Showing 27001 words to 30000 words out of 36747 words

Chapter 10 - GUBAR RAYUWATA BY FATIMA ABDALLAHI KANO .txt

Advertisement

wanka da baho.




Bayan su gama fito mata da kayan suka tsaya carko carko kamar masu shirin dukanta




"Ya ka ce mi mata shegen duka mana." Wani a cikinsu ya fada yana kallon Abdul.




Abdul ya ce "A'a ku barta kawai , domin duk abin dana ba ta na karba , dama taimakonta zan na aura , tana karuwa waya san cutukan dake jikinta .Ai yanzu na gane Allah ya yaye mini wahala."




Fa'iza duk ta rasa inda yake mata dadi ta kasa cewa komai




Abdul ya mika musu wannan kwadon gidan yana cewa "Rufe min gidana mu tafi."




"Kai Abdul akwai wani gardi fa a gidan kamar bacci yake ma." Wani a gefenshi ya yi maganar yana nuna gidan






Abdul da ranshi ya yi matukar baci ya kallesu yana cewa "To uban me ya sa bai fito ba ku koroshi tunda ba gidanshi ba ne ."




Kamar suna rige -rige suka fada Cikin gidan kai tsaye sukai dakin




Uncle duk yabi ya tsure ganinsu a kanshi "Ba yin Allah lafiya ."


Uncle ya yi maganar yana kallonsu daga kwance


"Tashi ka fita dan uwarka , kwarto kawai . Ita ma kwartuwar taka mun am she gidan mu."




Haka Uncle taji an fada , ba tare da ya gane wane ya yi maganar ba .




"Dan Allah ku yi hakuri, wallahi cutar barin jiki gare ni bana iya tashi."




Ba tare da sun ce komai ba suka dauko shi su su hudu , biyu sun rike hannaye , biyu sun rike kafafu .




Haka suka fito suka wurgo Uncle waje


"Kan uban can dama har yau wannan yana nan , to Allah ya kuma tonaki ."


Abdul ya karasa maganar yana kallon Uncle da yaji wurgi yana kwance a kasa




Suka rufe gidan suka hau mota sukai tafiyarsu .




Cikin mummunan takaici Fa'iza ta fara tattara kayan da aka watso mata , waje guda ta had'a su tana kallon tare da tunanin sauran kayan dake ciki, a cikin ranta ta lissafa yadda zata dauki kayan a hannunta ba tare dasun mata yawa ba .




A lokacin kuma hankalinta ya kai ga uncle yahaya da yake zararar da hawaye .
Wanda sa'ilin ta kuma kula da yadda gari ke rugugi sakamakon had'owar hadari .


Had'e rai ta yi tana kallon Uncle tare da matsawa kusa dashi tana cewa "Ni zan tafi , domin babu inda nake dashi bare na je dakai ."


Cikin tashin hankali Uncle yahaya ya zaro idanunsa ya fara magana a yanayin wahala.
"Ya za ai ki barni a nan Fa'iza, ga hadari , ina zan sa kaina , ban zata zaki mini haka ba."




Ajiyar zuciya ta yi sannan ta ce ,"Ka so gaskiya mana Yahaya ina ne zan kai ka , dama kowa yana da kaddarar shi , to ka dauki wannan matsayin abin da ba za ka ta'ba mancewa ba , shi ne Gubar Rayuwarka."




Tana gama magana ta juya da sauri tana kwashe kayanta , sakamakon tsawa da iska da aka fara.




Ba tare da ta ko kalli Yahaya ba tasa kai cikin sauri ta fara tafiya, sakin baki ya yi yana kallonta cikin mamaki ganin cewa da gaske fa tafiya ta yi ta barshi .


Wasu hawaye ne suka zubo masa yayin da ya fara ba za idanu da nufin neman wani ya taimake shi , amma babu wanda ya gani sai wani yaro dake gudu a keke sakamakon yayyafin da aka fara .




"Yanzu ya zan yi , wallahi da nasan abin da zai faru ke nan bazan zo legos ba , basu da mutunci yanzu sai su kone ni a gun nan ." Uncle cikin kuka ya sauke maganar yayin da aka tsuge da ruwan sama .Domin ko ita Fa'iza kafin taje inda zata wannan ruwan ya dake ta , bare Uncle naku dake guri daya.








Yau tun da gari ya waye Maryam take murna da fitar da zasi da Harun , mahaifiyar ta kawai ta sanar wa da wannan labarin , domin ta san malam na lado mahaifinta idan ya ji bazai yadda da wannan shirme ba ,




A tsakanin uwa da 'yah haka sukai maganar su , nan ta ba ta goyon baya tare da umarnin karta jima har Mlm ya tambaye ta.






Doya da kwai take soyawa , daga gefe kuma kana iya hangar wani kunu na gero wanda yasha kayan kamshi.


"Wai Nabila har yanzu ba a gama girki ba yunwa fa nake ji nasan ita ma Baba haka ."


Jafar ya shigo madafa yana wa Nabila maganar cikin mita ,




"Hmmm ." Kawai abin da Nabila ta iya fad'a ke nan


Jafar ba tare da hakan ya dameshi ba ya sake cewa "Kin san dai yau ne Yaya Umar ya ce zai kawo 'kannenshi ko , to ki musu girki dan Allah."




Ta kalleshi tana cewa, "Ban fa mance ba Yaya Jafar."


Ya karaso yana daukar doyar da zummar d'and'anawa.








Bayan Harun ya iso
ba 'ba ta lokaci Maryam ta fita suka tafi


"Ya kamata mu biya ki gaida momy na fa." Harun ya yi maganar yana kallon Maryam


Cikin shagwa'ba Maryam ta kalleshi tana cewa.










Share , like and comment......................📚










Gubar Rayuwata⚡🌹

By
Fatima Abdallaah kano
(Autar marubuta)





Editing❌


________________________________________




Page 37 & 38






"Amma gaskiya ba za mu dad'e ba."


Harun wani dad'i yaji ya rufe shi dajin amincewarta , hakan ya sa ya ce ,"Haba sarauniyata yadda ki ke so ai haka za ai besty na." Cikin 'kwarewa da farin ciki ya cigaba da tuki ya nufi gidan da yake kiran gidansu.


Wani gida ne babba suka shiga , Harun yana mata kalamai masu kwantar da zuciya har suka shiga cikin falo.




Maryam dakatawa tai cakk , sakamakon duhun da ta gani a cikin falon , saida Harun ya kunna haske sannan ta ji hankalinta ya kwanta .


"Duk kin wani furgita zauna mana baby bari shaf-shaf na shiga ciki na kira momy."
Harun ya yi maganar yana shige wa ciki.






Nabila kam tasha aiki sosai ta yi girke girke , duk saboda 'kannen Umar da zasu kawo musu ziyara .




Wajen minti biyar Harun ya yi bai fito daga dakin ba ,


Hakan ya sa Maryam ta yi shiru tana sa'ke-sa'ke cikin zuciyar ta


ba ta gama tunanin abin da ya rike su a ciki ba , sai ga Harun ya shigo jikinshi duk a mace ."Mene kuma ya faru."?


Maryam ta yi maganar tare da tashi tsaye


"Ina shiga ciki, na ga momy kwance wallahi hawan jininta ya tashi."
Inji Harun


"Subhanallahi." Maryam ta fad'a




"Amma karki damu , ki shiga ciki ki kula da ita dan Allah, ki kula min da mahaifiyata zan kira likita."


Da sauri Maryam ta fad'a dakin cikin tausayin Harun.






Duhu ta kuma gani cikin dakin , amma ba tare da ta nemi inda glove yake ba , ta nufi gadon wanda tana iya ganin mutum a kudundune a kai.
"Mama , Mama." Tana ta'ba mahaifiyar Harun tana kiran sunanta .




Wani tashin hankali ne ya bigi zuciyar Maryam tare da tsoro , sakamakon yadda taji tulin kayan Harun ne a kan gadon ba wai mahaifiyar shi ba ce .


Da firgici ta tashi tana shirin fitowa taji an rike ta.

"Innalillahi wa inna'ilaihir raji'un." Maryam ta fad'a sa'ilin da take da tabbacin Harun ne a gabanta



Dauuuuuu ya kunna glove din dakin yayin da yake rike da hannunta yana dariya.


A yadda mamaki ya kasheta ne ya sa ta kasa cewa komai, zuciyar ta tamkar ta fito musamman jin yadda ya fara magana.



"Kin ga yadda shiri na ya yi koh. Ga ki gare ni yau Maryam zaki ga irin san da nake muki , babu kowa a gidan nan daga ni sai ke yawan."
Ya karasa maganar yana fincike mayafin dake jikinta .






"Inna'ilaihir wa inna'ilaihir raji'un Harun , kaji tsoron Allah, na roke ka karka rabani da mutunci na , dan Allah." Cikin matukar kuka da firgici Maryam ta yi magana.






Dariya ya yi yana cewa ,"Haba Maryam, karki zama yarinya mana , wallahi tun lokacin da nake zuwa wajenki Wannan ranar nake jira , ban samu Zainab ba , domin na so mu shiga irin wannan yanayin da ita ,amma shegen yayan ta Mahmud ya hana."....




"Dan Allah Harun kar ka cutar dani, wallahi bazan jure ba."


Ya tunkud'eta ta fad'a kan gadon , haka har mai faruwa ta faru .
Sannan Harun yaji dadin rayuwar shi .










Bayansu su Umar sun shigo suka zauna a falo nan suka fara hira dasu Jafar da baba anje


Ya yin da Nabila ta fito daga wanka tana shiryawa.


Da siririyar murya kanwar Umar Salma , wacce take kusa da yayanta Nasir ta ce ,"Wai ina Nabilan ne to."?






Jafar ya ce ,"Ta na zuwa yanzu. "






Nabila ta karaso cikin falon sanye da wata doguwar riga abaya , wacce taji ado ga launi mai matukar kyau.




Tun daga 'bullowarta Nasir ya kasa jire idanunshi a kanta , har ta karaso ta zauna


"Ya ya Umar har kun zo."? Nabila ta yi maganar da Umar yayin da kuma ta ke kallon Nasir da Salma




" Kanwata mun iso, yau dai ga salma nan." Ya yi maganar yana nunawa Nabila kanwar shi .


Murmushi Nabila ta yi tana cewa, "Eh yayana ka cika alkawari kuma naji dadi."




Nasir ne ya 'ba ta rai yana kallon Umar da cewa ,"Haba Yaya Umar to ni ba za a gabatar dani ba."




Jin hakan ya sa kowa ya kalleshi suna masa Murmushi.


Umar tsaki ya yi yana cewa, "Nabila wannan matumburin kanina ne sunan shi Nasir."


"Haba Yaya Umar matumburi kuma." Nasir yayi maganar yana kallon shi .




Dariya suka kwashe da ita baki dayansu har da Umar yayin da ya ce ,"Ai Nasir din ne ya cika zance wallahi. "






Nasir ya kalli Nabila yana cewa ,"Baki gabatar mana da kanki ba sister. "




Cikin haushi Umar ya Had'e rai yana cewa, "Kun ji ba , baka ji an ce Nabila sunanta ba ,banan surutu bama kasan mene za ka na tambaya ba."


Dariya suka kuma yi wacce tafi ta d'azu , har ita Nabilan ya yin da Nasir yake kallon yadda dariya take mata kyau.




Sannan ta tashi ta nufi dakin girki domin kawo musu abinci , Nasir harda lekenta .






Lomar farko ta Nasir ya ce ,"Gaskiya Nabila kin iya girki sosai , sai ka ce a Australia. "




Wata harara Umar ya watsa masa tare da cewa ,"Su Australian girki suka iya? dan Allah ka yi hakuri ka yi shiru haba."


Dariya suka sake yi a karo na ba adadi
haka suka gama cin abincin cikin farin ciki da walwala .




Bayan su kammala suka tashi tafiya, nan ne Nasir ya karbi number Nabila sannan suka yi sallama. Sun matukar jin dadin wannan ziyara baki dayansu."














Fa'iza a gidan kawarta ta samu guri , inda ta tabbatar wa da kawarta zuwa gobe zata koma garinsu .




Tana tsakar gida a zaune ta yi tagumi , a lokacin ne wannan kawarta ta ta fito daga daki .




yadda ta ga Fa'iza ta yi tagumi tana kallon taurarin dake sama ya sa
kawarta cewa ,"Haba Fa'iza lafiya , kin zauna a farin wata kuma kina kallon sama ."




Fa'iza ta yi ajiyar zuciya tare da cire hannu daga tagumin da ta yi
"Ki dena damun kanki fa dan Allah." Cewar kawarta






Ajiyar zuciya Fa'iza ta kuma yi tana cewa, "A kwai abin da ban fad'a miki ba kawata, kuma nasan yanzu duk wannan ruwan saman da akai ga dare yana kwance a wajen nan."






"Topha waye ke nan." Cewar kawarta




Fa'iza ta fara bata labarin halin da Uncle yahaya yake ciki da kuma yadda ta baro shi .




"To yanzu ya kike so a yi masa Fa'iza, ki rabu dashi kawai , idan ya mutu Allah ya jikanshi , kema shawara nake baki tun kina da lokaci ki tuba wallahi, domin ya zama izina gare ki ga yadda Yahayan nan ya samu kanshi , ki manta da komai ki koma ga Allah domin shi mai gafara ne , kuma ba damuwarki ba ce idan Yahaya ya mutu , nan zasu sa wuta su kona shi , idan kuma yana raye to rayuwa ce zai gani ya more duk yadda Allah ya yi daidai ne ."


Yanayin zazzakar muryarta ya sa Fa'iza ta gamsu da zancen kawartata .






Fa'iza ta ce ,"Haka ne kawata , in sha Allah bana komawa karuwanci domin gobe ma yobe zan koma, Allah ya yafe mana. "




Kawarta ta ce ,"Yawwa Fa'iza ki je kawai ki kwanta saida safe. " Fa'iza ta shige dakinta ta rufo ta kwanta .


















Washe Gari


Hauwa ce zaune tana karyawa a lokacin mahaifin ta lu'utanal ya shigo


"Dady har yau baka samu time ba ni gaskiya yau zanje na ga Surayya."


Kai tsaye Hauwa ta yi maganar




Murmushi ya yi yana cewa, "Ehh gaskiya ne , ban samu lokacin ba kije abinki ki gaida mini da ambassador."




"Thanks dady."




Maryam babu wanda ta sanarwa da abin da ya faru , gashi tana cikin halin rashin lafiya , tun da Harun ya samu abin da yake so bai kuma waiwayarta ba , Allah sarki.
Tuni ya barta har ya samu wata , wacce yake da irin wannan nufi a gunta , amma abun da yake ba shi tsoro yadda babanta yake babban mutum ambassador,


Amma sai ya samu salama da ya yi tunanin ya ta'ba'yar malami ma ya zauna lafiya, bare yaran manya da suke chilling suke shoshalewa tabbas cikin sauki zai samu abin da yake so .














Umar ne bayan ya amsa wata waya da akai kiranshi ya tashi da sauri ya fita , a karshe gudu yasa kamar mai shirin tashi sama , yana sake nanata sakon da aka isar masa cikin wayar .


Jafar da Nabila ne zaune , sai baba anje , bayan sun gama karyawa
"Gaba na fad'uwa yake Yaya Jafar." Nabila ta yi maganar cikin damuwa.












Share and comment...................📚














Gubar Rayuwata⚡🌹
By

Fatima Abdallaah kano
(Autar marubuta)




Editing❌




_________________________________________


Page 39 & 40












Jafar ya kalli kanwar tashi yana cewa," nima haka Nabila, tun jiya da daddare ma kuwa."

Baba anje ta ce ,"Tofa! Ikon Allah, Allah ya sa alheri ne yake tunkaro mu."


Kafin su kai ga cewa Amin suka Umar kamar an wantsiloshi ya shigo yana haki idanunsa sun yi jajir , ga dukkan alamu akwai damuwa.




Duk tashi tsaye su kai kafin kowa ya ce komai yana ta sake saken abin da ya shigar da Umar wannan hali .




"Tantancewar sojin da akai babu shi ne ? Amma hakan ba zai tada hankalin Umar ba ." Jafar yake fada cikin zuciyar shi .






"Bai zo ba."??? Umar ya yi musu tambayar cikin tsananin jiran amsa .




Kallon juna suka yi alamun samm basu gane mene yake nufi ba .






Jafar ya karasa kusa dashi da cewa ," Kwantar da hankalin ka Umar, mene yake faruwa ne ."






Daga can wajen gidan kuwa wani saurayi ne mai jiki wanda ya ginu ya wadatu da farar fata, ya nufo gidan yana d'ingisawa , yayin da yake tafiya cikin isa yana tattare farar jallabiyar dake jikinshi .






"Sahid nake magana akai domin ya dawo Nigeria a daren jiya , kuma duk inda yake zanje na nemo shi." Umar ya fada tare da matukar nuna kiyayyar Sahid a zahiri








Duk wani tashin hankali suka ji ya sake bugar musu zuciya da kiran sunan maci amanarsu


"Assalamu alaikum."




Sautin sallamar da suka ji ke nan wacce ta daskarar dasu a tsaye


Tabbas yau idanunsu sun ga abin mamaki domin kuwa Sahid ne tsaye a gabansu , yayi wani kyau dashi yayi kiba .






Wasu zafafan hawaye suka zubo wa Nabila masu matukar ciwo






Umar ya kasa cewa komai domin zuciyar shi tana ayyana masa mummunan abu a kan Sahid, hakan ya sa yake 'kokarin sarrafa kanshi






"SAHID".


Jafar ya kira sunan shi




," Na'am Jafar, na sani cewa bani da bakin magana a gabanku , amma ba a son raina komai ya faru ba , na yi tafiya Britannia, jiya da na dawo nake jin labarin mutuwar Kalisa. "




'Kuummmm
Wani wawan duka da Umar ya kai masa , ya fadi ya bige da bango, Umar ya taso shi cikin tsananin takaici ya cigaba da dukanshi .




"Me nai maka ne , haka , mutuwar Kalisa ai haka Allah ya tsaro me ya sa za ka doran laifi."


Cewar Sahid ke nan yayin da Umar yake bibbige shi .




"Jafar ka yi masa magana mana ya dena dukana , ina ciwon kafa."




Jafar ya nufi bayan Umar ya ture Umar ya amshi Sahid.


Yadda Sahid ya ganshi a tsaye ya fara ajiyar zuciya da samun 'yancin da ya yi .




Ba tare da ya ankara Jafar ya kwarfe shi ya fadi ya bugu da bango, ya taso shi ya ma'kure shi kana ya fara magana.


"Burinka ya cika ba , Kalisa ta rasu , kuma ka zaune dukiyarmu."


Gummmm


Ya bugashi jikin wani karfe , sai jini .






"Jafar ku bari karku kashe shi mana , ya jigata sosai." Baba anje ta yi maganar tana kokarin kwace Sahid a hannun Jafar.




Jafar bai san lokacin da ya ture baba anje ba , Allah ya sa bafa fadi ba , ya kalleta cikin takaici da tarin hawayen dake idanunshi , yana cewa.






"Shin baki tuna lokacin da Kalisa take kwance ba ? ko kin manta sanda muka tashi aka yi garkuwa da Nabila, kin mance ranar da Kalisa tai Allah wadai dashi , mu bamu jigata ba ne baba ? ko kuwa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login