Showing 24001 words to 26566 words out of 26566 words

Chapter 9 - Miftahuzzarbil Book 2 Complete By Abdulaziz Sani Madakin Gini.txt

da yawa.
Yanzu babu abinda ya kamace mu face tunanin yadda zamu sake tarar waɗannan mugayen dodonni, domin tabbas sai sun dawo mana."
Koda jin haka sai hankalin Jafar, Yalisa da Hasiyatul Lauras ya dugunzuma aka rasa wanda zai ce ƙala.
A sannan ne Jafar ya fara da cewa,
"Tunda aka fara yaƙin nan bai ga Salusa ba."
Nan take ya tambayi Yalisa da Gulzum ko sunga Salusa?
Gulzum ya sunkui da kansa ƙas cikin alamun karayar zuciya yace,
"Ai salusa ta mutu kuma dodo Abulungu ne yayi mata wawan duka aka take kanta ya rugurguje duk da cewa kuwa na dutse ne, domin tarwatsewa yayi, yayi filla filla.
Yanzu haka gawarta na nan a inda muka gwabza yaƙi ni da Abulungu."
Yayin da Gulzum yazo nan a bayanin sa sai jikin Jafar da Yalisa ya ƙara yin sanyi kuma suka sake tsorata ainun da wannan bala'i da suke ciki.
Saida Gulzum ya kwana bakwai yana jinyar jikinsa.
Sannan ya sami ƙwari,harma yake iya takawa da ƙafarsa.
Tsawon waɗannan kwanaki ana ta ƙera sababbin ragogin ƙarfe da kuma majajjawar watsa ɗanyen mai da wuta.
Ice kuwa saida aka tara wanda inda za'a shekara ana ƙonawa bazai cinye ba.
Wannan karon dai sai Jafar ya bada shawarar a rarrabu wuri-wuri ayi kwantan ɓauna.
Ma'ana kada a tsaya a waje guda saboda ya san cewa suma su dodo Abulungu da sabon shiri zasu zo kuma da sabuwar hikima.
Su Jafar dai suka zamo kullum a cikin shiri da jira,don sun san cewa lallai su dodo Abulungu zasu iya zuwa a koyaushe.
Saida aka kwana goma sha huɗu ana jiran aga ɓullowar su dodo Abulungu amma shiru ko alamar su babu.
*********************
A can kogon dutsen dasu dodo Abulungu ke ciki kuwa sai da Abulungu ya kwana tara a kwance yana jinyar fuskarsa da ƙafarsa.
Sannan ya warke,harma ya iya tashi ya taka sawayensa.
Koda Abulungu yaga ya samu lafiya sai ya zabura da nufin ya ɗau kayan yaƙin sa ya koma birnin Hasiyatul Lauras ya yaƙe su shi kaɗai.
Cikin sauri matarsa dodanniya Kurdisa ta ruƙo hannun sa tace,
"Haba mai gidana kayi sani cewa ba'a ramuwa ranar gaba.
Ai zuwa da shiri yafi zuwa da wuri.
Ina mai sanar da kai cewa tabbas waɗannan abokan gaba ba zasu zauna haka ba,sai sunyi mana mugun tanadi don haka ya zama wajibi muma muyi musu tanadin da basu taɓa zato ba,yadda muna riskar su zamu gama dasu a cikin ƙanƙanin lokaci."
Abulungu yayi ƙwafa yace,
"Ai ni babu abinda ke mini takaici face ganin cewa da 'ya'yan cikina muke wannan yaƙi."
Kurdisa ta bushe da dariya tace,
"Ai maganin mai kwaɗayi kenan.
Inda ka haƙura dani kaɗai muna haihuwar dodanni irin mu ai da haka bata faru ba.
Yanzu gashi kaje ka haiƙewa bil'adama ta haifo 'ya'yan dake neman zama sanadin ajalinka.
In ba don ina tsoron kada a cuci 'ya'ya na a mayar dasu marayu ba ai da ba zan yarda a cigaba da yaƙin nan ba.
To kai kaɗai ne babba namiji a garin nan kuma kaine uban kowa,kaine kuma mai basirar kare mu daga kowane irin haɗari."
Sa'adda Kurdisa tazo nan a zancen ta sai Abulungu yace,
"Haƙiƙa kinyi gaskiya kuma na samu darasi don haka daga yau ba zan sake yarda na haiƙewa wata mace ba,in ba ke ba."
Nan take Abulungu ya tara gaba ɗaya mutanen sa waɗanda suka kasance 'ya'yan sa ne kaf yayi musu bayani cewa kowa ya fara shiri nan da kwana goma za'a koma birnin Hasiyatul Lauras ɗin.
Koda jin haka sai aka ruɗe da shewa ana kururuwa da ruri ana murna.
A sannan ne ya zayyana musu duk irin sabbin dabarun da za'a yi da kuma irin makaman da za'a tanada don a samu nasara a wannan yaƙi.
Ba tare da ɓata lokaci ba aka shiga aikin ƙera sabbin makamai.
Saida aka kwana tara ana ta shirye shirye, sannan komai ya kammalu.
A daren kwana na goma ne dodo Abulungu da jama'arsa suka kai sumame birnin Hasiyatul Lauras.
Kuma da tsakar dare suka shiga don ma kada a ji motsin tahowarsu.
Sai suka fara tafiya a dudduƙe da laɓe-laɓe domin a tunaninsu su Jafar na barci a cikin wannan lokaci.
Abinda basu sani ba shine tun daga ranar da akayi wancan yaƙi aka daina barci a birnin.
Lokacin da su Abulungu suka shigo tsakiyar birnin suna duƙe-duƙe da laɓe-laɓe kawai sai suka ji an fara watso musu raga,ɗanyen mai da wuta.
Wannan karon harda manyan duwatsu aka jeho musu yana ragargazar su.
Kafin su ankara anyi musu muguwar ɓarna.
Nan take Abulungu ya bada umarnin a koma da baya da gudu.
Ai kuwa nan da nan suka juya basu tsaya a ko'ina ba sai inda suka baro manya-manyan dawakansu masu kama da giwaye.
Da zuwa suka haye dawakan suka sake zaburo su a sukwane suka durfafo birnin Hasiyatul Lauras.
Suna isowa yaƙi mummuna ya sake ɓarkewa.
A wannan rana anci kasuwar mutuwa domin dubunnan ɗaruruwan rayuka sun salwanta tsakanin jama'ar dodonni da jama'ar Hasiyatul Lauras.
A lokacin ne Jafar da Yalisa suka shiga mugun hali na tsakanin mutuwa da rayuwa, domin duk jikinsu raunuka ne jini na zuba.
Jiri na ɗibarsu,suna faɗuwa,amma a hakan suka cigaba da gumurzu.
Aljani Gulzum kuwa da dodo Abulungu dama yau sun fito ne da niyyar ko rai ko mutuwa,amma ba gudu ba ja da baya.
Sai daya zamana dukkanin su sunyi fata-fata da juna, kowannensu ya sami saɓawar kamanni.
Tun suna iya yin yaƙin a tsaye suka koma yi a durƙushe.
A ƙarshe ma suka zub da makamansu suka kama kokawa suna cizo da yakushin juna.
Abulungu ya cafki kunnen Gulzum na hagu ya ciza da haƙoransa.
Sannan ya fincike shi da ƙarfin tsiya.
Gulzum yayi kururuwa yayi tsalle sama ya faɗo ƙasa tim saboda tsananin zafin daya ji.
(Wannan ya tunanin da boka karluz 😅😅😅,bambancin da aka samu shine,boka karluz dodon ne yayi watanda da kunnensa😅😅)
Koda Abulungu yaga ya samu wannan nasara sai ya ƙara mirginowa ya kaiwa hannun Gulzum wawura da gatso gatson haƙoransa.
Cikin zafin nama Gulzum ya goce shima ya kaima Abulungu cizo a marainan sa.
Ai kuwa yayi sa'ar damƙar su.
Take Gulzum ya taune su suka farfashe, ihun da Abulungu yayi saida ƙasa ta kama girgiza.
Nan da nan idanun sa suka ƙafe jikinsa ya sandare,komai nasa ya daina motsi.
Koda Gulzum yaga ya samu nasarar kashe Abulungu sai ya miƙe tsaye wuf ya kwarara kururuwa cikin ƙarfin hali da ƙwarin zuciya ya sungumi kulakensa biyu ya cigaba da ragargazar dodonnin nan.
Suma su Jafar koda suka ga an kashe Abulungu sai ƙarfi yazo musu suka cigaba da kashe dodannin.
Su kuwa dodannin gaba ɗaya suka rasa kuzari tunda suka ga an kashe ubansu don haka sai suka fara ƙoƙarin guduwa,amma damar hakan bata samu ba,don kewaye su su Jafar suka yi suka yi ta ragargazar su.
Ana cikin haka ne aka ga dodanniya Kurdisa tayi wani sabon ayarin dodannin jagora bisa kan dawakai ba adadi sun kawowa su Abulungu ɗauki.
A sukwane suka durfafo inda ake wannan yaƙi.
Tun daga nesa Kurdisa ta hango gawar mijinta ai kuwa nan take ta haukace ta dunga ihu tana ƙarawa dokin ta ƙaimi,don ta riski su Gulzum.
Koda su Gulzum suka hango wannan gagarumin ayari sai suka yarda dukkanin makamansu suka saduda,don sun san cewa tabbas ajalinsu yazo.
Saida ya rage saura baifi zira'i ashirin ba tsakanin su Kurdisa dasu Jafar kawai sai aka ga ƙatuwar macijiyar nan ta sarki Azmul gallar ta bayyana a gaban su Kurdisa.
Cikin razani dawakan nasu suka rinƙa turjiya suna juyawa da baya a guje,amma sai macijiyar ta sauko da kawunan ta ta rinƙa haɗiyar su Kurdisa daga su har dawakansu tayi ta tsince su ɗaya bayan ɗaya sai data ƙarar dasu gaba ɗaya babu wanda ya tsira.
Bayan ta gama lanƙwame sune ta juyo da kanta guda ta ƙare wa su Hasiyatul Lauras kallo,koda taga Jafar, Yalisa da Gulzum saita haɗiye su.
Sannan ta ɓace ɓat.
*****************************
Su Jafar dai sai gani suka yi an watsar dasu a tsakiyar fadar sarki Azmul gallar yana tsaye a kan su.
Azmul gallar ya dubi su Jafar ya ƙyalƙyale da dariya, sannan ya murtuke fuska yace,
"Sannun ku da hanya."
Jafar ya miƙe tsaye yana mai riƙe ƙugunsa da hannu biyu ya dubi Azmul gallar cikin alamun raini yace,
"Ya kai wannan sarki mene ne yasa baka ceto rayuwar mu ba da wuri sai bayan da kaga munsha baƙar wahala kamar zamu mutu?"
Sa'adda sarki Azmul gallar yaji wannan tambaya sai ya bushe da dariya yace,
"Ai ba zan iya ceto ku ba,face bayan kunsha wuya ainun, domin haka ƙa'idar kundin tsatsuba take.
Idan kuwa nace zan cece ku da wuri nima hallaka zanyi, domin fadar nan tawa gaba ɗaya ma ragargajewa zata yi, komai na cikinta ya ƙone.
Ni yanzu burina kawai kuyi sauri ku kammala karatun wannan littafi, domin sirrin shamharu ya bayyana gareni kafin ya gama haɗa abubuwa uku da zai ƙera kubar MIFTAHUL ZARBIL, wacce da ita ne zai iya buɗe fada ta inda nawa kundin tsatsuban ke ajiye ya ɗauko ya karanta.
Kuyi sani cewa a halin yanzu Shamharu ya tura su aljani markahul sabus nemo abubuwa ukun kuma har sun samo guda biyu saura guda ɗaya rak,wanda shine rabin ruwan tekun duniyar ku.
Tabbas idan baku gama karanta kundi ba kafin su samo rabin ruwan tekun tawa ta ƙare.
Don haka dole ne na ƙara saurin tafiyar ku a cikin kundin tsatsuba domin ku kammala karatun da wuri.
Ku sani cewa tafiyar su markahul sabus ta sami matsala domin a halin yanzu markahul sabus ya zama ma'abocin addinin musulunci don haka aljani Durmazalu ya sumar dashi sun gudu sun barshi a can cikin wani jeji.
Abinda da Durmazalu bai sani ba shine wannan rabin ruwan tekun ba zai ɗebu ba sai sunyi da gaske,amma inda suna tare da markahul sabus zai iya taimaka musu su ɗebi ruwan a sauƙaƙe."
Sa'adda sarki Azmul gallar yazo nan a zancen sa sai Jafar ya dube shi yace,
"Ya kai wannan sarki kayi sani cewa mu yanzu mun shiga cikin kundin tsatsuban shamharu munga irin bala'in dake ciki,kai kuma naka kundin mai ya ƙunsa?"
Koda jin wannan batu sai sarki Azmul gallar ya ƙyaƙyale da dariya, sannan yace,
"Ni nawa kundin tsatsuban babu komai a cikin sa face labarun nan na da dana yanzu na abubuwan al'ajabi dana tausayi waɗanda suka faru a tsakanin bil'adama tun daga kan mutanen farko kawo izuwa na yanzu.
Kuyi sani cewa a cikin wannan kundi nawa akwai hikayoyi guda dubu a cikin sa,haka kuma a cikin kowace hikaya akwai labarai dubu.
Idan har kuna son kuji kaɗan daga cikin irin waɗannan hikayoyi masu daɗaɗan labarai,ku nemi wani littafi mai suna "HIKAYA DUBU."
Yanzu littafin HIKAYA DUBU na nan a cikin birnin Misra a cikin gidan tarihin su a ƙarƙashin wata akwatu wadda aka sa wani gunki mai suna SARUƘ.
Wannan littafi ba zai taɓa ganuwa ba a wajen kowa ba sai nan da shekaru arba'in masu zuwa,don haka bana tsammanin zaku kai wannan zamani saidai 'ya'yan ku.
Zaku iya bar musu wasiyya don suje su duba littafin su karanta daɗaɗan Hikayoyin dake cikin sa.
Da wannan jawabi nake muku sallama sai mun sake saduwa a karo na uku."
Sarki Azmul gallar na gama wannan jawabi ne macijiyar nan ta sake haɗiye su Jafar suka tsinci kansu a gaban kundin tsatsuba,kuma shafi na ɗari uku da ashirin da biyar ne a buɗe.
Take shafin ya karanto kansa,sannan ya zuƙe su suka faɗa cikin kundi.
Haka dai suka yi ta tafiya a cikin kundi suna haɗuwa da masifu kala-kala a wurare dabam dabam sai da suka shiga har cikin shafi na ɗari shida da hamsin.
Sannan aka sake watso su tasu duniyar ta cikin kundin tsatsuba.
Wannan shine abinda ya faru gasu Jafar bayan sun baro birnin Hasiyatul Lauras inda suka yi mugun artabu da dodo Abulungu a cikin kundin tsatsuba.
(Wanda yanzu kuma sun zo shafi na ɗari shida da hamsin).
*****************************************
Al'amarin bokanya Samaratu kuwa wato mahaifiyar markahus sabus lokacin data baro fadar shamharu sai tayi ta tafiya har ta iso duniyar ƙasa.
Sannan ta nufi garinsu.
Cikin ƙanƙanin lokaci ta sauka a tsakiyar farfajiyar gidanta.
#######################
To masu karatu,iya inda nawa littafin MIFTAHUL ZARBIL na biyu 2 ya tsaya kenan,sauran duk sun falle,wannan iya rabin littafin ne.
Amma bari nayi muku summarizing ɗin abinda ya faru a iya na littafi na biyu 2.
***************************
Bokanya Samaratu ta isa gidanta,sannan kuma tayi bincike akan ɗanta wato markahul sabus,taga duk abinda ya faru dashi tun daga lokacin da suka samo narkakken dutse,zuwa duniyar ƙasa wato inda suka samo duwatsun wuta ma'ana duniyar su Sarudul Makam da 'yan uwansa.
Har taga lokacin da yayi imani da ubangijin musulunci har kuma sa'ilin da aljani Durmazalu ya shammace shi ya sumar dashi da wannan shuɗin hayaƙi.
Wannan al'amari ya jefa bokanya Samaratu cikin tsananin baƙin ciki inda ta cika da tsananin fushi ta tafi neman markahul sabus don ta tilasta shi ya fita daga musulunci.
In baku manta ba,a cikin littafin matsatsubi na uku 3 boka shamharu ya kama su markahul sabus harda Samaratu inda ya tura su su samo abubuwa ukun da zai ƙera kubar MIFTAHUL ZARBIL dashi,amma ya riƙe Samaratu a wajensa yace saidai idan sun kammala aikin su sannan zai sake ta kowa ya kama gabansa.
Wannan kenan.
Toh da yake ban karanta miftahul Zarbil na ɗaya 1 ba,ni dai abinda na fahimta shine Shamharu ya tafi izuwa wata hallarar tsafin sa inda ya bar bokanya Samaratu anan fadar sa ta Bahar zus.
Inda bansan ya akayi ba Samaratu ta kuɓuta sannan ta samu wani gagarumin ƙarfi har siffar jikinta ta sauya har fuka fukanta suka zamo guda miliyan ɗaya,sannan kuma ta hallaka gaba ɗaya dakarun shamharu dake bahar zus.
Ban san ya shi kuma Lu'umanu ya kuɓuta ba.
Wannan kenan.
To Samaratu ta tafi neman markahul sabus don ta tilasta shi ya fita daga musulunci.
To shi al'amarin markahul sabus kuwa,bayan ya farfaɗo kawai sai ya duba yaga ba abokanan tafiyar sa,anan ne yayi tunanin tabbas yaudarar shi suka yi.
Kurum sai ya tsaya yana tunani,daga ya nufi birnin Teheran,wato birnin sarki Lu'umanu saboda yadda Lu'umanu ya kulle shi a kurkuku tsawon shekaru hamsin in ban manta ba.
Shi kuma Lu'umanu bayan ya baro fadar Bahar zus sai shima ya nufi birnin sa na Teheran,da ya isa sai ya iske har sun naɗa sabon Sarki.
Nan take Lu'umanu kuma ya bayyana,koda suka ganshi sai dukkanin su suka firgice,babu wanda yafi tsorata face wanda aka naɗa a matsayin sabon sarki.
Anan Lu'umanu ya tambaye shi akan wannan babban ganganci da yayi,sai sabon sarkin yake sanar dashi cewa ai rabon shi da birnin tsawon shekara shida kenan.
Abin ya baiwa Lu'umanu mamaki,yace raina masa hankali yake son yi,inda sabon sarkin ya gabatar da shaidar shi wato wani zaki wanda yake a cikin gidan sarautar.
Shi kuma Lu'umanu tabbas yasan zakin domin da hannun sa ya kamo shi tun yana ƙarami kuma gashi zakin yanzu ya girma sosai.
Anan Lu'umanu ya yarda amma da yake azzalumi ne sai ya dubi sabon sarkin yace,duk da haka hukuncin kisa ne a kansa tunda ya zauna akan karagar sa😂😂😂.
Harya ɗaga takobin sa zai sare kan sabon sarkin nan sar kurum ga markahul sabus ya diro, sannan ya nuna Lu'umanu da ɗan yatsa yace shine ya kulle shi a kurkuku a cikin akwatin ƙarfe shekaru masu tsawo,amma daga yanzu zaluncin ya ƙare,kuma muddin yana so ya ƙyale shine ya karɓi addinin musulunci, Lu'umanu yace bai san zance ba,shi da musulmai sai yaƙi.
Anan ne suka kaure da faɗa,su faɗa nan su faɗa can,a inda markahul sabus ya tumurmusa Lu'umanu ya shaƙe shi,har Lu'umanu ya fara kakarin mutuwa ne kurum sai markahul sabus yaji an sure shi anyi sama dashi.
Shi kuma Lu'umanu ya tsaya yana shafa wuyan sa.
Karku manta,ni dai ban san ya akayi Lu'umanu ya tsira ba harya dawo Teheran,amma dai wannan asalin Lu'umanu ne, ma'ana asalin ruhinsa ne a gangar jikin sa.
Shi kuma markahus sabus sai da akayi can sama dashi sannan ya ganshi a cikin kejin ƙarfe sannan yaga mahaifiyarsa.

Anan nake maku sallama da fatan Alheri, tare da fatan idan an samu MIFTAHUZZARBIL na uku to zaki GA mun ci gaba da yardar Allah.
Nagode.
Najibullahi Muhammad #legends

7
8
9

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login