Showing 24001 words to 26260 words out of 26260 words

Chapter 9 - Zazzafan Rabo Part 1 Complete Hausa Novel By Aisha Umar Indabawa.docx

binta kawai nakeyi ,kinsan halinta kartazo ta taramana mutane a unguwa ,tace in Allah yayarda Allah zai sauk'ak'a abun yace Allah yasa tace to ameen ,su kuwa gidansu Abdul gabadayansu gani sukeyi basuyiwa adalciba ,sbd suna ganin dansune yajamata komai gashi yatafi yabarta cikin tashin hankali ,itadai hajiya Aisha tayanke wani hukunci daddynsu Abdul yana dawowa zata tare shi da mgnar ,Allah yasa tadace da abinda tayi kudiri ,sai dayadawo yagama duk abinda yakeyi ,tace inada magana dakai daddyn Abdul ,kuma dan Allah kayiwa maganata fahimta me kyau dan Allah badanniba ,yace to shikenan nima idan kingama sai nayi tawa ,tace to fara takan yace a a fara takin dai ,tace dan Allah alfarma nake nema kasa Abdul ya auri Salwa ,ya kalleta yace ya akayi tunaninmu yazo daya ,tunda naganta nayimada sha,awarta yarinyace me kyau a hankali da nutsuwa wannan k'addarar data fadamatane kawai akeganinta hakan ,idan mukak'i bamuyi mata adalciba tunda tasanadin yaronmu take cikin kunci datuni tadade a dakin mijinta ,wannan shine adalcin da zamuyi mata ,kuma musharewa iyayenta hawayen da suka dade suna zubarwa ,dan wlh yau yabani tausayi dan dakaganshi kasan uanacikin rashin hankali dan dai mutum ne metawakkali ,to in Allah yayarda wannan shine bakincikinsu Na k'arshe akan auren "yarsu .

Mommy tace saidai wani hanzari baguduba Abdul din shine babban tashin hankalin,kasan baya kaunar yarinyar nan tuntana k'arama ,yace nuna masa zakiyi umarnine dole yabimu karkiyimasa wasa kona sakan daya nace to Allah yasa adace .

Sai dayagamacin abincinsa sannan aka sanar dashi abinda aka yanke ,dadinsane mek'arfin halin cewa Abdul wata alfarma nake nema a wajen ka ,yace daddy kafada zanyima indai abin befi k'arfinaba ,yace atunanina ma befi k'arfinkaba yace to daddy inajinka ,yace my son su nakeyi ka auri Salwa,yamik'e da sauriinsa yadda kasan zai hantsila yace ni daddy ,menayimuku kukesan hadani da wadda bata kama kantaba ,nan danan idonsa yafara fitar da hawaye yace mommy hardake kinsanfa ra ayina nasan auren mace mekamun kai ,ko so kukeyi jinina yahau nima ciwon zuciyar daya kashe dan uwana nima yakasheni kowa ya huta,kucanja wata alfarmar dan Allah ,duk kuma jikinsu duk saiya yi sanyi ,Abdul mommynsa tasake kiran sunan sa a hankali ya amsa a muryar kuka ,kai kanka nasan kafara tausayin Salwa ,ace kunsan samari goma sunfasa akan wata matsala daya wadda dan uwankane ya haddasa mata ita ,bance bayan ita bazaka sake wani auren ba ,zakayi auren ka aduk sanda kaso ,yashare hawayensa yace to shikenan zanyi shawara da ita idan tace tanasona ,idan kuma tace batasona kunyarda za kuyi hkr duk suka amsa masa

๐ŸŒบ๐ŸŒบ๐ŸŒบZAZZAFAN RABO๐ŸŒบ๐ŸŒบ๐ŸŒบ

๐Ÿ’ซ๐Ÿ’ซ๐Ÿ’ซAisha Umar Indabawa ๐Ÿ’ซ๐Ÿ’ซ๐Ÿ’ซ

๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒนmarubuciyar littafin Meka Maidani๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน

ุจุณู… ุงู„ู„ู‡ ุงู„ุฑุญู…ู† ุงู„ุฑุญูŠู…

_________________

______

๐Ÿ…™๏ธŽ๐—ฎ๐—ฟ๐˜‚๐—บ๐—ฎ๐—ถ ๐Ÿ…ฆ๏ธŽ๐—ฟ๐—ถ๐˜๐—ฒ๐—ฟ๐˜€ ๐Ÿ…๏ธŽ๐˜€๐˜€๐—ผ๐—ฐ๐—ถ๐—ฎ๐˜๐—ฒ๐—ฑ๐Ÿ“š๐Ÿ–Š

https://www.facebook.com/101679598253281/posts/101680068253234/?app=fbl

_Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa illmantarwa, nishadantar tare da fadakarwa da jama'a bisa harshen hausa_

๐Ÿ”๐Ÿ…™๏ธŽ๐Ÿ…ฆ๏ธŽ๐Ÿ…๐Ÿ”

๐Ÿ“ฑtyping๐Ÿ“ฑ

๐Ÿ…ฟ๏ธ 1๏ธโƒฃ8๏ธโƒฃ

Wannan shafin sadaukarwane ga "yan kungiyar jarumai writers Association Allah ya'kara hada kanmu .

Shikuwa basusan tunaninsaba yagama shirya duk yanda zai salwantar da Salwa, ba tare da wani yasani ba ,kuma bazai ta6a bari wani yaganeba ,zai saki ransa yadda kowa zai yadda da ba shine ya aikata abinda yake shirn yiba ,ai wlh idan yayarda yagama da kansa cutar da yayiwa kansa ba kadanba ,cika kurinsa a gaban abokansa yatashi a banza Allah ma yakiyaye ,ai koda ace Salwa sauran ita kadai a duniya ya kwammace ya mutu a haka babu aure ,yawuce dakinsa yana tunanin abinda yake shirin aikatawa ,su kuwa Abdul yana fita sukayiwa Allah godiya da abun yazo da sauki ,mommy ce harda cewa kodaman Abdul yanasanta befadaba ,koda yake tun suna yara basa shiri gashi Abdul ya tsani salwa ,gaba dayan yarinyar tagama bata tausayi danma yarinyar tanada tawakkali dabasan irin halin da zatashigaba ,ai kuwa indai itace ta haifi Abdul saiya auri Salwa insha Allah ,shikuwa tunda yashiga dakinsa ya zauna yadinga tunanin waisu daddy mesuka hango da sukesan su hadasu aure da Salwa ,shi wlh ko sau daya beta6a tausayintaba sbd ita tajawa kanta ,shi kuwa kowa yasan a nutsu yake sannan a dauki wata ballagaza a hadasu aure da ita ,sai kace yarasa masoya a duniya .

Saida suka hadu a masallaci wajen sallar isha ,alh aminu yace da Mlm aliyu dan Allah idan bazaka damuba inasan mgn dakai ,yace babu damuwa nima daman Neman naka nakeyi ,to mezai hana musamu wajen zama ,suka samu wani dan gini abakin masallaci ,Baban Salwa ne yafara mgn ,daman akan kayan dakasa akawowa yarinyata ne tunda auren beyiwuba sai katuru wasu yaran su kwashe kayan ,yace a a kabawa medakinka tasa ,yace a a ai wannan yayi kalar na yara ,ainine nabata dan Allah karkayimin musu,duk ma wannan mutureta angaba da babinta,kagani hankalinka dan Allah alfarma nake nema a wajenka,ya dago kansa da sauri yace ni Alh kasan banida wani abun da za a nemi alfarma a wajena sai dai idan har yanzo kana nan da 'kodirinka Nasiyan gidana ,ni kuma kasan nagayama banida gatan da yawuce gidana ,yace a a kar kayimin mummunan zato a tunanina wannan mgnar tawuce har abada a waccan lokacinma rashin fahimtane ,kuma inaso ayafi juna har abada komai yawuce ,yace Allah ya yafe mana baki daya ,Alh aminu yayi gyaran murya daman alfarmar da nake nema itace ,inasan kabawa dana auren yarinyar wajenka wato Salwa ,yadago da sauri yace Alh wane dan naka kenan,yace Abdul mana ,aikasan banida wani d'an aduniya banda shi ,shidai abban Salwa yayi shiru yace kodai baka amince bane naji kayi shiru ,yace a,a abinne yazomin a bazata sbd banta6a tsammani ba ,yadda naga tun lkcin zayyad kak'i aurensu duk da yadda suke tsananin San junansu ,yace dan Allah kature wannan mgnar adaina tuna da,yace shikenan yawuce sai dai inada wani sharadi guda daya nidai ba,asan ran Abdul ba sai dai abar abinnan tunda baza a shiga rayuwarsaba ,yace karka damu komai zaizo da sauki tunda harya amince Abban Salwa yadago kansa da sauri yace Allah ngd ma Allah kasa wannan shine kukana Na 'karshe akan auren Salwa ,koda yashiga gida da farincikinsa yana gayawa ummanta ,ita kanta murna takeyi sai gdy takeyiwa Allah ,ni kuwa tunda naji abinda suke fada gaba daya hankalina yagama tashi sbd ni nasan nice zansha wahala a wajen sa nasan zai amsa musune dan ya wahalar dani ,to wlh fituwa zanyi nace banasansa dana aureshi gara nayi xamana a hakan babu aure ,hankalina saiyafi kwanciya ,dan auren sa bashida wani amfani a wajena ,da safe yashigo yana gaidasu Abba ,shikuwa Abba kamar ya hadiyeshi dan murna,inajin Abba yanace masa wai indai bayasona kawai yafito ya fad'akarya cuci kansa ,yace haba Abba aiko danna faranta muku aina yarda ,shikuwa Abba shimasa albarka kawai yakeyi ,shikuma sai dariya yakeyi wadda batakai zuciba ,da saurina nafito gaban Abba natsuguna inata kuka ,nace dan girman Allah Abba karkuyimin wannan hadin sbd basona yakeyi ba cemin yakeyi ballagaza wadda tagama zubarda mutuncinta a titi ,kullum sai yayimin wannan gorin mayaudarine Abba dan Allah Abba katemakamin banasansa na tsaneshi .

Mari kawai naji a fuskata nadago Abba nagani a tsaye yana huci ,salwa kinbani mamaki duk da wannan halin naki da kikagama ambata shibe gujekiba har kece zaki wulak'antashi to wlh baki isaba kinyi kadan ,aurene babu fashi dakeda Abdul tunda harya nuna yana kaunarki ,keda kinada hankali ai bakida masoyinda yafi shi tunda rufa miki asiri yayi ,nidai banda kuka babu abinda nakeyi ,shi kuma munafikin sai ban hkr yakeyi azuciyarsa kuma yana cewa Allah yakiyaye ya auri Salwa a matsayin matarsa ,a yadda akasa bikinsu sai Salwa tagama jarabawar k'arshe ,ma,ana tagama karatunta gaba daya kenan tunda sunfarama jarabawar sai ayi komai cikin kwanciyar hankali ,a daddafe ta dinga duba littafanta dan tariga da ta saddak'ar dabaci zatayiba ,shikuwa ya yanke shawarar yabarta da karatunta kar dukan yayimata yawa ,a yadda ya shirya zaiyimata sanadin karatun to Amman yanzo yabarta ta tsira dashi ,kusan sati biyu tana jarabawar a haka har suka gama ,ko fau zee bata yadda ta gayawa wannan mgnar ba ,tadaice mata kawai an faga bikinne ,itadai fauxee shiru kawai tayimata dan daka kalleta kasan akwai abinda yake damunta ,ita kuma fauxee bame irin bincikennan bace bare tace saitaji komai sai kawai tabar mgnar .

A ranar da yatabbatar tagama zana jarabawarta ta k'arshe ,yazo har cikin mkranta yace a kiramasa ita yana office din sa ,tunda sak'on yasameta taji gabanta yafadi ,daman gawasu mugayen mafarkai da takeyi bataki zuwaba sbd tasan sauran ,sbd tsoron da takeji taroki fauxee data rakata ,Amman taki tace kinsan zan iyayin laifi a wajen sa ,ta tafi ita kad'ai tana addu,ar Allah yakareta ,tabude k'ofar office din a hankali ta hada da yin sallama ,yanata "yan rubuce -rubucensa tace gani ya Abdul yayimata banxa ,tasake mai -maitawa Amman ko dago idonsa beyiba ,itama tayi zuciya ta kama murfin k'ofar zata fita ya dago idonsa da sauri yace kinsanni basa,an wasankiba ne ni nafi k'arfin kiyimin hakan salwa ,idan kinga dama kingama abinda kikeyi kijirani a wajen get zamu tafi tare badai kin nace sai Abdul ba to muzuba nidake ,nace masa to kawai ,nace nifa nagama yace saikijira a get Mesa da mutane sbd kar mutuncina ya zube ,tafito tayiwasu fauxee sallama da sauran " yan mkranta tafito bakin get xaman jiransa ,harsu fauxee suka fito suka tarar da ita abakin get dinsukace tazo sukaita gida Amman taki yadda dan tasan wani sharrinne zai biyo baya ,ta Dade sosai a zaune harta yanke hukuncin tayi tafiyarta dan wulak'ancin yayi yawa ,sai kuma taganshi a mota ,tayi mamakin budemata gaban motar da yayi ,danko dawasa bata ta6a shiga gaban motarsaba ,itadai Salwa taga basu nufi hanyar gidaba ,tace ina kuma zaka kaini yace inda kikafi dacewa dazama ,sai kawai nayi shiru narabu dashi ,tagadai tafiyar bata wasaba ,tunda ga nan tashiga damuwa ,sai dasu kayi tafiya menisa ya kalleni yace bani wayarki Salwa babu musu namik'a masa ,yace ayaune zanyi mgninki waike kinata murna zaki auri gaye kamata ko ,to wlh nayi miki nisa ,tabude bakinta sosai tace wai kai ina zaka kainine kodai saceni zakayine,yace inma zatarce ai bazan saci irinkiba wadda tayi kwantai a aure aketa neman kai da ita ,ai danasani nabawasu Abba shawarar ayi sadaka dake ,koya bada sanarwar idan damesan bazawara yafito anbashi ,banda irin "ya" yayan irin tsofaffinan da suke wahalar da "ya " yansu suyimusu fitsarin kwance suyi amai a zaune duk wata 'kazanta dai dakika sani ,suma yaran saisu nemarwa kansu sauki su nemar masa auren ki ,kinga sai kije kiyita bautar aure ,yawani kallleni kagasu salwa matar dattawa ,nidai kuka kawai nasakar masa ,shikuma dariya kawai yasa banta6a tsammani yana dariya irin hakaba ,jeji kawai muketa wucewa nadago idonsa dasukafarayin ja ,nace dan Allah kamayar dani gida karkasamin iyaye cikin tashin hankali tunda banta6ayin nisa dasuba ,ke da Allah yiwa mutane shiru gulmamma ,sai dayaga munfara shigowa cikin 'kauye munbar jeji ,ya tsaya a wajen wasu masu saida kifi ,yasiyo yadawo to a nan nema naga ansa samu naka ,nadafe 'kirjina nace kardai ace nan ne samu nakan da akefada ainaji kamar ance hanyar jos ne ,yakalli yace idan kingadama kici idan kuma yinwa tak'arasakine kinga nahuta da auren dolen da za,ayimin ,wayarsace yayi 'kara yadauka da sallamarsa inajin yanacewa a a mommy har yanzo bamu 'karasaba kinsan jos danisa kuma bamutafi da wuriba tace to Allah yakiyaye yace ameen akularmin da sultan kafin nadawo in Allah yayarda gobe zamu dawo sukayi sallama yakashe wayar ,yacigabada cin kifinsa yana hadawa da lemon roba da alama yagama shirinsa natafiyar ,shi daman yayiwa gida bayanin zasuyi tafiya daga wajen aikinsu ,to shine mommynsa tabugo masa dantaji lfyarsa ,shikuwa Allah Allah yakeyi ya aiwatar da abinda yayi 'kodire shikenan yahuta da tashin hankalin da zai shiga ,nidai harnafa tsorata danaga duhu yafara gashi har yanzo bamukai inda zamuba ,tunda naga mommy takira hankalina ya kwanta ashema a gida ansan da zuwan namu tare dashi Amman babu Wanda yagayamin Na kwantar da hankalina har nafara bacci ,gazaman mota ga yinwa Amman bazan iyacin wani abun ba ,warin mai yasani nafarayin amai ,yatsayar da motar ,nace dan Allah bakaga inda katsayar da motarba ,baka tsoro wani abun yasamemu ,yace ke kadai dai fito Salwa nan ne gidan ki Na sure ,nakalli wajen babu wani mahaluki a wajen banda manyan duwatsu babu komai a wajen ga wajen ba'kikkirin abin tsoro ,ga duhu yafarayi ,nace dan Allah ya Abdul mubar wajen nan ,yace bakiji abinda nacemikiba gidan auren ki nakawoki bana sanki bana 'kaunarki ,naga yana Neman yatafi yabarni nayi saurin rik'e masa rigarsa ya fizge narike k'afarsa nace hayi hkr dan Allah karka barni anan wajen bansan mugayen abubuwan da suke wajen nan ba ,katemakamin ya Abdul ka kaini wajen mutane ,ni kuma nayimaka alkawarin bazan sake dawowa wajenkuba dan Allah ya Abdul ,yace kinga Nina sauri nakeyi kar abinda zai sameki ya hada dani ,tabude but din motarsa ya dauko wata jaka ya ajiyemin ya dauko kudi a aljihunsa da yawa yazubamin a cikin jakar yace to Salwa ga sadakinki yasa dariya yadire wata Leda akan jakar ,yayi saurin barin wajen da gudunsa kukane kawai ya kwacemin nasaka k'ara dan awajen sai kayi wajen minti nawa mota batazo wucewaba sbd rashin kyan wajen ga Nisan wajen nace wayyo ya Abdul kacuceni.

7
8
9

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login