Showing 15001 words to 18000 words out of 257774 words

Chapter 6 - MUHIBBA Book Complete by Sameena Aliyou.txt

*šŸ‘‘āœØMUHIBBAHāœØšŸ‘‘*



*008*




*Ā©ļøSameena Aleeyou...āœšŸ½*




Tinda ya kwanta yake wasu irin mafarkai marassa kyau, da fari mafarkin matarsa Aliya da mahaifinsa yai, bayan yayi addu’a ya sake komawa wani mafarkin ya kuma tadashi... Wannan karon akan K’annensa guda Uku ne, abinda ya gani cikin mafarkin sosai ya tada masa hankali... Tsaye ya hangi Yazeed da Fu’ad rik’e da takubba a hannayensu ko wanne takwabin dake hannunsa na d’igar da jini wanda yake jajazir.... Sunayensu ya ambata cikeda tashin hankali ganin abindake rik’e hannayensu, cikin kid’ima ya nufi yanda suke a tsaye suna maida huci suna nunasa da takubban dake hannayensu lokaci guda suka fashe da dariya basu daina nunasa da takubban ba... Mamakin dariyarsu yake bayan abinda ya gani rik’e hannayensu, k’arasowar da zai kusansu sai hango wani d’aki yai a bud’e cikin jerin wasu d’akuna... Basu daina dariyar da suke ba har Mahmood ya nufi cikin d’akin mai tsananin duhuwa.... Saidai yana shiga d’akin ya hango mahaifiyarsu zaune saman gadon sarautar masarautarsu... K’irjinsa yaci gaba da bugawa sanda ya hango d’an uwansa da yakeda tabbacin ya fita zakka cikin sauran ā€˜yan uwan nasa durk’ushe kan wata yarinya sai darza mata wuk’ar yake... Ga jini na kwarara amma da alama bata mutu ba.... Cikin zafin nama ya ambato sunan Jamal da k’arfin gaske, saidai ko gizau Jamal bai ba saima ci gaba da darza mata takwabin da yake... Tsalle Mahmood yai ya finciko Jamal don ceton yarinyar amma mai..? Yana d’agosa saiji yayi an luma masa takwabi a cikin cikinsa... Mahmood ya rik’e cikinsa yanda jini ke malala a k’asa.. Ya d’ago yana duban ā€˜yan uwansa guda Uku rikeda takubban saidai bazaice ga wanda ya caka masa ba cikinsu, maida dubansaga mahaifiyarsu dake zaune saman Karagar mulkin yai saidai wannan karon matarsa Aliya ya gani ba mahaifiyarsu ba...Hannu yake mik’a mata alamun neman taimako amma inaa batai ko gizau ba tana nan zaune saman Karagar mulkin saima sakin dariyar da take mai firgitarwa... A hankali yake ji numfashinsa na d’aukewa jikinsa na zamewa har saida ya fad’o kan yarinyar da Jamal ya gama yankata da takwabi, su duka biyu jini na malala daga jikkunansu.... A daidai wannan lokaci ne ya farka daga baccin cikeda tsananin tashin hankali... Addu’o’in da sukazo bakinsa kawai yake iya karantawa had’ida jero hasbunallah wa ni’imal wakil... A hankali yake jin natsuwa na sauk’o masa cikin zuciyarsa... Hannu ya mik’a ya kunna side lamp kana ya dubi k’aramar agogo dake gefen bedside ya nuna k’arfe 4:30am, anata kiraye kirayen assalatu... Shafe fuskars yai da duka hannayensa biyu kana ya mik’e ya nufi bathroom ya d’auro alwala, shimfid’a abin sallah yai amma ko tsayuwar sallar saiji yai ya kasa... Ya zauna nan bakin gado abubuwan na kuma zuwa masa... Wannan wane irin mafarki ne mai cikeda rud’ani da kuma tashin hankali.... Mai wannan mafarki yake nufi...? Take yaji wani b’angare na zuciyarsa na raya masa _Akasarin munanan mafarkai Daga shed’an ne ka nemi tsari da kariya daga shedan.._ Ya sauk’e nannauyan ajiyan zuciya yana mai kuma shafe fuskarsa, tabbas ā€˜yan uwansa bazasu iya kashe ran wani ba koda bawa ne balle nashi.... Ya fuzar da fuci a hankali yana neman tsari daga shaid’an da kuma munanan abubuwan da ya gani a cikin baccinsa... Ya jima zaune wajen har saida ya soma jiyo kiran sallar asubahi... Ya mik’e ya d’auki cazbaha da k’aramar littafin azkar d’insa na hisnul Muslim kana kana ya nufi masallacinsu dake nan cikin Masarautar....
Nan cikin masallacin ya tadda Jamal zaune yana wurdi da alama sallar nafila ya ida yana jiran k’arsowar imam a tada sallar asuba... Yarima Mahmood ya saki murmushi a hankali natsuwa na sauk’o masa, tabbas wannan mafarki nashi daga shed’an ne... Of all people bazai yuwu ma ace Jamal ne zai caka masa wuk’a ba... Nan ya k’arasa had’ida zama gefen Jamal d’in... Suka sakar ma juna murmushi kana Jamal ya mik’a masa hannu alamun masabaha... Zamansa da kad’an kaw Imaam ya shigo suka tada sallah....
Bayan an ida sallah ne suka jera suna fitowa a tare suka nufi b’angaren mahaifiyarsu... Suna tafe Yarima Mahmood ya d’anyi gyaran murya kad’an kana ya dubi Jamal yace ā€œNikam har yanzu Yazeed na nan da halinsa na k’in zuwa sallah...? Naga tinda na dawo bana ganinsa a jam’i and Fu’ad ya akai yau bai fito sallah ba...?ā€

Murmusawa kad’an Jamal yai wanda murmushin d’abi’arsa ce kana yace ā€œBabu abinda ya canza da Yazeed Yaya... Fu’ad kuma baijin dad’i ne shisa baka gansa ba...ā€

Yarima Mahmood ya jinjina kansa a hankali suna tafe cikin kamfacecen masarautar nasu da duk yanda suka gifta sai bayi sun risina Sun gaidasu.... A haka suka iso sashen mahaifiyar tasu...
Jakadiya ce Tai masu iso kana suka shiga suka taddata zaune saman abin sallarta da alama itama sallar Ta ida tana gabatar da wurdi...

A jere sukai zama irinta rak’umi saman Darduma dake a saitin mahaifiyar tasu wanda dama dominsu darduman yake aje wajen, dik sanda suka shigo gaisheta a nan suke zama...

Ta ida addu’o’inta suka shafa a tareda yaran nata, murmushi fal fuskarta take dubansu....Tsananin k’aunarsu na ratsa dik wani kafa na jikinta, Mahmood ne ya soma gaidata sannan Jamal... Ta amsa masu cikeda so da k’auna had’ida shi masu albarka... Daga nan ne take sanar dasu jiya Galadima ya sanar da ita cewa Yau d’in da yammaci zasuyi zama kan maganar wanda zai gaji mahaifinsu Sarki AbdulJabbar mai rasuwa...

Sosai suka natsu suna sauraren Mahaifiyar tasu sanda taci gaba da fad’in ā€œSadauki..!ā€
Yarima Mahmood ya d’ago yana dubanta, Giwa taci gaba da fad’in ā€œNa riga na zab’eke matsayin wanda ni nakeso ya gaji mahaifinku, toh amma Galadima ya tabbatar min cewa cikin masu neman sarautar nan harda Majidad’i d’an d’an uwan mahaifinku Wambai da kuma biyu daga cikin yaran Marigayi Talba mai rasuwa, sannan da shi kanshi Chiroman gari yana neman Karagar Masarautar garin nan... Dan haka ni a nawa b’angaren na tsaida kai, kuma na tabbata king makers bazasu bani kunya ba, domin kaw daga Galadima har Waziri a b’angaren mu suke, kuma sunyi Na’am cikin masu neman sarautar Masarautar nan babu wanda ya dace ya maye gurbin mahaifinku sai kai Sadauki....ā€ Ta k’arashe kyakkyawan murmushi saman fuskarta, yayinda Jamal yaci gaba da jinjina kai yana furta ā€œTabbas Maami, Yaya shi kad’ai ya dace ya gaji Abbah... Cikin duka wad’anda kika lissafo, sannan dama ance kyaun d’a ya gaji mahaifinsa... Kuma idan har sarauta ya fice daga gidan nan haka munaji muna gani za’a sallamemu mu bar Fada mu koma cen wani k’auye a nad’amu hakiman k’awye... Yaya you’re the rightful heir to the throne... Kai ka cancanta ka d’ale wannan karaga...!ā€ Ya k’arashe yana duban d’an uwan nasa kyakkyawan murmushi saman fuskarsa....
K’uri Mahmood yai masu yana dubansu kana ya sauk’e ajiyan zuciya a hankali yana mai shafe fsuksrsa da tafukan hannunsa, ta yaya zai sanar dasu ba abinda ya dawo dashi Masarautar nan ba kenan.. Ta yaya zai sanar dasu ba neman mulki bane gabansa, ta yaya zai sanar dasu abinda ya dawo dashi yasha bambam da abinda suke tinanin shi ya dawo dashi.... Muryar Giwa ya sinkayo tana ci gaba da fad’in ā€œKai nake sauraro d’ah na nasan bazaka bani kunya ba...!ā€
K’ak’aro gajeren murmushi yai irinta masu mulki kana ya soma fad’in ā€œAllah shi taimaki Giwar Sarki AbdulJabbar, Allah shi taimaki Mai babban d’aki... Allah shi taimaki Gimbiya Turai d’iyaga Sarki Jamaludden na k’asar Benin, La princesa de benin (the Princess of Benin), La reina de jos (the Queen of Jos)... Mi hermosa madre (Kyakkyawan mahaifiyata) Allah yaja zamaninki...!!ā€

Tinda ya soma mata kirari take dubansa da murmushi saman fuskarta, hannu tasa ta shafi fuskarsa kad’an k’walla tab idanunta... Tana matuk’ar k’aunar Mahmood, akwai wani abinda ya banbanta dashi cikin ā€˜yan uwansa...

Yarima Mahmood ya d’an kamo hannunta ya sumbata su duka biyu d’in suna sakarwa juna murmushi kana ya soma fad’in ā€œMaami, bawai na banbanta da ra’ayinki bane... Bawai bana son amsar tayinki bane... Ke duk kin wuce haka a wajena... Umarni kawai zaki bani nabi.... But Maami, sarauta ba layina bane... Almost 14 years bana Masarautar nan saidai nazo lokaci zuwa lokaci, da yawan wasu abubuwan ban saba dasu ba, ban San ya ake gudanar dasu ba... Maami idan nace zan amshi sarautar Masarautar nan hakan na nufin tamkar sabon karatu zan fara, dole na koyi abubuwa da dama.... Inaga zaifi kyau Idan aka nad’a wanda yafini cancanta da dacewa da rik’on Masarautar...ā€

Cikin saurin Yarima Jamal Ke girgiza kai yana fad’in ā€œNo, no Yaya... Babu wanda ya dace ya kuma cancanta face kai, Yaya kana so mun fice daga Masarautar nan ne cikin k’ask’anci da tozarci...? Yaya kana sona fidda matan mahaifinmu a d’akunansu akaisu wani k’auye ne..? Yaya so kake mu fice daga cikin gidan da aka haifemu aka renemu cikinsa...? Yaya so kake mu bar asalinmu da abinda muka gada... Nasan duk bazaka so abubuwanda lissafo su faru ba....!ā€ Ya k’arashe cikeda kulawa...
Giwa kam k’uri taiwa Mahmuda tana kallon sarautar Allah...

Yarima Mahmood ya kamo hannayen Yarima Jamal su duka biyu d’in suna duban juna sanda Mahmood Ke fad’in ā€œDik ba wannan nake nufi ba Jamal, kuma bana fatan d’aya daga cikin abubuwanda ka lissafo su faru, sannan Allah ya albarkaci mahaifinmu da yara maza d’ai d’ai d’ai har guda hud’u and we are all entitled to the throne.... Ga Yazeed gaka nan, even Fu’ad zai iya zama sarki ba wani abu bane.. Ba lallai sai Babba ba k’aramin cikinmu ka iya zama kan Karagar mulkin nan hardai yanada damar data mallaka masa hakan... So Maami why not a tsaida d’aya daga cikin ā€˜yan uwana....ā€ Wata kakkausar murya ce da ko shakka babu sun San mai ita ta katsesu da fad’in ā€œBabu wanda ya isa, babu mahaluk’in da ya isa ya fitar da mulkin Masarautar nan daga hannun ahalinmu... Babu wanda ya isa ya fitar dani daga gidan mahaifina, Mu kad’ai ne jinin sarauta, mu kad’aine muka gaji sarautar... And yes Yaya, you’re absolutely right... Naji dad’i daka d’auki shawarina... For the first time we’re on the same page, kai kanka ka amince babu wanda ya cancanta ya zama sarki face ni Yazeed..!!!D’add’aya yake maganar yana takowa cikin katafaren d’akin hannayensa guda biyu hard’e ta baya, cikin taku mai cikeda k’asaita yake tafiyar nasa tamkar wani Amale... saida ya iso dadai tsakiyar d’akin kana ya karkato yana fuskantar Mahmood, lokaci guda yake furta ā€œAnd now that we are on the same page, inaso ka jaddadawa wad’annan masu sarautun Gargajiyan kar wani daga cikinsu yayi gigin shiga gonata, ina rantsuwa da mahallicina idan d’ayansu yayi kuskuren jayayya dani da sarauta ta, ba rawaninsa kawai da muk’aminsa zai rasa ba, zai iya rasa abinda yafi wad’ann mahimmanci a wajensa... Ina nufin zai iya rasa ransa..!!ā€ Ya k’arashe cikin tsananin huci...

Girgiza kai kad’an Mahmood yai kana yace ā€œAnd kana tunanin kaine wanda ya dace da kujerar..?ā€

Saida ya kuma takowa kad’an murmushin bai bar saman fuskarsa ba kana yace ā€œI’m far better than right... I am perfect... Yeah Perfect..!ā€ Ya k’arashe cikeda pride

K’uri Mahmood yai masa yana dubansa , lokaci guda ya mik’e tsaye suna fuskantar juna shida Yazeed, idanu cikin idanu suke duban juna kana Mahmood ya soma fad’i cikin dakewar murya ā€œWanda duk yace shine toh ba shi bane, sannan ba’a shugaba mai zafin zuciya wanda baida jarumtar kwantar da zuciyarsa idan rai ya b’aci, ba’a shugaba maras d’a’a da ganin girman na gaba, ba’a shugaba maras tsaida dokokin Ubangijinsa... Shi shugaba ya kamata ya kasance mai taushin zuciya sannan Jarumi, taushin zuciya domin ya tausasawa al’ummansa yaji k’ansu sannan ya kwantata adalci a tsakaninsu, Jarumi domin ya zamto sulke wajen kare al’ummansa da tsaresu daga abokan gaba... Mai bin dokokin Ubangijinsa domin ya zamto abin koyi ga Al’ummarsa... Mai girmama na gaba domin wad’anda suke k’asa dashi su girmama shi.... Ta yaya nake tunanin zaka iya zamtowa shugaba bayan baka aikata d’aya daga cikin abinda na lissafo... Nayi kuskure da nai zaton zaka iya maye gurbin mahaifinmu.... Yanzu na tabbata baka cancanta ba Yarima Yazeed....!!ā€ Ya k’arashe yana mai kuma matso da fuskarsa dab na Yazeed cikin muryarsa mai cikeda amo....

Shu’umin murmushin ne nasa saman fuskarsa, lokaci guda ya lank’wasa Kai kad’an yana mai k’arewa Mahmood d’in kallo kana yace ā€œToh waye ya cancanta..? Kai...?!ā€ Yai murmushi mai sauti irinta masu mulki kana yaci ya a da fad’in ā€œIdan duk kanada qualities d’in daka k’irgosu abu guda d’aya tak da ka aikata ya rushesu... Yarima Mahmood... Mak’aryaci yafi dacewa da shugabanci irinta siyasa amma ba shugabanci irinta Babban Gida ba..!!!ā€

Cikin zafin nama Mahmood dake tsananin huci yake furta ā€œDon’t Yazeed... Don’t you dare cross the line...!!!ā€

Yazeed da ko a jikinsa Murmusawa ya kumayi kana yace ā€œOh really now... Your Royal highness..! Baka so a fad’i naka aibun, bayan Kai ka iya fad’in na wasu cikeda k’warin gwiwa... Ai ba’a sarki matsoraci mai tsoron Ta kife... K’aryar Jarumta kake...Yarima Mahmood..!!!ā€

ā€œYazeeeedddd!!!!ā€ Ya daka masa uban tsawa had’ida d’aga hannunsa da niya watsa masa mari... Saidai tuni Jamal ya shige tsakaninsu yana tausan Mahmood ā€œYaya please don’t... Kar ka mareshi... Kayi hak’uri dan Allah....Allah ya huci zuciyarka..!ā€

Idanuwansa da suka kad’a sukai jazir yake duban Yazeed dasu, abinda da wanda bai iya b’acin rai ba sai abin ya zama abin ban tsoro... Kana iya hango yanda k’irjin Mahmood Ke hawa yana sauk’a alamun tsananin bugun zuciya da b’acin rai....

Lokaci guda yake nuna Yazeed da d’an yatsa kana yaci gaba da fad’in ā€œI’ll warn you for the last time Yazeed.... Do...not..try..me!!! Do..not..cross..the line..!!!ā€ Daga haka sa kai yai ya fice cikin sassarfa da tsananin b’acin rai...

Yazeed ya rakasa da muguwar kallo kana ya kuma sakin shu’umin murmushinsa, gyara zaman rigarsa yai had’ida kuma hard’e hannayensa ta baya d’abi’ar masu mulki, ya maido da dubansanga mahaifiyarsu data cika tai fam, ta tsaresa da idanu cikin tsananin b’acin rai....

Dukda ya hango tsananin b’acin rai a idon mahaifiyarsu hakan bai hanasa sakin murmushi da gefen bakinsa ba, kana ya isa kusan k’afafunta ya zauna yana mai gaidata, ya k’arashe yana fad’in ā€œA saka min albarka Maami na...!ā€

Daga Giwa da Yazeed ya d’auko hannunta guda ya d’aura saman kansa alamun saka albarka har Jamal dake tsaye tamkar statue kallon mamaki suke bin Yazeed dashi... Shifa ko a jikinsa da alama, baima san yayi laifi ba... Yazeed bazai tab’a canzawa ba, Ta zaci aure zai canza Yazeed gashi yayi yara har biyu amma halinsa na nan babu abinda ya ragu saima wandake k’aruwa... Har kullum addu’an shiriya takewa Yazeed amma kaman dad’a tab’arb’arewa yake... Tana ji ya gama fad’in iyaka abinda zai fad’i tamkar wani mai bata sak’o kana ya mik’e yai ficewarsa cikeda k’asaita wanda Ke matuk’ar masa kyau...

Jamal ya bisa da kallo har ya b’acewa ganinsa kana ya maidoda dubansaga mahaifiyarsu da ko shakka babu k’walla yake hangowa cikin idanunta, dukda k’ok’arin dannesu da takeyi, shid’in yafi kowa sanin mahaifiyarsu yasani idan abu na matuk’ar damunta... Bai wata wata ba ya isa yanda magungunata Ke aje ya d’auko da kansa yana b’alla mata dan bazai iya jiran wata kuyanga tazo bata magani ba... Sai faman sannu yake mata yana tausanta... Jinjina masa kai kurum take abubuwa da dama k’unshe cikin zuciyarta... Idanma aka ce an bar karagan mulkin nan tsakanin yaranta kad’ai tasan wani yak’i ne mai zaman kansa... Sai yanzu maganan Tal’udu ke kuma dawo mata da yace yaga k’ura mai duhuwan gaske da dandatson mayak’a... Amma koda za’a tashi wannan masarauta bazata tab’a bari dai sarautar ya kufce masu ba... ā€œWambaiā€ sunan da zuciyarta ta ambata...

Take ta sanar da Jakadiya Tai mata kiran Ubandoma...

***

Tsaf ta shirya cikin jan leshi d’inkin doguwar riga da yai matuk’ar amsarta, ta d’aura alkyabba fara k’al wanda Umaima ta Aiko mata da safen nan... Tsaye tai gaban full length mirror tana duban Wai ita SAUDATU ke sanye da kaya ta mulki da sarauta yau d’in... Ta tina sanda ta fice daga Masarautar cikin k’ask’anci da tozarci yau sai gashi ta dawo cikin karamci da girmamawa... Tabbas Saudatu ta mutu Muhibbah ce a raye yanzu...Ta saki murmushi mai ciwo a hankali kumatunta suka lotsa... A fili take furta ā€œYou better be ready, cos my revenge is action...!!ā€ Ta k’arashe cikin tsananin karaji tana mai duban fuskarta cikin madubi.....


(Anya bakiyi kuskure ba Muhibbah...? Muje zuwa..)



SameenaAleeyoušŸ“š
[5/29, 9:41 PM] +234 703 453 9908: *šŸ‘‘āœØMUHIBBAHāœØšŸ‘‘*




*009*





*Ā©ļøSameena Aleeyou...āœšŸ½*




Zama yai gefen bedside yana jiran fitowarta dan yaji alamunta a closet, ya sani bazai wuce shirin school take ba...
Idanunsa suka sauk’a kan picture dake aje gefen bedside d’inta, ya jima yana duban picture d’in... Lokaci guda ya saki murmushi a hankali dan bazai tab’a mance ranan da sukai hoton ba a cen k’asar Spain, lokacin family d’insa na cikeda Farin ciki, inama abubuwa zaku koma kaman yanda suke before.... Yasa hannu ya d’auki hoton yana shafawa a hankali... Zahra da fitowarta kenan daga closet sanye cikin shiga irinta ā€˜yanmakaranta tsaye tayi tana duban mahaifin nata yanda yai k’urima picture d’insu, lokaci guda tausayinsu gaba d’aya na kuma kamata.... Ta d’an tako kad’an kana ta zauna gefensa...
ā€œGood morning Paa...ā€ Ta fad’i sanda take zama...
Gyara zamansa ya d’anyi yana mai aje picture d’in kana yace ā€œGood morning my love... Da fatan kin tashi lafia..?ā€

Jinjina masa kai tai kana tace ā€œLafia Paa... How about you Paa..? You seemed worried... Is something bordering you..?ā€
K’ak’aro murmushi yai had’ida shafa kanta kad’an ā€œBabu komai Princess, do you want me to take you to school by myself...?ā€

D’an dubansa tai da mamaki kana ta murmusa ā€œC’mon Paa, kai da kanka kake ce min nan ba Spain bane, things are different here...Well, I’m starting to get used to it... Nasan bazamu tab’a komawa kaman yanda muke a baya ba... It hurts tho..!ā€ Ta k’arashe tana mai zura safar k’afanta....
Dubanta yake da wasu irin idanu, shi kad’ai yasan mai yakeji cikin zuciyarsa, yanada good relationship da d’iyarsa, bazaiso wani ko wani abu ya b’ata wannan alak’a mai kyau da yakedashi shida d’iyarsa ba, Amsar socks d’in da take k’ok’arin sakawa yai lokaci guda ya sauk’o daga saman gado yana zira mata safar a k’afarta... Zahra tai masa K’uri tana dubansa had’ida tunanin anya ba wani abin Ke damun Paa d’inta ba... K’ok’arin amsar safan take tana furta ā€œPaa you don’t need to do this... Zan iya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login