Showing 15001 words to 18000 words out of 36747 words

Chapter 6 - GUBAR RAYUWATA BY FATIMA ABDALLAHI KANO .txt

Advertisement

mota ta bige su , a sa'ilin da sam ba su ganta ba
hakan ya sa motar ta su ta kwace ta nufi daji
"Innalillahi wa inna'ilaihir raji'un, abin da suke fad'a ke nan


Umar ya bude murfin kofa
da nufin su fi ce a irin wannan gudun da motar take " Kalisa fita , fita kar kiji tsoron komai. "


Amma ina Kalisa duk ta rude rigarta ta makale
" Kai ka fita Umar ka fitaaaaaaa". Kalisa ta karasa maganar a yanayin firgici da ta ga sun kusa dukan wani dutse .




Kauuuu motar ta bigi dutse ta tashi sama , a lokacin suka fado kasa dukkansu , yayin da motar ta kama da wuta tun daga saman sannan ta fad'o kasa .




Kalisa ko shurawa ba tai ba


matukin waccen motar yana ganin haka ta faru kawai ya gudu abin sa ya bar su .Duk da shima yaji rauni .




Cikin mummunan yanayi Umar ya tashi kanshi duk jini , yana tashi ya fad'i kasa yaja jikinshi da kyer ya nufi Kalisa.


Yanayin tashin da ya yi mata ya tabbatar masa fa ta mutu bugu da kari wani karfe da ya gani a cikin gwiwarta ya tsagata .


Wani tashin hankali ne ya ziyarce sa ya kwalla ihu yana kiran sunanta da dukkan muryar da Allah ya hore masa.








Share ,like and comment...........๐Ÿ“š
Gubar Rayuwataโšก๐ŸŒน

By
Fatima Abdallaah kano
( Autar marubuta)






*AUTAR MARUBUTA CE*โœ๐Ÿป๐Ÿ‘ผ๐Ÿป
๐ŸŒน__________๐ŸŒน_________๐ŸŒน__________๐ŸŒน_________๐ŸŒน
_Faduwar wani tashin wani_
_Yau ake yi, gobe sai labarin_
_Burina Rayuwata, rubutuna dan masoyana_
_Cikawa da imani fatana_๐Ÿคฒ๐Ÿผ
<><><๐ŸŒน><><><>๐ŸŒน<><><>๐ŸŒน<><><><>๐ŸŒน<><><><><>๐ŸŒน<><>





Page 21&22

Cikin tsantsar mazantaaka Umar ya yi jarumta ya nemi mutane
Allah ya taimaa ka wasu mutane suka kawo dauki .Wanda har motar asubiti da 'yan sanda suka karaso
Yadda Umar ya ga an dauki Kalisa ya sake tabbatar masa Kalisa ta tafi ta barshi

Timm ya fadi kasa kamar matacce , asubitin cikin gari aka karasa dasu , tare da turasu emergency
Sai ga su Nabila sha'be -sha'be cikin kuka da matukar tashin hankali
suna isa wajen doctor ya fito daga d'akin Umar
da sauri suka tare shi , Jafar ne ya ce "Ya jikin na su likita."?


Baba Anje cikin damuwa ta kallo likita tana sauran amsa


" Ita macen tana ICU room, gaskiya akwai bukatar a yi mata aiki, shi na mijin yana sume , amma nan da anjuma..... "




Likita maganar da yaji a bayansa ne ya sa su duk baba anje saurin juyawa
"Likita ya jikin Kalisa ta." Umar ya fad'a cikin wasu ruwan hawaye dake shirin zubo masa
"Haba malam ka koma ka kwanta , komai zai iya faruwa da kai a wannan yanayi kana bukatar hutu da kulawa."
Dactor ya yi maganar yana kallon Umar
Umar ya karaso gabansu , kawai Nabila ta fashe da kuka ta rungume Jafar


ita ma baba anje duk tausayin Umar ya rufe ta da ganin ciwon dake tare dashi
"Dan Allah yaya Umar ka je ka huta a halin yanzu kaji abin da doctor ya ce ."
Jafar ya yi maganar Nabila kwance a kirjinsa yana rike da hannun Umar.




Umar ya janye hannunshi tare da fara cewa ," Ni bana jin komai Jafar , yanzu kawai Kalisa ce damuwar , domin karku mance akwai bukatar yi mata aiki tun kafin wannan accident din."


Wasu zafafan hawaye suka zubo masa sannan ya ci gaba da cewa ,"Na ga karfe ya huda gwiwar Kalisa, na ji zafi a zuciyata kuma na bayar ta rasu , yanzu kawai lafiya zamu nema mata. "


Baba anje cikin tashin hankali ta ce "Gaskiya ne , innalillahi wa inna'ilaihir raji'un."






Dactor ya ce "Tom gaskiya ciwonta ni bazan iya dubata ba , ku jira kwana biyu likita yana zuwa." Yana gama maganar ya wuce


Ba zato sukaji Umar ya shako sa ,"Kai wanne mara hankali ne , har gobe zamu jira tana cikin wannan yanayin, ina imaninka da tausayinka ka je fa su."?




Likita da ya ji shakar sa ta yi yawa cikin wahala ya fisge ya hankade Umar "Kai mahaukacin ina ne , bari na kira security su fitar da kai." Dactor din ya karasa maganar ya nufi wajen masu gadi




Umar ya ce , "Mu dauki Kalisa mu koma babban asubitin dactor Aisha hakan zai fi."


Nabila ta yi ajiyar zuciya tana kiran sunan Allah .










Mahmud ne ya fito waje yana duban yanayin anguwar yadda tsarinta kullum yake sake burgeshi , duba ga manyan gidaje da sanyin anguwar
hakan ya sa har yau ya kasa komawa gida, har Aminu ya koma , amma shi ba shi da niyya , amma babban dalilin 'kin komawarsa a kan Zainab ne .


Sake bude idanunshi ya yi yana sake kallon abin da ya hango daga gefe ,
kofar gidan wani mutum malam na lado , wanda har almajirai yana dasu


Mahmud ido ya sake zubawa yana kallon ikon Allah






"Mene Harun yake yi anan".
Mahmud ya tambayi kanshi .


Daga bisani lokacin da Harun ya kula da Mahmud ya yi murmushi ya nufo wajensa.


" Malam Mahmud me ake kuma anan." Harun ya tambaya lokacin da ya karaso gaban shi




Mahmud zuciyarshi wata irin tafasa take masa kamar ya kai masa duka, amma ya daure ya kalle shi yana cewa "Mene ka zo yi a wannan anguwar."?


Harun ya sheke da dariya har da tafawa , sannan ya ce ," Mahmud ni wallahi ma dariya kake bani , to mene ya dameka dani, sannan kuma kar ka yi zaton na bar Zainab, Wallahi ban bar ta ba , kai ne kamin shamaki da ita , amma wallahi kasa a ranka da zarar na zama soja wallahi sai na kawar da kai dan na samu Zainab, ka rubuta ka aji ye ni Harun ni ne ajalinka. "




Ajiyar zuciya Mahmud ya yi yana cewa, " Mu yi mu gani , kar kai tunanin dan ka 'bata Asma'u na ya zamo ina jin tsoron ka......."


Mahmud bai karasa maganar ba Harun ya dakatar dashi da cewa ,"Zan yi wulakanci idan nasa kaki , wallahi Mahmud sai na wulakantaka, zaka gani."


Ya wuce ya yi tafiyarsa


Ran Mahmud ya matukar baci sosai , gida ya shiga cikin bacin rai , ya shiga cikin lambu ya kasa tsaye ya kasa zaune , kawai maganar Harun ce take masa yawo , cikin ranshi yake sake nanata zancen
"Tabbas Harun azzalumi ne , zai aikata duk abin da yake so, yanzu mene mafita."?


Mahmud ya dafa kanshi da ya farai masa ciwo " To ko dai na shigar dashi kara. "?
Ya tambayi kanshi , tare da bada amsa kuma
" Gaskiya 'a'a wannan ba shawara ba ce ."
Ya tsuguna kamar mai shirin yin kuka , sannan ya tashi tsaye yana kallon sararin sama yana ajiyar zuciya.


Da sauri ya dawo da kanshi kasa tare da rudewa da farin cikin shawarar da ta zo masa,
da sauri ya shiga cikin gidan ya wuce d'akinshi ya dauko wayarshi dake caji ya zauna a bakin gado .


Sannan ya fara danna wayar yana cewa, "Hhh kwananka ya kare Harun." A daidai lokacin yana kiran numbar Hauwa 'yar gidan lu'utanal


Kamar jira take karaf ta dauki kiran "Ya Mahmud manyan gari kwana biyu." Ta yi maganar cikin yaren turanci





Murmushi Mahmud ya farayi sannan ya ce "Ke dai bari Hauwa ai kasar ta ku ce , wallahi ina cikin tashin hankali."




"Subhanallahi yayana meke damunka." Hauwa tai maganar cikin tsantsar kulawa


Nan take Mahmud ya fara zuba kai tsaye "Wallahi Hauwa Harun ba shi da imani mazunaci ne yadda kika san ba dan halak ba , azzalumi ne , mata yake lalatawa ke har HIV yana d ita ."




Jin ya yi shiru ne ya sa ta kwashe da dariya ๐Ÿ˜‚


"Au dariya zaki mini." Ya yi maganar cikin haushi


Hauwa cikin dariya ta ce ,"Yi hakuri, nasan daga ji haushin sa kake ji , domin nasan da yana kusa da kai sai Allah. To amma ni mene nawa a ciki."




Mahmud ya sanar mata da komai tun daga waye Harun , har zuwa yau din nan , tare da neman alfarma ta sanar d mahaifin ta Lu'utanan


nan Hauwa ita ma ranta ya baci ta kashe waya ta fita falo


Mahaifiyarta Hajjiya Bilkisu na zaune ta fad'a jikinta ta kamata .


"To mene kuma ko sirikin nawa ne." Hajjiyan ta fad'a


Hauwa ta tashi ta bata rai tana cewa "Momy wani ne ..."




Lu"utanan Sadik ya shigo ya tari numfashinta yana cewa "Ya taba ki ko me? fad'a min mamana."




"Dady a cikin sojojin da zaku diba akwai Haruna Sani mu'a zu , irin wannan d'auri ne ya dace dasu." Ta karasa maganar cikin kwalla




Hakan ya sa Lu'utanal hankalinsa ya tashi "Manana waye ne shi mene ya miki."


Nan ta fad'a masa waye Harun kuma da kalar barnar da yake da kuma wacce zai idan ya samu aikin soja .




Nan ita ma Hajjiya Bilkisu tai Allah wadai dashi
yayin da Lu'utanal Sadiq Muhammad ya tabbatar wa Hauwa za ai bincike a kan shi .












"Yawwa dady ina so zanje gidansu Surayya, domin tun da ta dawo daga America bamu had'u ba."


"Okay gidan ambassador koh."? Lu'utanal ya tambaya.


" Eh can dady."




"To ki bari idan na samu lokaci sai mu je tare."


Hauwa ta ce ,"Okay dady."












.A halin yanzu Kalisa ta dawo hayyacinta , doctor Aisha tana iya yinta domin samawa Kalisa lafiya , sai dai ta tabbatar musu fitar da ita ne kawai mafita .
Jafar har gida ya je neman Sahid sai dai tun jiya mahaifinsa ya tabbatar ba ya nan , sannan dukkan SMS din sa basa tafiya .


Ran malam Aminu ya yi matukar baci sosai dana mahaifiyarsa, musamman jin halin da Kalisa ke ciki ma ya tabbatar musu gobe zai zo garin ya ga jikin nata , kuma zai nemo Sahid din in sha Allah, Jafar jikinsa duk ba dadi ya koma asubitin.








Shugaban makaranta ne da Uncle Yahaya da bayis tare da wasu malamai biyu zaune a falonsu Laila.
Gefe guda kuma ga Laila da mahaifiyarta zaune ,ga kuma barrister Adam ran shi bace .




"Dan Allah barrister Adam ka duba wannan lamarin, mun yi kuskure sosai wanda a tarihin DR.DD ba a taba irin sa ba , amma a matsayin mu na masu ilmi mu yi sulhu dan Allah barrister." Shugaban makarantar ya aje maganar cikin tausayin kanshi .




Amma barrister Adam kamar sun sake fama masa ciwo haka ya fara magana.


"A she kuna da ilmin kuka aikata hakan , ni fa na gama magana kawai ku je ku nemi lauyan da zai tsaya muku , dan haka ku fitar mini a gida kawai."




Idanun shugaban makarantar ya ciko da ruwa ya kalli barrister yana cewa, "Wannan makaranta ita ce cigabana rufin asirina wallahi sunan ta zai baci barrister ka taimake ni."




Barrister tsaye ya tashi yana cewa "Ciwon zuciya ne ya sameta yanzu a kan ku , ta ya zan share wannan lamarin kamar ba kaunar ta nake ba ko ina jin tsoron ku."
Uncle Yahaya ya yi kasa da kai cikin jin haushin kansa.








Laila kuwa ganin yadda shugaban nasu Doctor Dauda ya shiga wani yanayi ya sa taji duk tausayinshi ya kamata, cikin sanyin murya Laila ta ce ,"Dady."!




Barrister Adam ya kalleta yayin da duk kowa ya maida hankali gare ta .




"Ni ce aka yi wa komai dady amma abin kai ne ya shafa , bani da wani farin ciki sama da kai, hakan ya sa wannan ciwon dole ya barni tun da ina tare da kai."




Tai ajiyar zuciya tana sake cewa "Ina matukar girmama shugaba kuma wannan tarbiyar ku ce


Duk abin da ya faru da kai wanda ba za ka taba mancewa dashi ba kuma idan ka tuna kanajin ciwonsa to wannan shi ne Gubar Rayuwarka."


Ta aje maganar tana kallon uncle Yahaya ,yayin da ya yi kasa da kanshi .


Mahaifinta ta kalla barrister Adam tana cewa "Dady dacter ba shi da laifi dan Allah ka janye karar."


Kowa ya kalleta cikin mamaki tare da sa'ke-sa'ke kala-kala da kowa ya ke yi a ransa.




Cikin wani Murmushin ta kaici barrister Adam ya ce "Babu ruwanki Laila wannan maganar kar na sake jinta a bakin ki , dole ne na dauki mataki, shin ko baki san wanne kalar jiwo suka jawo miki ba ne , ke ce kawai Allah ya bani kuma duk wanda ya yi kuskure irin wannan dole hankali na ya tashi idan ban dauki mataki ba Laila."




Cikin hawaye Laila ta tashi tsaye tana kallon barrister da dukkan girmamawa ta fara magana.







"Dady ni kaina nasan kana kaunata ,
amma wannan shi ne Gubar Rayuwata domin ba zan taba mancewa ba amma dan Allah dady ka janye karar."




Ta karasa maganar yayin da wasu hawaye suka zubo mata.




Hakan ya sa barrister Adam ya kalli Uncle Yahaya yana cewa .












Gubar Rayuwataโšก๐ŸŒน
By


Fatima Abdallaah kano
(Autar marubuta)














*AUTAR MARUBUTA CE*โœ๐Ÿป๐Ÿ‘ผ๐Ÿป
๐ŸŒน__________๐ŸŒน_________๐ŸŒน__________๐ŸŒน_________๐ŸŒน
_Faduwar wani tashin wani_
_Yau ake yi, gobe sai labarin_
_Burina Rayuwata, rubutuna dan masoyana_
_Cikawa da imani fatana_๐Ÿคฒ๐Ÿผ
<><><๐ŸŒน><><><>๐ŸŒน<><><>๐ŸŒน<><><><>๐ŸŒน<><><><><>๐ŸŒน<><>






Page 23 & 24






"Laila ina kaunar ta." Ya fad'awa Yahaya
sannan ya kalli doctor ya ce "Na janye karar tare da sharadin matukar Laila ta mutu sanadin wannan ciwon to akwai babban tashin hankali."


"Babu abin da zai samu Laila in sha Allah barrister, sannan na yi alkawarin duk in da magani yake zan ke nema mata har ta sami lafiya."


Shugaban ya yi maganar cikin tashin hankali da rawar murya


"Lafiya ta Allah ce kuma ni zan cigaba da nema mata magani , dan haka zaku iya tafiya nasan kun bar d'alubai a makaranta."


Barrister Adam yana gama maganar ya shige ciki .


Sannan suka yi sallama da Hajjiya da Laila suka fito


DR Dauda cikin fusata ya fito ranshi matukar bace suka dauki hanyar makaranta, babu wanda ya ce da kowa komai har suka isa makarantar




Suna shiga shugaba ya sa a fito assembly hakan ya sa wasu malaman mamaki da tunani


Bayan kowa ya fito suma malaman suka hallara


Kowa yana iya ganin 'bacin rai da damuwa a fuskar dactor,


Bai jira wani gabatar da abin da aka saba ba ya fara magana


"Wato duk kun debi zancen Laila kun yada a gari ta fadi ta kamu da ciwo , shi ke nan


ina jan kunnenku da duk yarinyar da wani malami ya ce yana sonta suka fara soyayya zamu dauki mummunan mataki wallahi a kan su."




Ya kalli Uncle Yahaya sannan ya ce " Daga yau mun sallami Yahaya a wannan makaranta, babu wanda zaike kawo mana farmaki ba mu dakatar dashi ba , idan kunne yaji ."


'Dalubai suka karasa masa maganar cikin murya mai karfi


Wani abu ne ya tirnike zuciyar uncle Yahaya da abin da shugaba ya yi masa .
Hakan ya sa bayan ya koma office ya je ya same shi




"Shugaba sallama ta fa kayi gaban d'alubai." Uncle Yahaya ya yi maganar cikin maraici


haka shi ma shugaba ya fara magana "Hukuncin da zan maka ke nan domin haka ne ya dace da kai , kuma kaji ka sani ko albashi ba zan biyaka ba , zan yi amfani dashi na gyara 'barnar da kamin cikin makaranta, fitar mini a office."


Uncle Yahaya ya fita cikin damuwa ya nufi gida .


koda yaje gidan ya ga ya masa duhu kakarshi ta bar masa duniya , babu wani hanyar samun kud'i da yake dashi yanzu, bare ya nemi matan da ya saba , duk yaji duniya ta masa zafi sosai .


Yana cikin wannan yanayin ne sai ga kiran Fa'iza ya shigo masa , ba tare da ya boye yanayin da yake ciki ba ya fara magana da ita .














Da baba anje da Nabila ne zaune a d'akin Kalisa dake asubiti,
a wannan lokacin ne baba ta kร lli Kalisa tana cewa "Yau dai Kalisa na ga jikin naki da sauki Allah ya dorar dashi."




Kalisa cikin zuciyar ta ta ayyana cewa "Kawai dauriya nake baba , amma Allah ne yasan abin da nake ji."


Nabila ce ta ce "Amma aunty Kalisa cikin ba ya ciwo ko."?


Kalisa tai murmushi kawai


Umar da Jafar ne suka shigo a lokacin tare da sallama


" Ina kuka shiga ne haka tun safe."?
Baba anje

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login