Showing 15001 words to 18000 words out of 26566 words

Chapter 6 - Miftahuzzarbil Book 2 Complete By Abdulaziz Sani Madakin Gini.txt

tamau a hannu ya kasa motsi.
Kawai sai ya fashe da kukan takaici.
Markahus sabus ya dube shi ya ƙyaƙyale da dariya yace,
"Yau fa ake yinta ga zaki a hannun kyanwa,harma kyanwar ta sashi kuka.
Ashe dai ba girma ne ƙarfi ba.
Daga yau kuma babu batun kuri ko cika baki, domin baba ma da babansa."😅😅😅
Durmazalu ya dubi markahus sabus ya daka masa harara.
Sannan yace,
"To ƙaramin mara kunya ai dama ni banyi kuri ba tunda farko, domin saida na gaya maku cewa komai zai iya faruwa ga dukkanin mu ban ware kaina ba nayi kuri."
Haka dai aka cigaba da tafiya da su har izuwa wani lokaci mai tsawo.
Sannan aka iso wani babban gida wanda babu mai girmansa a duk faɗin birnin.
Gidan ya kasance an gina shine da farar darma.
Duk iya yawon markahus sabus a duniya bai taɓa ganin gida mai girman wannan ba.
Koda aka shigar da su cikin gidan kuwa sai gashi ana ratsawa da su ta cikin waɗansu ƙayatattun fadoji na alfarma.

Mu HADU a part H DON JIN CIGABAN WANNAN KASAITACCEN LITTAFIN
NAJIBULLAH MUHAMMAD🥰**MIFTAHUZZARBIL**
LITTAFI NA BIYU 🤝😍
PART H 😊
NA ABDUL'AZIZ SANI MADAKIN GINI 😎
TYPING AHMAD MUNNIR🤝
POSTING NAJIBULLAH MUHAMMAD 💪

Note: kuyi hakuri akan rashin isasshen posting akan lokaci. Kuyi sani cewa hakan ya faru ne sakamakon yanayin rayuwar da ya, Wanda ku kanku kunsan halin da ake ciki.
Don haka ku rinka yi mana uzuri.
A koyaushe muna fatan Allah ya taimakemu tare da fatan Allah ya tattara mu a cikin gidan Aljannar Firdausi Nuzila🤝😍🩷🙏

MARUBUCIN YACI GABA DA CEWA...

Duk iya yawon markahus sabus a duniya bai taɓa ganin gida mai girman wannan ba.
Koda aka shigar da su cikin gidan kuwa sai gashi ana ratsawa da su ta cikin waɗansu ƙayatattun fadoji na alfarma.
Kowace fada guda ɗaya ta ninka fadar nan ta Baharzus sau uku a girma,kyau da ƙayatuwa.
Saida aka wuce fadoji shida sannan aka tsaya da su a ta bakwai.
Ita dai wannan fada ta bakwai ta kasance uwa ga sauran fadoji shida na baya,kuma duk abinda ke cikin ta fari ne sol babu baƙi ko wata kalar dabam.
Abubuwan al'ajabi kuwa gasunan birjik ba adadi, domin anan ne suka ga kifaye na yawo a fili ba a cikin ruwa ba,haka kuma suka ga mutum mai rabin jikin zaki.
Wato kansa da hannayen sa ne na mutum,amma daga cibiyar sa zuwa gangar jikinsa da ƙafafuwan sa duk na zaki ne,haka ma ƙirjinsa irin na zaki ne wanda ke cike da gashi.
Wannan mutum na kishingiɗe bisa wata doguwar kujera ta alfarma ya riƙe wani babban tambulan cike da ruwan inibi yana sha,kuma yana karkaɗa jelarsa alamar yana jin daɗin ɗanɗanon ruwan inibin a bakinsa.
Koda aka shigo dasu markahus sabus cikin wannan ƙasaitacciyar fada sai mutumin nan mai rabin jikin zaki ya washe fuskar sa da murmushi ya ajiye tambulan ɗin ruwan inibin akan ƙaramin tebur dake gabansa.
Sannan ya dubi su markahus sabus yace,
"Lale marhaban,ina mai yi muku barka da zuwa birnin Madinatul Aslik yaku hadiman boka Shamharu."
Cikin tsananin mamaki su markahus sabus suka dubi juna.
Sannan suka maida hankalinsu ga mutumin suka yi shiru.
Caraf sai markahus sabus yace,
"Ya kai wannan sarki mai karamci,ya akai ka san da zuwan mu nan kuma yanzu me kake nufin aiwatarwa da mu har da kasa aka kamo mu aka gurfanar damu a gabanka?"
Koda jin wannan tambaya sai mutumin ya bushe da dariya.
Sannan yace,
"Ya kai markahul sabus kayi sani cewa ni sunana Sarudul Makam kuma nine sarkin wannan duniya ta Madinatul Aslik.
Babu wani sarki a cikin duniyar sama ko ta ƙasa ko ta tsakiya wanda bansan da zamansa ba,kuma bansan da shirin sa ba,ko burin rayuwar sa.
Kuyi sani cewa duk abinda ya faru gareku naji kuma na gani a cikin madubin tsafina.
Yanzu haka kun fito ne daga birnin duwatsu inda kuka samo narkakken dutsen da yafi kowane dutse girma a duniyar ku.
Yanzu kuma kuna son ku wuce izuwa duniyar ƙarshe ta nan ƙasan bakwai,don ku ɗebo dutsen wuta.
Idan kuka sami nasara ne zaku je ku ɗebo rabin ruwan tekun duniyar ku.
Sannan ku kaiwa Shamharu waɗannan abubuwa uku,don ya ƙera kubar MIFTAHUL ZARBIL wacce da ita ne zai buɗe fadar Saukatul Askur ta sarki Azmul gallar,don ya ɗauko kundin tsatsubansa ya karance shi saboda ya sami sirrikan tsafinsa.
Ko ba haka bane?"
Markahus sabus yace,
"Zancen ka dutse ne."
Sarudul Makam ya sake bushewa da dariya yace,
"Kuyi sani cewa gaba ɗaya duniyoyin nan guda bakwai dake nan ƙarƙashin ƙasa na ƙarƙashin ikon mahaifiyata,kuma duk 'yan uwana ne ke mulki a sauran duniyoyi shida.
Rana guda aka haife mu mu bakwai,amma nine na fara fitowa daga cikin ta,sai kuma Saradul Hasal, Saradul Algaz, Saradul Hisnu, Saradul Badal da kuma Saradul Imzan,wanda shike sarautar duniyar ƙarshe.
Ina mai sanar daku cewa gaba ɗayan mu mu bakwan nan bama ga maciji kuma kowa na ƙoƙarin kashe kowa.
Ba komai ne ya haddasa haka ba face kishi akan mulki.
A da can kafin mutuwar mahaifiyar mu duniyoyin bakwai a ƙarƙashin wannan duniyar tawa suke,kuma mahaifiyar mu ke mulkin ta.
Amma da ta kwanta ciwon ajali sai ta raba mana duniyoyin ta baiwa kowa guda ya mulka,don gudun rigima a tsakanin mu.
A halin yanzu kowa daga cikin mu so yake ya haɗe duniyoyin bakwai ya mulka shi kaɗai.
Kun ga kenan dabarar da tayi ba tayi amfani ba tunda dai rigima ta karƙe a tsakanin mu.
Nayi bincike na gano cewa sai nayi wani aiki sannan zan iya mallakar waɗannan duniyoyi shida kuma aikin ba zai yiwu ba saida taimakon halittu irin ku.
Don haka ni yanzu zuwan ku nan rahama ce a gare ni,don tamkar cikar buri na ne.
Lallai bazan bari ku gusa daga nan ba face kun bani haɗin kai nayi wannan aiki tare da ku."
Koda sarki Sarudul Makam yazo nan a zancen sa sai markahus sabus yayi ajiyar numfashi yace,
"Ya kai wannan sarki ina son na nemi wata alfarma guda ɗaya a wajen ka kafin ka sanar damu wannan aiki da zamu tayaka."
Sarudul Makam yace,
"Faɗi abin da kake buƙata."
Markahus sabus yayi gyaran murya sannan yace,
"Ya kai wannan sarki kayi sani cewa a duniya babu abinda nake so kuma nake matuƙar son gani face gimbiya Sima.
Ina son ka sanar dani halin data shiga,tun daga lokacin dana rabu da ita.
Tunda kace ka san duk abinda ke faruwa a ko'ina a cikin kowacce duniya."
Koda jin haka sai sarki Sarudul Makam ya ƙyalƙyale da dariya sannan yace,
"Ai wannan aiki ne mai sauƙin gaske,kuma ina yima albishir da cewa bama gaya maka zanyi ba.
Zan nuna maka al'amarin ne a zahiri yanzu take kaga duk abinda ya faru gareta."
Nan take Sarudul Makam ya shafi wani jan allon tsafi,saiga hoton abubuwan da suka faru ga gimbiya Sima na zayyana daki-daki tun daga lokacin da markahus sabus ya tafi da ita gida wajen mahaifiyarsa Samaratu kawo izuwa lokacin da aka yi gagarumin yaƙin nan nasu aljani Abtarul Hudeis da su sarki Lu'umanu sa'adda Hubairu da gimbiya Sima za suje garin nan inda gidan kayan tarihi suke har kuma izuwa lokacin da aka ɗaura auren gimbiya Sima da jarumi Hubairu a birnin Laharim aka kafa tutar musulunci a garin.
Koda markahus sabus ya gama ganin waɗannan abubuwa,sai idanunsa suka ciko da ƙwalla ya fara zubar da hawaye,don yasan cewa shike nan ya rasa gimbiya Sima har abada.
Nan dai markahus sabus ya shiga tunani a zuciyarsa yana mai cewa yanzu mene ne amfanin rayuwar sa tunda dai duk gwagwarmayar da yake yi akan gimbiya Sima ne,kuma gashi ya rasa ta.
Markahul sabus ya tuno da wahalar da yasha a hannun sarki Lu'umanu kuma ya tuno da gwagwarmayar da yayi da dodo kiryanu sa'adda yaje ɗebo tsumi.
Haka kuma ya tuno da yadda rayuwar sa ta kasance a hannun matsafan duniya sai yawo ake da shi a kaishi can a wulla shi can ba shi da wani iko nasa.
Ya sake yin nazari akan hanyar da zaibi ya kuɓuta sai yaga ai a duniya babu waɗanda suka gagari matsafa face ma'abota addinin Musulunci, tunda yanzu ma gashi a zahiri yaga yadda su Abtarul Hudeis suka sami nasara akan su Lu'umanu.
Nan take markahul sabus yaji zuciyarsa ta aminta da addinin musulunci, kuma yaji yana son shiga cikin addinin sai dai kash bai san yadda zai shiga cikin addinin ba.
Sarki Sarudul Makam ya dakawa aljani Markahus sabus tsawa yace,
"Tunanin me kake yi?
Bani hankalin ka nan don kaji aikin da zamu yi yanzu.
Wannan aiki ba komai bane face zamu tafi tare daku izuwa waɗannan duniyoyi guda shida dake ƙasan wannan, domin mu yaƙe su ɗaya bayan ɗaya,mu kashe na kashewa mu kama na kamawa,har dasu 'yan uwan nawa kuwa.
Sannan ku shiga cikin baitul malinsu ku ɗauko mini wasu ƙahonni na zinare guda shida.
Ma'ana a cikin kowacce baitul mali akwai ƙahon zinare guda.
Idan aka haɗa jimila ne zai zama shida,idan na mallaki waɗannan ƙahonni guda shida zan soka sune anan cikin tsakiyar duniya ta.
Sai na yi hakan ne zan iya mulkar waɗannan duniyoyi guda shida.
Kuyi sani cewa waɗannan ƙahonni guda shida 'yan ƙanana ne mitsi-mitsi,amma mu ba zamu iya taɓa su ba da hannuwan mu.
In kuwa muka taɓa su take zamu narke mu zagwanye.
Ba komai bane ya haddasa hakan ba face cewar mu a jikin mu babu jini face ƙashi da tsoka zalla.
Kuma dole sai mai jini a jikine zai iya taɓa waɗannan ƙahonni."
Koda jin wannan batu sai mamaki ya kama su markahul sabus.
Boka Jinshan ya dubi sarki Sarudul Makam yace,
"Ya zaka ce babu jini a jikin ku?"
Sarudul Makam yayi murmushi yace,
"Ai dama nasan ba zaku amince ba,don haka yanzun nan zan nuna muku zahiri."
Nan take Sarudul Makam ya ɗauko wata zureriyar wuƙa ya feraye hannun sa saiga ƙaton nama ya zaftaro yana lilo,amma ko ɗigon jini babu face ƙasusuwa da jijiyoyi ba kyan gani.
Cikin sauri su markahul sabus suka kau da kansu ga barin kallon hannun.
Sarudul Makam ya ƙyalƙyale da dariya sannan ya kamo yankakkiyar tsokar dake reto a jikin hannunsa ya maida ita mazaunin sa.
Take wajen ya haɗe kuma ya shafe kamar ba a taɓa yanka ba.
Al'amarin daya ƙara baiwa su markahul sabus mamaki kenan.
Boka sulbaini ya dubi Sarudul Makam yace,
"Ya kai wannan sarki shin mutanen dake sauran duniyoyin ƙasa duk irin ku ne?"
Sarudul Makam yace,
"A'a ba irin mu bane.
Kuyi sani cewa duk mutumin daku ka gani anan ɗana ne ko kuma 'yata.
Ma'ana duk nine na haifi gaba ɗayan mutanen wannan duniyar tare da matata guda ɗaya.
Kuma ga matar nan tawa a tsaye a gaban ku."
Sarudul Makam yayi nuni izuwa ga wata wadar tsohuwa tukuf.
Launin jikinta gaba ɗaya ja ne jajur.
Kuma haka duk mutanen garin suke.
Sarudul Makam ya cigaba da cewa,
"Idan kuka je duniya ta biyu zaku iske cewa launin mutanen garin gaba ɗaya fari ne, saboda haka launin matar Sarudul Hasal take.
Matar Sarudul Algaz shuɗiya ce,matar Sarudul Hisnu baƙa ce,matar Sarudul Badal koriya ce,matar Sarudul Imzan kuwa ruwan ɗorawa ce.
A taƙaice dai kowacce jama'a yanayin mahaifiyar su ne."
Salusa ta tsoma baki cikin wannan zance tace,
"Ya kai wannan sarki na fahimci cewa makami baya tasiri a jikin ku,ta yaya zaka yaƙi sauran 'yan uwanka dake cikin duniyoyin shida?"
Sarudul Makam yayi dariya yace,
"Haƙiƙa babu wani ƙarfe da zai iya tasiri a jikin mu domin ko an daddatsa mu anyi gutsin gutsin da mu sai jikin mu ya haɗe ya manne,kamar yadda yake.
Bari na baku misali ku gani."
Nan take Sarudul Makam ya sake luma waƙunnan a cikin ramin idonsa guda ya ƙwaƙulo ƙwayar idon ya ajiye ta akan tebur.
Kogon ramin idon yayi zururu babu kyan gani.
Koda Sarudul Makam ya durƙuso da fuskarsa ƙasa daf da kan tebur ɗin sai ƙwayar idon nasa tayi tsalle ta koma cikin gurbin ramin idon da kanta.
Sarudul Makam ya bushe da dariya sannan ya murtuke fuskar sa a lokaci guda.
Kawai sai ya buɗe wata akwati ya ɗauko wata irin takobin haske.
Ita dai wannan takobi in ka taɓa ta da hannu sai kaji baka taɓa komai ba,amma a zahiri surarta ta haske ce.
Ƙotarta kawai ake iya taɓawa asan an taɓa ta.
Sarudul Makam yace,
"Kunga wannan takobin ta musamman ce nine na ƙirƙire ta daga cikin sirrikan tsafina.
Da wannan takobi ne kaɗai za'a iya kashe irin mutanen mu, domin duk wanda aka sara da ita take zai zagwanye ya narke.
A halin yanzu na ƙera irin wannan takobi guda miliyan dubu ɗaya da ƙwaya biyar.
Ina dakarun yaƙi guda miliyan dubu ɗaya cif kunga kenan akwai sauran takobi guda biyar,kuma ba ta kowa bace face taku ku biyar ɗin nan,dama na tanade su ne saboda ku don nasan cewa kuna tafe."
Cikin matuƙar tsoro boka sulbaini ya dubi sarki Sarudul Makam yace,
"Au kana nufin cewa muma zamu tayaku yaƙin ne?"
"Ƙwarai kuwa,idan ma baku jagoranci yaƙin ba ba za mu yi nasara ba.
Kunga shike nan muna gama yaƙin sai nasa a ɗebo muku duwatsun da kuka zo nema a can duniyar ƙarshe ku yi tafiyar ku salin alin cikin kwanciyar hankali."
Koda jin wannan batu sai markahus sabus yayi tsaki yace,
"Ina fa batun salin alin kace dai bayan mun sha muguwar wuya ko kuma bayan mun halaka?"
Sarudul Makam ya ƙyalƙyale da dariya yace,
"Koma mene ne ai ba kuda zaɓi dole ne kuyi yadda na tsara in ba haka ba kuwa yanxun nan na azabtar daku da irin azabar da baku taɓa ɗanɗana ta ba."
Salusa tace,
"Kai kuwa wace irin azaba ce wannan wadda bamu taɓa ɗanɗana irin ta ba?"
Sarudul Makam yayi murmushi yace,
"Karki damu yanzun nan zan jarraba miki ita."
Nan take sarki Sarudul Makam yasa aka zo da wata ƙatuwar kwalba wadda aka rufe ta da wani irin faifai na ice.
Kawai sai yasa aka kama Salusa da ƙarfin tsiya aka sata a cikin kwalbar aka rufe da wannan faifai.
Yin hakan ke da wuya sai jikin Salusa ya fara daddarewa yana sala sala kamar ana feraye ta da zabira.
Nan fa Salusa ta rinƙa ihu saboda tsananin azaba,saida ta suma.
Sannan ne sarki Sarudul Makam yasa aka fito da ita daga cikin kwalbar.
Salusa dai bata farfaɗo ba sai bayan sa'a guda.
###########
Sarudul Makam ya dubi su markahul sabus yace da su,
"Duk wanda yayi mini gardama daga cikin ku haka zan yi masa."
Ya sake nuna salusa da ɗan yatsa yace,
"Ke kuma idan baki gamsu ba da wannan azabar akwai wadda ta ninka ta sai a jarraba miki ita kiji nata ɗanɗanon."
Cikin tsoro da kuka salusa tace,
"Kayi mini rai haƙiƙa na gamsu da wannan ma."
Markahul sabus ya bushe da dariya sannan yace,
"Amma dai salusa kinyi wauta koda yake ban yi mamaki ba domin 'yar fari ce ke zaki iya yin abinda yafi haka,amma in banda wauta wa zai nema wa kansa wahala."
Gama faɗin haka ke da wuya sai Sarudul Makam yace,
"Yanzu za a kai ku masauƙin ku don ku huta,amma ku kwana da shiri domin gobe da safe zamu yi shiri mu tafi wannan yaƙi."
Nan take dakarun nan da suka zo da su suka sake surarsu suka ɗora su akan manyan jemagun nan.
Su kuwa jemagun sai suka buɗe fukafukansu suka yi sama.
Sannan suka cigaba da tsala gudu a sararin sama.
Saida akayi tafiyar daƙiƙa ɗari sannan aka sauke su markahul sabus a masaukensu.
Masaukin ya kasance wani tamfatsetsen gida mai tsananin girma da faɗi domin aljani Durmazalu bai isa ya ƙure ƙarshen sa ba a cikin sa'a uku duk da cewa kuwa yana da fukafukai miliyan ɗaya.
Shi dai wannan gida a cike yake da hadimai sai tafiyar da aikace-aikacen su kawai suke.
Bayan an kai su markahul sabus cikin wani babban ɗaki sai aka kawo musu abinci da abin sha kala biyu.
Kalar farko irin na mutane ne irin su boka jinshan.
Kala ta biyu irin na aljanu ne.
Nan take suka kama ci da sha aka bar salusa ita kaɗai a gefe guda tayi zugum da tagumi kamar zata fashe da kuka kuma dama ga raɗaɗin ciwon jikinta,ga yunwa ga ƙishirwa.
Nan fa tausayin ta ya kama markahul sabus yace,
"Yake salusa taso mana kizo muci abinci."
Salusa ta gyaɗa kai tace,
"Ai ni babu abinci na anan.
Ni kam ina ganin cewa sarkin nan fa baya ƙaunata kawai so yake ya halaka ni.
Ku dubi fa yadda jikina ya zama sala-sala."
Rufe bakinta keda wuya sai ga wani hadimi ya shigo ɗauke da wani ƙaton faranti.
Akan farantin dafaffiyar dalma ce ke fitar da tururi.
Kai tsaye hadimin ya ajiye farantin a gaban salusa.
Koda taga abinda ke cikin farantin sai tasa hannu biyu ta rinƙa ɗiba tana shanye wa.
Da yake jikinta na dutse ne sai ruwan darmar data sha ya rinƙa manne jikin nata.
Cikin 'yan daƙiƙu kaɗan duk ciwon jikin nata ya ɓace ɓat.
Kawai sai su markahul sabus suka ji tayi wata irin gyatsa mai kama da rurin giwa.
Tana gama gyatsar ta dubi jikinta taga ya warke sumul gaba ɗaya, kawai sai ta bushe da dariyar farin ciki.
Tayi ta ƙyalƙyala dariyar kamar ba zata daina ba.
Dariyar ce ta baiwa su markahul sabus dariya suma suka hau ƙyaƙyatawa.
Kashe gari da sassafe sarki Sarudul Makam yasa aka zo aka ɗauki su aljani Durmazalu aka tafi dasu izuwa can fadarsa.
Da zuwa suka iske dakaru miliyan dubu ɗaya a tsaitsaye a jere kan layi,sahu sahu kowannensu riƙe da takobin haske.
Sarki Sarudul Makam na tsaye a gaban su yana kallon yawansu da kuma daidaiton tsayuwar su.
Koda aka zo da su markahul sabus sai aka gurfanar dasu a gaban sa.
Nan take ya ɗauko takubban haske guda biyar ya rarraba musu.
Sannan ya umarce su dasu shiga cikin sahun mayaƙan.
Ba tare da fargabar komai ba suka bi umarni.
Kawai sai sarki Sarudul Makam ya fara bayani kamar haka:
"Yaku mayaƙana kuyi sani cewa a yau ne ranar da zamu jajirce iyakar jajurcewar mu.
Yau ne ranar da zamu zamo iyaye ga sauran duniyoyin dake ƙasanmu,kuma yau ne ranar ƙwatar ranmu da cikar burin mu.
Ina mai kira a gare mu gaba ɗaya damu sallama rayuwar mu don kare mutuncin mu.
A matsayina na mahaifin ku ina mai horonku da kada ɗayan ku yaji tsoro ya gudu daga filin daga.
Kuyi sani cewa kamar yadda muke wannan shiri na son mallakar sauran duniyoyin nan haka suma suke nasu shirin na son mallakar mu.
To amma sunyi sake ɗan zaki ya girma,kuma sun manta da cewa wanda ya riga ka kwana dole ne ya riga ka tashi.
Ya ku 'ya'yana kuma mayaƙana kuyi sani cewa ga baƙi nan su biyar a tare damu, waɗannan baƙi sune za suyi mana jagora a cikin wannan yaƙi kuma su kaɗai ne zasu iya shiga cikin baitul malin duniyoyin ƙasa su ɗauko mana ƙahonnin nan guda shida."
Lokacin da sarki Sarudul Makam ke wannan jawabi sai su boka jinshan suka nutsu suna sauraronsa.
Koda jin cewa sune zasu jagoranci wannan yaƙi sai markahul sabus ya matsa daidai kunnen boka jinshan yayi masa raɗa yace,
"Ya kai jinshan kayi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login