Showing 39001 words to 42000 words out of 59456 words

Chapter 14 - YAR LESBIAN CE COMPLETE DOCUMENT BOOK.txt

Axo a daukesu, Murmushi mamy tayi tace toh Wannan na hanunka na Twins dina ne Agaida Hafsat din...tashi yayi yace Zasuji Mamy...Rungome Twins tayi daga bisani takaisu Har Wajen motar Nazir bye bye Kawai suke Mata Har motar tabar harabar gidan. Cikin mota labarin Zamansu Agidan Mamy Kawai Sukeba Nazeer, Shi kam Wani Abun ma dariya yake bashi,wani kuma gaba daya Shirme ne. Kallonsu yayi yace bakunce yazeed baya dariya ba? Mubeena tace Ai yanzu yana mana manya ne kawai baya musu...dariya Nazir yayi yace Wake so nakira mishi Antynshi???? Atare Sukace nine-nice, dialling number din Feenah yayi tana dagawa yace Twins keson magana dake, Mubeena ya mika mawa aiko tana Amsa tafara bata labarin mai Kyau....daga bisani Mubeen ya Amsa Shima dai labarin nashi Kenan...Nazir ne yadan Matsa daidai kunanshi yace kace Abaka Aunty Leemah. Aiko haka yace Ana bashi,Nazir ya karba yasa phone din a hands-free, fira mubeen yake da Leemah Suna dariya, Ita batasan dawar garin ba, Cewa tayi Ina yaya Nazir? gashinan yana dravin, Mubeen ya bata Amsa. Kace mishi nace "i missed him" Ok Mubeen yafada Suka kashe wayan...Nazeer murna yake Kamar yatashi yataka Rawa ga Sweet Voice din babyn shi dayaji ga kulawar data Nuna Akanshi....Mubeen yace yaya Nazir tace tayi missing dinka. Ai najita Mubeen Ta kusa Zama big Aunty dinku kullun kuna tare da ita...Mubeena tace yaya Nazir dakkota Xakai ta dawo gidan mu? Eh Mubeena Idan ma bata dawoba Xan rinka kaiku gidana kullun kuna ganinta! Yeeee Suka fada Atare daidai lokacin da Nazir yayi parking a harabar gidansu....fitowa Sukai da gudu Sukai cikin gida. A parlo Suka tarar da mum tana kallon Wa'azi A Sunnah Tv. Fadawa Sukai jikinta mum I miss you Suka fadi atare....Nima Nayi kewarku Twins dina...Mubeena tafara Zancenta mum yaya Nazir yace Xai kawo mana Aunty Leemah very Soon. Mum Cikin Rantatace ai nafada ma daddyn Shi be yarda ba, Afili cewa tayi Allah yasa. Feenah ce Zaune tana kallon Leemah, matsowa feenah tayi tarike Hanunta tace besty gaba daya kin Chanza, Idan na tambayeki Saikice bakomai, bakomai kuma Zaki Zauna kina tunani Abinda ba Halinki bane Ada. Kara hada hanuwasu leemah tayi tace besty ki yarda dani babu Abunda nake boye miki, kausar dake Saurarensu tace Haba Leemah yazakice bakomai kigafa har dan Ramewa kikai, haka Kawai Za'ai ta miki magana kiyi Shiru ne, kawai kedai bakya Son musan Sirrin dake Cikin Ranki. Haba Kausar kunsan dai babu Yanda za'ai na boye muku Wani Abu... babu wani Kausar ta katseta Wannan karan kinfara boye boye Amma Kije idan tayi tsami ma Ji. Shiru Leemah tayi kasan zuciyar ta kuma cewa take Son yaya Nazir ke damuna da Rashin jin muryarshi....Kausar ce ta katse mata tunani wajen fadin kutashi muje time din Malan ne yanzu. Feenah Cewa tayi ni banajin dadi Kuje ni bacci Zanyi, besty meke damunki Leemat ta mata tambaya? babu Ruwanki da matsalata kema tunda kin rike taki......Uhum Leemah tace Abunma dariya yabata dan Tunda Suke da feenah basu taba fada Akan Wani Abuba, Hijab ta jawo tasaka Suka fita da Kausar. tashi take kokarin yi takasa Alamar Ciwon marar da takeji yayi yawa, Cije baki tayi da Ker ta tashi tashiga toilet, bayan minti biyu tafito daret Inda kayanta yake ta nufa, dube dube Kawai take bataga Komai ba, Ahankali tace Oh God banida pad, juyawa tayi ta koma Kan kayan Leemah tana dubawa, wata takkadace ta gani ta dauka, takaddar kuwa Sai kamshi take, Rubutun tafara dubawa Ahankali tace, kamar Writhing din yaya Nazir! budewa tayi tafara karanta Abunda Ke Ciki, Xaro Ido tayi lokaci guda tasaki kara hade da murmushi, dama wannan Shine Abunda Leemah Ke boyemun dariya tasaka Ita kadai, take taji Ciwon dake jikinta ya Rabu da ita.....Alhmdullah ta fada da karfi! my besty Amaryar my best nd Only bro kai Naji dadi....jakarta ta dauko taciro paper tafara Rubutu Kamar haka """"""""I Smile because you are my Sister in-law, i Laugh because you will married my brother, don't forget am ur besty that i love you So much""""""" tana gamawa takara Sakin murmushin jin dadi ta Saka pepper din Cikin na farko ta dauki pad din ta Maida kayan Yanda Suke...tayi Hanyar toilet tana yar rawar ta. *Kuyi hakuri da dan kadan din nan, iam so much busy 2days* πŸ’–πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’–πŸ’‹πŸ’‹πŸ’– YAR LESBIAN CE πŸ’–πŸ’‹πŸ’‹πŸ’–πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’– By Nadeeya moh'd Ahmad (πŸ’–Whatsapp: +2347010902548 http://arewapost.tk πŸ’‹NadseerπŸ’‹πŸ’™πŸ’‹) dedicated to Xaynab Ummu mahbub Page...27 Zaune yake Cikin Office dinshi wanda ya kayatu da kayan Ado, Sanyi A.c. da kamshin turare Shi ke maka Wlcm Idan ka Shiga....wata Nursing ce tayi knocking, yace yes Come in, Shiga tayi rire da wasu papers A hunanta, tana Shiga ta Aje kan table din dake gabanshi, juyawa tayi Xata fita, "yace ke" juyowa tayi tace Sr,,,,,beko kalletaba yace kiramun Fadila, Ok Sr ta fada tayi waje....Mintuna kadan Wata yarinya black beauty da Bazata wuce 17yrs ba ta Shigo Cikin Office din, daret Kujera ta jawo ta Xauna tana kallonshi, baki iya gaisuwa ba yazeed ya wurga mata tambaya? durkusar da Kai tayi kasa tace Gud Morning! Be Amsa ba yace kince kina sona da Aure kuma kina wani Nokewa kamar ba mace ba. Shiru tayi ba Amsa, kikai Shiru Ina magana! Turo kofar Akayi fadila na ganin Haka ta tashi ta fita...Shima yazeed mikewa yayi yana daga ma wacce ta Shigo hand βœ‹get out from my Office... Haba yazeed kabari kaji Menene ya kawo ni mana,,,, kifita nace yazeed ya fada da karfi. Hawaye ta fara pls yazeed ka dakata na fada maka dalilin Xuwa na...yazeed ya tsana kuka A Rayuwarshi Dan Haka ya Xauna be kara mata mgn ba....itama karasawa tayi ta Xauna, dan Allah kayi Hakuri da Abin da yafaru A baya Wlh Sharrin Shedan ne, nayi nadama Hakan Bazata kara faruwa ba, for give me pls. Naji Mufeeda Abinda ya kawoki kenan ko? Kin fada tashi kifita, Amma.....katseta yayi tashi kifita Mufeeda Rai Abace yayi maganar😑 tashi tayi ta karasa gab dashi Cikin Muryar Shagwaba tace Naji Honey Dan Allah kabari mucigaba A yanda muke da...gaba daya yazeed Ji yayi jikinshi ya Saki, turaren da tasaka gakuma yanayin yanda tai maganar duk Sai yaji wata irin kasala gashi ya kasa ture Ta.....Saitin face dinshi takai Tata face din tace Kayi Shiru Honey! Jawota yayi kan jikinshi ta fada kan cinyarshi, Naji yazeed yace, Amma waye yace kisaka wannan turaren? Honey nifa Shine turarena da'iman, Ok Naji kiss me for a minut, Cikin wata irin murya tayi magana, Honey Ni banaso Xaka kara fishi dani...be Bari takarasa maganar ba yasaka bakinshi Cikin Nata....Itama tanajin haka takara hade bakin Nasu waje daya....kissing din juna Kawai Suke gaba daya Sunfita Hayyacinsu Sun mance A inda Suke.....knocking din da Ake Shi ya dawo da Mufeeda da Sauri ta Cire bakinta tana maida Ajiyar Xuciya,,,,,, tashi tayi ta koma kujerar dake kallon tashi, Shima gaba daya yazeed ya chanza idonshi ya koma kamar garwashi....da Ker ya iya daga murya yace "Yes" turo kofar Akai Aka Shigo, Mufeeda na ganin Yusuf ne ta tashi ta fita kamar munafuka, Shima wani irin kallo Yusuf ya watsa ma Mufeeda ya karaso ya Xauna. Shine inata Knocking ka Shareni? Sorry banjiba ne... yayi ita wannan me tazoyi nan bayan Kace kun Rabu? Yatsina face yazeed yayi yace tazo wai bani hakuri kan Abunda ya faru. Kallonshi Yusuf yayi yace Shine kayi mata kuka? Mtsww kukafa Kace! Toh idan ba kuka kayiba Menene ya jawo jan ido? Ko Anyi 1round ne Yusuf ya karasa maganar yana kashe mai ido daya...kallonshi Yazeed yayi yace Zakafi Kyau da dan jarida ba Likita ba! dariya Yusuf yayi yace Allah Ko? banxa yazeed yayi dashi domin Shi kadai yasan yanda yakeji...Yusuf ne yace ya maganar mu, kokuma har Yanzu kana kan bakarka ta yar 30yrs??? Shiru yazeed yadanyi daga bisani yace No na chanza Ra'ayi! Oh Wow da Kyau Yusuf ya fada yana mai Alamar jinjinaπŸ‘ kenan Kashirya yin Aure kafin ka karasa Shekara 30 din? Yusuf ba dolena ba kafin wannan Shegiyar Mufeeda din takarasa Kasheni! Murmushi Yusuf yayi yace Kasamu wacce kakeso kenan? No ni ban Samu ba, dama Wata yarinya ce Anan kwanaki ta dameni tana Sona da Aure lokacin bana kulata, So yau nakirata muyi maganar tana wani wresting din time dina. kallonshi Yusuf yayi yace Wace yarinyace Anan Hospital din wacce ban santaba? Fadila mana yazeed yabashi Amsa atakaice:: Tunani yusuf yayi kadan Cikin Zuciyarshi " Lallai yarinyar Tanada Hankali da natsuwa Amma Ko Kadan bata dace da yazeed ba gsky" Afili yace toh kai yazeed kana Sonta ne? da Sauri yazeed yace kai nifa Kawai Xanyi Auren nan ne Sabida Na kare mutumcin kaina if Not wlh Saina karasa 30! Kuma ni gaba daya yarinyar ma Yanzu bataimunba, Ina mata magana Tana Abu Kamar wata munafuka, Nifa Nafison Mace mai kuxari wacce Xata iya kallon Cikin idona tayi magana, ba irin wa'inan matanba Kana mgn Ana Sunkuyar da kai.... fantastic Yusuf ya fada yana murmushi, yanzu Dr yazeed indai kasamu mace wacce Xata iya kallon idonka tayi mgn Xaka Aureta koma wacece? Ofcouse yazeed ya fada....da Kyau Abokina tashi muje kasaukeni a gida..tashi Sukai Suka fita atare. fitowarsu kenan daga lecture, hostel Suka nufa....Suna Xuwa Sukai Room dinsu, Kowacce Xubewa tayi Akasa Alamar Sun gaji. Kausar tace daga gobe dai mutum Xai tafi ya huta Kafin ya dawo yaji da Exam din karshe...Leemah ce tace kedai Bari, karatu da dadi da wuya. Aidai Ankusa Feenah ta fada yayin da take kokarin jawo wayarta,,,,,ganin mai kiran yasa feenah Murmushi da gangan kuma tasaka a hands-free, Hallo big yaya! Sisto ya kike, Lfy yaya Ina mum, tafita dasu Mubeen, goben Xaku dawo kuwa??? Kallon Leemah tayi daketa lumshe ido tana Murmushi da Alama cikin jin dadi take! No bro tunda hutun Na week ne Basai munzo ba. da Sauri Nazir yace Har Leemah? toh Kai yaya Nazir Nace Ni baxanzo ba kuma kake tambayar Wata Leemah. Am..ehhhh....dama kawai na tambaya ne Nazir ya fada Cikin inda inda, Feenah Cikin Ranta tace "wai su Soyayar tasu kuma da haka tazo, Arasa wanda Za'ayima boye boye Saini" kwafa tayi Afili tace, toh yaya Nazir Naga dai Xuwan baida wani Amfani Shiyasa. Yanada Amfani mana Sisto, kawai kudanxo muganku ma muji dadi Ai yanada Kyau, Murmushi feenah tayi tace "Aa" yaya kawai...katseta yayi yace idan kin Xauna mai Zakiyi Achan kudaizo yafi daga Haka ya kashe wayar....gira feenah ta daga Sama ta tabe baki tace Ikon Allah. Kausar tace Shi yaya Nazir kullum Saiyace ina Leemah Nikuma baya tambaya ina nike kodai....da Sauri Leemah ta katseta toh aikema yusuf Ke kadai yake waya dake.eh aini Soyayya Nake dashi kuma Yana tambayarku....feenah tace Ummm Soyayya Ruwan Xuma wasu na bayya tasu wasu Kuma na Sirrintata Lallai Soyayya Ansha wuya! Cikin Rashin kuxari Leemah tace besty Suwaye? A film ne Feenah ta bata Amsa. tashi Kausar tayi tace ni bari naje Na kwaso Sauran kayana domin gobe gaba daya nakeson na Mayar dasu, kai Kausar Kodai khady tanimi Sulhu kun Shirya Xa'aje Ayi Abinda Aka Saba..tsaki Kausar taja tace kincika maida Abu baya,,,Um um Kausar kidai fadi gsky dama daxun naga kina dan ciccije lips Feenah ta fada tana kallon Kausar:::Afusace kausar ta fita tace kanku Akeji. Tana fita Leemah ta mike tace bari naduba Abu....Wajen kayanta ta nufa tana kokarin Neman takardar dan dama duk lokaci xuwa lokaci Saita duba Letter din da Nazir yayi mata! Karo taci da takardar da Sauri taciro ta juya baya.....kallonta kawai Feenah keyi tana Murmushi. budewa tayi ta ware Ido ganin paper din tazama biyu, ta farkon tafara budewa tana ganin rubutun tagane Rubutun feenah ne! Gabantane ya fadi Cikin Ranta tace" Shikenan ta gani" karantawa tayi ta juya tana kallon Feenah wacce ta daure face Kamar batama San da Mutum a dakin ba. Tashi tayi takarasa kusa da ita, my Feenah am Sorry Namiki Laifi..katseta feenah tayi mekikaimun? Ehm...dama naga...toh Dan kinga Shine yaxama kinmun laifi, kece kikaima Kanki lefi tunda har kika iya barin Abu Na damunki Cikin Xuciya, koma menene dalilinki na boyemun I don't know! Kuka Leemah ta fashe dashi ta Rungume feenah, namiki Laifi besty wannan Shine Abu nafarko da nataba boye miki, kuma Shima inada dalilin yin Hakan. Haba Leemah Wani irin daliline Xai hana Ki fadamun Abu mai muhimanci irin wannan? feenah Idan Baki mance irin Rashin kunyar damuka Sha yiba,Zakiyi fargabar Ranar da Yaya Nazeer Zeji labari, kada Kiyi tunanin Abun ya tsaya Acikin gida ne kadai, Kinsan fa duk Abinda mutun ke aikatawa na boye dole wataran Sai Abin ya fita waje, kokin mance hausawa nacewa ba'a Cewa gaskiyar Mutum ta kare saidai Ace karyar Mutum ta kare.feenah bangare guda ga tsananin Kunya danakeji gaba daya Sirrin Jikin junanmu muriga da mun Sani Sannan Nazo na aure yaya Nazir da wani idon Xan kalleshi. (Hi Leemah help me Ask her😊 ni Kaina kun dade kuna bani kunyaπŸ™ˆπŸ™Š) Ajiyar Zuciya feenah tayi yayin da hawaye ke Sauka kan face dinta, Lallai yau nakara nadamar Abinda na Aikata Abaya! Leemat ai bake bace dajin kunyata nice ya kamata Naji taki, Amma Kuma Leemah yazamuyi da kaddara tunda tariga fata? Kawai inaganin kucigaba da Soyayarku har Allah ya nuna mana aurenku, Sabida ai Allah yariga yasani munyi laifi Abaya kuma Yanzu munyi nadama Mun tuba, Allahu gafururrahim ne kuma Shi ke rufama bawa Asiri Aduk Halin da yatsinci Kanshi, Leemah tun farko ba'a gane kedin kinayi ba, bekamata kixauna kina daga hankali ba tunda kedin kin tabbatar Yanzu kowani kikaga yana aikata irin laifunmu Zaki mishi Nasiha, duk kicire wannan Aranki maganar jin Kunya babu tunda wannan sirri ne tsakaninmu Kawai. Hakane Leemat ta fada Allah ya tabbatar mana da alkairi Ya kara Rufa mana Asiri duniya da lahira. Amn Feenah ta fada Suka Rungume Juna Cikin farin Ciki. WASHE GARI yau ta kama Ranar Hutu gaba daya daluban Cikin Shiri Suke na tafiya gida....ba'abar Su Feenah Abaya ba dankuwa driver Suke jira ya karaso,Yayin da Kausar ita nata har yazo ta tafi, besty Saiki Sauka Agidanmu ko? No Feenah gida Zaku Ajeni...Oh Na mance yanxufa ni Sirika ce, duka Leemah takaima Feenah Suna dariya daidai Sanda driver yayi parking gabansu, karasawa sukai gaba dayansu baya Suka Shige Haruna yajasu Suka bar Wajen. Nazir ne yashiga Cikin gidan yana Kiran "mum" Amsawa tayi tace gani a kitchen fa, karasawa Nazir Yayi yasameta tagama girke girke kwashewa take tana kaiwa Kan dinning table...mum duk Wannan Abinci Haka da yawa bayan Feenah ita kadaice, waye ya fada Maka ita kadaice, dad dinku yau Zai dawo, Sosa kai yayi yace ai namance ne, Ai dole kamance! Sai Wani rawar kafa kake Kamar Yau Zaka fara ganin Feenah din. bahaka bane mum Kinsan nadade banganta ba, Uhum Kaji dashi mum ta fada,Oya tayani Shirya Abincin Nan. Zaune Suke Yusuf Na fadin wlh Yazeed jina Nake Kamar naje Zaria Ayau! dan Allah katashi katafi mana, duk Ka Wani ishe Mutane kan yarinya karama. bakasan menene Soyayya ba namaka Uxuri kaikam yazeed. Eh Naji angaya Maka Koda naci Xan Auri Karamar yarinya da Soyayya ne? Kawai dan ina tausaya ma kaina nane. Hakane fa yusuf yafada Yana dariya, ina tausaya Maka Ranar da Xaka Zama wawa awajen yarinya karama. Allah ya kayuta Yazeed ya fada da karfi......inno ce tafito tana tsaka Lfy Ko Halimatu ta karaso ne?? Kallonta Yayi ya wurga mata Harara, bansan kanayi ba Sainaga idonka Akasa, badai Yau Amadi na hanya ba wlh Zaka maimaita duk Abin da kake mun, tsaki yazeed yaja yace Saime toh inno?? Sai Ubanka ya maidani, tsaka yau ina Cikin farin Ciki ka batamun Rai Allah Saiya Sakamun. Yusuf dake ta faman dariya yace inno nima Wlh yau farin Ciki Nake Sosai...da Sauri Inno tace Ai shi yazeedu ko Ranar idi ce tazo A bakin Rai yake Aini Alhmdullah Zuwa gobe Narabu da kunnama mai Zafin harbi. Tashi yazeed yayi yace idan kagama biye Mata Kasameni. Wayyo Sunanka Suri yau tsaka, dariya Sosai Yusuf yayi yace Inno tamu. Uhum yusufa yushe Zakayi Aure? Inno Sai yarinyar tagama Karatu. dafatan dai ba katuwa bace irin kafurar yarinyar nan? Inno Wannan yarinyace kawar Halimatu ce kunama gaisawa da ita, Laaaa Kafso kake so dama? yarinya Mai hankali....dariya Yusuf yayi yace inno ba kafso ba kausar take....Oho Aini ban Iya Sunan yan boko din nan ba. toh inno bari na tafi, duk Abinda Yazeed ke Miki ki fada ma Abba dan yace mun wai Aure yakeso Shiyasa yake Miki haka! Bude baki inno tayi tana Salati yusufa Ashe Shiyasa Ranar da yakawo Kafura Naganta tafito daga wajenshi tana Sanda????? mamaki Yusuf yayi Cikin Ranshi yace Chafff Inno ta ganshi, Afili Cewa yayi Inno Ai aure yakeso Sosai, Kinsan feenah Kawar Halimatu kuwa? Kai dan Nan nikuwa nasanta itama tana Miskilanci irin na tsaka.yawwa Inno kawo kunnanki kiji! Mika kunne tayi Yusuf ya fada mata mgn. Tashi Naga tayi tana Rawa Tana haka Za'ayi yusufa... Karfe 5 daidai na yamma driver ya Sauke Su Feenah A mamakenken gidansu Wanda Leemah baccinta take batasan Anzoba, daka mata duka feenah tayi tace tashi Sarkin bacci! Adan tsorace ta tashi, haba Feenah bayan Nace Agida Xan Sauka kikasa y kawo ni nan. Ai naga Nan din ba daji bane. Nidai kirashi ya kaini, Sakko da kanki. Atare Suka sakko Leemah na Kiran Haruna....daidai Kuma Sanda mortar Nazeer tayi parking A harabar gidan, tare Suka fito da dad Suka nufo Wajen Su feenah. da Sauri feenat ta karasa ta Rungume dad, dady ur wlcm. Tnx Ummina. Karasowa Leemah tayi itama tana mishi Sannu, Amsawa yayi Cikin Sakin fuska,,,,Nazir Kuwa gaba daya idonshi nakan Leemah, dad ne yace mukarasa Ciki, Wai tafiya zatai dad feenah ta fada tana kallon Leemah, Aa halimatu muje kici Abinci kihuta sai Nazir ya kaiki Anjuma, toh Leemah tace tabi bayansu jiki A Sanyaye, Shiko Nazir murmushi kawaii yake najin dadi. πŸ’–πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’–πŸ’‹πŸ’‹πŸ’– YAR LESBIAN CE πŸ’–πŸ’‹πŸ’‹πŸ’–πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’– By Nadeeya mohd Ahmad (πŸ’–Whatsapp: +2347010902548 http://arewapost.tk πŸ’‹NadseerπŸ’‹πŸ’™πŸ’‹) dedicated to Xaynab Ummu mahbub *This would page is for All Online Hausa writers SistersπŸ’•πŸ’•πŸ’•πŸ’•πŸ’•πŸ’•πŸ’•Allah ya karo fasahaπŸ‘ love you All* *Safiyya Abdullah Musa Huguma* *Khaleesat Haydar* *Jidda ja'o* *Hafsat Rano* *Zahra Muhd Mahmud* (Surbajo)

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login