Showing 6001 words to 9000 words out of 41234 words

Chapter 3 - RABON KWADO BOOK 1 COMPLETE .txt

Unknown   

18 Jan 2025

4657

to tashi muje kici,sai ki dauko su iman daga falo ki kyautar dasu"
Kadan naci abinci na daukosu dama tunda naxo tare muke kwana,bacci nayi bansan lkcn da yan asibiti suka dawo baπŸ™
Washegari tun asuba nayi wanka dan inason barin gidan tun kafin mai gidan ya farka daga bacci.
Da yake weekend ne har 9 ina xaman jiran yaya tazo dan tana bangaren mijinta.da yake gidan babba ne gsky kuma an kashe masa kudi iya kudi,dan duk gidan ya fatima yafi na sauran haduwa.
Kiran wayarta nayi a kashe dan haka tea kawai na hada na rubuta letter na ajiye mata a gado nace mata kirana akayi muna da text 10 shiyasa na tafi kuma daga can xan wuce gida.
Daqar na samu abin hawa kasancewar safiya ce kuma unguwar shuru kowa yana cikin gida dan saida nayo tpy mai nisa kafin na samu amma duk ban damuba sbd sa kai ance yafi bauta ciwo.
Ammi batai mamakin ganina ba dan tasan halina,kuma tasan bama jituwa da gidan ya fatima,abbi ne dai yake ta tmby ko lpy na dawo yanxu kamar an koro ni?


"Abbina mafarkinka nayi shine yau da safe nace ni saina xo na ganka"na fada a shagwabe.
Dariya yayi


"Khadijatu bakya gajiya da shirme,kin baro su lpy dai koh?"
Amsa masa nayi na shige daki.
Da ya fatima ta kira kuwa nasha fada wajen ammi nidai bance komai ba tunda nazo gida.


A kwana a tashi babu wuya a wajen allah.
Yau muke saka ran dawowar ya sadiq,amma bansan mai yasa ba yau din banajin dadin jikina ga gabana da yaketa faman faduwa.
Haka na fara shirin xuwa scul ina karanta du addu'ar data xo bakina.
A scul ba haka na yini sukuku,da muka fito a lecture na fara kiran number din ya sadiq dan jin ko wani abu ne ya sameshi.


Hello yanmatanah"naji ya fada hakan ya tabbatar min yau a masoyi yake mgn,dan naga ko jiya da mukai waya sai wani rawar qafa yake waishi angon wata5 ne.


Yaya kun sauka ne?"


Eh mun sauka heartbeat tun dazu amma office na wuce dan akwai wani record da nakeson bayarwa"


Tom saika qarasa gidan nima yanxu tapiya xanyi"


Har kun gama lecture dinne?"


Aa kawai inason xuwa gida ne dan tun safe gaba na yake faduwa"


Subhanallah!kina addu'a dai koh?"


Eh nayi"


To kije gidan anjima zamiyi waya"
Sallama mukayi na kamo hanyar gida.
Ina shigowa layinmu na hango motoci biyu a qofar gidanmu,ga wasu mutane a tsaye dana hango a gefe.
Gaba nane ya tsananta faduwa,tunani kala kala da zullumi sun cika min xuciya.
Banbi takan mazan da suke qofar gidan ba na fada gidan a sukwane.
Mutum na fara cin karo dashi a kwance an lullubeshi da farin gyalle,abbi a tsugunne a gefe yana sharar kwalla sai ya ruqayya itama da take rusar kuka.
Gabana ne ya cigaba da bugawa kamar xai fado,ya ruqayya na nufa ina tmbyrta ina amminah dan banason gargina ya tabbata.
Nuni tayi min da daki ba shiri na fada dan tabbatarwa.
Ammi na zaune akan sallaya tana jan carbi,lokaci lokaci tana share kwalla.


Ammi meya faru?waje ya mutu?"Na tmby ta rarrauniyar xuciya.


"Sai hqr auta yayarku fatima ta rigamu gidan gsky"


Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!!ya fatima?ya fatima kuma?ya fatimanmu ce ta rasu??
Cak!nunfashina ya tsaya Inda duhu ya fara mamaye idanuna wanda daga lkcn banqara sani meya faru ba kawai dai na bude ido na ganni a gadon asibiti.


Ya zainab ce zaune a gefe na,kana ganinsa xaka gane tarin damuwar dake tare da ita.
A hankali abubuwa suka fara dawo min inda wani kuka yazo min bai daci.


Ya zee da gsk ne?da gsky ya fatima ta rasu?da gsk ta tafi ta barmu baxamu qara ganinta ba?yanxu shikenan...."
Ya xainab ce ta saka hannu ta rufen baki.


Ya isa haka,baki ga halin da kk ciki ba?bakiga tsahon kwana biyun da kk dauka ba numfashi a tare dake ba?ki inason ki qara janyo mana wata damuwar?"kuka ne yaci qarfinta dan dole tayi shiru.nima kukan nake ina jadadda cewa wai ya fatima ta rasu.


Auta yaya ta rasu,yaya ta tafi baxata qara dawowa ba,mutuwa ba qarya bace fatanmu allah ya jiqanta da rahma,duk da tayi mutuwar shahada dan bata kai ga haihuwa ba allah ya karbi abinsa"
Haka muka hadu mukaita rabxar kuka.


"Yaya inasu ammi?"na tmby da dasasshiyar muryata.


"Dukkansu suna gida karbar gaisiwa kinsan yau sadakar uku,amma duk dare suna zuwa duba ki"
Allah mai iko ashe dai da gsk nayi kwana biyun ba motsi,allah kenan mai rayuwa da mutuwa.
Turo qofar da akayi ne yasa muka tsagaita da kukan.nusaiba ce da ya sadiq,wanda shima kallo daya xakayi ka gano yar ramar da yayi.
Da gudu nusaiba tazo ta rungume ni tare da sakin kuka.haka muka hadu ba mai rarrashin wani shidai ya sadiq fita yayi sai gashi sun dawo da doctor.
Dubani yayi tare da rubuta magunguna sannan yayiwa ya sadiq bayanin xasu riqeni xuwa gobe idan sunga jikin da sauqi xasu sallame ni.
Godiya ya sadiq ya masa kafin ya sadiq din ya xauna ya fara mana nasiha mai shiga xuciya.sosai nasiharsa tayi tasiri a xuciyoyinmu,saida ya tabbatar mun samu nutsuwa kafin su bar asibitin.
Da dare su abi sukaxo da su ya aisha amma wai babu ya fatima,allah mai iko.nan ma wani sabon kukan mukasha,Daqar abbi ya shawo kanmu da nasihar yadda da qaddara don hatta ammi ma kukan take.
Sai can dare suka tafi.ya zee ta samu bacci amma ni tunanim rayuwa kawai nake.haka fa rayuwar take yau kananan gobe baka nan.
Tuno ranar da dukkansu sukazo gida muka hadu akaita wasa da raha da kuma shirye shiryen suna idan ta haihu,ashe bama zata haihun ba bare ayi sunan.
A ranar da zasu tafi mijinta yazo daukanta,na rakata ina dauke da iman datayi bacci dansu ya aisha tun yamma suka tafi ita kuma ta zauna tace sai mijinta ya dawo daga aiki xaixo ya daukesu,har na saka iman a mota ina musu bye bye ta jawo kunne na.


Wato kina ganin daddyn shahid bazaki gaida shi ba koh?kewai a rayuwarki bakya yafiya ne?"


Turo baki nayi nace"to bana gaidashi ba"


Baki gaida shi ba na sani kawai dai kin fada ne,kuma zanyi maganinki tunda bakyajin mgn"Tace tana sakin kunne na.


Kiyi hqr kinji sweet yaya"nace ina kamo hannunta.


Idan kinason na hqr sai kin yafewa mijina"


Ganin mijin ya shiga mota yasa banyi mgn ba na tafi ina mata waving da hannu ashe na bankwana nayi mata😭.
Haka naita tunanin abubuwan da suka faru tare da ita,bansan lkcin da bacci barayo ya sace ni ba.
πŸ’™πŸ’™RABON KWADO...πŸ’™πŸ’™πŸ’™








Tare da Er mutan ungogoπŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹




Gaisuwa da jinjina gareku masoya abin kaunata,musamman yan khayratie's hausa novels allah ya bar xumunci.🀝🀝






πŸ…Ώ31-πŸ…Ώ35


Washegari wajan 11 na safe ya sadiq ya dawo asibitin,inda yaje ya karbo takardar discharge kafin ya shigo.


Ina kwana"nace ina satar kallonsa ganin ya tsaya yana kallo na.


Lpy lou,ya jikin?"


Da sauqi"


Ya haqurinmu?"ya kuma tmby.


Kwal kwal idona ya ciko da kwalla.


Kinga ni ba kuka nace kimin ba,ina ya zee din?"


Yanxu ta fita bansan ina taje ba"


Shine take barmin princess dina salon azo a sace min ita?"


Murmushi nayi kawai ina qara satar kallonsa dan ramar dana ga yayi.


Ya sadiq naga ka rame?"


Ba dole ba nernah?kina gadon asibiti rabi rayuwa rabi mutuwa"


Allah sarki ya sadiq,allah ya bani ikon faranta maka tsahon eayuwata"na fada a xcytah dan bana iya sakewa dashi indai mu kadai ne a guri,duk da dadai nasan bazai cutar dani ba,amma idan muna tare da nusaiba hira mukesha sosai.


Khadija kinga yadda allah yake al'amarinsa koh?a yadda na tsara washegarin dana dawo zan tura wajen abbi amma sai wannan rashin ya samemu,kinga dole a jinkirta zuwa lkcn da komai xai dai dai ta"


Allah ya kaimu"nace cikin jin kunya.


Wa yaga khadijan abbi amarya"ya fada da sigar wasa.
Haka yaita jana da hira har ya zee ta dawo muka tattaro muka dawo gida.
Har lkcn muna samun masu xuwa gaisuwa duk da abbi ya hana zaman makoki.
Ina maqale dasu iman dan tausayin yaran nakeji yana ratsa zuciyatah,Allah ka haskaka kabarin ya fatima amiin😭.


Bayan kwana biyu kowa ya watse dan abbi haka yace su ya aisha su koma gidajensu xaman ya isa haka ita dai ta riga ta tafi ba dawowa zatayi ba.
Tafiyarsu ta karamin kadaici dan su shahida ma wai anxo an daukesu daga gidan kakarsu.


Tsahon sati biyu bana zuwa scul,hakan yasa abbi ya ringa fada dan dole na na shirya na tafi dama nasan ba'a son ran ya sadiq naqi xuwa ba dan bayasan takura ni ne kawai,ga exams da muka kusa farawa.


Yau satin ya fatima 3 da rasuwa.
Ina kwance a daki ina karatun text naji an daga labule,duk a zato na ammi ce amma ga mamaki na naga abbi.
Saurin tashi nayi xaune ina gyara dankwalin kaina tare da yiwa abbi sannu da xuwa ganin yana niyyar shigowa dakin.
Ban gama mamaki ba sai danaga yana zama a gefen gadon.


Abbi ashe ka dawo?daxu na tmby Ammi tace ka fita"


Eh khadijatu na dawo"yace yana kama hannu na.
A hankali na zame na kwanta akan qafarsa kasancewata mai son jiki😊.


Khadija wannan zuwan dan ke nayi shi,ina neman wata alharma ne a wajenki shiyasa na tako da kaina a matsayina na mai nema"


Abbi alfarma kuma?har inada abinda zaka nema a wajena?"Nace ina wasa da yatsun hannunshi.


Eh,fitarnan da nayi naje can wajen sirikan marigayiya fatima ne,kuma a zaman da mukayi mun yanke shawarar ranar asabar mai xuwan nan za'a mayar da auren fatima kanki"


Wata zabura da nayi bansan lkcn da na fado a kan gadon ba.


Abbi kamar ya?ban fahimci me kace ba"Nace duk a rude.


Kinga inaso ki kwantar da hankalinki,muma bawai mun yanke hukunci ne haka kawai ba.bayan fatima ke kadai ce wadda zata iya riqe yaranta da gsky,kuma xaki riqesu kamar kece kk haifesu,koba danni ba khadija ki tausayawa rayuwar yaran nan ki maye musu gurbin mahaifiyarsu"


Wayyo allah na,Allah yasa mafarki nake akan wannan batu,kai ko mafarki nake nasan to yau mummunan mafarki nayi.


Khadija ki min mgn mana,bawai kuka nace kiyi mini ba"na jiyo maganar abbi.


Kuka?dama kuka nakeyi?Wayyo wlh ina ganin na haukace.


Abbi dan Allah ka taimaki rayuwata karka hadini aure da mijin ya fatima,abbi akwai wanda yake sona tsakani da allah dan allah ku tausaya masa"nace ina ja da baya.


A hankali abbi ya kamo ni ya kwantar dani akan qafarsa,bai kuma mgn ba sai daya ga na fara samun nutsuwa.


Khadija kk ce akwai wanda kk so?"


Eh Abbi,wlh ya sadiq yana qaunatah,Mutuwar nan ce ta hana a aiko manya daga gidansu"


Shiru yayi na tsahon lkc kafin ya kira sunana.


Khadija yanxu a matsayi na mahaifinki ashe baxan iya baki umarni kibi ba?a dazu naxo miki a matsayin mai neman alfarma a yanxu kuma ina mai baki umarni ne,inaso ki saka a ranki zuwa ranar asabar zaki bar gidan nan da sunan aure"bai tsaya bi takaina ba ya tureni daga jikinsa ya fice daga dakin.
Daga inda ya tureni nidai haka na kasance a kwance,ban sani ba suma nayi?kai ba suma bace qila mutuwa nayi tunda ance idan mutum ya mutu yana jin abinda mutane suke cewa kamar yadda nima ina iya juyo wayar da abbi yakeyi da mutane cewar ranar asabar akwai daurin auren yar wajensa.


To wai har gani mutum yanayi idan ya mutu??na tmby kaina ganin ammi ta shigo dakin ta riqoni fuskarta da alamar tausayawa daqar nema idan ba kuka tayi ba.


Khadija kiyi hqr kinji?ki yiwa abbinku biyayya insha allah zakiga ribar hakan"


Wai ammi batasan na mutu bane take tayimin mgn?bari dai nayi mata bayanin na mutu suje kawai su binne ni.


Ammi"


Naam khadija kiyi hqr kinji,kiyita addu'a allah yasa haka shiyafi alkhairi"


Wayyo masu karatu wlh na haukace,nashiga uku da gsk na hauka ce.......




Wait a moment....πŸ˜ŠπŸ’™πŸ’™RABON KWADO...πŸ’™πŸ’™






It's me Er mutan ungogoπŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
πŸ’™πŸ’™RABON KWADO...πŸ’™πŸ’™




Er mutan ungogoπŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹






πŸ…Ώ46-πŸ…Ώ50


wai auta yaushe zaki bar wahalar da kanki kibar asarar hawayenki?Abinda kk yiwa kuka ya riga da ya faru,to y not ki samawa zcyrki sauqi ki dauki qaddara"ya aisha tashe ganin na samu damar kuka.


Banyi mgn ba domin nasan duk abinda zan fada mata bazata fahimta ba kunga maganar bata da amfani.


Da yamma ina kwance ina saqa da warwara ya aisha tazo ta zauna a kusa dani.


Ki tashi kije kiyi wanka"
Banyi musu ba na tashi dan ni kaina nasan ina buqatar wanka.


Dana fito kaya na tarar akan gadon sababbi ne na dauka na saka dan banida lkcn tsayawa tambaya.


Ga kayan kwallaya nan kiyi"naji ya aisha tace.


Kallonta kawai nayi.


Banajin zan iya shafa wani abu"nace ina niyyar kwanciya.


Ko kwalli baxaki sakawa wannan kodadden idon ba?"


Ya ilahi!!banasan damuwa.Daukan kwalli nayi na saka tare da daukan hijabin dana cire.


Ki bude jakar can akwai hijabi,bakya ganin wannan yayi datti?"


Jakar na nufa kawai dan naga abin bana qarewa bane.jin an fara kiran magriba yasa na fasa kwanciyar na tada sallah dan nayi alwala danaje wanka.


Dana idar ma zama nayi ina azkar din yammaci.sai danayi issha kafin na tashi akan sallayar.kamar jira take ta wani biqon plat din abinci.


Karba kawai nayi na fara dannawa badan inajin dadin abincin ba.


Kiyi hqr kinji auta?insha allah zakiyi alfahari da wannan auren,kinsan dai abbi yana sonki bazaiyi abinda yasan zai cutar dake ba.maganar sadiq kuma ki ajiye gefe ki rungumi mijinki da 'yay'an yaruwarki"


Surutanta taita yi dan maganarta bata min rai take.wai zanyi alfahari da wannan qaddararran auren?na rungumi mijinah?uban waye yace mijina ne?wlh na kusa fara dura ashariya tunda baza'a barni na huta ba.


Turo qofar akayi tare da sallama.Abbi ne da mijin ya fatima yana binsa a baya kamar tsohon munafiki.
Da gudu shahida da iman suka zo suka dafe ni,su kansu yaran yanxu haushinsu nakeji.
Turesu nayi a jikuna ina tsugunnawa ina gaida abbi.


Sama sama ya amsa min kafin ya fara yiwa ya aisha mgn.




Kin karbo takardar sallamar ne?"


Eh abbi na karbo"


To ita ta gama shiryawa dai koh?"


Eh ta gama"


To khadija ga mijinki nan zaku tafi,kya qarasa jinyar acan dakinki,Allah ya qara sauqi ya bada zaman lpy"yace yana kallo na.


Tirqashi!!wato ni ko irin gatan da masu gata suke dashi na sallama da mahaifiya da karbar nasiha a wajenta ni bazan samu ba?bani da gatan da za'aje gida a dauko ni sai a asibiti?wannan ua alama ce ta an gaji dani,taya ma mijin zaiga daraja ta bare kuma miji irin wannan?"


Tunani nane ya tsaya danjin ya aisha ta kama hannuna ta nufi hanyar waje dani.


A wata muta ta sakani kafin tace.


Auta kiyi hqr,nasan akwai abubawa da dama daba haka ya dace ayi ba,amma inaso ki cire komai a raki kuma ki ringa tuna waye abbi da kuma matsayinsa a wajenki.Akwai wata akwati zaku gani duk kayanki ne na buqata,sauran suna cikin wardrob,Ammi tace tana miki fatan alkhairi"


Kifa kaina nayi a cikin cinyoyi na dan ganin abbi yazo bakin motar,inaji sukai sallama dashi suka shigo cikin motar.
Dukansu a gaba suka zauna saini a baya,inajin tashin motar na sawa raina nayi bankwana ta walwala,kuma nayi dammarar karbar ko wani matsayi ne a gidan tunda hakan aka zabar min.
Shiru motar tayi sai surutun su iman da suke tayi ba qaqqautawa,shidai da eh ko a'a yake binsu dashi.


Jin motar ta tsaya yasa na tabbata ta faru ta qare.inaji duk suka fita a motar amma ban dago ba.


Malama ki fito kona janyo ki wlhnajiyo muryarsa a gefe na.


A hankali na dago kaina dan nasan zai iya aikatamin abinda yafi haka.
Saurin kare fuskata nayi dan ganin hasken daya dalle min fuska.a hankali na zuro qafata wadda na tabbatar ba gidan ya fatima muka zoba,to inane nan?Allah yasa gidan yankan kai ya kawo ni su yankani na huta.


Ganin yayi gaba ya fara tpy yasa nabi bayansa.Ganin girman gidan da qofofin da muke wucewa yasa na gasgata zargina.


Ki jirani anan"yace ba tare da ya juyo ba ya cigaba da tafiya.
Guri na samu na zauna ina tunanin inda kuma su iman sukayi dan dana fito banfansu ba.
Ganin ya dade bai dawo ba yasa nace qila ciniki ne bai fada ba.
πŸ’™πŸ’™RABON KWADO...πŸ’™πŸ’™






Written by:Er mutan ungogoπŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹








πŸ…Ώ41-πŸ…Ώ45




Dana koma daki ma wani sabon kukan na dasa.
Da gsk na rasa ya sadiq?da gsk ya sadiq ba RABONA bane ba?lallai duk wadda ta samu ya sadiq tafi kowa sa'a a duniya,ni kuma dana rasa shi pa?ni kuma nafi kowa rashin sa'a.


Da dai daya yayyena suka fara zuwa,inda kowacce tazo tausata take da bani hqr,abin takaicin ba wadda ta bani goyon baya a cikinsu,nidai a ganina zuwan nasu bashida wani amfani.
Haka suka tattara suka tafi ba wani cigaba,dan har lkcn naqi cin abinci kuma ban bar yin kuka ba.
A jiya zuwa yanxu harna rame,fuskata kuwa kamar an hura baloom sbd kumbura,muyarta kanta zuwa yanxu ta dashe,hawayena ne dai basu kai da qafewa ba.
Ina a kwance sallah ce kawai take tayar dani,ga wani azababben ciwon kai dake damuna.
Wayata ce ta fara neman agaji amma banyi niyyar dauka ba,dan tun rana ake ta faman kirana nasan bazata wuce yan scul dinmu ba ace banxo test ba.
Jin qarar wayar ta fara damuna yasa dole na miqe na dauko dan da alama mai kira bashida niyyar dainawa.


"Heartbeat"shine sunan da yaketa reto a saman wayar,banda niyyar daukar wayar saima tasata a gaba da nayi ina rusa kuka.
Mai zai kira ya fada min bayan yasan na rasa shi?kodai ya yarda da qudirina na guduwa ne?
Da sauri na daga wayar.Daga can naji yace"khadija!!


Naam"nace da dasasshiyar muryata.


Har yanxu bazaki bar yin kuka ba koh"


Bafa kuka nake ba"


To naji,inason qara baki hqr ne,khadija bawai dan mun rasa juna shikenan mun daina rayuwar farin ciki ba,dan allah ki saki ranki,ki bada hadinkai ayi abinnan lpy kinji?dan allah kada kiyi wani abu dazai badawa abbi rai,kindai san fishin iyaye akan yayansu"
Kuka nake kawai,dan yanxu na tabbatar na rasa shi,wlh da gsk na rasashi😭.


Kinci abinci kuwa?"
Naji yace.


Eh"


Bakici ba nasani,kuma idan kinason mu shirya ki tashi ki dauko abinci kici,idan ba haka ba kafin gobe zakiji lbrn nabar garinnan"


Dan allah karka tafi,wlh xanci"na fada ina qara sautin kuka.
Baiyi mgn ba sai tari da yake tayi tun inayi masa sannu har nayi shiru ina kuka.


Ya sadiq ka gani koh?kaga zamu cutar da kanmu sbd farin cikin wasu koh?"na fada danjin tarin ya lafa.


Dif!!ya kashe bawar ba tare da yayi mgn ba,haka naita bin number din amma bata shiga.


**-**-**-**-**-*-*


Yau ta kama Alhamis,wanda a lissafinsu abbi saura kwana biyu daurin aurenah,zuwa lkcn duk wanda ya gani saiya tausaya min,sbd na lalace kamar ba khadija yar gayu ma'abociyar san ado da kwalliya ba.
Ina zaune a tsakiyar yayyena da suketa yimin magiyar naci abinci,amma ni duk hankalina ba'a kansu yake ba,tunanin nusaiba da ya sadiq nake,dan tun ranar da mukai wayar nan banqara samunshi a waya ba,nusaiba ita kanta na kasa samunta,gashi har lkcn ban qara ganin qeyarta a gidan ba.


Khadija!khadija!!ko khadijan bata nan ne"najiyo muryar abbi na kwalan kira.
Saida gabanah ya fadi danni yanxu tsoron kiran abbi nake.
Ya ruqayya ce ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login