Showing 18001 words to 21000 words out of 26566 words

Chapter 7 - Miftahuzzarbil Book 2 Complete By Abdulaziz Sani Madakin Gini.txt

sani cewa nifa ina ganin cewa mutanen nan fa sun raina mana hankali.
Ya za'a yi mu da bamu da ƙarfi da kuma taurin rai irin nasu,amma suce wai mune zamu jagoranci wannan yaƙi?"
Jinshan yayi ƙwafa yace,
"Kaidai bari kawai ai ni tun jiya na gama suƙewa inda nasan cewa nafi ƙarfin mutumin nan da tuni nayi wa shege dukan tsiya na koya masa hankali, gajeren banza me kamar a kife da kwando🤣🤣🤣🤣(kuji pah boka jinshan da ƙarfin hali🤣🤣shi ya manta cewa shima gajere ne kamar waziri kuddaru 🤣🤣)
To in banda ma rainin wayo ya mu da aka turo mu wani aikin kai kuma saika tsare mu kace sai munyi maka naka aikin.
Sannan zamu aiwatar da namu?"
Markahul sabus yace,
"Ai abin ma ya wuce rainin wayo saidai a kira shi fin ƙarfi da zalunci."
Suna cikin wannan magana ne sarki Sarudul Makam ya gama jawabi kuma ya bada umarnin a tafi izuwa duniya ta biyu.
Kawai sai aka ga wata wawakekiyar ƙofa ta buɗe saiga jemagu na ta tuttuɗowa daga cikin ta har saida guda miliyan dubu ɗaya suka shigo kuma dukkanninsu suka sauko ƙasa suka tsaitsaya cak a waje guda.
Nan da nan mayaƙan nan guda miliyan dubu ɗaya kowa ya hau kan nasa jemagen.

Mu hadu a part I don Jin cigban wannan Kasaitaccen labarin.**MIFTAHUZZARBIL**
LITTAFI NA BIYU 2❤️
PART I 💪✋
NA ABDUL'AZIZ SANI MADAKIN GINI 😎
TYPING AHMAD MUNNIR 🤝
POSTING NAJIBULLAH MUHAMMAD 💪

MARUBUCIN YACI GABA DA CEWA...

Kawai sai aka ga wata wawakekiyar ƙofa ta buɗe saiga jemagu na ta tuttuɗowa daga cikin ta har saida guda miliyan dubu ɗaya suka shigo kuma dukkanninsu suka sauko ƙasa suka tsaitsaya cak a waje guda.
Nan da nan mayaƙan nan guda miliyan dubu ɗaya kowa ya hau kan nasa jemagen ya zauna.
Babu abinda zai baiwa mutum mamaki face kowa ya san nasa jemagen, domin idan mutum yayi kuskure ya hau wanda ba nasa ba,sai kaga jemagen yayi wani irin ruri.
Cikin sauri mutum zai sauka yaje ya nemi nasa.
Bayan kowa ya gama hawa nasa jemagen sai kuma aka ga waɗansu jemagun guda biyar sun shigo.
Su dai waɗannan jemagu sun fita dabam da sauran, domin sun kasance masu irin siffa dabam,kuma duk farare ne.
Da shigowar jemagun sai suka sauka a gaban su markahul sabus suka yi layi.
Sarudul Makam ya dubi su markahul sabus yace,
"To ga naku ababen hawan ai saiku hau."
Ba tare da wata gardama ba suka hau.
Daga nan sai Sarudul Makam ya kawo takubban haske da garkuwoyi ya rabawa su markahul sabus.
Sannan yace,
"Ina yi muku fatan nasara, domin yanzu nasarar ku itace nasarar ku bisa abinda kuka zo nema."
Sarudul Makam ya matsa kusa da boka jinshan yace,
"Idan ka dawo saika koya mini hankali kayi mini shegen duka koh?"
Koda jin haka sai mamaki da kunya suka kama jinshan ya sunkui da kansa ƙas.
Sarudul Makam yayi murmushi sannan ya zunguri ɗaya daga cikin jemagun dake ɗauke dasu markahus sabus.
Nan take jemagun biyar suka tashi sama suka wuce kan gaba.
Sannan sauran jemagun guda miliyan dubu ɗaya suka bisu a baya.
Sarudul Makam ya tsaya yana kallon su sa'adda suke ficewa ta cikin wawakekiyar ƙofar nan har saida suka ɓace masa da gani.
Sannan ya tuntsure da mahaukaciyar dariya cikin tsananin farin ciki yana mai cewa,
"Shikenan burina ya gama cika wannan karon."
Haka dai markahul sabus suka cigaba da tafiya a cikin ƙarƙashin ƙasa,sai da suka yi tafiyar kwana uku.
Sannan suka iso birnin Sarudul Hasal wanda ake kira Madinatul Hiluz.
Birnin Madinatul Hiluz ya sha bambam da birnin Madinatul Aslik inda sarki Sarudul Makam ke mulki, domin su gidajensu an gina sune da zallan fararen duwatsu,saidai suma babu ƙasa ko tsirrai sai wannan farin Dutse wanda ya malale ko'ina.
Lokacin da su markahul sabus suka shigo cikin wannan birni na Madinatul Hiluz tsakiyar dare ne,don haka garin yayi tsit,kamar ba mutane kuma garin gaba ɗaya a haskake yake babu duhu.
Mutum bazai taɓa ganewa cewa dare ne ba face ya ɗaga kai sama yaga ƙananan taurari a cikin sararin sama.
Sannan ya hango su markahul sabus kamar tsuntsaye suna shawagi a sama.
Su dai su markahul sabus sun zama tamkar makafi domin jemagun da suke kansu ne ke musu jagora sai inda suka nufa dasu.
Lokacin da jemagun suka iso wani gabjejen fili mai tsananin faɗi da tsawo sai jemagun suka sauko ƙasa gaba ɗayansu suka jeru a layi suka kafa sansani.
Koda su markahul sabus suka duba can gaba nesa da su cikin babban filin sai suka hango cincirindon mayaƙan sarki Sarudul Hasal tamkar yuyar ƙudajen duniya.
Al'amarin daya firgita su markahul sabus kenan,zuciyoyin su suka fara duka.
Markahul sabus ya dubi boka jinshan, sulbaini, salusa da kuma aljani Durmazalu yace,
"Ku dubi mayaƙan can fa yanzu dasu zamu yi yaƙi ai yawansu ya ninka namu sau ɗari.
To wai shin sun san da zuwan mu ne har suka yi shiri haka?"
Kafin wani daga cikin su Jinshan yace wani abu sai suka ga wani doki mai fukafukai ɗauke da sarki Sarudul Hasal ya ratso ta tsakiyar yuyar waɗannan mayaƙa a sama ya taho gare su sai daya rage saura kamu bakwai a tsakaninsu.
Sannan dokin mai fukafukai ya sauko.
Nan fa aka fara kallon kallo tsakanin sarki Sarudul Hasal dasu markahus sabus.
Gaba ɗaya surar jikin Sarudul Hasal iri ɗaya ce sak data Sarudul Makam tamkar Hassan da Hussaini.
Inda suka bambanta kawai shine,shi Sarudul Hasal kunnen sa na hagu a yanke yake, kuma an huda kunnen an maƙala masa wani ƙaton yari mai ƙawanya.
Bayan Sarudul Hasal ya ƙarewa su markahul sabus kallo sai ya tuntsure da dariya.
Sannan ya daka musu tsawa duk suka firgice,hantar cikin su duk ta kaɗawa suka ji kamar su ruga.
Jinshan, Sulbaini, Durmazalu da kuma Salusa suka fara ɓoye fuskokinsu.
Markahul sabus ne ya tsaya ƙyam bai firgice ba.
Sarudul Hasal yace,
"Ya ku waɗannan 'yan tatsitsan halittu yanzu kune jaruman da ɗan uwana Sarudul Makam ya turo don ku yaƙe mu,ku shiga baitul malin mu ku ɗauko ƙahon zinare?
Ƙaryar ku tasha ƙarya, domin ko shi da kansa yazo nan mun fi gaban nan bare ku da waɗannan 'yan mayaƙan nasa da basu taka kara sun karya ba."
Cikin ƙwarin zuciya da tarar aradu da ka markahul sabus ya dubi Sarudul Hasal yace,
"Ya kai wannan sarki kayi sani cewa ba'a sanin maci tuwo sai miya ta ƙare.
Haka kuma ai ba yawa bane alamun nasarar yaƙi, domin mazajen ƙwarai masu zuciyar dutse ƙalilan na iya samun rinjaye akan mazaje masu zuciyar ƙarmami komai yawansu."
(Gaskiya markahul sabus ya faɗi magana 😅😅😅)
Koda jin wannan batu sai zuciyar Sarudul Hasal ta kama tafarfasa tamkar ƙirjin sa zai tsage ta faɗo.
Daga inda yake tsaye markahul sabus na iya hango yadda ƙirjinsa nasa mai cike da gashi irin na zaki ke hurowa kamar zai kumbura ya fashe.
(Ran maza ya ɓaci, markahul sabus ka taɓo tsuliyar dodon dake tsaka da barci😥)
Duk da dakakkiyar zuciya irin ta markahul sabus sai da gabansa ya faɗi shima yaji kamar yayi tsalle ya durga daga kan jemagen sa ya ruga da gudu,amma sai ya dake ya ƙaddara a ransa cewa tabbas yau mutuwarsa tazo.
Sarki Sarudul Hasal ya ɗagawa jama'arsa hannu alamar a afkawa su markahul sabus.
Sannan ya zaburi dokin sa.
Nan take dokin ya zabura a sukwane ya durfafo inda su markahul sabus ke tsaye cikin matsiyacin gudu har yana tashi sama yana sauka suma kuwa dakarun nasa sai suka rufa masa baya sai ga dawakai masu fukafukai a sama tamkar gaba tsuntsayen duniya ne ke taron biki.
Koda ganin haka sai markahul sabus ya waiga ya dubi su Durmazalu yace,
"Ya ku 'yan uwana kuyi sani cewa yau fa mun gamu da gamon mu.
Batun gudu ko ɓuya babu shi kuzo kawai muma mu tare su ayi karon batta ai ita kanta mutuwar ma mutuwa take."
Jinshan yace,
"Wace ce kuma mutuwar ka santa ne?"
Markahul sabus yace,
"Ai ba komai bane mutuwar ba face bala'i da masifa kasan kuwa idan tsanani yayi tsanani suma cinye kansu suke yi."
Yana gama faɗin haka ya ɗaga takobin sa ta haske yayi kururuwa ya zunguri cikin jemagen da yake kai kawai sai jemagen ya ruga da gudu ya tunkari su sarki Sarudul Hasal.
Nan da nan sauran jemagun suka rufa masa baya.
Tun gabanin a haɗu wuri ya cika da ruri da kururuwar mayaƙa na ta cin burin a gwamutsu don a fara tamore.
Koda ya rage saura kamu ɗaya a haɗe sai sarki Sarudul Hasal yayi tsalle sama ya bar kan dokin sa ya bangaji markahul sabus da ƙirjinsa na zaki.
Markahul sabus yayi tsalle ya faɗo ƙasa sumamme.
(😳😳😳😳😳😳 Gaskiya markahul ya gamu da gamon shi kuwa, gaskiya halittun duniyar ƙasa akwai masifa)
****************
Al'amarin daya firgita su Durmazalu kenan suka yinƙura da nufin su juya da baya sai aka afka musu da sara bisa dole suka tsaya suna kare kansu da maida martani.
Nan fa wuri ya hargitse.
Cikin daƙiƙu kaɗan aka sumar dasu Durmazalu ya rage saura dakarun sarki Sarudul Makam da kuma su Sarudul Hasal ana ta artabu.
Idan takobi ta haɗu da takobi sai kaga walƙiya da tartsatin wuta na tashi.
Duk wanda ya sake kuwa aka sari jikinsa take yake narkewa walau a cikin mutanen sarki Sarudul Makam ko a cikin mutanen Sarudul Hasal.
A wannan yaƙi dai Sarudul Hasal ne ya zama GAGARABADAU domin duk inda yasa a gabansa saidai kaga yana karkaɗe maza suna zubewa ƙasa matattu, domin yafi kowa ƙarfi,ƙwarewa, juriya da kuma jarumta.
Sai da aka samu sa'a biyar ana wannan yaƙi su markahul sabus basu farfaɗo ba daga dogon suman da suka yi,kuma duk wannan dudufniya akan su ake yi in ba don ma gawarwakin waɗansu sun danne su ba da tuni an karairaya su.
Koda ya rage baifi saura mutum dubu ɗari huɗu ba daga cikin mayaƙan Sarudul Makam,sai sarki Sarudul Hasal ya juya da baya ya cigaba da ragargazar maza yana ihu da kururuwa mai firgitarwa,yana neman inda su markahul sabus suke.
Kamar haɗin baki sai su markahul sabus suka farfaɗo a lokaci guda.
Cikin sauri suka tutture gawarwakin da suka yanyame su suka miƙe tsaye.
Koda suka yi arba da sarki Sarudul Hasal bisa dokin sa mai fukafukai ya durfafo su yana ihu riƙe da takobi a sama sai suka ruga da gudu cikin tsananin tsoro suna ihu suna waige, domin mutuwa suka gani muraran.
Markahul sabus ne a ƙarshen baya yana waigowa yaga Sarudul Hasal a saman kansa ya ɗaga takobin sa zai fille masa kai.
Saboda tsananin razana markahul sabus bai san sa'adda yace,
"Ya ubangijin musulunci ka cece ni daga wannan bala'i."
Gama faɗin hakan ke da wuya takobin Sarudul Hasal ta dira a wuyan markahul sabus.
Wata ƙara ta faru tamkar dutse aka sara.
Take takobin Sarudul Hasal ta narke.
Shi kuwa markahul sabus sai yaji wani irin ƙarfi ya shige shi wanda bai taɓa jin kamar sa ba.
Kawai sai ya shaƙo wuyan sarki Sarudul Hasal suka kama kokawa da naushin juna.
Nan fa Sarudul Hasal ya raina kansa don cikin ƙanƙanin lokaci markahul sabus ya haɗa masa jini da majina.
Dakarun Sarudul Hasal kuwa suka yi caa akan markahul sabus suna saransa,amma kamar susa suke masa,baima kula dasu ba, kawai sai yaci gaba da tumurmusa Sarudul Hasal.
Da yaga yana neman ɓata masa lokaci sai ya ɗaga shi sama ya fyaɗa da ƙasa ya take wuyansa da ƙafa guda.
Koda ya kama hannunsa guda yaja da ƙarfi sai hannun ya tumɓuke daga gangar jikin.
Sarudul Hasal ya kwarara ihu saboda tsananin zafi da zugi.
Markahul sabus ya cigaba da tsintsinka shi saida yayi filla filla dashi.
Koda ganin yadda akayi da Sarudul Hasal sai gaba ɗaya mayaƙan nasa suka fashe da kuka suka yi caa kan markahul sabus.
Yayin da markahul sabus yaga sunyi nasa rubdugu sai ya ƙwaci takubba biyu a hannunsu ya ci gaba da ragargazar su shi kaɗai ya zama shaiɗani a tsakiyar su ya rinƙa cinikin mutuwa.
Su boka jinshan kuwa da sauran tsirarun dakarun Sarudul Makam suka koma gefe ɗaya suna kallon ikon Allah, domin al'amarin ya wuce sanin su.
Markahul sabus bai gushe ba yana saran mayaƙan nan ba har sai bayan sa'a biyar.
Sannan ya ƙarar dasu gaba ɗaya.
Yana gamawa da sune ya faɗi ƙasa, saboda tsananin gajiya ya kama haki da numfarfashi.
A lokacin ne su boka jinshan suka rugo gareshi don su rungume shi,amma sai Durmazalu ya cafkosu da hannu ɗaya su ukun yace,
"Akul kuka raɓe shi.
Kuyi sani cewa a halin yanzu markahul sabus ya zama ma'abocin addinin musulunci, domin sunan ubangijin musulunci ya kira ya sami wannan gagarumin ƙarfi mai ban al'ajabi.
Duk wanda yaje kusa dashi daga cikinmu ƙonewa zaiyi tunda mun kasance ma'abota tsafi.
Abin da zamu yi kawai mu lallaɓa shi har mu gama ɗebo ƙahonhunan nan guda shida."
Koda jin haka sai boka sulbaini yace,
"To mai ze hana ne muma mu bada gaskiya ga wannan addini na musulunci tunda gashi yanzu a zahiri mun ga ƙarfin ubangijin sa.
Kuma in ba don markahul sabus ya kirawo sunan sa ba,da tuni yanzu gaba ɗayan mu mun hallaka."
Koda jin wannan batu sai aljani Durmazalu yace,
"Duk wanda yayi yunƙurin karɓar wannan addini a cikin ku saina hallaka shi.
Dole ne kubi a sannu mu kammala wannan aiki wanda mai girma shamharu ya turo mu."
Sa'adda markahul sabus yaga su Durmazalu sun noƙe a baya sunƙi zuwa wajen sa sai ya miƙe tsaye ya taho inda suke.
Kafin ya iso daf dasu sai aljani Durmazalu yace,
"Dakata anan karka ƙaraso nan wajen mu."
Cikin mamaki markahul sabus yace,
"Don me zaka ce kada na ƙaraso wajen ku ashe ku ba 'yan uwana bane abokan tafiyata?"
Durmazalu ya bushe da dariya.
Sannan yace,
"Ai daga yau ka zamo dodo a garemu domin kana kusantar mu zamu ƙone, domin ka zama ma'abocin addinin musulunci.
Abin da nake so da kai shine muje yanzu kayi mana jagora mu ɗauko ƙahon zinare a cikin baitul malin wannan gari in yaso mu wuce izuwa sauran duniyoyin guda huɗu mu ɗauko ragowar ƙahonnin.
In dai muka sami nasarar hakan da wannan ƙarfi naka muma zamu bada gaskiya da wannan addini na musulunci."
Yayin da markahul sabus yaji wannan batu sai mamaki ya kama shi daya ji cewar shi yanxu ya zama musulmi alhalin kuma bai san yadda ake shiga addinin musulunci ba,amma kuma ya san cewa tabbas yanzu yayi imani da ubangijin musulunci.
Markahul sabus ya dubi aljani Durmazalu yace,
"Idan har kun amince zaku bada gaskiya ga addinin musulunci bayan nayi muku jagora mun ɗebo ƙahonnin na amince nima."
Ba tare da wani ɓata lokaci ba markahul sabus ya wuce gaba su Durmazalu suka bishi a baya har izuwa cikin baitul malin sarki Sarudul Hasal,suka ɗauko ƙahon zinare.
Sannan suka fito.
Daga nan kuma suka sake nutsewa cikin ƙarƙashin ƙasa suka isa duniya ta uku anan ma aka tafka gagarumin yaƙi,kuma markahul sabus ne sanadin nasarar yaƙin aka ɗauko ƙahon zinare aka wuce izuwa duniya ta huɗu.
A haka dai saida suka je har duniya ta bakwai suka sami nasarar ɗauko ƙahonnin shida suka dawo da baya suka kawowa sarki Sarudul Makam.
Cikin tsananin murna ya karɓa.
Sannan yasa aka ɗebo duwatsun wuta aka basu suka yi sallama dashi suka tafi suna murna shima yana yi.
Koda suka fito daga cikin ƙarƙashin ƙasa kafin wani daga cikinsu yayi wani yunƙuri tuni aljani Durmazalu ya fesawa markahul sabus wani shuɗin hayaƙi.
Take markahul sabus ya faɗi ƙasa sumamme.
Durmazalu yayi sama dasu boka jinshan tare da duwatsun wuta suka ƙule a cikin gajimare suka bar markahul sabus anan cikin daji a kwance bai san halin da yake ciki ba.
Wannan shi ne abinda ya faru gasu markahul sabus bayan sun sami nasarar samo abubuwa guda biyu,waɗanda shamharu ya tura su samowa,don a ƙera kubar MIFTAHUL ZARBIL wacce da itane za'a buɗe fadar sarki Azmul gallar a ɗauko kundin tsatsuban sa.

MU HADU A PART J DON JIN CIGABAN WANNAN KASAITACCEN LITTAFIN.**MIFTAHUZZARBIL**
LITTAFI NA BIYU🤝❤️
PART J ❤️💯🩷
NA ABDUL'AZIZ SANI MADAKIN GINI 👑
TYPING AHMAD MUNNIR 🤝
POSTING NAJIBULLAH MUHAMMAD ❤️💯

MARUBUCIN YACI GABA DA CEWA...

Wannan shi ne abinda ya faru gasu markahul sabus bayan sun sami nasarar samo abubuwa guda biyu,waɗanda shamharu ya tura su samowa,don a ƙera kubar MIFTAHUL ZARBIL wacce da itane za'a buɗe fadar sarki Azmul gallar a ɗauko kundin tsatsuban sa.
********************
Al'amarin su Jafar kuwa lokacin da iskar kundin tsatsuba ta watso su waje cikin tasu duniyar sai suka faɗo gaban kundin tsatsuba,kuma shafi na ɗari uku da ashirin da huɗu ne a buɗe.
Nan fa suka kama haki da numfarfashi kamar ran su zai fita.
Koda Jafar ya dubi Yalisa da Gulzum sai tsoro ya kama shi.
Ba komai bane ya haddasa hakan ba face ganin Yalisa ta ƙara girma sosai,ta zama cikakkiyar budurwa,shi kuma Gulzum furfurar kansa ta ƙaro.
Kamar yadda Jafar ya tsaya yana kallon su cikin mamaki suma haka suke kallon sa cikin matuƙar mamaki domin shima ya girma,ya zama saurayi harda gashin baki a fuskarsa da wani ɗan ƙaramin saje.
Gaba ɗaya kamannin Yalisa dana Jafar sun sauya sun ƙara kyau.
Kamannin Gulzum ne kaɗai basu sauya ba face wannan ƙarin furfura da ya samu.
Jafar ya dubi Yalisa yana mai nuna ta da hannu yace,
"Yalisa kece kuwa?"
Itama sai ta nuna shi tace,
"Jafar kaine kuwa?"
Nan take suka rungume juna suka kama kukan farin ciki shi kuwa Gulzum sai ya bushe da dariyar murna.
Sannan ya dube su yace,
"Ai nasan dole ne kuyi mamakin yadda kuka yi saurin girma haka,amma bai kamata kuyi mamaki ba idan kuka yi la'akari da yawan shafukan da muka shiga a cikin kundi.
Ku duba da ku gani a cikin shafi na ɗari uku da ashirin da huɗu muke yanzu.
Wannan na nuni da cewa yanzu mun sami shekara shida da 'yan watanni a cikin kundi duk da cewar yanzu a cikin gaggawa muke karatunsa,amma bamu isa mu ragewa kanmu lokaci ba ko mu ƙara,dole ne sai mun yi shekara ashirin cif a cikin sa.
Sannan zamu kammala karanta shi."
Koda jin wannan batu sai jikin Jafar dana Yalisa yayi sanyi gaba ɗayan su suka koma gefe ɗaya suka zauna cikin matuƙar damuwa,duk suka yi zugum suna tunani mai zurfi.
Koda ganin haka sai tausayin su ya kama Gulzum ya ƙaraso garesu ya dafa Yalisa yace,
"Ya shugaba ta wai shin tunanin me kuke yi ne haka ke da Jafar?"
Yalisa tayi ajiyar numfashi tace,
"Ni kam ba komai nake tunani ba face mahaifina wanda yau rabona dashi shekara shida kenan.
Haƙiƙa inda nasan wannan al'amari zai kasance mini da ban nemi na karanta wannan littafi ba."
Sa'adda Yalisa tazo nan a zancen ta sai hawaye ya zubowa Jafar yace,
"Yake masoyiya ta kiyi sani cewa nima tunanin nawa mahaifin nake, kuma nayi nadama bisa halina na rashin jin magana da karambani, domin karambani na bai haifar mini da komai ba face tsananin wahala, ƙunshi da tashin hankali.
In da nasan cewa zan shiga cikin wannan hali da ban nemo ki ba,mun

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login