Showing 24001 words to 27000 words out of 41234 words

Chapter 9 - RABON KWADO BOOK 1 COMPLETE .txt

Unknown   

18 Jan 2025

4654

ya qare haka kema dan duk daya kuke a wajena,dan haka inason ki bani hadin kai,Domin dole saida hadin kanki komai xai tafi dai dai"


Broz irin mutanen nan ne masu wahalar sha'ani,amma kina fahimtar halayensa kin gama dashi,sbd hk saikin jure"


Tom ngd"


Banason gdy,yanxu ina wayarki?"


Tashi nayi na dauko mata calculator dita.


Karba tayi tana jujjuyata kafin taja tsaki ta miqe ta fita.




Ganin shiru bata dawo ba yasa na koma na kwanta,domin sai naji zcyta sakayau kamar na sauke wani nauyi a kaina,ko ba komai na amayar da damuwata.


Mubina ce ta shigo.


Sannu sis"


Murmuhi kawai nayi.


Kixo ummi na kiranki"


Hijabi na nasaka kafin na fita.


Can gefe na zauna dan ummin ce da aunty anisa sai daddynsu shahid.




Fada ta shiga
yi mana sosai tare da nuna rashin jin dadinta akan abinda tazo ta gani.


Haduwa sukai suna bata hqr nidai kaina a qasa.saidata gama kafin ta tashi ta fita ya bita yana qara bata hqr.




Anjima zan bayar da saqo a kawo miki kinji?ki qara hqr kinsan irin wannan abun sai mutum ya jure dan inaso ki shirya yaqin janyo hankalinsa da mallakar zcyarsa.zuwa gobe nake tunanin zamu koma,amma idan bamu tafi ba zan dawo"


Daga mata kai nayi ina qara jaddada qoqari irin nata,tare da samar mata matsayi a zcyta dan ko ba komai ta nuna qauna da damuwa akan lamarina.
[07-23, 20:47] Sistoh: πŸ’™πŸ’™RABON KWADO....πŸ’™πŸ’™








Er mutan ungogoπŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹










πŸ…Ώ111-πŸ…Ώ115








Har dare ni kadaice a gidan dan yaranma bansan inda ya kaisu ba,ko su ummin suka bi oho.




Wani nishadi nakeji danasan yana da nasaba da amayar da abinda yake zuciya.


Sosai lamarin auren ya sadiq idan na tuno yake bani mamaki,amma a kalaman ammi sai nake ganin kamar tilasta masa iyayensa sukayi.


Koma yayane nidai na dau aniyar cireshi a raina koda ta qarfin tuwo ne.


Ina kwance shiru bayan nayi shirin bacci,dan yar calculator din ma dana ke sauraran radio ko nayi game mai miciji itama babu,dan da ita nake tunanin aunty anisa ta tafi.




Da sallama ya danno kai cikin bed room din,wanda nayi saurin miqewa daga kwanciyar da nake domin tsahon zamana a gidan bai taba takowa koda bakin qofar dakin bane.


Fuskarsa ba yabo ba fallasa ba kamar yadda na saba ganinta ba koda yaushe a hade.


Ganin ya nemi gefen bed din ya zauna yasa na qara matsawa can qarshen gadon duk da girman daya ke dashi.


Saida ya gama shan qanshinsa da danne dannen wayar data zama kamar ibada sannan ya kalloni.


Ganin yadda na takure yasa ya tabe baki kafin yayi mgn.




Ga saqo nan anisa ta bayar a kawo miki,kuma daga yau ba wani zakina tmby wani abu idan kina buqata ba,ni dana ajiyeki niya kamata ki tmby"ya fada tare da ajiye qatuwar ledar hannunsa ya fita.


Har yakai bakin qofa ya juyo.


Tace ki hada wayar yanxu akwai sim card a ciki zata kiraki"yace ba tare daya juyo ba.


Jin zancen waya yasa nayi saurin durowa tare da bude ledar cikin gaggawa.


Kayan bacci ne masu kyau da tsada kusan kala biyar sai turaruka da banbi takansu ba na dauki kwalin wayar na budeta.


Masha allah!na fada cikin zaquwa tare da raya cewa wannan wai wayata ce?Ipone 7 pa,wayyo dadi ashe nima inada rabon riqe irin wannan wayar.


Jikina har rawa yake na kunna wayar tare da fara processing.




Sosai nake murna da jaddada kalmar nan ta mahaqurci mawadaci.


Banyi mintina da kunna wayar ba kira ya shigo wanda nafi tunanin na aunty anisa ne.


Assalamu alaikum"naji an fada wanda ko ba'a fada ba na gane muryarta ce.


Wa'alaikissalam aunty anisa"


Naam aunty khadija ashe ya kawo saqon?"


Cike da jin nauyin auntyn data kirani dashi nace.


Eh ya kawo na gode sosai"




Nafa fada miki banason godiya.yanxu abinda nakeso dake gobe da safe idan allah ya kaimu kwalliya zakiyi ta kece raini,sannan ki shiga kitchen ki shirya masa kunun gyada da qosai,kafin kije ki kirashi kice yazo yayi b/fast.ki cire wani abu a ranki ko wata kunya kiyi abinda nace,wannan shine matakin farko da zaki fara dauka,dan inason kafin a dawo da yaran ace wannan bangaren mun gama dashi kingane koh?"


Eh"nace ina jinjina irin wannan aiki data sakani mai wahalar aikatuwa.




Kamar yadda na fada sai kinyi hqr kin jure,bawai kinayi so daya ya disgaki zakiyi zcy kice bazaki kuma yi ba,Aa haka zakita jurewa har allah ya karkato miki da hankalinsa.bana tunanin zaiqi cin abincinma dan jiya sosai ummi tayi masa fada kuma naga alamar fada ya shigeshi.Nidai fatana khadija karki bani kunya,kiyi duk abinda nace miki kinji?na taqaitaccen lkc ne insha allah"




Tom aunty anisa insha allah zan qoqarta"


Yawwa qanwata,yanxu kiyi bacci ta yadda zaki tashi da wuri kiyi abinda ya dace,goben zamuyi waya"


Tim saida safe"nace ina zare wayar daga kunnena,tare da fargabar yadda zan tunkari wannan babban al'amari.




washegari kamar yadda Aunty anisa ta sakani haka nayi nayi kwalliya na cakare wanda ni kaina inada tabbacin nayi.zakifi tunanin gasar sarauniyar kyau zani.


Iphone dita na dauko na shiga daukan pictures,inda suka fita yadda ya kamata musammanma da kyan camera ya hadu da good background😊.


Abinka da an dade ba'a haduba haka na bata lkc na wajen daukar picx din kafin na shiga gyara wadrop dan shirya kayansu iman da aka kawo wanki tun shekaran jiya.


Saida na tabbatar na gyara kayansu kafin na fara gyara nawa dan shiryasu yadda ya kamata.


Ledar jiya na dauko tareda zazzage kayan akan bed.


Kayan na fara dagawa wanda nayi saurin cikwikwiyesu na saka a wadrop dan kunya ma kayan suka baniπŸ™ˆ


Turarukan ma sunmin qamshi sosai,inda ba bata lkc na fara turara gidan da turarukan.


Haka na cigaba da aiki na cikin nishadi ina shaqar qamshin turaren.


Ba bada lkc na gama komai dan gidan ba dattine dashi ba.


Kitchen na fada na shirya kunun gyadar tare dayin qosan naje na jera a dinning ina sake saken ta ina zan fara tunkarar sashensa?to idan najema mezance?




Ganin banida wani zabi daya wuce yadda aunty anisa tace yasa nayi qundunbala tare da qunar baqin wake na nufi sashen duk kuwa da fargabar yadda zai karbi baqon al'amarin daya cika min zcy.




Tofa! nafi mintuna 30 a bakin qofar ina tunanin ta yadda zan fara knocking qofar.


Jin an bude qofar yasa naja da baya da sauri tare da diriricewa kamar mara gsky,bayan luguden da zcyta takeyi ganin mamaki kwance a fuskarsa.nasan mamakin bai wuce na ganina da yayi a qofar sashin sa ba.


Ganin ya tsaya riqe da qofa yana kallona yasa nayi qoqarin aro nutsuwa da dauriya na yafa.




Dama inaso na fada maka na gama b/fast ne"na fada cikin dauriya.




Nace ina buqatar abinci ne"ya fada yana qara gyara tsayuwa.


Shiru nayi ina kuma jin takaici a raina.




Tunda bance ina buqata ba zaki iya bace min anan gurin,idiot kawai"yace tare da banko qofar.




A hankali na zame a wajen na zauna dan nasa qafafuna bazasu iya kaini daki ba.


Idiot?nice idiot?meyasa yakeson kira na da wannan sunan?idan zan iya tunawa wannan shine karo na uku daya kirani da wannan sunan.Amma yanxu banga laifinshi ba,da banzo inda yake ba da bazai fada min haka ba.


Why aunty anisa?meyasa kike tunanin zan iya mallakar mutumin dayafi kowa tsanata?meyasa kikeson na cusa kaina inda nakeda tabbacin bazan samu shiga ba?


A hankali na miqe ina goge hawayen fuskata,dan banaso ya kuma fitowa ya sameni a bakin qofarsa,dan bansan me zai kuma fada min ba.


Ina shiga dakin na fizge dankwalin kaina tare da wullar dashi,sannan na kifa na cigaba da kuka dan samun sauqin zcy.


Inaji wayar ta fara qara naqi dagawa,tunowa da ba mai kira sai aunty anisa yasa na share hawayena tare da daga wayar.


Matar broz yaya dai?inata zumudin kira naji bayani dan nasan yanxu broz ya dade da tashi a bacci"


Qaqalo murmushi nayi tare da cewa "ina kwana aunty anisa"




Shiru naji tayi kafin tace"an samu matsala koh khadija?"


Aa"nace da muryata da take rawa dan kukane ya tahomin.


Kiyi hqr kinji?dama na fada miki sai kin jure"




Aa aunty anisa,kiyi hqr wlh bazan iya ba,daddyn shahid da irin mutanen da suke saurin sarrafuwa bane,kuma na sanar dake tun farko baya sona,bai bata min kallon mutunci ina qanwar matarsa ba bare yanxu da nake amsa sunan matarsa"




Haba khadija,bai kamata kiyi saurin karaya haka ba,nasan halin ya abdul sosai shiyasa naje so kema ki gane halinsa kiyi hqr dashi har zuwa lkcn da zaku fahimci juna"


Banason yi mata musu ko gardama a qoqarinta na ganin ta saita min rayuwar aure,hakan yasa nayi shiru kawai ina kuka.




Khadija!


Naam"




So nawa ne abu ya sameki kikayi kuka ya warkar miki da matsala ko damuwa?kuka ba shine mafita ba,banaso duk abinda broz zai miki ki yarda ya gano fishinki ko gazawarki"




Aunty anisa ki gane,daddyn shahid nice bayaso,da yake yanason ya fatima kin taba ganin wani abu ya hadasu?"




Naji baya sonki,shine yanxu nakeson yasoki fiye da yadda yaso duk wata mace daya taba so.idan kin yarda dani kinsan bazan cutar dake ba khadija kawai ki yarda kuma ki amince da duk abinda na fada miki.Ya abdul ba dutse bane bare kiyi tunanin bazai lanqwasu ba.inaso ki share hawayenki yanxu kiji wani matakine wanda zamu shirya na gaba"


Dan dole na share hawayena ina sauraron duk abinda take fada ba tareda na ayyana zan iya aiwatar da hakan a raina ba.






Sosai take tausata da qarfafamin gwiwa har saida taga na yarda na dauki duk wasu shawarwarinta.


Da yamma ma wanka nayi na kumayin kwalliyar,badan wai koxai yaba ba saidan kawai nabi shawarar aunty anisa,kuma koba komai gyara yana da dadi nima naji dadi a raina.


Tuwon semo nayi da miyar kubewa kamar yadda aunty anisa ta sakani,bayan na cinye qosan danayi da safe dan dama kadan nayi.


Haka shima na jere a dinning kafin na zauna a falo inayin game dita mai ajiπŸ˜„
[07-23, 20:48] Sistoh: πŸ’™πŸ’™RABON KWADO.....πŸ’™πŸ’™










Er mutan ungogoπŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹








πŸ…Ώ106-πŸ…Ώ110








sai wajen 9pm ya shigo kamar kullum fuskarnan a hade kamar hadari.




Sannu da dawowa"na fada cikin fargabar abinda zai biyo baya.




Ko inda nake bai kalla ba bare nasa ran zai amsa.


Bin bayansa nayi da kallo kafin na koma mazaunina Ina jinjina hali irin nasa.Amma a yadda aunty anisa take fada wai yana da sauqin kai,ko ina sauqin kan yake anan oho.




Kiran aunty anisan ne ya katsemin tunani.




Ita dai baiwar Allan nan ta damu da lamarina.




Khadija broz ya dawo koh?"ta fada.


Ni lamarinta har mamaki yake bani,tana abuja amma tasan duk wani motsi nasa da duk lokutan dayake gabatar da abubuwa?




Kiyi qoqari kiyi abubuwan dana fada miki kinji?"


Aunty anisa yanxu ma fa ko sannu da zuwana bai amsa ba"


Nasan bazai amsa ba dama khadija,yanxu ki bari zai fito kallon News falon saiki gabatar masa da abincin,insha allah indai yaga abincin zaici dan yana matuqar son cimar"




Da To naita binta har mukayi sallama.


Inanan zaune kuwa sai gashi ya fito,nan ma ko inda nake bai kalla ba ya fara kunna tv.


Ganin ya kishingida ya fara kallon labaransa yasa na tashi na shiryo masa abincin a babban faranti na kawo na ajiye a center table.


Flat na dauka na zuba abinci,kafin na zuba masa tataccen inibi a cup.




Ga abinci"nace ina kallonsa.




Wani mugun kallo ya watsa min nida abinci kafin yayi mgn.




Is better for u ki bar wahalar da kanki,ki daina bata lkcnki kina yaudarar zcyrki.Bakida abinda zaki burgeni dashi,zaifi miki ki cigaba da zama a matsayin yar aiki kamar yadda na shawarce ki tun farko"ya juya ya cigaba da kallonsa kamar bashine yayi mgnr ba.




Gwiwa a sace na fara tattare kayan abincin zcytah na zafi.


Kitchen nakai kafin na koma daki.kashe wayar nayi na sakata a drower,dan nasan dole aunty anisa ta kira.


Bazan qara kunna wayar bama bare ta kuma fadan wani abu dazan jawa kaina raini.






Tsahon kwana uku ban kuma yarda mun hadu dashi ba,dan yunwa ce kawai take fito dani daga daki.wayar ma tun a ranar ban kuma waiwayarta ba,dan zamana haka ya fiye min alkhairi da nakai kaina a wulaqanta ni.






Dauke nake da cup na fito daga kitchen ina shirin komawa daki naji ance.




Zo nan"




Saura qiris cup din ya fadi dan na tsorata sosai,banyi zaton da mutum a falon ba sai yanxu.


Falon na qarasa na nemi guri can nesa na zauna na fara shan custard din dake cikin kofin.


Tashi naga yayi,ga mamakina naga yazo kusa dani ya zauna.




Daxu munyi waya da ummi ta fadan Mubina gobe zatazo holyday,kuma nasan ummi zata turota ne C.I.D,dan haka zakiga abubuwa na faruwa karki dauka wani abun ne.sannan Me anisa zata fada miki ta dameni da kira?"


Nidai banyi mgn ba,hasalima ni ba wani fuskantar abinda yake cewa nake ba.




Kunnena ya kama yaja da qarfi wanda yasa dole na saki qara.




Banaso ina yiwa mutum mgn yayi min shiru"


Nidai Allah ya isa nake ja a zcyta dan ba qaramin ja yayiwa kunnen ba.


Sum sum na tashi na bar gurin ina qara jajjada allah ya isa.




Sosai naji dadin xuwan mubina,inda muka baje munata shan hira kasancewarta gwanar surutu,dama kadaici ya isheni.


Tare mukayi girki muka jere a dinning kafin mukayi wanka.


Das!na fito a cikin wata maroon din shaddata datasha aiki.duk da banyi wata kwalliya ba nayi kyau ba qarya.






Wannan duk kwalliyar yayan namu ce?kice haka ake kasheshi da wanka"ta fada da sigar wasa.


Murmushi kawai nayi ina feshe jikina da turare.




Nipa qamshin abincin nan duk ya hargitsani,nidai ci zanyi nasan ke saikin jira mijinki"tace.


Falo na dawo na kwanta ina kallon pictures a wayarta inda ta dawo falon tanacin abinci tana min bayanin hotunan daki daki.


Da sallama ya shiga hannunsa dauke da qaramar leda.


Fuskarsa dauke da murmushi ya qaraso yana amsa sannu da zuwan da mukayi masa a tare.
Nidai kallon mamaki kawai nake masa.ban gama mamaki ba sai danaga yaxo Daf dani ya zauna tare da dora kansa akan kafadata yana kallon wayar.




Nernah yau na gaji sosai wlh"yace da wata murya da bansanshi da ita ba.




Tuni na daskare a wajen,dan numfashima daqar nakeja.
Sosai abin ya bani mamaki dan gani nake kamar a film.


Mubina me kk yiwa matata taqi yimin mgn?"yace yana kallon mubina.




Ai kunfi kusa yaya,gatanan ka tmbytah,maybe dan baka dawo da wuri bane tanata jiranka ku ci abinci"tace tana cigaba da cin abincinta hankali kwance.




Wayyo allah!πŸ™†πŸ™†




Gyara kwanciya ya qarayi a jikina yana wani lumshe ido.


I'm sorry nernah,Dauko mana plat ga abin dadi na kawo miki"yace yana janyo ledar daya ajiye.




Nernah"na maimaita a zcyta.ya sadiq kadai ke kirana da wannan sunan,sai shi yanxu dan munafinci zai rada min?A iya tunanina duk tsahon zamanmu ko sunana bai taba ambata ba.




Wata dabara ce ya fado min,bashi ya iya bariki ba?hmmm




Ba fushi nake ba,kasan kaima bazan iya fishi dakai ba"nace ina sakar masa wani killer smyl.


Kallona yake da alama na mamaki ne,sai kuma yayi saurin dauke idonsa daga kaina.




To maza dauko plat din"yace.




Gafa abinci can yana jiranka,kuma kasan sbd kai nayi"na fada a shagwabe.


To duk zanci a kawomin"ya fada still yana kallona.


Ina barin falon na jingina da bango ina maida numfashi dan ba qaramin qoqari nayi ba.


A trey na jero abincin na kawo inda muka zauna qasan carpet din ya wani bude qaramin bakinsa shi a dole saina bashi abinci.


Yadda yake langwabewa yana zuba min shagwaba kamar wani qaramin yaro shi zaifi baku mamaki,ita kuwa mubina in banda dariya ba abinda takeyi.


Idan ka ganshi yanxu bazata taba tunanin daddynsu shahid bane wanda ka sani,dan yadda yake shagwaba ko iman batayin irinta.
Nima duk shagwabata saida na sara masa dan wannan har PHD yayi akan shagwabaπŸ˜„




Shagwabar ma tafi cin abincin yawa,nidai biye masa nakeyi dan na qagu a gama cin wannan abincin.


Dan dole na bude nawa bakin yana zubamin loma.haka dai muka gama shirin film din na tattare kwanuka nakai kitchen.


Daga nan ban dawo falon ba nayi daki.


Wanka na sake nayi shirin bacci dan nace bazan koma falon ba,dan bazan iya wannan shutting din ba.




Wayatah na dauko na kunna na dannawa aunty anisa kira,dan nasan ban kyauta mata ba,kuma inaso ta bani shawara akan wannan rikitaccen al'amarin.




Sannu khadija kin kyauta"tace bayan ta amsa sallamar.




Amin afuwa auntynah"nace ina murmushi.


Ba wani aunynkikin samu miji shine kk manta dani"tace tana dariya




Aunty ba haka bane wlh"


To yanxu ya ake ciki?"




Lbr na bata duka kafin tayi shiru kamar bazatai mgn ba.


Kinsan me khadija?wannan ma wata hanyace mai sauqi Allah ya kawo mana,dan haka zagewa zakiyi kiyi duk wani abu daya kamata,akwai abubuwa masu tarin yawa anan gaba,dan haka sai mun qara shiri sosai"


Amma aunty.....




Khadija banason kina karaya haka,zaki iya kiyi kawai"




To Aunty nagode"




Yanxu ina mubinan?"


Na barsu a falo"




To maza ki koma ayi hirar dake,kuma duk abinda yayi ki biye masa,zamuyi mgn da mubinan itama"




Tom aunty saida safe"




Na dade zaune a gefen gado ina tunanin wannan baqon al'amari kafin daga bisani na zira hijabi akan kayan baccin duk da kasancewarsu masu kauri na fita.




Mubina ce kawai a falon tana waya naje kusa da ita na zauna.


Wai yau baza muyi bacci bane?"nace ina kallon agogo ganin 11 harta wuce.


Saida ta kashe wayar kafin itama ta kalli agogon.




Kinsan in mutum yana tare da masoyi baya sanin lkc yayi"tace tana dariya.




Qarasowarshi yasa na fasa mgn,inda yake sanye da farar riga mai qaramin hannu sai wando baqi ina gwiwa.


Laptop din hannunsa ya bude bayan ya zauna can wata kujera.




Yaya ana shirin bacci kana shirin aiki?"mubina tace.




Idan banyi yanxu ba mubina gobe bani da lkc"ya fada yana kallon abinda yakeyi.


Tom nidai saida safe"tace tana miqewa.


Bayanta nabi dan ni kaina baccin nakeji.


Wanka ta shiga inda ni kuma na nemi maqwanci.




Wai mene haka kin wani bar mijinki a can kinzo nan"tace bayan ta fito daga wankan.


Shiru nayi mata kamar banji ta ba.


Hawa gadon tayi tana jan blanket din dana rufa.


Wlh ki tashi ki tafi gurin mijinki babu ruwa na"




Dan allah mubina ki kyaleni,ni anan nake kwana'"nace inajan blanket din daga hannunta.




Kafa min idanu tayi kamar zata cinye ni.




Amma wlh khadija bakida wayo,to mijin naki wa kk barwa?"


Ke na barwa kije ki tayashi hira"nace ina dariya.




Ke wlh baki isa ba sai kin tashi kin tafi"tace tana jana.




Kaji mata da qarfin hali,dan allah ki barn..."




Sallamarshi ce tasa nayi shiru ina qara jan blanket tare da rufe jikina.




Tashi mu tafi"yace yana wani tsare gida kamar ba shagwababben nan ba😜.


Ganin ba alamar wasa a fuskarshi yasa na miqe ina turo baki.


Hannu ya miqomin ba musu na kama ya riqoni muka fita🀝




Muna fita ya juyo.




Daga yau banaso na qara zuwa nace ki tashi mu tafi,idan kunne yaji...."yace tare da sakin hannuna yayi gaba.




To meye hakan?yana nufin a part dinsa zan ringa kwana?Wayyo ni hadiza naga ta kainaπŸ™†














Masu bibiyar littafin RABON KWADO..πŸ’™πŸ’™
Muna gdy,da fata za'ayi mana afuwa na rashin yin typing na kwanaki,hakan ya faru sakamakon rashin lkc da bana samu,amma insha allah zan ringa qoqari inayi ko da babu yawa.ngd




Sannan akwai mistake na page number da nayi zansa 101-105 nasa 111-115 ina fatan za'amin afuwa.








Er mutan ungogon ce daiπŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
[07-23, 20:48]

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login