Showing 21001 words to 24000 words out of 41234 words
lalle?
Haka na raya a raina ina sauke idanuna da suka cika da kwalla akan hannayena wadanda yanxu suka fi kama dana maza sbd ko digon lalle babu a farce na.
Saida na kusa kammalawa suka dawo.
Zuba musu abincin nayi bayan na cire musu kayan dan karsu bata.
Daki naje na kwanta dan sosai jikina yake amsawa.
Inaji shahida na fada min ga abokan dadynsu nan,nidai ban motsa ba tunda na gama jera musu komai a dinning.
Bansan lkcn da bacci yayi gaba dani ba wanda ban farka ba sai azahar.
Da hanxari naje nayi wanka tare dayin simple make up wanda tunda nazo gidan cream ma saita raya min nake shafawa.
Haka na saka wani light purple din leshina nayi daurin zamani,dan yau haka kawai naji ina sha'awar hakan kodan ranar farin ciki ce?
Fita nayi don samawa cikina haqqinsa,inda na samesu suna buga game da shahid da daddynsu,yayinda su iman suke ta ihu da alama kowa da wanda yakeson yayi winning.
Har na gama cin abincin basu kula dani ba,don hk dana gama ma daki na koma na kunna calculator ta ina sauraron waqoqin da ake sakawa a gidajen radio.
Aunty wai daddy yace kisa mana kayanmu sannan ki zuba abincinsu grandy ki fito mu tafi"shahid yace.
Tashi nayi naje na zuba abincin a cooler kafin na qara gyara musu kwalliyar na koma na kwanta.
Nayi zaton sun dade da tafiya kawai naga iman wai nazo inji daddy.
Barinmu kk yi muna zaman jiranki ko kuwa ajiyemu kk yi?wlh kk wuce 2mnt zaki sha mamaki"yace yana jan hannun iman.
Kaji mutum ni nasan dani za'a tafi ne?
Da sauri na koma daki dan dokin yau zan fita har naje naga amminah.
Kiyi hqr da wannan nayi typing mai yawa zan turo bansani ba nayi delete.
Ku buyoni.
[07-23, 20:47] Sistoh: ππRABON KWADO....ππ
Er mutan ungogoπππ
π
Ώ86-π
Ώ90
Da sauri sauri na dauko mayafina wanda zai shiga da kayan jikina,na zira takalmi nayo waje.
Yauma a front sit na samesu sai shahida dake baya.
Shiga nayi ba bata lkc mukayo waje.
Wayyo zo kuga farin ciki kwance a fuska ta.inaji suna hira jefi jefi nidai Allah Allah nake na ganni a cinyar ammi dan nayi missing sosai.π
Kwantar da kaina nayi inashan AC tare da zubawa titi ido ina ganin abinda yake wakana.
Can gidansu muka fara zuwa dake unguwar kuntau.
Sosai gidan ya tsaru kaida gani kasan na masu abun neπ.
Ban gama shan kallo ba saida muka doshi sassan gidan,kai na taqaice muku kamar yar qauye na zama.
Ganin sun danyi min nisa yasa na saita kaina tare da qara sauri kar naje na rasa qofar da suka shiga.
Da sallama na qarasa shiga falon inda duk hankalinsu ya dawo kaina.
Zubewa nayi a gaban ummi ina kwasar gaisuwa wadda tun shigowata murmushi yake wanxuwa a fuskarta.
Mata ne guda uku wadanda suke cikin shigar alfarma,duk da nima kayana ba marasa kyau bane amma duk sainaji na takura.
Nidai inajinsu suna jana da hira kawai murmushi nake musu dan burina inganni a dakin ammina.
Sama sama nakejin hirar tasu inda Nake satar kallonsu cikin dabara.
Kana ganinsu kasan yayan ummi ne,dan duk kamar danake ganin daddynsu shahid nayi da Ummi sai naga ashema nafila ne.
sinasir din da mukazo dashi Suka baje a qaton plat sukaita jana har saida na sako muka fara ci tare.
Broz haka Auntyn tamu ta qware a girki?shiyasa har wata qiba kk ta musamman"babbar cikinsu ta fada dan da alama itace sakuwarshi,dan sauran biyun kansu daya kamar yadda komai da suka saka iri daya,saidai daya tafi daya fari amma duk daddynsu shahida ya fisu fari dan kamar ba dan nigeria baπ
Har suka gama shaqiyancinsu bai kulasu ba don inaga muskilanci sana'arshi ce.
Tuni yaran suka watse kowa ya shiga wasa,nidai duk a takure nake dan ko ido bana iya dagowa.
Mubinah kinga kuje dakinku da khadija naga ta kasa sakewa damu"Ummi tace
Wadda aka kira da mubinah dince ta kama hannuna mukai saman benen gidan.
Allah sarki malam talaka"na fada a raina ganun irin aljannar duniyar dake kan benen.
Wani daki muka shiga wanda aka tsara komai da kalar red,dan dole na saita kaina dan karta fahimci halin danake ciki.
Haba matar broz dan allah ki saki jikinki,kinga nan ma gida ne dan duka an xama daya"tace tana zaunar dani akan gadon dakin.
Murmushi nayi kawai.
Kinga mu kamar yar uwa haka muka daukeki dan Allah ki saki jikinki"ya kuma fada.
Dai dai nan dayar ta shigo dan nafi tunanin twins ne.
Sakani a gaba sukai suna taban lbr dan dole na saki jikina,dama ni banason nayi shisshigine nida ba yar kowa ba,amma da naga ba wannan a ransu tuni na saki jiki munata hirar scool.
Kasancewarsu masu surutu yasa cikin lokaci kadan mukai kamar dama can mun san juna.
A shekaru zamu iya sa'anni dasu koma su girmeni dan yanzu suna level 200 ne a wata private university dake nan kano.
Sosae nake jin dadin hirar dan rabona da samun wanda zamuyi hira irin hk har na manta.
Iman ce ta shigo da gudunta tana kwalan kira.
Aunty!Aunty wai daddy yace ki fito zamuje gidan Ammi"
Kafin nayi mgn mubina ta riqota.
Aunty kuma iman?ba mummy ba?daga yau mummy zaki ringa cewa kinji darling?"tace tana kama habarta.
Kai kawai iman din ta daga mata.
Kinji broz wai har zai dauke mana ke,shifa haka yake da takura"mufida ta fada.
Har bakin mota suka rakoni bayan munyi sallama dasu ummi.
Ganin da sukayi su shahid a front sit yasa suka fito dasu suka sakani a front sit din.
Nidai yaqe kawai nakeyi dan banason yazo ya bata min rai dan shi yana can gefe yana waya.
Yanxu sai yaushe zaku xo dan allah"nace ina kallonsu.
Kafin aunty anisa ta koma zamuxo insha allah kinsan ita a Abuja take aure jiya sukazo da mijinta da yaranta biyu,basu dade da fita ba kuma kikazo wai ya tafi kaisu park ne"mubina tace dan da alama shahida ita ta gado dan itama surutu ne da ita kamar parrot.
Saida ya gama wayar kafin mukai sallama suka koma mukuma muka bar harabar gidan.
Farin cikina ne ya qaru lkcn danaga mun dosh shiga layinmu.wayyo duk wanda yabar gida gida ya barshi.
Tunanina ya tsaya cak lkcn da mukazo dai dai gidansu ya sadiq.
Ko yanxu yana ina oho?ko yaji sauki allah ne masani.Ko ina nusaiba tayi saurin mantawa dani haka oho.
Bansan mun qaraso qofar gidanmu ba sai da naji an buga murfin mota da qarfi.
Ba shir na dawo hankali na inda naga ba kowa a mota saini kadai.
Da hanxari na bude na fito inda tuni yaran sunyi cikin gida sai gogan naku a tsaye jikin mota.
Banbi ta kansa ba da gudu na shige gida ina dokin ganin Ammina.
Gidan cike yake da yaya da jikoki dan gaba daya su ya aisha da yaransu sunanan.
Duk da farin cikin ganinsu da nakeyi amma inajin haushi akan mantawa dani da sukayi,dan haka direct wajen ammi nayi na rungumeta tare da fashewa da kuka.
[07-23, 20:47] Sistoh: ππRABON KWADO...ππ
Er mutan ungogoππππ
π
Ώ91-π
Ώ96
Ke kuma lapiyarki daga shigowa sai kuka?idan kinsan kuka zakimin ki tashi ki bani guri"Ammi tace dan taga kukan bana qarewa bane,dan su ya zee sunyi mgnr duniya banyi musu mgn ba.
Saida nayi mai isata kafin na share hawayena.
Ammi har kema kin daina sona koh?korata ma kikeyi sbd bakiso ki ganni koh?"nace hawaye na qara zubomin.
Haba auta,taya zaki ringa fadar haka bayan kinsan kaf cikinmu Ammi tafi ji dake"ya zee ta fada.
A baya dai idan aka fadi haka zan gasgata,amma yanxu wlh bakwasona"nace cikin kuka.
Kinga ni wannan dramar ta isheni haka,keda kika dade bamu ganki bs maimakon kizo ki faranta mana rai sai kizo kina mana kuka"ya ruqayya ta fada.
Tashi kawai nayi na shiga dakin Ammi na fada gado tare da cigaba da kuka na.
Allah sarki uwa!Ammi ce ta zauna kusa dani tare da dora kaina akan cinyarta tana gogen hawayen fuskata.
Ya isa haka kinji auta?kar kije kanki yayi ciwo.kiyi hqr nasan ba'a kyauta miki ba,kullum da zancenki nake tashi a raina,amma ina mgn Abbinku zai fara fada,ko yanuwanku ba yadda basuyi zasuje ganinki ba ya hana,a cewarsa a barki zuwa wani lkcn sai aje"
Amma kuma Ammi..."
Dan allah ya isah haka auta,ki tashi kije cikin yanuwanku kamar yadda kuka saba,Abbinku ya fita shima yana dawowa kije ku gaisa"
Dan dole na tashi na fito fallon,inda sukayo kaina caaa.
Waikina nufin har yanxu baki cire komai a ranki ba khadija?kalli yadda kk rame dan allah"ya aisha tace.
Nidai kawai kallonsu nakeyi daya bayan daya,dan basu san halin da nake ciki ba,kuma na daukarwa kaina alqawari ko naman jikina ake gutsira a gidan nan bazan taba fada ba,idan na mutu dai sai suje su dauki gawata.
Ganin Ammi tana kallona yasa na saki jiki idan anyi abin dariya nayi dan hira da raha akeyi kamar yadda al'adar gidanmu take indai muna tare to fara'a bata barin fuskokinmu.
Ana haka Abbi ya shigo,inda ya zauna shima aka taba hirar dashi kafin ya tashi.
Zumbur na miqe.
Ammi bari naje gidansu nusaiba"
Kin tambayi mijinki zaki wani wajene bayan nan?"ammi tace tana kallona.
Komawa kawai nayi na zauna dan bani da amsar bayarwa.
Ke kuwa auta sallah guda ko lalle baza kiyi ba"ya ruqayya tace.
Ya ruqayya kenan,a wannan anguwar ina zanga mai lalle?ni kinga kaina nema ya damenu ba kitso,kiyi mun ko kalba ce"nace tare da cire dan kwalin kaina.
Ke wai yaushe kika zama qazama ne,ga kanta Ammi dan allah"ya zee tace tana tamin kai.
Ammi dai bata ce komai ba,sai ya ruqayya data miqe tsaye.
Ina wayarki take"tace tana kallona.
Ni nama manta inada waya dan can na barta a kan gado.
Wayar ammi ta karba ta fara kira,bansan wazata kira ba,nadai naji tace wai dan allah zamu fita tare.
Jin tace na tashi muje naji fita yasa na zira mayafi mukai waye.
Can wajen salon din bakin titin layinmu mukaje.
Mun dan sha zama kafin kazo kanmu.
Sosai nakeji iska na shiga kaina bayan an wanke min relaxer ana gyaran kan.
Tsaf aka gyaranshi yanata qyalli da gamsu,ya ruky ta biya kudi muka fito.
Gidan mai lalle mukaje duk da yamma ta fara haka muka samu daqar tayi min hadadden jan lalle na son kowa qin wanda ya rasaπ
Cikin qanqanin lkc na dawo mace sai dai rama da duhun dana qarayi.
Ana kiran sallar magriba muka dawo gida.
Kowa yaita yaba lallen,kafin suka fara shirye shiryn tafiya.
Yaya yanxu yaushe zakuxo"na fada kamar nayi kuka.
Munason zuwa auta amma abbi ya hana mu kuma bamusan dalilinsa nayin hakan ba,kedai ki cigaba da haquri zakici riba insha allah"
Haka ina gani suka tafi,na dawo muna hirar yaushe gamo da ammi dan su shahida suna wajen abbi.
Ammi dan allah ki barni naje gidansu nusaiba"na fada a shagwabe.
Ba hanaki nayi ba auta,mijinki shike da ikon barinki fita bani ba.
Cikin hikima ta ringa min nasiha tare da nusar dani akan muhimmancin haquri dayiwa iyaye biyayya.
Har bayan issha muna jiran dan milkin baixo ba,ni kuwa addu'a nake allah yasa ma yaqi zuwa mu kwana.
Zuwan almajirin ammi yasa na rubuta gajeren saqo a paper nace yakai gidansu nusaiba.
Ai kuwa cikin qanqanin lkc sai gata ta bayyana a gidanmu.
Daku muka qule bayan mun gama ihun ganin juna.
Lallai nusaiba manyan qasa,ai banyi tunanin xaki xo ba"
Kinji ki maizai hana ni zuwa nida nake son ganinki"
Ba wani da kinason gani na ai xakixo inda nake"
Wlh ki tambayi ammi ina zuwa nace ayimun kwatancan gidan,ammin ce tace wai abbi ya hana kowa zuwa dan dole na hqr"
Nima haka dazu tace,nusaiba na rasa gane dalilin dayasa abbi yayi haka"
Ke bafa komai,kawai dai ya fison ki nutsu ne,sbd idan kina ganin yan gida xakiyita tada hankalinki ne"
Uhmm,ni kuwa ina ya sadiq dina?"
Wata muguwar harara ta kwada min kafin tace.
"badai kina nufin har yanxu kina wahalar da kanki akan abinda kk san bazaki samu ba?"
Kamar ya?"
Kamar yadda wanda kk wahala a kanshi,kk kasa nutsar da hankalinki ki rungumi mijinki sbd shi,shi kuma yaje yayi aure tuni ya manta dake dan yanzu matarsa nada qaramin cikiπ€°.
ππππππππ
Manage it plss.
[07-23, 20:47] Sistoh: ππRABON KWADO...ππ
Er mutan ungogoππππ
π
Ώ96-π
Ώ100
Karya ne,wlh karya kk nusaiba kice ya sadiq zai manta ni hakakuma qarya ne kice zai auri wata bayan ni"na fada ina riqo wuyan hijab din jikinta.
Kallona kawai ta tsaya tana yi.
Khadija wai yaushe zaki dawo hankalinki ki daina abubuwa irin na jahilai?da aurenki kk dakon soyayyar wani?to gsky ce bazan fasa fada miki ba kuma zan qara maimatawa ya sadiq yayi aure ya manta dake"tace tana fizgewa daga riqon da nayi mata tare da ficewa a dakin.
Kifa kaina nayi a katifa ina maimaita maganganun nusaiba.
Ya sadiq why?meyasa xakayimin haka?da gsk ka manta dani?ka manta dumbin soyayyar danake maka?wayyoo...
Jin an zauna a kusa dani yasa nayi saurin dagowa.
Ammi ce take bina da kallon tuhuma.
Kukan me kk?"ta jefomim tmby.
Shiru nayi ina qoqarin tsayar da kukan dan bansan amsar da zan bata ba,gashi banga alamar wasa ko sassauci a fuskarta ba.
Meya hadaku da nusaiba najiyo hayaniyarku?"ta kuma tmby.
Nan ma shirun nayi tare da qasa da ido dan ko hauka nake bazan iya cewa ammi sbd ya sadiq yayi aure nake kuka ba.
Khadija!
Da sauri na dago dan na manta rabon ammi da kirana da wannan sunan.
Saboda Abubakar yayi aure kike kuka?ko kinason ki fada min har yanxu baki cireshi a ranki kin manta dashi ba?"
Nan ma banyi magana ba.
Kin dauka yadda baki da hankali da tunani haka shima yake da zaita dakon soyayyarki kina matar wani?ko kuwa so kike yayiwa iyayensa butulci kamar yadda kika yiwa naki iyayen kika kasa xama da mijinki lpy?kin zata tunda ya rasa ki shikenan bazaiyi aure ba?ko zaman jiranki xaiyi ki kaso naki auren kixo ya aure ki?"
Wlh,wlh,wlh khadija idan baki gyara rayuwar aurenki kin xauna da mijinki lpy ba xaki sha mamaki na.shashasha kawai,ki tashi ki ficemin anan mijinki nacan na jiranki."
jikina ba qarfi na miqe dan gsky ran ammi ya baci sosai dan bantaba ganinta a wannan yanayin ba.
Mayafina na dauka kafin na nufi dakinta,dan tuni ta fito ta barni anan.
tana zaune a gefen gadon naje na tsugunna a gabanta.
Ammi dan allah kiyi hqr"nace cikin kuka.
Ke zan bawa haquri khadija,kije ki gyara rayuwar aurenki wannan ne kawai zaisa na sakko.ki tashi kin barsu suna jira.
Haka na fito ina kuka inda Abbi ma yayi min fada nidai kuka kawai nake na shiga mota muka tafi.
Shiru motar sai shassheqar kukan da nakeyi.
Aunty me akayi miki kikeyin kuka?"shahida dake gefena tace.
Jin banyi mgn ba yasa ta mayar da tmbyr ga daddynsu.
Daddy me akayiwa Aunty take kuka?"
Ummina gata nan ki tmbyta nima bansani ba"yace yana cigaba da driving dinsa.
Tun daga nan ba wanda ya kuma cewa komai har mukaje.
Dan tuni iman ma tayi bacci.
Jin munxo yasa na fita ban jira kowa bai nayi gaba abina.
Sosai na raya daren da kuka,tare da roqar allah ya ciremin son ya sadiq daga raina,dan nasan yanxu yayi min nisa,son maso wani kawai nake.
Washegari ma ko falo ban iya fitowa ba,sbd kaina da yakemin axababben ciwo.
Aunty ki shiryamu inji daddy zamuje park"Iman tace tana jijjigani.
Baby bazan iya ba kaina yana ciwo kinji?"
Daga kai tayi ta fita a dakin.
Nidai ina kwance kawai ihun shahid na jiyo.
Bansan lkcn da na tashi da gudu nayi kitchen inda ihun yake fitowa ba.
Inannalillahi!
Na fada na riqo shahid dayake ta tsalle yana riqe da hannu,da dukkan alamu qonewa yayi da ruwan zafi,sbd ga cattle nan da ruwa a yashe a qasa.
Shahid meya kawoka kitchen? dama kuna zuwa kitchen?"na fada a rude dan ganin yadda yake kuka,amma ba wata qonewa bace mai yawa.
Cak!na tsaya dan ganin daddynsu tsaye a bakin qofar kitchen din da sauran yaran.
Riqo hannun shahid din yayi tare da tmbyrsa garin yaya ya qone?
Wanka zanyi kuma ba ruwan zafi a heater din toilet dina shine nazo na diba anan shine na qone"na fada yana kuka.
Kallona yayi wanda bazan iya fassara ko wani irin kallo bane yaja yaransa sukai gaba.
Nima jan jiki nayi na koma daki ina tunanin to kallon na menene?nidai bani nace yaje ya dibi ruwan zafi ba,asalima bansan zaiyi wankan ba.
Sbd mugunta shine kikeso ki kashemin da ko?to na gaji da wannan abun naki bazan iya ba"daddynsu shahid ya fada yana figoni daga kwancen da nake.
Nima na gaji,wlh na gaji da wannan abin naka,ko anfada maka baiwa aka kawo maka?"nima na fada a fusace dan da gsk na gaji da wannan rayuwar rashin yancin.
Ni kike fadawa haka koh?sbd....
Aaaaa,karka fara,karka fara dabi'ar daba taka ba babanah,dukan mace?"
Da sauri na bude ido dan jin muryar ummi,domin na shirya kawai saukar mari nake jira.
Aunty anisa ce ta kamani tana sharen hawayen fuskata wadanda bansan ma suna zuba ba.
Inda ummi ta ja shi suka fita yana wani huci.
Khadija me kk yi masa haka har ya fusata yake qoqarin kai miki hannu"?aunty anisan ta fada.
Kukan da yazo min ya hanani mgn,inda suka rufu akaina sunata rarrashi na,dan gaba dayansu sukazo.
Kafin wani lkc zazzabi mai zafi ya rufeni.
Daqar naci wani abun mubina ta bani magani nasha na kwanta.
Sosai naji relief bayan na farka,inda suka shiga nan nan dani dan har lkcn suna gidan.
Bayan na idar da sallah aunty anisa ta zauna tana fuskanta ta,domin a lkcn mu kadai ne a dakin dan su mufida sun fita.
Khadija!
Naaam"na amsa da dasasshiyar muryata.
Inaso ki dauka cewa yanxu kina tare da fatima zaki ita fada min duk abinda na tmbyki,domin nima ina miki kallo matsayi daya danasu mufida"
Nafi kowa sanin halin broz,kuma nafi kowa sanin wayeshi.Na fahimci akwai matsala a zamantakewarku tun jiya da kukaje gidan ummi,Dan nayiwa broz sanin da kallo yayi nasan abinda yake nufi,kuma lkcn fatima tananan ba haka ya saba yiba dan muka hadu,hakan yasa nace muzo yau dan inason nayi wani abu akan abin kafin na koma"
Dan haka yanxu ki fada min mene ya hadaku dazu?"
Banyi mgn ba sai hawayen da suka zubomin"
Kinga ba kuka nace kimin ba,idan kuma baki yarda dani ba bazaki iya fadan damuwar ki ba shikenan"
Tabbas zan fada mata kodan na samu sauqi a cikin xcyta,duk da akwai wadanda sukafi cancanta na fadawa damuwata kafin ita amma yanxu sun min nisa,ammi danake tunanin zata fahimceni itama fushi take dani.
Dama can ya tsaneni tun ba yau ba,kuma akazo aka hadani aure dashi.ya fadamin tun kafin nazo gidan nan xan zauna ne a matsayin yar aiki......
Haka na bata lbrn abubuwan da sukafi damuna dan nasan bazasu fadu duka ba.
Mundau tsahon lkc ba wanda yayi mgn kafin ta kalleni.
Kina nufin tsahon lkcn nan zaman da kuke kenan?"
Daga mata kai kawai nayi.
Kuma ba wani mataki da kike shirin dauka a kai?kinsan dai rayuwa bazata cigaba a haka ba,kuma idan na fahimceki kina nufin ko abincinki bai taba ci ba,bare aje ga sauke haqqin aure"
Shiru nayi.
Shikenan,insha allah zanyi iya qoqarina kamar yadda idan su mubina ne a irin wannan conditon din sai inda qarfi na