Showing 9001 words to 12000 words out of 12964 words
Chapter 4 - TSATSUBA BOOK 8&9 By Abdulaziz Sani .pdf
wannan farar
tsuntsuwa ta sihiri ce take yi musu jagora don zuwa inda hular lamsara take..
×××××× ×××××××××××
ACAN BIRNIN askandariyya kuwa sai bayan tafiyar su yarima
hulkas da tazarar sa a bakwai sannan aka ga wata irin gagarumar iska tana saukowa kasa
daga sama
wadda ta dugunzuma hankalin komai da kowa dake
birnin saboda karfinta
nan fa bishiya suka rinka karyewa suna zubewa kasa rufin gidaje ya rinka kwayewa kasa
ya kama girgiza
ba komai ne ya haddasa wannan masifa ba face iskar
fuka fukan aljanin dake dauke da sarki shardas da bokansa
labarusa
sai da aljanin ya duro kasa bisa tsakiyar gidan sarautar
sarki hulbasu sannan inda ya duro din ya wawake yayi rami
mai zurfi sannan iska ta dauke
nan fa jama a suka kama guje guje da iface iface aka dimauce sosai kai kace
sama da kasa ce zata hade saboda tsananin razanar da
jama ar suka yi sakamakon ganin abubuwan uku wato
ganin wannan shirgegen Aljani da kuma sarki shardas
da bokansa Labarusa
har sarki shardas ya zare takobinsa zai nausa cikin
gidan sarautar sarki hulbasu sai boka labarusa ya
tsaidashi ya dauko madubinsa na tsafi ya nunawa sarki
shardas abin da ya faru a birnin kafin su iso
koda sarki shardas yaga yadda aka kashe gaba dayan
dakarunsa su sadauki murzanu a bayan gari da dukkan
shirin da su yarima hulkas sukayi aka gudu da matarsa
shadila sai ya kamu da tsananin bakin ciki nan take gaba
dayan jikinsa ya kama makyarkyata kamar wanda aka tsoma a cikin ruwan kankara, zuciyarsa
kuwa ta kama tafarfasa
kamar zata kone bai san sa adda ya dakawa bokan nasa
labarusa tsawa ba yace tsayuwar me muke yi a nan
alhalin kana gani makyanmu sun tafi dauko hular
lamsara maza muje mu kure musu gudu mu karkashesu
cikin alamun tsananin tashin hankali da karayar zuciya
boka labarusa yace ai zuwa da wuri yafi zuwa da wurwuri
idan muka ce zamu cigaba da wannan tafiya a wannan
aljani ba zamu taba iya riskar abokan gabarmu ba
kafin su isa inda hular lamsara take, wannan dokin
sihiri da yarima hulkas yake bisa yafi wannan aljani
namu karfin gudu sau arba in dole ne mu samo wani
doki wanda zai iya cin musu, cikin zakuwa sarki
shardas ya ce
to taya zamu iya samo namu dokin da zai cimma
nasu?
Koda jin wannan tambaya sai bokan ya zauna a kasa
dirshan ya karanta wadansu dalasiman tsafi na musamman guda uku ya tofa akan tafin
hannunsa na hagu sannan ya doki kasa da
tafin hannunsa sau uku
faruwar hakan keda wuya sai kasa ta fara girgiza a gabansa
nan take ta dare sai ga wani murgujejen jan doki
ya faso daga cikinta girman wannan doki ya ninka
nasu yarima shardas sau uku
koda ganin wannan doki sai boka labarusa ya mike
tsaye zumbur cikin matukar farinciki ya shafi dokin
sannan ya dubi sarki shardas cikin murmushi yace ya shugabana
ina tabbatar maka da cewa
a cikin sa a iku kacal
wannan doki zai iya cimma su yarima hulkas muna
riskarsu sai mu kashesu mu kwace wannan tsuntsu na
sihiri tayi mana jagora izuwa inda hular lamsara take
koda jin wannan jawabi daga bakin boka labarusa
sai sarki shardas ya daka tsalle ya haye bisa kan jan
Dokin
shi kuwa boka labarusa sai ya bace bat ya sake bayya
akan dokin kuma a gaban sarki shardas ya juyo ya dubeshi
cikin murmushi
yace to sarkin sauri saika sarrafa dokin na gani idan
zaka iya
sarki shardas ya mai dawa boka labarusa murmushi yace
ai kowa a bangarensa sarki ne inda dai batun karfi ne ko jarumtaka nine
zan jagoranceka wannan aikinka ne ba nawa ba
da jin haka sai boka labarusa ya bushe da dariya
Nima Al amin Ahmed Misau na tayasu sannan ya shafi
wuyan dokin kawai sai dokin ya zabura da karfi ya
falfala da azababben gudu na gaban kwatance da al ajabi
saboda karfin gudun dokin har tashi sama yake yana
tsallake gidaje koguna da tsaunika kuma a cikin dakika
biyar kacal ya ke shafe tafiyar sa a goma,
Hakika tsafi gaskiyar maishine in ba tsafin ba babu yadda
za a yi a sami doki mai irin wannan karfin gudun '
''
AL'AMARIN su yarima hulkas kuwa bayan sun shafe tafiyar
wata guda a cikin sa'a bakwai da karfin sihirin tsafi sai
dare ya fara riskesu a cikin wani daji don haka sai
sarki hulbasu ya bayar da shawarar a tsaya a yada zango ba tare da wata gardama ba
hailur dasu yarima hulkas suka amince, nan da nan aka
kafa tantuna sannan kuyangin sarki hulbasu suka
shirya abinci
hailur ya zauna tare da yayansa yarima hulkas da jaruma
siyama da kuma matansa shadila da zalina, shima sarki
hulbasu sai ya zauna tare da matarsa luzuraina da kuma dansa yarima barmas
suna cin abinci
ita kuwa jaruma rulaiya wacce har yanzu babu wanda ya
taba ganin fsukarta ko ya san labarinta face yarima
hulkas sai ta koma can gefe daya ta nisanta da kowa ta
zauna tana cin abincinta
ita kadai a kusa da farin dokinta na sihiri a lokacin da
dokin ke yin kiwo abinsa yana cin ciyawar kasa
koda sarki hulbasu ya hango jaruma rulaiya a can gefe
daya ita kadai sai ya dubi yarima hulkas yace me yasa
waccan abokiyar tafiyar taka har yanzu taki yarda tabude
fuskarta
mu gani kuma me yasa take gudun jama a shin ba zaka bamu labarinta yanzu ba ?
Sa adda yarima hulkas yaji wadannan tambayoyi sai yayi dan guntun murmushi
sannan yace ba don waccen bakuwar ba da tuni na
dade da shekewa barzahu ta ceci raina a baya don haka
tana bina bashi
labarinta yana da yawa gami da ban tausayi da al ajabi kuyi hakuri sai mun sami
lokaci isashshe
caraf sai hailur ya tari numfashin yarima hulkas yace
ai kuwa ni indai haka ne bai kamata ka barta ta rinka
kadaita haka ba
tashi kaje wurinta ka debe mata kewa saboda na ga alamar
cewa kamar tana cikin damuwa da tunani tunda tama
kasa cin abincin sosai
koda jin haka sai yarima hulkas ya mike tsaye cikin murna
ya tafi wajen jaruma rulaiya,
da ganin haka sai yarima barmas ya dubi jaruma siyama yace
kawata idan bazaki damu ba nima ina son nayi wata
magana mai muhimmanci tare dake
koda jin haka sai jaruma siyama ta murtuke fuskarta ta daka
masa harara amma tana hada idanu da hilairu sai ta mike
tsaye ta kama hannun yarima barmas taja shi
izuwa gefe daya suka kama hira cikin raha da nishadi
lokacin da yarima hulkas ya isa inda jaruma rulaiya ke zaune
sai ya isketa cikin tunani mai zurfi don haka sai da ya
kira sunanta sannan tasan da zuwansa, yarima hulkas ya dubeta cikin alamun
damuwa ya ce yake jarumar mata kuma sarauniyar kyawawa
me ya faru naga kinyi tagumi kina tunani mai zurfi haka
koda jin haka sai rulaiya tayi doguwar ajiyar
zuciya sannan ta dubeshi cikin alamun fargaba ta
ce
yakai hulkas kayi sani cewa tun da muka yada zango a nan
wajen naji zuciyata na bugawa da karfi ina ji a jikina
cewar akwai wani mugun abu dake shirin samunmu
lallai zamanmu anan yana da matukar hadari kasani
cewa dama ina da niyyar baka irin horon yakina a cikin wannan
tafiya tamu saboda na san cewa zai amfaneka
don haka yanzu saika mike tsaye mu fara, tana gama
fadin haka sai ta mike tsaye ta zare takobinta guda biyu
shima yarima hulkas sai ya mike tsaye ya zare tasa takobin
nan take suka ruguntsume da azababben yaki mai
tsanani
koda su sarki hulbasu suka ga jaruma rulaiya na kaiwa
yarima hulkas mugayen hare hare tana neman hallakardashi har ma ta dan yankeshi
kadan a damtsen hannunsa na hagu sai gaba dayansu
suka yunkura zasu afkawa jaruma rulaiya amma sai jaruma
siyama tayi tafi tasha
gabansu tace kada ku shiga wannan yakin domin baso take ta hallaka shi ba yaki take
koya masa
kuyi tunani mana inda kasheshi take son yi ai ba za ta
ceci rayuwarsa ba a baya ba kuma idan a yanzun take son kasheshi gaba dayanmu
babu wanda ya isa ya hanata don karfin damtsenta
da iya yakinta da kuma karfin sihirinta domin karfin
tasirin sihirin tsafinta ya ninka namu sau goma
gama fadin haka keda wuya sai suka fara ganin abin
al ajabi domin nan take suka ga yarima hulkas ya fara iya
duk irin yanayin yakinta sai gashi yana iya kare hare haren
ta kuma yana mai da martani sai da suka shafe rabin sa'a
suna bakin gumurzu har ma yarima hulkas ya sami nasarar dukan kirjin jaruma
rulaiya
ta fadi kasa cikin hanzari ya ruga gareta ya bata hannunsa
ta kama ya tasheta tsaye sannan ya
dubeta cikin damuwa yace
Ki gafarceni yake jarumai jarumai koda jin haka, sai jaruma rulaiya tayi murmushi tace
aini farinciki na yi da naga yanzu ka sami nasarar kani
kas
tabbas ka sami horon yaki irin nawa, gama fadin
hakan keda wuya sai jaruma rulaiya ta dafe kanta
ta kwalla ihu kuma ta sulale kasa sumammiya
al amarin da ya razana kowa ke nan a wajen aka rugo
izwa kanta sa adda yarima hulkas ya rungumeta a kirjinsa
cikin dimauta
cikin hanzari aka yayyafa mata ruwa nan da nan kuwa
ta farfado cikin tsananin mamaki da kaduwa yarima
hulkas ya dubeta yace menene ya sameki kikayi ihu
kika fadi kasa sumammiya alhalin kina tsaye cikin
koshin lafiya
Jaruma rulaiya tace '' A duk sa adda wannan Aljani wanda
ya raineni yayi mini wahayi haka nake kasancewa
barci ne yake daukata mai nauyi shiyasa kaga kamar na suma
aljani Arwasul masadul ya sanar dani cewa abokan gabarmu
sarki shardas zasu iso nan ya riskemu a cikin sa a biyu
kacal
mai zuwa don haka ya gargadeni da mu hanzarta a
cigaba da tafiya kuma yayi mini albishir cewa zamu
iya isa kogon da hular lamsara take a cikin sa a biyun
koda jin wannan batu sai kowa ya mike tsaye zumbur
aka shiga shirin gaggawa aka kwashe komai aka
hau dawakai aka kama tsala azababben gudu a cikin
daren wannan farin tsuntsu na sihiri nayi musu jagora
a sama a cikin iska
dokin jaruma rulaiya ne akan gaba yana dauke da mutum uku
wato ita kanta jaruma
rulaiya yarima hulkas da jaruma siyama
a cikin sa a biyu cif suka iso bakin wani katon kogon
dutse wanda gaba daya bayansa sama da kasansa
a shafe yake babu alamar kofar shiga, Al amin Ahmed
Misau, kowa dake wajan sai da yayi iya kokarinsa
wajan gano inda kofar shiga take amma yarima hulkas na
dafa wani wuri a jikin dutsen sai kofa ta bude suka yi arba
da cikin kogon wanda yake da tsananin haske yadda ko allura ce ta fadi za a
iya ganinta
babu komai a cikin kogon dutsen face kayan yaki iri iri
masu tsohon tarihi na manyan sarakuna da manyan
jaruman da suka shude
nan take suka hango hular lamsara a can sama bisa kan wani dutse mai tudu
kowai sai jaruma rulaiya ta dubi yarima hulkas ta ce maza
kaje ka dauko waccen hula ta lamsara anyi tane domin kai kadai kuma kai kadai ne zaka
iya daukota a nan cikinmu
Saikuma Jarumi Al amin Ahmed Misau, Amma bari na
barshi yauko saboda naci girma hmm, koda gama
fadin hakan sai yarima hulkas ya ruga da gudu ya je ya
dauko hular lamsara yana daukowa kuwa
sai kofar gogon dutsen ta fara rufe kanta, A guje yarima ya
fito yana fitowa sai ya daga hular sama da nufin ya sanyata
a kansa amma sai yaji an doki kirjinsa
saboda karfin dukan bai san sa adda ya saki hular
lamsara tayi sama ta fada kan wani tsauni mai tsawon
gaske ta kama gangarawa a lokacin da shi kuma yai
sama izuwa kan tsaunin ya fado kasa magashiyan yana
aman jini yana daga kansa sama sai yaga sarki shardas
tsaye a kansa yana yi masa murmushin mugunta boka labarusa na tsaye bisa wani jan doki a
gefe guda
kawai sai sarki shardas ya yunkura da nufin ya ruga inda hular
lamsara take ya dauketa ya sanyata amma sai yaji an daure kafafuwansa
da hannayansa da wata tufkekiyar sarkar karfe ta sihiri
ba wani ne ya daure hannun sarki shardas ba face bokansa
boka labarusa cikin tsananin mamaki da kaduwa sarki shardas ya dubi boka
labarusa yace saboda me zaka ci amanata ka hanani
daukar hular lamsara?
Koda jin wannan batu sai boka labarusa ya bushe da
dariyar mugunta sannan ya murtuke fuskarsa yace
dashi
tabbas sai yaune na tabbatar da cewa kai wawa ne mara basira
kana zaton tsawon
shekarun danake yi maka bauta inayi ne saboda kaunarka
idan har ka dauki haka to kayi babban kuskure
masu iya magana sunce so sone amma san kai yafi kowanne, Aski yazo gaban goshi
domin A halin yanzu littafi ya kusan karewa, ina yi maka
bauta ne saboda zuwan wannan rana da zan mallaki
hular lamsara saboda nasan cewa idan na mallaketa tamkar
na mallaki duniyar nan ne gaba dayanta, dukkanin
sarakunan duniya sai sun dawo karkashin ikona, duk
wata dukiya ta duniya sai ta zama tawa ni kadai a bincike
na nagano cewa kaine kadai sarkin da zanjingina
dashi na tsorata dukkanin bokaye da sarakunan duniya
tunanin mallakar hular lamsara tunda an san kana
nemanta kuma kowa yana tsoronka, koda boka labarusa yazo nan a zancensa
sai sarki shardas ya kuma wani gagarumin uban ihu cikin
bakin ciki ya dubi boka labarusa yace in dai don hular
lamsara ka daureni da wannan sarkar sihiri to ina umartar
ka da ka gaggauta kwanceni domin na yaki makiyana gasu
tsaye a gabana kada su kashe ni a banza na rantse
da darajar iyayena nabar maka hular lamsara bana bukatar
ta
ni dai ka barni na tsare mutuncina da rayuwata, koda jin
wannan batu sai boka labarusa ya bushe da dariyar mugunta
lokaci guda ya murtuke fuskarsa yace haba shardas ta
yaya kake zaton cewa bera zai taba yarda yayi
zumunci da mage ? Kada ka manta cewa sama da
shekaru talatin bayanake tare da kai tun kana matashi babu
wanda ya san
halinka sama dani yaudara cin amana da rashin imani duk takenka ne
shin a rayuwarka ta duniya mata nawa ka mayar gwagware ? Shin a rayuwarka ta duniya
yayaye nawa ka mayar marayu ? Al amin Ahmed Misau
Nayi imanin cewa baka san adadinsu ba
ai dama ance rana da yawa ta barawo rana daya tak ta
mai kaya
koda gama fadin haka sai boka labarusa ya dubi sarki
hulbasu yace ga wanda ya sa ka yanka danka da hannunka
kuma yasa bakin ciki ya kashe ubanka sai ka dauki fansa akansa boka labarusa ya sake
duban jaruma rulaiya wacce har a sannan fuskarta a rufe
take cikin bakin kyalle yace da ita ke kuma ga wanda ya
kashe ubanki ya mallake dukiyarsa gaba daya ya janyo kika girma a inda babu
mutane sai ki dauki fansa kema ni bani da wata alaka daku
burina kwai na mallaki duniya koda gama fadin hakan
sai boka labarusa ya tashi sama kamar tsuntsu ya dira
a can sama bisa wannan tsauni ya nufi inda hular lamsara
take koda ganin haka sai jaruma rulaiya ta dubi yarima
hulkas tace idan muka bar wancan bokan ya mallaki hular
lamsara zalunci zai shimfida a doron kasa, muma sai mun
zama bayinsa
ni zanje na yakeshi na kawai dashi kai da jaruma siyama
da sarki hulbasu ku yiwa sarki shardas irin kisan gillar da kuke son yi ku daukar mana
fansar zaluntarmu da yayi koda gama fadin hakan sai jaruma rulaiya ta cire bakin
kyallen dake fuskarta su jaruma siyama sukayi arba da
tsananin Kyawunta
sai suka cika da tsananin mamaki kawai sai suka ga jaruma
rulaiya ta daka tsalle sama tamkar daga cikin baka aka
harbota ta dira akan wannan tsauni ta nufi inda boka
labarusa yake yarima hulkas, jaruma siyama sarki hulbasu suka tunkari inda sarki shardas yake
daure a cikin sarkar
sihiri koda yaga sun durfafo shi sai ya kama kyalkyala dariya
al amarin da yayi matukar basu mamaki kenan sarki hulbasu
ya dubeshi yace saboda me kake dariya alhalin ka san
cewa KISAN GILLAH zamuyi maka domin mu huce takaicin
bakin cikin da ka kunsa mana, al amin Ahmed Misau
Sarki shardas yayi murmushi yace ina yin wannan dariya ne
saboda dalilai guda biyu rak !
Dalilin farko shine, ba zaku iya kasheni ba inda bana daure
cikin wannan sarkar tsafi, kunga kenan ku ba jarumai bane
nikuwa na zalunceku ne saboda nafi karfinku, babu
yadda zakuyi dani don haka zan mutu ina mai farin ciki
da alfaharin na mutu a jarumi abin tsoro, dalili na biyu
kuma da yasa nake yi muku dariya shine ko kun
kasheni yanzu kamar kun kashe maciji ne baku sare
kansa ba
saboda wannan bokan nawa boka labarusa idan ya mallaki
hular lamsara sai yafini barna da zalunci a doron kasa kun
ga kenan a karshe kuma kuma rayuwarku zata
kasance a cikin bautarsa da takaicin zaluncinsa wata kila duk ya karkasheku
sarki shardas na gama wannan jawabi sai ya cigaba
da kyalkyala dariyarsa
Yana cikin dariyar ne sarki hulbasu ya zare takobinsa ya kafta masa
mummunan sara a kaurin kafarsa ta hagu nan take kafar
ta guntule jini yai feshi da tsartuwa sarki shardas ya kwarara uban ihu sakamakontsananin zafi
da zugin da ya
ratsa sassan jikinsa koda ganin haka sai shima yarima
hulkas ya zare tasa takobin ya sare kaurin kafar
sarki shardas ta dama wato suka mayar dashi gurgu.
A dai dai wannan lokaci ne suka jiyo karafkiyar karafa
a can saman wannan tsauni suka