Showing 18001 words to 21000 words out of 26260 words

Chapter 7 - Zazzafan Rabo Part 1 Complete Hausa Novel By Aisha Umar Indabawa.docx

waremin nasake sosai ,idan yafita suyita hirarsu ko suyi kallo ,dadewar da tayine mutane suka ankara da ita har akafarayin sallama da ita to Amman ita abin baya gabanta sbd tasan abun baxai ta6a yiwuwaba gani takeyi kamar baxata ta6a aure a rayuwartaba sbd irin matsalolin da akesamu a aurenta nata.

Suna zaune da magariba wani yaro yayi sallama yashigo ya gaishesu suka amsa ,aunty tace muhusin yaya akayi ,yaya nazir ne ya aikoni wai ana kiran bakuwar gidan nan ,nayi saurin cewa ni yace eh ,nace kace banananan anti tace a a kace tana xuwa ,yafita dan sanar da aiken da akayimasa ,nace aunty ya zakiyimin hk ,shikenan Salwa sai akace kindaina kula kowa a duniya ai ba,a hk ,bakisan kowaye mijinkiba sai Allah ,ba haka bane aunty kinsan matsalata banasan ayimin tanbarin wani sunan banda Wanda akayimin ,tace ai komai daga Allah ne kiyi hkr in Allah yayarda komai yaxo 'karshe to shikenan aunty ,nadauki mayafina nayi waje gabana yayi mugun faduwa sainaga kamar ya Abdul sai danakarasa kusa dashi sai naga ashe irin tsayiwarsace kawai ,nagaisheshi ya amsamin da dariyarsa ,toya gida Salwa Allah yasa bantakura mikiba ,nace babu komai ya gyara tsayiwarsa ina fatan kowa lfy nace lfy lau ,nidai sunana nazir kuma ni dan unguwarnanne ga gidanmu can ,yanunamin wani hadaden gida ,kuma nine babba inadakanne Bihar hudu mata saimu biyu nida kanina nidai asalinmu"yan katsinane gaba da baya aikine yakawo iyayena nan ,sai inda nake aiki a kanfanin dan gwate kingane nadaga masa kaina ,kumani da gaske nakeyi babu wasa dan ina ganinki naji kawai kece matar tawa nadanyi murmushi shima yatayani ,to "yan matana meye ra,ayinki a kaina,nace to kabani lkc ba yanxo zanbaka amsaba babu damuwa Salwa to bara nawuce dan naji anfara kiran sallah ,nace to Allah yabamu alkairi yace amin Salwa nawuce gida shima yatafi ,bamuyi wata mgn da aunty khadijaba har saida mukayi sallar isha,i naci abinci dan ita da mijinta sukeci ,nake gayamata duk yadda mukayi dashi,tace gaskiya kinyi sa a dan nazir mutumin arzikine gasan addini sai dai ubangiji yasa albarka nidai dariya kawai nayi ,tace da alama dai yayi nasara tunda naga kina dariya nace nidai banceba tace zakicene wataran duk sukasa dariya ,nidai yaya yana dawowa najege daki danna barsu susake dan nasan aunty khadija saita gayamasa ,nidai tun safe natashi nayi duk abinda xanyi harya fice becemin komaiba nima kuma bangayamasaba a hirar da mukayi da Aunty ne takegayamin irin murnar da yayi nidai murmushi kawai nayi ,yau kuma sai bayan isha,i yaxo da kamar karna fita saida aunty tayi mgn ,tundaga nesa nahangoshi gaskiya nidai akace na aureshi nayi sa,a dan gaskiya irin mijin da nakesone gakyau ga iya gayu Allah yatabbatar mana da alkairinsa ,ya'karaso to ginbiya kinkasa k'arasowa to ni gani a gabanki sai yadda kikayi dani nayi murmushi ,nace kai kuwa da abin dariya kake ,nagaisheshi ya amsa nanfa muka dinga hira ,haryakecemin wai ummansa tana gaisheni nace to ina amsawa,to Salwa gani gareki meye sakamakona ,kaikuwa da gaggawa kake ainace maka kabani lkc ,to bani tarihinki tunda kinji nawa to aini kasan unguwarmu kuma tunda kasan yaya aika sanni yace hk me to yanxo mekike karanta naji yayanmu yace kina karatu a B u K tace hakane (social science) yace dakyau Allah yabada sa,a nace amin mukayi sallama nashigeyaa gida ,tunda nashiga gida nake tunanin yadda mukayi dashi kawai nakeyi ,nidai addu,a kawai xandingayi Allah yasa munafikin da yasaba 6atamin aure Allah karyabasu ikon 6atamin wannan domin nasa raina da samun masoyin arziki ,wasa wasa soyayya mekarfi tashiga tsakaninmu da nazir yadda wani bayasan 6atawa dan uwarsa rai,duk "yan gidansu sungama sanina duk da ina gidan ya yazid kowa cewa yakeyi nayi sa,ar samun yaron arxiki sai dai Allah yasa ayi a sa,a yau dai nashiya tunsafe nace sai wajen ummana ,aunty yadinga magiyar naxauna kodai wani abun yayimin nace Allah babu komai nafara hada kayana tadinga magiya.

Kuyi hkr da wannan kunsan typing da wahala

๐Ÿ’˜๐Ÿ’˜๐Ÿ’˜๐Ÿ’˜ZAZZAFAN RABO๐Ÿ’ž๐Ÿ’ž๐Ÿ’ž

๐Ÿ’ซ๐Ÿ’ซ๐Ÿ’ซAisha Umar Indabawa๐Ÿ’ซ๐Ÿ’ซ๐Ÿ’ซ

๐ŸŒŸ๐ŸŒŸ๐ŸŒŸmarubuciyar littafin Meka Maidani๐ŸŒŸ๐ŸŒŸ๐ŸŒŸ

๐Ÿ“ฑtyping๐Ÿ“ฑ

๐Ÿฆšpage 1๏ธโƒฃ4๏ธโƒฃ๐Ÿฆš

Kuyi hkr masoyana kunsan typing da wuya ga hidimar gida,

Ina barar addu,ar ku ,d'an makotanmune yarasu yaro meshiga rai Allah yajikan Ahmad yayi masa rahma ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜ญ

***kiyi hkr naje gida nakwana biyu ,Amman xandawo insha Allahu ,tace saida kikasabamin da xaman mutum biyu sannan kice za kitafi ,nace kiyi hkr zandawo mukayi sallama nafito duk fuskarta babu dadi sbd yaya sai dare yake dawowa ,a bakin layinmu aka sauke ni,nikuma nak'arasa da kafata cikin layinmu ,a dai dai get din gidansu Na hangoshi a tsakiyar mutane sun shinfida babban cafet da alama yana cikin farin ciki ,nace to Allah yatemakeni nawuce lfy ,dan nasan halin mutumina ,Na sunkuyar da kaina banasan yaganni asheyaganni ,harna kusa wucewa yace Salwa andawo daga yawan tazubar dinne ,nace la yaya bangankabane ina wuni nayi saurin tsugunawa ,anje gidan amare aci naman kaji ,dan Allah Salwa kirage kwadayi dasan abin duniya ,kamar Na nutse dan kunya yadda naga sauran abokan nasa sunsa dariya ,na sunkuyar da kaina nawuce ina takaicin abinda yakeyi min a gaban mutane shi gani yakeyi kamar burgewa yakeyi ,nadawo da farin cikina Amman tun kafin nak'arasa gida ya wargazamin komai ,Allah kadinga sakamin akan irin wulak'ancin da yakeyi min tunda nidai nasan babu abinda nakeyi masa ,bazan iya fada dashi ba ,dan umma ma gani takeyi rashin kunya nakeyi masa dan batasan abinda yakeyiminba ne sai dai Allah yayimin maganinsa shi kuwa Abdul bayan ta wuce dariya yasa ,wani abokinsu yace gaskiya Abdul abinda kakeyi bekamataba ,kai bakada wani abinyi saidai kadinga kunyata yarinyar mutane ,idan Santa kakeyi kafito mana kagayamata ,Amman abinfa yayi yawa ,in kuma bakaso to ni inaciki Santa nakeyi da gaske bawasaba ,yace to ni ina ruwana ,aini koda kyau ta akabani Salwa babu abinda zanyi da ita ,idan har kaga nakar6i Salwa to saidai idan a aljanna akace za,akasa ko mommy tace idan ban auretaba zata tsinemin albarka ko tace babuni babu ita to aguje zanyarda ,Amman "yar aikin gidana tafita matsayi da mutunci tunda ita bata wulak'anta kantaba ,Amman kai idan kanaso zanshegema gaba Amman duk abinda yabiyo baya babu ruwana,Na tabbar da idan ummanka taji babu abinda zai hana ta zazzabgama mari tace bakada hankali ,duk sauran abokan sukasa dariya ,wani daga cikinsu mesuna amir yace gaskiya katsani yarinyar nan aiko cikin shege tayi iya horon da za,ayi mata kenan ,idan nice yarinyar sainayi maganinka tunda kaine munafikin ta ,yanxo tasamu miji na kece raini Amman kayi mata bakinciki ,yace kodai kaima kanacikine amir ,aini idan inaso munafincinka bazaiyi tasiriba a kaina ba dan dai khairiyya tashigemin gabane ,dana shiga kuma sati biyu za asa agama komai tunkafin irinku munafikai kushiga maganar ,to tunda kun maidani munafiki abar maganar nabarku da halinku sukasa dariya wai yaji tsoro, suka shiga wata hirar,shi kuwa habu direba banda dariya babu abinda yakeyi yaji mugunta suna hada ido da Abdul saiya gintse fuska kamar ba shine yakeyin dariyarba ,yace kai zonan yaxo ya tsuguna kamar xaiyimasa sujjada ,yakama kunnensa yace banhanaka irin wannan munafinciba ,to shiga gida kace da nana me aiki takawo mana lemo da cake da wannan zaman banzan da mukeyi mundan tauna yashige gidan da saurin sa ,sukace gaskiya Abdul wannan direban naku yanada abin dariya ,kasan kwanaki a titin gidan gwanna naganshi yatsayarda wata yarinya ita kuma daga ganinsa a babbar mota sa kankanba takeyi masa,shi kuma sai dashe uban baki yakeyi ,kai idan kaga abin saiya baka dariya ,lokacin kuma yaci wata arniyar shadda wannan takance da wannan telan ya6atamaka wadda ko sawa bakayiba yace naganeta ,yace ranar kuma yayi sa,a a motar megida take kaga abin yayimasa dai dai kenan ,Abdul yace aishi haka yake ,ai ina ganin Na mema masa auren Salwa koda zankashe miliyoyin kudine tunda bawata tsada zatayiba ,wani ya kalleshi yace yanzo natabbarda bakada hankali Abdul sai kace "yarka ,to ko da " yarkace aika tanbayi ta,ayinta "yan wajen sukasa dariya ,lallai Abdul ka6atawa Ammar rai shida baya magana saida kak'ular dashi yayi magana,in Allah yayarda bakada mata sai Salwa ,kafin yak'arasa yakifamasa mari ,Allah ya isa tsakanina dakai kuma hakan bazai ta6a kasancewaba mugu kawai me mugun baki kagani a kanka .

Yace aini idan an bani inaso tunda duk yadda akesan mace takai ,sai dai tanada mahassada a gari masu kashemata aure ,kaidinma wada kakeyi abokina dakasan abinda tayi daka gujemata ,kometa ni ina Santa ai akwai kaddarar mutum kuma indai Allah yarubuta babu Wanda ya isa yahana ,shima habu direban dan naga 'katan 'kauyene shiya kuma rufamata asiri xaiyi wani yace aiko me Salwa tayi bazata rasa me aurentaba wlh ,dan Allah to abar maganar munafincin yarinyarfa mukeyi kenan ,saikace kannen uwarta munafikai kawai ,yadauki mukullin motarsa yafice da gudu sunsan halinsa bayasan irin wannan abun ,danshi ko maganar budurwa bayaso bare yace ya nasan wata Ammar kenan sai dai idan sunayi yace Allah yashiryeku tunkafin kutafasa zaku kone ,ita kuwa salwa da bakinciki tashiga gidan ko ummanta saida tagane a fuskarta tadaiyimata shirune ,itadai Allah yasa bada matar yayan natasukayiba ,dan bata kaunar ace itace ta turata danta takura musu ,tagaida umman tata tace kowa lfy sai a lokacin hankalinta ya kwanta ,a hankali kuma tasaki ranta sukaci gabada da hirarsu da salwan ,mamaki sosai salwa tadingayi dan kullun umman tata cikin yimata fada take akan taki yin hankali ,sai da salwan tayi tunani sosai sannan tagane sakin fuskar umman tata ,zuwan nazir ne ,to ko dai itama Allah ya amshi addu,ar da tadade tanayine .

Sai da akayi kiran sallar magariba sannan tamik'e danyin haramar sallah ,saida aka idar sannan umma tace to Salwa ga abincinan saiki zuba kici ,tace to umma ,tamik'e dan taduba taga umman metadafa ,sai taga tuwan shinkafa da miyar zogale ,miyar sai kanshi takeyi dan tayi niyar tabari sai tayi sallar isha sannan taci ,Amman budewar da tayi taji baxata iyaba tazuba tafito tsakargida hartanacewa da umma yaushe tayi wannan girkin batasani ba ,kinata aikin bacci ai bazaki saniba itadai tasa dariya ,abbanta bayadawowa sai anyi sallar isha,i ita kanta taga tsabar farincikin da yanuna da yaganta ,yace kaga "yan Hutu har gidan yayan naki ya isheki ,nidai nayi dariya nace sannu da zuwa Abba ,yace saukar yaushe nace da safe ,nace dagyar suka barni nadawo ,yace ai kuwa bakomawa zakiyiba ,bakiga yadda Abdul yake mitar tafiyarkiba ,wai kintafi bakya duba littattafanki gashi yajin aikin yayi nisa kuma kuna komawa xaku fara jarabawa nidai nayi shiru,yace Salwa iyayen yaronnan da kikasamu a gidan yayanki ,sunsameni a kasuwa wai sudai da gaike sukeyi tunda yaron da gaske yakeyi ,wai yamatsamusu basasan a dauki wani lokaciba nidainarufe fuska sbd zancen banawabane ,munacikinyin maganar saiga ya Abdul nan yashigo banso Abba yagayamasaba sainaga yawani washe baki yace Allah yasanya alkairi yasa ayi damu ,gaskiya Abba a wannan lokacin kar,a dauko wani dogon lokaci sbd abinda yake faruwa ,yace insha Allah hakan bazaifaruba ,yace Allah yasa.

Kamar da wasa abu ya kankama angama komai sunkawo kudin aurensu dansu a yadda sukeso Abba yasa musu sati biyu sai dai k'arfin badayaba ,dole suka hkr akasa wata uku shima ba,asan ran angonba .

Iya kuwa Salwa gdy kawai takeyiwa Allah shi kuwa Abdul duk ba,nasan ransaba ,sbd yanacewa Salwa bata cancanci samun yaro kamar nazirba sbd nutsuwarsa dasan addininsa shi kuwa yafisan tasamu babban mutum Wanda yayi sa,a da babanta koma yafi abban nata ,sabida acewarsa tazubar da mutuncinta da kimarta a idon wadanda sukasan wacece salwan saidai hakan Allah yanufa ,shida da yazowa da Abba akan mgnar habu direba tunda shima yafinkanci dan duniyar kansa sai kuma Abban yafara xuwar masa da mgnar shi kuma yanajin kunyar abban bare yayi bayani ,to Amman duk da hk yasan yadda zaiyi ,shi wlh gabadaya yatsani salwan koyace ba ita yatsanaba halinta yatsana ,danshi baya shiri da marakamunkai Salwa batasamu komawa gidan yayantaba sbd komawa makaranta da sukayi ,shi kuwa Abdul yanatasan suhadu da Salwa dan yayimata tatas to bashida hanya sai a school ,bayan sun fito saga laccar sukasamu wata bakin bishiya suka xauna daman kawai kujeru a wajen ,fauxee yace Salwa nifa yinwa nakeyi dan bankaryaba Amman kinga dan guzirina a jaka ,tazuge jakar tafito da cake da kaza da lemon roba tace to bismillah Salwa,kinga nifa nakarya ta harareni tace ai yanzo ya zazzage tunda yaufa mun wahala ,ta dauki cake takai bakinta tace kinsan kuwa rahma ta haihu ,nace dan Allah me akasamu tace "yan biyu duk maxa mukace to Allah yaraya mata mukace amin a tare ,takai hannunta kan kazar kenan ta dauki cinya kenan takai bakinta suka hada ido dashi ,yayimata alamar tazo da hannunsa ,ita kuwa tunda suka hada ido dashi gabanta yafadi ,banda innalillahi babu abinda take fada

๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒนZAZZAFAN RABO๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน

๐Ÿ’ซ๐Ÿ’ซ๐Ÿ’ซAisha Umar Indabawa๐Ÿ’ซ๐Ÿ’ซ๐Ÿ’ซ

๐ŸŒŸ๐ŸŒŸ๐ŸŒŸMarubuciyar littafin Meka Maidani๐ŸŒŸ๐ŸŒŸ๐ŸŒŸ

๐Ÿ“ฑtyping๐Ÿ“ฑ

๐Ÿฆšpage1๏ธโƒฃ5๏ธโƒฃ๐Ÿฆš

______

๐Ÿ…™๏ธŽ๐—ฎ๐—ฟ๐˜‚๐—บ๐—ฎ๐—ถ ๐Ÿ…ฆ๏ธŽ๐—ฟ๐—ถ๐˜๐—ฒ๐—ฟ๐˜€ ๐Ÿ…๏ธŽ๐˜€๐˜€๐—ผ๐—ฐ๐—ถ๐—ฎ๐˜๐—ฒ๐—ฑ๐Ÿ“š๐Ÿ–Š

https://www.facebook.com/101679598253281/posts/101680068253234/?app=fbl

_Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa illmantarwa, nishadantar tare da fadakarwa da jama'a bisa harshen hausa_

๐Ÿ’ž๐Ÿ’ž๐Ÿ’žina godiya masoyan wannan littafin ina matukar jin dadin yadda kuke kaunarsa ๐Ÿ’ž๐Ÿ’ž๐Ÿ’ž

Tak'arasa gabansa tace gani Mlm,yace Salwa babu gaisuwa tayi saurin sunkuyar da kanta,tace daman ina shirin gaishekan ne sai kayi maganar ,duk yafiskanci a tsorace take ,yayi fuska kinayin karatun kuwa ,kokuwa auren kikasa a gaba ,ita dai tayi masashiru ,yace Ashe har yanzo salwa bakidaina kwadayiba wato kedai Allah yazuba miki kwadayin naman kaza ko ,shi yasa a koda yaushe kike likewa "ya" yan manya ko to kishiga tai tayinki ,wuce kibani waje sai wata murna kikeyi zaki aure dan manyako ,to idan bakiyi wasaba duk saina gayamasa duk tantirancin da kikayi ,kinga shima saiya fasa ,saina daukeki idan nayi aure kidinga yiwa matata wanke -wanke da shara da rainon yara wuce kibani waje munafika ,nakasa daga k'afata sbd tsabar kunya ,dan a bayan wasu samari yayimin yasake daga murya yace wuce nace ballagaza ,da kukana nayi hanyar get dan ko jakata bantsaya daukaba kuka nakeyi sosai ,da dariya ya wuce yace shegiyar yarinya idan ta kalli mutum da idonta sai yaji wani abun a ransa tunda kintafi wlh test zanyi me muhimmanci daman basan karatun naki nakeyi ba,ya wuce office dinsa da sauri ,ya dauki sauran tarkacensa yayi cikin holl din,fauxee tana bakin bishiya taga wucewar Salwa da sauri kafin tayi yinkurin binta harta fice ,tace tabdijan wlh Salwa idan zaki dinga biyewa Mlm Abdul kullum sai kintafi gida ,danshi hakan yakeso ,tanacikin zancen taji sauran dalibai sunagudun shigacikin holl din ,itama da gudunta tak'arasa tana shiga taga Ashe test zaiyi ita kanta Allah ne yarufa mata asiri ,dan da zamanta zatayi dan wajen yayimata dadin zama ,minti talatin yabayar yace kuma duk Wanda beyiba yayiwa kansa ,itadai tace tasan dan Salwa yayi danya cuceta ,ita wlh hartafara tsanarsa ,mutum yatakurawa yarinyar mutane ,ita ba wani laifin take yi masaba ,ita tarasa wace irin tsana yakeyiwa Salwa ,itadai tarasa asalin gabar ,da haka dai tagama abinda takeyi ta tafi gida ,tana addu,ar Allah yasa karya kayarda Salwa dantaga da gayya yayi .

Koda Salwa takoma gida gaba daya duniyar tayimata zafi ,sai dai taitayin addu,a Allah yarabasu lfy dashi,dan tafara zargin shine yake gayawa samarinta wani abun suke fasawa Allah yayimata maganin munafikin ta ,shirye shiryen bikina akeyi sosai ,gashi kuma sauran wata uku nagama karatuna nikaina nayi mamakin Dabe kayar daniba ,Allah ne kawai ya tsallakar dani a wajen sa Allah bebashi ikon yin hakanba ,a yadda nazir yakeso so yakeyi ayi fati kamar kala biyar Amman gaba daya nahana sbd ba ra ayina bane ,shi kuma yace ko guda dayane sai anyi sbd "yan wajen aikinsu ,dolena Na hkr nabi ra,ayinsa ,shirye shiryen azumi akeyi gadan -gadan dan befi saura sati daya afaraba ,nazir yazo wai menake bukata na amfanin azumi ,nace wlh bana bukatar komai ,yayi-yayi dani Amman nakiyin mgn ,yace to shikenan saida yatashi tafiya yadiremin dubu goma shima saida mukayi rigima dashi sannan na kar6a mukayi sallama yatafi .

Mommy da Daddy suna zaune suna lissafin shekarun sultan ,mommy tace aini bana maita shekarunsa da ranar haihuwarsa ,domin ranarce ta bakinciki a rayuwata ,ranace dana rasa d'ana danafi so a rayuwata sai kawai tasa kuka ,daddy Abdul yace ni matsalata dake kenan duk lokacin da Muke hira irin wannan saikin 6atamin rai badama ayimaganar shekarun sultan saikinyi kuka ai kowa baya wuce lokacinsa ,Allah ne yabamushi kuma ya dauke abinsa addu,a ita yafi bukata a yanzo ,Allah yajikansa da rahma ,shine gatan da zakiyimasa kenan addu,arki ta dinga isa wajensa ,tashare hawsyenta tace abinne nakasa mantawa dashi a rayuwata ,sai dai ina fatan Allah yamantar dani har abada ,yace addu,a itace maganin duk wata damuwa ,tace inayi sai dai nak'ara akan wadda nakeyi ,yace to sai a bada himma ,tace Allah yabani iko da juriyar duk abinda zaisameni nan gaba nadauki dangana .

Sultan ne yashigo da gudunsa yana kuka sosai ,kukan da yakeyi yayi mugun yawa idonsa idonsa yayi jajir dashi ,sai neman shidewa yakeyi ,hajiya Aisha tamik'e da sauri ta rik'e shi tana tanbayarsa me akayimasa koda faduwa yayi ,tadinga dudduba hannunsa da k'afarsa ko zataga wani alamar ciwo Amman duk iya bincikenta bataga komaiba ,tarikeshi tana sake tanbayarshi yace ba babansu khairiyya bane yace karna sake shigar masa gida tunda ni shegene waini babata "yar iskace waini a titi babata ta haifeni ,ni kuma uncle yacemin ummata ta mutu har yace nadingayi mata addu,ar Allah yashiryeta kuma inayimata kullum ,wlh sainagayawa uncle dina yaje suyi fada yayi musu dukan tsiya ,hajiya Aisha ce tasake fashewa da kuka daman irin wannan ranar nake gudu ,wlh bazamu yadda ba kotuce zatarabamu ,mun rasa abinda mukayi masa a gaskiya a wannan karan kodakai kayadda mu bazamu yadda ba ,aigaramu yataremu yagayamana duk abinda yaga dama ,dayasamu k'aramin yaro yagayamasa ,tarike sultan din sukayi daki dashi ,yi shiru kaji k'arya yakeyi a Asibiti aka haifeka ba,a titiba ,yasake kallanta yace to mommy meye shege tace zaginefa karnasakejin kafada kaji sbd babu kyau ,wuce a zubama abinci kaci kaji,karna sake ganin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login