Showing 1 words to 3000 words out of 257774 words
Chapter 1 - MUHIBBA Book Complete by Sameena Aliyou.txt
*MUHIBBA*
*001*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM
Daga yanda take zaune cikin mota tana iya hango dogon ginin gidan, gidan da ko ba’ace ba Kai tsaye zaka kirasa da gidan sarauta sabida yanda aka tsara ginin ga kyau ga girma had’ida tsawon gini.... A iyaka shekarun da tai bataga gidan ba tabbas ba wani abu muhimmi da ya canzu da tsarin ginin gidan saiko fenti da abinda ba’a rasa ba... Idan bata b’ata lissafi ba yau shekaru ak’alla goma sha biyar kenan rabonta da wann masarauta mai bak’in tarihi a gareta... Shin ta yaya ma zata mance shekarun, bacin dik wani iftila’in rayuwa da gwawarmaya data fuskanta wannan Masarauta shine sila... Masarautar dake tafe da K’ADDARAR rayuwarta a cikinta, Masarautar da ta canza labarin rayuwarta, Masarautar da take tamkar Kurkuku a idanunta, Masarautar da aka ginata kan mulkin zalinci a zahiri kuma ana rud’in mutane da yaudararsu da kyawawan d’abi’u na k’arya... Masarautar da babu tausayi balle jin k’ai cikinta....
Lokaci guda Ta saka bayan hannunta Ta goge hawayen da suka d’igo mata.... Matashin saurayi dake zaune gefenta wanda a k’alla bazai gaza shekaru 30 a duniya ba, girgiza kansa yai kad’an had’ida fuzar da huci a hankali.... Lokaci guda yake furta “HIBBAH da zaki bi shawarina Ki janye wannan k’udiri naki, Ki mance komai ki fawallawa Allah lamuranki da sannu zai saka miki, na tabbata bayan abinda suka miki Keda iyayenki Allah bazai barsu ba, Wllhi sai ya saka maku... So please Ki janye wannan k’udiri naki...Mulkin duniya bamai dawwama bane suma wataran zasu tafi yanda mahaifanki suka tafi... So please ki janye wannan k’udiri naki....!”Ya k’arashe cikeda kulawa.....
Murmushi mai ciwo budurwar mai kimani shekaru 29 tai kana tace “Ansar wllhi wllhi bazan janye k’udirina ba... Wllhi sai na tozarta su a idon duniya... Sai na ruguza mulkin zalunci da sukeyi... Sai na nunawa duniya su wasu irin mutane ne... Wllhi bazan barsu haka nan ba, yanzu ne daidai lokacin da ya kamata na dawo, daidai lokacin da suka rasa mahaifinsu, na tabbata yanzu ne zasu soma yak’in neman mulki ni kuma zanyi amfani da wannan daman...!” Cikin tsananin karaji tai maganar tana mai duban Ansar kana ta maida dubantaga ginin masarautar, lokaci guda ta kuma sakin murmushi mai ciwo kana ta soma fad’in “Iyalan Sarki AbdulJabbar na dawo gareku, saidai wann karon ban dawo a matsayin Saudatu ba, bak’ar yarinya mummuna abin wulak’antawa...MUHIBBAH, a matsayin Muhibbah na dawo, abar soyuwa a gareku... Ku yi shirin tarban rugujewarku, k’uncinku da kuma tashin hankalinku... Zan zame maku musiba da annoba, zan zamto yunwarku na kuma zamto abincinku, kaman yanda zan zamto k’ishin ruwanku na zame maku ruwan shanku.... I’ll take you down to the ground, all of you... D’aya bayan d’aya... Wllhi sai na jefaku cikin tashin hankali had’ida k’uncin rayuwa fiyeda yanda kuka jefa nawa da na iyayena ciki... Wllhi sai na tarwatsaku da duk wani mulki da sarauta da kuke tak’ama dashi.... Alk’awari ne..!!!” Ta k’arashe tana mai kuma yarfe wasu hawayen da suka zubo mata....
Suna nan zaune cikin mota daga cen gefen kwalta yanda Ansar yai parking suka soma jiyo sautin siren... Gaba d’aya Unguwar ya d’auka da k’uwa sai kaucewa ake ana bada hanya, kana iya hango motoci na alfarma sun doso babban gate d’in Fadar, ko wata mota d’auke take da lambar Jos Emirate Council.... Ga wani zabgegen mutumi da jajayen kaya irinta dogarai ya zarkwad’o tuk’ek’iyar dorina daga waje yana korin mutane yana fad’in Ku gafara ‘ya’yan talakawa... Yarima MAI JIRAN GADO ya iso mahaifarsa.....”
Duban Ansar tai kana ta maimaita abinda bafajen nan yake fad’i...
“YARIMA MAI JIRAN GADO...?” Tai maganar d’aukeda alaman tambaya...
Jinjina mata kai Ansar yai kana yace “From what I heard, yau ake saka ran isowar Babban d’an Sarki AbdulJabbar mai rasuwa, Wato Yarima MAHMOOD AbdulJabbar Mahmood... Shine babba cikin yaran Sarkin, da alama ya iso kenan daman yau ake saka ran dawowarsa daga K’asar Spain cen Madrid....”
Katsesa tai da fad’in “Na riga nasan shine Babba cikin asararrun yaran Sarki AbdulJabbar, saidai tambayar da zan maka Wai dama dik tsawon shekarun nan baya k’asar nan...?”
Fuzar da iska kad’an Ansar yai kana yace “K’warai baya k’asar nan, kuma na tabbata rikicin karb’an Mulkin gidansu ya sanyashi dawowa don ba don haka ba, Yarima Mahmood bazai tab’a dawowa Nigeria ba, shekarunsa kusan goma sha biyar kenan a turai...”
Gabanta ya yanke ya fad’i lokaci guda.... D’agowa tai tana kuma duban Ansar dake ci gaba da kwararo mata bayani kana ta dakatar dashi da fad’in “Wait, kace shekara sha biyar baya Nigeria...?”
Jinjina mata kai yai kana yace “K’warai shekaru goma sha biyar baya Nigeria, yana cen k’asar Spain tareda marigayiyar matarsa da d’iyarsa mai kimanin shekaru goma sha hud’u..”
Muhibbah Ta kuma katsesa da fad’in “Marigayiyar Matarsa...?”
Amsar ya jinjina kai yace “Shekara guda kenan da rashin matarsa da yayi, ‘Yar k’asar nan ne saidai daga yanda naji labari ita matar tasa d’iyar talakawa ce ba d’iyar masu mulki ko sarauta ba, hasalima tsangwamar matar tasa da iyayensa sukai ya sanyashi yanke shawarin barin k’asar da iyalinsa gaba d’aya, a nan Nigeria ya aureta suka tafi Spain tare, Allah ya albarkacesu da yarinya k’wara d’aya mace, and last year sunzo Nigeria sai tsintar gawarta akai a cikin d’aki har yau ba’a San cause na mutuwarta ba, ba’a San mai ya kasheta ba, kawai dai gawarta aka tsinta a d’aki .... Bayan watanni kad’an ya kuma rasa mahaifinsa Sarki AbdulJabbar the same shekaran da ya rasa matarsa Gimbiya Aliya, shekaran ta zamto shekarar k’unci ga Yarima Mahmood, toh tin daga nan ya d’auki d’iyarsa suka koma k’asar Spain bai kuma lek’o Nigeria ba sai yanzu da batun mik’a Mulki ya taso... Kaman yanda kika sani Sarki AbdulJabbar yanada k’anne ‘yan Uba wanda suma harin wannan kujera ta sarauta suke... And na tabbata Hajiya Turai Giwar Sarki AbdulJabbar bazata tab’a bari sarautan nan ya subce daga hannun yaranta ba....”
Ambato Hajiya Turai da yai ya kuma sanyata jin wani irin tuya a k’irjinta tamkar ana barbad’a garwashin wuta....
A hankali ta furta “Ya isa haka banson jin labarinsu, balle sunayensu....”
Ansar ya d’an dubeta a kaikaice kana ya girgiza kai yace “Kuma a hakan kike cewa kin shirya rayuwa cikin masarautarsu... Tell me Hibbah, Ta yaya zaki fuskanci mutanen da ko sunayensu baki sonji balle har kiyi rayuwa taredasu under same roof, Hibbah na rok’i arzikin ki Dan Allah Ki janye k’udirinki, let’s focus on our relationship please...” Ya k’arashe cikin marairaice mata murya....
Sauk’e ajiyan zuciya tai kana tace “Doc, please not now... Dan Allah kamin wnn alfarmar, ka barni na cika burina, na tarwatsa ahalin Sarki AbdulJabbar kaman yanda suka tarwatsa nawa ahalin, nai maka alk’awari da zaran na cika wannan buri nawa, zan sanar da Mummy da kaina a saka mana rana.... Nidai kawai babban taimako da zaka min shine ka shigar dani wannan masarauta na sami gurbin zama cikinta....!”
Yanda tai maganar ya sanyashi d’an dubanta kad’an kana yace “Naji, zan shigar dake Masarautar nan, zaki sami gurbin zama cikinta, amma da sharad’i....”
D’agowa Ta d’anyi had’ida dubansa kad’an kana tace “Mecece sharad’in...?”
Ansar ya d’an daidaita zamansa kad’an kana yace “Nurse, sharad’ina shine randa na kawoki Masarautar nan zaki sanar dani abinda Iyalan Marigayi Sarki AbdulJabbar suka miki da har kike yunk’urin tarwatsa tsakaninsu....”
Gabanta ya yanke ya fad’i, ta sani tina wannan bak’in labari na nufin tashin hankalinta ne, amma batada zab’i idan har hakan zaisa Ansar ya shigar da ita wannan masarauta toh zata tuno baya, za kuma ta waiwayi bak’in shafin rayuwarta da a kullum idan Ta bud’esa sai ta shiga matsanan cin tashin hankali domin kaw duk wani k’uncinta daga nan ya soma....
Ansar ya katse mata tinaninta da fad’in “Do we have a deal...?”
K’ak’aro murmushi tai kana Ta jinjina masa kai a hankali kana tace “Zan sanar daki My Dr....!”
Murmushi yai a hankali kana yayi key wa motar yana fad’in “Ya kamata mu d’auki hanyar Bauchi kafin Mummy Ta soma kiranmu....”
Muhibbah Ta d’an murmusa a hankali itama kana tace “I’m sure inada missed calls d’inta ma Dan wayata throughout kashe take...”
Jinjina kai yai idanunsa naga kwalta yake fad’in “Kunfi kusa ai, though idan anyi dare fad’an wa ni za’ai dukda cewa Kece na kawo Ki rubuta jarabawa...”
D’an b’ata fuska tai kad’an kana tace “Naji dai, Babu mai shiga tsakaninmu da Mummy ta...”
Murmushi yai wnn karon kana suka d’auki hanyar Bauchi....
***
JOS(FADA)
Zaratan mazaje ne guda Uku tsartsaye a bakin Kamfacecen parlor na alfarma, ko wannensu sanye cikin shiga irinta mulki da sarauta, rigar Kufta da wandonta harmada da hula da takalmi, Dik yanda mazaje masu kyau suke wad’annan mazaje zasu amsa sunan... Hannayensu hard’e suna duban Mutumin dake k’arasowa garesu mai tsananin kamanni dasu saidai shi ya d’ara masu a shekaru, hannunsa na dama rik’e da hannun matashiyar budurwa mai kimanin shekaru 14 da suke tafe tare... Fadawa kuwa sai ci gaba da kod’asa suke suna wasashi....
_Allah ya yika Sarki... Mahamuda jikan Mahamuda, Dan na gada kafi Dan na koya... Allah ya baka gidanku, Mahamuda yayi sarauta Mahamuda zai kuma yi... Gaba salamun baya salamun, Allah yaja zamanin Sarki Mai jiran gado..._
Ire iren kirarin da suke masa kenan... Biyu daga cikin samarukan nan masu jiran k’arasowarsa murmushi ne fal fuskokinsu yayinda guda d’aya ya had’e Rai tamkar yaga ajalinsa, dan kirarin nan da Fadawa keyi jinsa yake tamkar ana yaryafa masa narkarkiyar dalma cikin k’irjinsa....
_Tafiya mai cikeda sark’ak’iya, rud’ani, tausayi, Fansa, sadaukarwa had’ida soyayya_
SameenaAleeyou📚
[5/20, 10:31 PM] +234 703 453 9908: *MUHIBBAH*
*002*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Cikin taku irinta wanda jinin mulki da k’asaita ke Yawo a jini da b’argon jikinsa yake k’arasowaga ‘yan uwan nasa, lokaci guda ya saki hannun budurwar dake rik’eda ita, duban masarautar nasu yake da wane irin idanu, Masarautar da ya rasa matarsa farin cikinsa a acikinta, Masarautar da yai alk’awarin k’aurece mata tsawon rayuwarsa... Toh amma yau ganin ‘yan uwansa haka ya sanya zuciyarsa karaya, shakka babu yayi kewar gida, d’aya daga cikin samarukan ne ya tako har gabansa, su duka biyu suna duban juna cikeda shauk’in sake ganin junansu, matashin bai iya furta komai ba sai rungumesa da yayi siririyar hawaye na d’igo masa murmushi bai bar saman fuskarsa ba, sosai suka rungume juna, kana matashin ya soma furta “Yaya... Yaya Barka da dawowa gida....Nayi murnan ganinka, na gode da ka amsa kiran Maami Welcome home...!” Ya k’arashe kyakkyawan murmushi saman fuskarsa, mutumin da ya kirada Yaya ya d’an buga kafad’arsa kad’an kana ya furta “Na gode _(Príncipe Fu’ad, Estoy feliz de verte_,)naji dad’in ganinka...” Daidai lokacin d’aya saurayin ma ya k’araso had’ida kai masa runguma, suka rungume juna cikeda Farin ciki kana matashin ya furta “Sannu da zuwa Yaya... Barka da sauk’a...!”
Murmushi ya kumayi da gefen bakinsa kana yace “An gaida Veterinarian... Na gode k’warai Prince Jamal... Gracias...!”
Saurayin da ya kirada Jamal ya murmusa kad’an kana ya matsa gefe daidai lokacin da Yarima Mahmood ya d’ago yana duban d’aya d’an uwan nasu wanda da gani ya girmema wad’ancen samari biyun, su duka biyu Sun kafe juna da idanu kaman babu mai motsawa Daga matsayarsu, lokaci guda d’aya matashin ya d’an saki murmushi wanda da gani kasan cike take da ma’anoni kana ya soma takowa cikin tsananin mulki, tak’ama, sarauta da kuma isa... Hannayensa duka biyu a hard’e yake takowa, ko ba’a ce kasan wann bawan Allah mulki da sarauta Sun gama ratsasa Sun kuma jik’asa...
Har ya k’araso gaban Yayan nasu bai furta koda kalma ba sai wannan shu’umin murmushin dake bisa fuskarsa... “Yazeed...!” Yarima Mahmood ya furta cikeda kulawa....
Yazeed ya kuma sakin murmushi mai bayyana hak’wara wannan karon kana ya k’araso ya rungume d’an uwan masa yana mai furta (“Bienvenido a casa hermano) Barka da dawowa gida Yaya....!” Yai masa gaisuwar cikin harshen Spanish...
Murmushi ya saki a hankali saidai kafin ya sami zarafin amsasa ya sinkayo muryar Yazeed cikin sigan rad’a daidai lokacin da suke rugumeda juna, saitin kunnensa yake rad’a masa “Karka rud’i kanka da kalaman da wad’ann dogarai Ke maka kirari dasu... Till now ba’a tantance wanene Magajin Kujerar masarautar nan ba... Sannan Jarumi masanin al’adun cikin gida shi ya cancanci rik’on kujerar ba wanda ya shafe shekaru a k’asar turai ba....!” Yai maganar fuskarsa fal murmushi...
Yana k’ok’arin janye jikinsa, Mahmood ya damk’o damtsensa kad’an, saitin kunnensa shima yake rad’a masa “Hausawa na cewa Ba’a sanin maci tuwo sai miya ya k’are... You might be right, I might not be familiar with all you’ve listed, but let me remind you this,(Hermanito) K’aramin k’anina... As they say D’an na gada yafi D’an na koya, so as long as jinin sarauta yana yawo a jijiyoyin jikina, Mulkin Masarautar nan ka iya fad’owa hannuna... Saidai duk bama wannan ba... Ka sani bashi ya dawo dani ba... Inada babban dalilin da yasa na dawo wannan masarauta wanda yafi yak’in neman mulki da sarauta...Mantén esto en mente (Ka aje hakan a zuciyarka) k’aramin k’anina....!” Ya k’arashe yana mai gyarawa Yazeed rigar kuftarsa had’ida d’an buga kafad’arsa guda.... Yarima Mahmood ya d’aurada “Na gode da tarban da ka min... Prince Yazeed...!” Ya k’arashe kyakkyawan murmushi saman kyakkyawan fuskarsa....
K’uri Yazeed yai masa har saida yasa kai ya shige yayinda sauran ‘yan uwan masa suka rufa masa baya...
Suna dosowa mashigar parlorn kuwa bayi suka soma zubewa suna gaidasu....
Parlor ne da ya amsa sunansa wajen tsari da had’uwa, dik yanda royal parlor yakai to wannan parlor yakai, iyaka tsayewa ya gama tsaruwa, parlor ne da za’a iya kiransa da Aljannan duniya...
Daga cen center kana iya hango wata kyakkyawar mace fara tas mai d’an jiki da tsawo zaune saman Hamshak’iyar kujerar, k’afarta d’aure suke saman babban pillow da akai mata kwalliya da asalin fatar damisa, kayan dake jikin matar kad’ai zai tabbatar maka dik yanda mulki da sarauta ta duniya take wannan mata ka iya taka wajen.... A haka bazakai zaton takai shekarun da take ba sabida jin dad’i da kuma kwalliya da gayu, sai ka k’araso sosai ka fahimci girma ya sauk’o mata, Dattijuwa ce ‘yar kimanin shekaru 65 a duniya....
Saida wata mata da ko ba’a fad’i ba zaka fahimci Jakadiya ce ta shigo cikeda risinawa ta sanar da isowar Yarima Mahmood kana tai masu izinin shigowa....
Fu’ad ne gaba sai Jamal Ke biyedashi sannan Mahmood Ke take masu baya... Matar Ta fad’ad’a murmushinta idanunta tab k’walla... Babban D’anta mafi soyuwa a gareta take hangowa tsakiyar ‘yan uwansa, ji tai tamkar Ta mik’e Ta rungumesa, Ta kasa b’oye tsananin Farin cikint dikda cewa a b’angaren Mahmood d’in ba hakan ne Ta kasance ba, sam babu d’igon annuri a fuskarsa saima kallon k’urilla da yake wa mahaifiyar tasa.... Wasu irin hawaye masu tsananin d’umi ne yaji suna zuwa cikin idanunsa, yayi saurin sadda idanunsa k’asa
A hankali matar ta mik’e tana k’ok’arin kamo hannayensa, hannayenta duka biyu tasa had’ida tallafo fuskarsa, yai saurin kauda fuskarsa gefe saidai tuni matar ta rungumesa tana matsan k’walla...
Take akai dismissing dik wani wanda ba ahalinsu ba cikin parlorn...
Cikin tsananin rawar murya take furta “Sadauki, ashe zaka dawo... Barka da dawowa Magajin Babanshi... Naji dad’i da baka watsa min k’asa a idanuna ba, ka amsa kiran da nai maka, ka dawo mahaifar ka...!”
Kaman wanda ya tina wani abu, ya saki murmushi wa mahaifiyar tasa for the first time tin bayan shigowarsa parlorn...
Hannayenta cikin nasa yake furta “Maami kin wuce haka a wajena, kiyi hak’uri da na sab’awa umarninki a baya... Por favor perdoname Maami na...!” (Ki yafe min Maami na)
Ta saki murmushi cikeda jin dad’i had’ida mamakin canzawar da Sadauki yai, kodashike tinda ya amince zai dawo Masarautar tasan tabbas tasan ya canza, lokaci guda ta janyo hannunsa suka zauna saman kujerar alfarmar dake parlorn, wani irin shauk’i da k’aunar d’an nata ke ratsa dik wata k’ofa Ta zuciyarta, murmushi mai gauraye da Hawaye a fuskarta take furta “Har kullum albarka ta ce a tattaredaku gaba d’ayanku....” Ta d’ago tana duban Jamal da Fu’ad kana tace “Ina Yazeed...?”
Duban juna sukai kaman bazasu ce komai ba sai Mahmood ya tari zancen da fad’in “Ya tarbeni Maami... Duka ‘yan uwana sunmin tarba mai kyau da naji dad’insa... Madallah da ahalin marigayi Babana Sarki AbdulJabbar... Madallah da ahalinki Giwar Sarki....!!” Ya k’arashe yana mai kod’a mahaifiyar tasa...
Ta kuma sakin murmushi cikeda shauk’i, Mahmood yai mata k’uri yana jira yaji Ta tambayi d’iyarsa Zahra, saidai sam Maami bata tambaya ba, ko dashike yasan hakan ka iya faruwa Dan haka baiyi mamaki ba....
Tuni Maami Ta mik’e taci gaba da bada order na shagalin da ake shirin had’aka da dare a fadar dan sanar da dawowar Babban d’anta...
Shiko Mahmood Fu’ad ya tambaya ko Ina Zahra take... Nan Fu’ad ke sanar dashi tana cen sashen Yazeed...
Jinjina kansa kurum yai kana ‘yan uwan Jamal da Fu’ad sukai directing nasa zuwa nasa b’angaren yanda aka gyara masa, babban abinda ya dad’a baiwa Yazeed takaici shine cikin sashen Marigayi Mahaifinsu aka baiwa Mahmood masauk’i, da gaske da k’arfi so ake a mallaka masa sarautar gidan, bayan dik tsawon shekarun da ya d’iba yana jiran wannan mulki ta fad’o hannunsa, dik wani taron sarakuna na mahaifinsu idan bazai sami halarta ba shi yake wakiltawa, komai na mahaifinsu shine akai, sai yau rana tsaka Mahmood da bai sha wahalan komai ma masarautar ba ace shi zai gaji mahaifinsu, idan akai haka tabbas ba’ai masa adalci ba, da yawan mutane suna masa lak’abi da Wakilin Sarki wasu kaw Magajin Sarki suke kiransa, yau rana tsaka ace D’an uwansa ne zai gaji sarautar da ya jima yana buri bashi ba, tabbas hakan ba mai yuwa bane, bazai tab’a barin hakan Ta kasance ba...
Da wannan tunanin ya k’arasa sashensa cikin huci tamkar zai kifa k’asa...
***
Zuhrah matar Yazeed ne da yaranta guda biyu Najimi mai kimanin shekaru 6 saiko mace mai kimanin shekaru 4 zaune a hamshak’in Parlorn nasu sai zuba surutu suke had’ida murnan ganin ‘yar uwarsu Zahra wacce sauk’arta a k’asar kenan... A haka Yazid ya shigo tamkar zai kifa k’asa, D’iyarsa Noor Ta tafi a guje tana k’ok’arin d’alewa jikinsa take fad’in “Daddy guess who’s here....” Saidai Yazeed bai ko bari ta k’arashe ba ya tureta daga jikinsa cikeda tsawa... A matuk’ar razane yarinyar ta kauce kaman zata kurma ihu... Ta juyo a guje zuwaga mahaifiyarta.... Kuyangin dake kaikomo tsakanin sashen tuni suka soma k’amewa suna kuma zubewa k’asa sanin k’asaita da mulki da Ubangidan nasu kedashi,