa Allah daya nuna min halinki tun wuri dan nasan kunyar da zaki sani naji nan gaba sai yafi Wanda naji yau dan haka Kausar wlh duk San da nake miki hak'ura zanyi dake dan wlh bazan iya zama da B'??R??UNIY?? ba, dan haka ki tafi gidanku idan kin gyara halinki na dawo dake," Kausar kuka ta fashe dashi tana
"Khalid karka yimin haka wlh Sharrin shaidan ne bansan ya akayi nake sata ba yanzu inkace natafi gida Khalid ka tona min asiri sati biyu da aure aga nakoma gida,tsaki yayi yabarta awajen yace kar yadawo ya sameta bazai iya zama da b'arauniya ba,kuka Kausar taringayi sosai tana nadamar d'aukewa Habiba zobe yanzu wane riba taci daya wuce shan kunya ga aurenta na rawa, Khalid k'ara dawowa yayi da mukullin mota ahannu yace tazo ta fita zai kulle gida dan zai mayarwa da Habiba zobenta,ba irin rok'on da Kausar bata masa ba yak'i sai daya ga ta d'auko hijabinta yayi waje ,itama tafito tana kallonsa kamar ba Khalid mai k'aunarta ba dan yanzu ita k'iyayyarta ta hango k'arara a idonsa,motarsa yaja yabarta a tsaye.
Kausar data isa gida kuka take sosai inda hankalin Hajjo ya tashi ba irin tambayar da bata mata ba akan ta gaya mata mai yafaru tak'i akarshe yayanta ta k'ira Murtala yazo shima yana tambayarta fir tak'i tagaya masa,Hajjo sa Murtala tayi ya kira Khalid awaya suji lafiya,Murtala yabi shawararta ya kira Khalid bayan sun gaisa yake cemasa sun ga Kausar ta dawo gida ko lafiya,ce masa yayi maganar bata waya bace zai zo gida ya samesu ya katse wayar,bayani yayiwa Hajjo abinda Khalid yace taringa sallati tana mai yafaru haka sati biyu da aure Allah yasa dai Kausar ba wani gagarumin Abu tayi ba.
Khalid kuwa dayaje gidan Fahad bai sameshi ba, Habiba yasamu a zaune a Palo sai cika take tana batsewa dan fad'a sukayi sosai da Fahad dan dagewa tayi ita fa Kausar ta biyata zobenta ko Khalid ya biyata sai da Fahad ya mata kaca kaca tukuna yabar mata gidan,tana ganin Khalid taja tsaki,hakan datayi kuwa ya masifar k'ona mishi rai,matar datake masifar girmama shi sai gashi Kausar ta janyo mishi raini agurinta,mik'a mata zoben yayi yace mata bayan sun tafi suka d'aga karkashin gado suka gani,dasauri ta amshe tana murna shikuma yajuya dan yatafi bud'ar bakin Habiba sai cewa tayi,
"Danji naji amma ban yarda akarkashin gado aka gani ba kai dai bakayi dace mata ba,ga k'yau amma ba hali", bai ce mata komai ba yafice zuciyarsa na tafasa da bacin ran abinda Habiba tayi masa yanufi gidansu Kausar tana can a kunshe a d'aki tana ta kuka,sallamarsa dataji ne yasa ta Mik'e ta zauna ta dafe k'irjinta dan tasan yau Hajjo sai ta kusa kasheta da duka intaji abinda tayi,Hajjo tabarma ta shimfid'a masa ya zauna bayan sun gaisa ya gaya mata abunda Kausar tayi masa, sallati Hajjo taringayi tana tafa hannu tana tunanin anya kausar ita kad'ai ce batada aljanu masu sata, sata hak'uri tabawa Khalid tace dan Allah kar dan haka yafaru yace zai saketa tana tunanin Kausar Aljannu ne ajikinta dasuke sata sata zata sa mallami yamata ruk'iya jikin Khalid ne yayi sanyi daya tuna fa kad'an da aikin aljannu,cemata yayi babu komai zai dawo yaji mai mallamin yace,sallama ya mata ya tafi,Kausar dake d'aki sai kuka take data ga yatafi baice akirata ba,Hajjo zuwa tayi ta sameta tace mai yakai ta sata Ashe har yanzu bata daina sata ba,fad'a sosai Hajjo taringayi uwa ta ari baki Kausar ita dai sai kukanta take tana nadamar abinda ta aikata.
Washegari wajen wani babban mallami Hajjo takai Kausar tace ya dubata ko tana da Aljannu,Mallamin kuwa dayayi yan adduoinsa yace Kausar bata da wani aljannu San zuciya ne kawai da tariga tasaba tun tana karama sai andage mata da adduar Allah ya shiryata,itama a matsayinta na mahaifiyata ta Dage da addua,ahaka suka koma gida Hajjo ta dage da adduar Allah Ya shurya Kausar taku ma sa ana tayata yiwa Kausar addua,kullum sai anyo mata rubutu tasha.
Khalid kuwa tunda yabar gidansu Kausar ya kira Hajiya zulaihat yaga mata abinda Kausar tayi masa, amadadin Hajiya zulaihat taji haushin Kausar tausayinta ne yarufeta dan tana tunanin Kausar ba ita kad'ai bace,hak'uri tabawa Khalid akan ya maida Kausar tana tunanin ba yin kanta bane Aljanu ne da ita,yadage ya ringa taya Kausar addua,da wanan shawarar da hajiya zulaihat tabawa Khalid zuciyarsa tayi sanyi,amma dayake Khalid yanada zuciya da ruk'o yakasa manta abinda Kausar tayi masa, sai da Kausar tayi wata d'aya a gida yaje gidansu ya d'aukota Kausar tabi tayi baki ta rame kullum cikin kuka take da nadamar abinda tayi.
Tunda ta koma Khalid yake k'afa k'afa da ita indai zai kwanta bacci sai yayi pillo da kud'insa Wanda hakan kesa Kausar kuka sosai dan yanzu Khalid baya baya yakeyi da ita baya sakin jiki da ita,ko waje zasuje sai yaja mata kunne akan karfa tayi d'an halin.
ALLAH MAJI ROK'O
shekara d'aya kenan da Auren Kausar bata k'ara sata ba tun zoben Habiba data sata, dan Khalid babu irin gwajin da bai mata ba dan yaga ko har yanzu inta ga Abu zata d'auke da gangan zai ajiye kud'i yanda ya ajiye haka yake zuwa yasamu abunsa,gwaji iri iri yamata amma Ina ba Kausar d'in data sani bace a da,dan ALLAH SAMIU DUA NE MAJI ROK'ON BAWANSA MAI KUMA SHIRYA BAWANSA A DUK LOKACIN DAYASO.
Khalid kuwa bak'aramin murna yayi da canzawarta ba ahaka zamansu Yakoma normal,Kausar duk lokacin data tuna irin b'arnar datayi kunya kan kamata dan kwanaki ta had'u da Aunty Oke a hanya bud'ar bakinta sai cewa tayi B'??R??UNIY??R ??M??RY?? dafatan ka daina sata dan sata ba cyau,aranar bak'aramin kunya kausar tasha ba da kuka ta dawo gida tana ta data sanin abinda tayi abaya.
Whuuuuuuuh Readers Allah yarabamu da San zuciya irin na Kausar masu hali irin nata Allah ya shiryesu Allah ya shiryemu gabaki d'aya bisa tafarkin addinin musulunci kuskuren da mukayi a wanan novel d'in Allah ya yafe mana anan muka kawo karshen wanan novel mai tak'en B'??R??UNIY??R ??M??RY??.