Showing 21001 words to 24000 words out of 26566 words
Chapter 8 - Miftahuzzarbil Book 2 Complete By Abdulaziz Sani Madakin Gini.txt
ɗauko wannan tsinannan littafi ba."
Sa'adda Jafaru ya faɗi haka sai hawaye ya zubowa Gulzum ya rungume Jafar yana mai cewa,
"Ya kai abokina ka sani cewa ita kazar wahala in dai mutum ya yankata dole ne ya ƙarasa fige ta.
Inda muna da rabon barin wahala da tun haɗuwar mu da jarumi Hubairu zamu rabu da ita, domin da tuni mun karɓi addinin musulunci a hannun sa.
In kuwa mun karɓi addinin musulunci da baza mu buɗe kundin tsatsuba ba har mu fara karanta shi."
Koda Jafar yaji wannan batu sai yayi shiru yana mai nazari a cikin ƙwaƙwalwar sa.
Daga can saiya janye jikinsa daga na Gulzum ya dube shi.
Sannan ya dubi Yalisa yace,
"Kun san wani abu kuwa?"
Su biyun suka kaɗa kai alamar basu sani ba.
Jafar yace,
"In da ace zamu sake saduwa da jarumi Hubairu da mun bada gaskiya ga addinin musulunci,kuma mun nemi gafarar sa bisa cin amanar sa da muka yi, domin ni yanzu ina ji a cikin zuciya ta cewar wannan addini na musulunci shine gaskiya.
Tsafi da bautar gumaka kuwa ba komai bane face toshewar basira da ɓata.
Ku tsaya kuyi tunani inda tsafi gaskiya ne ya za'a yi mu kasa ceton kanmu daga cikin wannan bala'i tunda ke Yalisa kin gaji tsafi.
Kuma me yasa duk irin ƙarfin tsafin sarki Lu'umanu jarumi Hubairu ya sami nasara akan sa?"
Sa'adda Jafaru yazo nan a zancen sa sai jikin Yalisa dana Gulzum yayi sake yin sanyi sosai suka yi shiru basu ce komai ba.
Har Yalisa ta buɗi baki zata ce wani abu sai kundin tsatsuba ya buɗe kansa izuwa shafi na ɗari uku da ashirin da biyar.
Saiga hoton wani babban birni mai ƙayatattun gine-gine.
A ƙasansa anyi rubutu kamar haka:-
--------------------------------------------------------------
*"Wannan birni, birni ne na wuya da daɗi,an ƙirƙire shi kimanin shekaru dubu baya.
Mai karatu shigo cikin sa kasha kallo"*
--------------------------------------------------------------
Koda siririyar muryar nan ta gama karanta wannan jawabi sai iskar cikin kundi tayi fitar burgu ta zuƙe su Jafar suka zama 'yan mini-mini suka shige cikin sa.
Kawai sai tsintar kansu suka yi a tsakiyar wannan babban birni.
Birni ne mai ban sha'awa da ban mamaki.
Gaba ɗaya gidajen garin an gina sune da tubalin zinare,kuma duk iri ɗaya ne babu wanda yafi wani faɗi ko tsawo.
Ko'ina ka duba wata irin ciyawa ce ta lulluɓe ƙasa mai tsananin taushi da daɗin takawa.
Wani abin mamaki shine mutanen garin gaba ɗayan su yara ne ƙanana waɗanda ba sufi shekara bakwai bakwai ba,kuma duk kansu ɗaya shekarun su ma ɗaya.
Gaba ɗayan su kyawawan 'yan matane babu namiji ko guda ɗaya.
Abinda zai ƙara baiwa mutum mamaki shine suna ta aikace-aikace irin wanda manyan mutane masu ƙarfi ke yi.
Kai wani aikin ma ko aljani Gulzum aka sada shi dashi sai ya jigata ainun.
Koda ganin su Jafar sai yaran nan suka yanyame su suna shewa da murna kuma suna tattaɓa jikin Jafar da Yalisa suna masu mamakin ganin irin surar jikin su.
Wasu suka yi ta taɓa ƙirjin Yalisa wasu kuma suka rinƙa taɓa gashin bakin Jafar da sajensa.
Al'amarin daya fusata Jafar kenan ya daka musu tsawa.
Bisa mamaki sai Jafar yaga duk sun razana suna ja da baya sun daina taɓa su.
Ba zato,sai ƙofar wani gida ta buɗe sai ga wata doguwar mace kyakkyawa 'yar kimanin shekaru arba'in ta fito.
Kallo ɗaya zaka yi wa matar ka san cewa tana da nasaba da waɗannan yara, domin kamar su ɗaya da ita.
Matar ta tsaya ta ƙarewa su Jafar kallo.
Sannan tayi murmushi tace,
"Marhaban da manyan baƙi ina yi muku barka da zuwa birnin jinsi ɗaya.
Ku biyo ni izuwa cikin gidana domin mu tattauna muhimman al'amura."
Tana gama faɗin haka ta juya ta nufi cikin gidan data fito daga ciki.
Ba tare da wata fargaba ba su Jafar suka bi ta a baya.
Da shigar su cikin gidan sai kansu ya ɗaure, saboda ganin irin kayan da aka shirya a wani tangamemen falo.
Duk wani abu na jin daɗin rayuwar duniya akwai shi a ciki.
Abinci,abin sha kuwa gasu nan iri-iri harda wanda su Jafaru basu taɓa gani ba a rayuwar su duk da irin yawon da suka sha a cikin kundin tsatsuba.
Duk abinda su Jafar ke buƙata ba sai sun ɗauko ba da hannun su.
Suna miƙa hannu abin zai taso da kansa ya dira a hannunsu.
Bayan sun ci,sun sha,sunyi hani'an sai matar nan ta sake dubansu tayi murmushi.
Sannan tace,
"Yaku waɗannan manyan baƙi masu daraja kuyi sani cewa ni sunana Hasiyatul Lauras.
Gaba ɗaya yaran nan da kuka gani a cikin garin nan 'ya'yana ne ni na haife su.
Duk shekara ina haihuwar 'ya'ya dubu arba'in kuma ban taɓa haihuwar ɗa namiji guda ɗaya ba.
Waɗannan 'ya'ya nawa basa girma iyakar girman su kenan yadda kuka gansu.
Wannan al'amari na jefa ni cikin matuƙar baƙin ciki duk da cewar bamu rasa komai na jin daɗin rayuwa ba.
Ina matuƙar son naga na haifi ɗa namiji kuma ina son ya kasance 'ya'ya na suna girma,amma abu ya gagara.
Yaku waɗannan baƙi kuyi sani cewa ba wani abu ne ya haddasa mini wannan masifa ba face wani azzalumin sarkin dodanni wanda yake zuwa mini duk shekara yana saduwa dani.
Yana gamawa dani zai tashi yayi tafiyarsa.
Bayan tafiyar da da tsawon rabin sa'a saina fara haihuwar'ya'ya har saina haifi guda dubu arba'in.
Shi dai wannan sarkin dodanni komai nasa irin na mutane ne face hannayen sa da ƙafafuwan sa waɗanda suke irin na goggon biri.
Ko'ina a jikin sa gashi ne.
A fuska ya kasance kyakkyawa kuma babu gashi a fuskar sa.
Ya kasance murɗaɗɗen ƙato mai tsananin ƙarfin damtse.
Babu wani makami dake tasiri a jikin sa bare yayi masa lahani.
Idan zaizo ya kan zone tare da mutanen sa waɗanda suka kasance irin sa kuma sukan zo bisa dawakai su da yawa,ba zan iya misalta muku adadin su ba.
Kafin kuzo nan nayi mafarki da zuwan ku,kuma a cikin mafarkin an nuna mini cewa kune zaku yaƙi wannan dodo da jama'arsa kuyi mana maganinsu.
Kuyi sani cewa duk abinda nayi mafarkin sa wannan abu yana faruwa a gaske don haka ni yau ina cikin matuƙar farin ciki da ganin ku."
Yayin dasu Jafar suka ji wannan batu sai suka dubi juna cikin matuƙar mamaki.
Sannan Jafar ya dubi Hasiyatul Lauras yace,
"Yake wannan mata mai baiwar haihuwa kiyi sani cewa mu bamu mayaƙa ba,ta yaya zamu iya tarar wannan basamuden dodo alhalin kince makami baya tasiri a jikin sa da kuma na jama'arsa.
Kuma kince baki san yawan adadin su ba?
Ai ko ba komai sarkin yawa yafi sarkin ƙarfi bare ma mu bamu da ƙarfin."
Hasiyatul Lauras tace,
"Ni dai bani da wata shakka akan ku,na tabbatar da cewa zaku iya kawar da dodo Abulungu da jama'arsa indai kuna da niyya saidai idan ba kwa son ku taimake ni.
Ku sani cewa idan ma baku yaƙi dodo Abulungu ba indai ya iske ku anan sai ya kashe ku, domin bai yarda yaga wata halitta kusa dani ba,face waɗannan 'ya'ya nasa."
Koda Hasiyatul Lauras tazo nan a zancen ta sai Jafar, Yalisa da Gulzum suka sake duban junansu cikin tsananin damuwa.
Yalisa ta cizi yatsa tace,
"Kash!
Sai mutum baya nan sannan ake sanin muhimmancin sa.
Yau ga ranar Mazalish inda tana nan yanzu ne zata yi tunanin dabara cikin gaggawa."
Jafar yace,
"Ƙwarai kuwa ai rashin Mazalish a gare mu ba ƙaramar asara bace."
Shi kuwa Gulzum sai ya matso ƙwalla daga cikin idanun sa yace,
"Haƙiƙa kowa ya tuna da bara baiji daɗin bana ba."
************************
Jafar yayi shiru ya sake shiga sabon tunani da nazari.
Daga can sai ya dubi Hasiyatul Lauras yace,
"Yake wannan mata shin a wani lokaci su dodo Abulungu ke zuwa?"
Hasiyatul Lauras tace,
"Su kanzo ne duk ƙarshen shekara da magriba kuma yau saura kwana goma cif su zo."
Yayin da Jafar yaji wannan amsa sai yayi shiru ya sake yin tunani.
Sannan yace,
"Kince ƙarfe baya tasiri a jikin su,to shin suna iya lalata ƙarfe ne da ƙarfin hannun su?"
Hasiyatul Lauras tace,
"A'a basa iyawa,amma dai suna zuwa riƙe da muggan makamai wasu ma ko a labari ban taɓa jin masu kaifin su ba da tsinin su."
Jafar yayi murmushi.
Sannan ya dubi Hasiyatul Lauras yace,
"Abinda nake so dake shine ki tara 'ya'yan nan naki gaba ɗaya ki gaya musu cewa su fara shiri zamu yaƙi su dodo Abulungu nan da kwana goman kuma kisa a ƙera mana ragar ƙarafa mai yawa wacce da itane zamu kama su Abulungu mu rinƙa watsa musu wuta suna ƙonewa.
Ina ganin da wannan dabara ne kaɗai zamu iya samun galaba akan su."
Koda jin wannan batu sai Yalisa, Gulzum da Hasiyatul Lauras suka cika da tsananin mamakin irin basirar Jafar da yadda yayi tunanin wannan hikima a cikin ƙanƙanin lokaci haka.
Daga wannan rana 'ya'yan Hasiyatul Lauras suka fara ƙera ragogin ƙarfe.
Sannan aka tanadi gunguma-gunguman itatuwa aka kunna gagarumar wuta.
Kuma sai akayi waɗansu majajjawa na ƙarafa waɗanda za'a rinƙa watsawa mutanen dodo Abulungu ɗanyen mai da wannan wuta.
Ita dai wannan wuta kullum ƙara zuba mata gunguma-gunguman itatuwa ake tana ci dare da rana.
Jafar ya raba 'ya'yan Hasiyatul Lauras izuwa kaso uku.
Kaso na ɗaya aikin su shine hawa kan bishiyoyi su ɓuya.
Da zarar mutanen Abulungu sun zo wucewa su jeho musu ragogi.
Kaso na biyu aikinsu kuwa shine watso wannan ɗanyen mai.
Su kuma kaso na uku aikin su shine watsa musu wuta.
Jafar ya samu wani ƙaton kulki ya baiwa Gulzum yace,
"Kai kuma ka ruƙe wannan idan kaga mutanen Abulungu a cikin raga waɗanda wuta bata kama ba kayi ta dukan su da wannan kulki ka kashe na kashewa ka sumar dana sumarwa."
Ba tare da gardama ba Gulzum ya karɓi kulkin yana mai murmushi,amma zuciyarsa cewa yake,
"Anya kuwa shegen yaron nan ba mugunta ya shirya mini ba.
Idan kuma garin dukan dodannin sun kamani fa?
Shikenan tawa ta ƙare."
(😂😂😂😂Kai dai Gulzum akwai shegen tsoro yasin😂)
Haka dai aka cigaba da shirye-shirye har kwanaki goma suka cika.
A rana ta goman ne tunda yamma suka samu wurare suka ɓuya wato suka yi lamɓo suna jiran ƙarasowar su dodo Abulungu.
Har magriba tayi shiru ba'a ji motsin komai ba.
Al'amarin daya sa su Jafar suka ƙosa kenan domin sun matsu waɗannan abokan gaba suzo domin ganin mugun tanadin da suka ya isa su gama da su.
Bayan an saka jimawa kawai sai aka jiyo ƙarar sawun kofaton dawakai daga can nesa.
Jim kaɗan kuma sai ƙarar tayi yawa ta matso kusa kuma ihun dodannin da gurnanin su ya cika dodon kunne da kuma hayaniyar dawakansu.
Koda su Jafar suka hango yawan waɗannan dodonni sai suka firgice,ƙiris ya rage basu tsure da gudawa ba, domin sun san cewa wannan shiri da suka yi bai isa ya gama da waɗannan miyagun dodonni ba.
Har Yalisa da Gulzum sun yunƙura zasu ruga da gudu sai Jafar ya daka musu tsawa yace,
"Ina zaku?
To ku sani cewa idan ma kuka gudu kunyi gudun banza tamkar ma kun fallasa kanku ne yadda za'a yi saurin hallaka ku.
Kawai ku tsaya mu jarraba iyakar sa'ar mu.
Ai da mu mutu ragwage gwara mu mutu jarumai."
A daidai wannan lokaci ne wata zuga mai yawa ta dodanni tazo zata gifta sai masu raga suka watso ragogin su akan su.
Nan take ragogin suka lulluɓe su suka rinƙa faɗowa ƙasa daga kan doki.
Kafin su miƙe tsaye kuwa aka rinƙa watso musu ɗanyen mai da wuta.
Nan fa dodannin suka rinƙa kamawa da wuta suna ci kamar ƙarmami suka rinƙa ihu da ruri mai razanarwa.
Da yake dodo Abulungu na daga can baya sai ya ɗaga hannu sauran dakarun sa suka tsaya cak.
Shima ya tsaya yana mamakin wannan baƙon al'amari domin tunda yake zuwa wannan birni fiye da shekaru arba'in baya ba'a taɓa kawo masa hari ba sai yau.
Abulungu ya hanga da kyau yaga ashe 'ya'yan sune da kansu suke yiwa jama'arsa wannan ɓarna.
Nan take ya baiwa mutanen sa masu kwari da baka umarnin su ruga su harbo dukkanin yaran nan dake kan bishiyoyi masu jeho raga.
Nan take 'yan kwari da bakan suka zaburi dawakansu suka durfafi yaran.
Tun daga nesa suka fara harba kibiyoyi saiga yaran na faɗowa ƙasa matattu.
Da yake suma yaran suna da yawa basu fasa jeho ragar ba, suma masu watso ɗanyen mai da masu watso wuta basu fasa ba.
Nan fa wuri ya ƙara hargitsewa da ihun dodannin dana yaran aka rinƙa gasar ɗaukar rayuka.
Har yanzu dodo Abulungu na daga can baya a tsaye kan doki da wasu fadawan sa da kuma dubunnan dakaru suna kallon abinda ke wakana.
Babu yadda mutum zai iya gane ɓangaren da suka fi mutuwa tsakanin mutanen dodo Abulungu da mutanen su Jafar.
A wannan lokaci Gulzum ya taka muhimmiyar rawa, domin ya ragargaji dodannin nan da wannan ƙaton kulki dake hannun sa.
Da yawa sun baƙunci lahira wasu kuma yayi daga-daga da sassan jikin su ba zasu taɓa moruwa ba.
Jafar kuwa yana daga cikin masu watsawa dodannin ɗanyen mai ita kuma Yalisa tana cikin masu watsa wuta.
Koda dodo Abulungu ya fuskanci cewa babu alamar nasara ga mutanen sa saiya fiddo da wani ƙaho ya busa.
Faruwar hakan keda wuya mutanen nasa dake artabu dasu Jafar suka juya da baya a guje suka koma wajen Abulungu 'yan kaɗan dasu alamar cewa an kashe su da yawa.
SAI MU HADU A PART K DON JIN CIGABAN WANNAN KASAITACCEN LABARIN MAI CIKE DA DIMBIN ABIN AL'AJABI, JARUMTA, DA SOYAYYA.
Najibullahi Muhammad**MIFTAHUZZARBIL**
LITTAFI NA BIYU 🤝❤️
PART K 🥰🤝
NA ABDUL'AZIZ SANI MADAKIN GINI 👑
TYPING AHMAD MUNNIR 🤝🥰
POSTING NAJIBULLAH MUHAMMAD ❤️❤️💯
ONE LOVE 💕😘
MARUBUCIN YACI GABA DA CEWA....
Faruwar hakan keda wuya mutanen nasa dake artabu dasu Jafar suka juya da baya a guje suka koma wajen Abulungu 'yan kaɗan dasu alamar cewa an kashe su da yawa.
Koda Abulungu yaga haka saiya kwarara ihu cikin tsananin baƙin ciki.
Daga can ya ɗago kai ya dubi sauran dakarun nasa dake baibaye dashi yace,
"Yaku mayaƙa na abin dogaro na kuyi sani cewa haƙiƙa yau Hasiyatul Lauras ta shirya mana mugun nufi na ƙarar damu,amma duk yadda aka yi ta samu taimakon wasu baƙin halittun, domin bata da basirar shirya wannan hikima.
Abin dana ke so daku yanzu shine mu tattara waje ɗaya gaba ɗayan mu,mu haɗa ƙarfi waje guda mu shige su lokaci guda,don ayi ta ta ƙare."
Koda jin haka sai dodannin suka fara jeruwa sahu-sahu a waje guda.
A can ɓangaren su Jafar kuwa tuni sun fara murna,don a zatonsu dodannin sunji tsoro sun gudu,don haka sa'adda suka ga dodannin na jeruwa a sahu-sahu sun ɗauka tafiya zasu yi su bar garin.
Ba zato, ba tsammani kuma sai suka ga dodannin sun taso musu a sukwane gaba ɗayansu ba'a rage ko guda ba.
Nan fa su Jafar suka tsure.
Ita dai Hasiyatul Lauras da rarrafe ta ruga cikin gidanta ta maida ƙofa ta rufe.
Jafar da Yalisa kuwa sai suka ruga bayan Gulzum suka ɓuya.
Sauran yaran nan kuwa masu jeho ragogi da masu watso mai da wuta ko gezau basu yi ba sai kawai suka tsaya suna jiran isowar abokan gaba.
Koda ganin yadda waɗannan yara suka dake suka cire tsoro a zuciyarsu sai Gulzum yaji shima ya daina tsoron komai.
Take yaji ƙwarin gwiwa da ƙarfi ya shige shi.
Kawai sai ya kama wata ƙatuwar bishiya ya cisgota daga cikin ƙasa ya ruƙe ta a matsayin makami ya zamana yana da makami biyu kenan,wato ga ƙaton kulki,kuma ga bishiya.
Da isowar dakarun sai wuri ya ƙara hargitsewa da ihu da kururuwa.
Dodanni na mutuwa yara na mutuwa.
Nan fa aljani Gulzum ya zama kamar ifritu a tsakiyar dodannin nan ya dinga ragargazar su da kulki da bishiya.
Duk inda yakai duka saidai kaga suna zubewa ƙasa matattu ko sumammu.
Duk wannan ɗauki ba daɗi da ake yi Jafar da Yalisa na kan kafaɗar Gulzum sun maƙalƙale sunƙi yarda su sauko ƙasa.
Sa'adda Jafar yaga yaran nan suna ta ƙoƙari duk da cewar ana ta kashe su sai kunya ta kama shi ya dubi Yalisa yace,
"Yake masoyiya ta a gaskiya zamu ji kunya idan har aka samu nasara a yaƙin nan bamu taɓuka komai ba.
Zaifi kyau muyi iya yinmu koda kuwa zamu hallaka."
Ba tare da wata gardama ba Yalisa ta karɓi wannan uzuri nan take suka daka tsalle daga kan kafaɗar Gulzum suka kaiwa yaran ɗauki.
Wannan karon sai Jafar ya shiga cikin masu watso wuta ita kuma Yalisa ta shiga cikin masu watso ɗanyen mai.
Ai fa sai wurin ya ƙara hautsinewa fiye da da, domin Jafar da Yalisa sunfi waɗannan yara zafin nama.
Shi kuwa dodo Abulungu yana cikin ragargazar yaran ne ya hango Jafar, Yalisa da Gulzum yaga irin ɓarnar da suke ta wuce misali sai yayi kururuwa ya zaburi dokin sa ya durfafi Gulzum, saboda ganin cewa yafi ɓarna.
Koda ya riske shi sai suka kaure da matsiyacin faɗa.
Abulungu ya dinga kaiwa Gulzum sara da suka da wata irin lafceciyar adda mai girma da kaifi.
Gulzum ya dinga karewa da kulkin ƙarfen dake hannunsa kuma yana maida martanin duka da bishiyar dake hannunsa.
Duk da girma irin na aljani Gulzum dodo Abulungu ya fishi faɗi da tsawo.
Nan fa suka yi ta Artabu harya zamana kowannensu ya fara gane kuskurensa, domin dodo Abulungu ya samu nasarar yankar Gulzum har sau uku da wannan lafceciyar adda.
Shi kuma Gulzum ya mammaka masa bishiyar nan a fuska ya haɗa masa jini da majina.
Fuskar dodo Abulungu duk ta kumbura ba kyan gani.
Cikin tsananin fushi dodo Abulungu ya shammaci Gulzum ya danƙara masa sara a ƙafa.
Take wajen yayi rami jini yayi tsartuwa sama.
Gulzum ya kwarara ihu saboda tsananin zafi da zugi ya durƙushe a ƙasa,amma sai shima ya shammaci Abulungu ya danƙara masa bishiyar nan a ƙoƙon gwiwarsa.
Take ƙafar Abulungu ta karye ɓas shima ya faɗi ƙasa yana mai kwarara uban ihu.
Koda jama'ar Abulungu suka jiyo ihun sarkin sai suka ruga inda yake suka ɗauke shi suka juya da baya gaba ɗayansu suka sake runtuma wa da gudu suka bar birnin gaba ɗaya,ɗayansu bai tsaya ba face matattun dake kwance fululu a ƙasa.
Nan take Gulzum ya faɗi ƙasa sumamme saida su Jafar suka watsa masa ruwa.
Sannan ya farfaɗo.
Daga nan 'ya'yan Hasiyatul Lauras da ita kanta suka fara haƙa kabarurruka suna binne gawarwakin yaran da suka mutu suna kuka.
Abin dai abin tausayi.😢😢
Babu wanda zai ga sa'adda yaran ke binne 'yan uwansu bai zub da hawaye ba.
A wannan lokaci ne Hasiyatul Lauras ta kawo magani aka sanya wa masu raunuka hadda aljani Gulzum, amma duk da haka bai dawo cikin hayyacinsa ba.
Sai bayan sa'a uku a cikin falon Hasiyatul Lauras.
Bayan farfaɗowar Gulzum ne Jafar da Yalisa suka ruga gareshi suka rungume shi suna kuka, saboda ganin halin daya shiga.
Gulzum ya dube su sa'adda shima idanunsa suka ciko da ƙwalla yace,
"Yaku 'yan uwana ku daina kuka saboda wannan hali dana shiga, domin ni namiji ne kuma an san namiji sha gwagwarmaya ne.
Koda na mutu a wannan yaƙi bai kamata ku damu ba tunda nima na salwantar da rayuka