Showing 15001 words to 18000 words out of 22575 words
Chapter 6 - SARKIN SADAUKAI Complete by Mansur Usman Sufi .txt
tsira tare da yaro Humair makaho,
Tsawon wannan lokaci da suka shafe a cikin gidan duk wani abu da suke buƙata na sha'anin rayuwa da sun bukace shi sai suga ya bayyana gaban su,
Kuma a iya tsawon wannan lokaci shaƙuwar soyayya ta ƙara kullu wa ainun tsakanin jaruma Husnaila da saurayi Hizmal
A ranar kwana na ukun ne da la'asar sakaliya su Hizmal suka kammala shiri domin cigaba da gudun tsira, domin tseratar da rayuwar yaro Humair,
Bayan sun kammala shirin ne
Sai saurayi Hizmal ya giya yaro Humair a gadon bayan sa,
Sannan suka durfafi wata kofa ta musamman a cikin gidan domin su fita,
Lokacin da suka isa bakin kofar sai suka tarar da kofar a garƙame babu alamun wajen da za'a bude ta,
Al'amarin da ya dugunzuma hankalin su kenan ainun suka shiga dogon nazari,
Suna cikin wannan hali ne kwatsam bazato babu tsammani sai suka ga wani aljani ya bayyana gare su ya faɗi yayi sujjada,
Aljanin yakasance gabjejen kato mai tsawo da kwarjini, yana da fuka fukai guda huɗu, da jela guda ɗaya, yana da kwalakwalan idanu jajur tamkar garwashin wuta, hancin sa kuwa ashafe yake tamkar bada shi yake shaƙar numfashi ba, a haɓar sa yana maƙale da dogon gemu fari sol mai tsawon kamu huɗu
Hakika wannan aljani ya cika mai ban tsoro gami da muni
Su kansu su saurayi Hizmal a matsayin su na zaratan Jarumai sai da suka firgita da sukayi arba da aljanin,
Aljanin ya ɗago da kansa sama ya dubi Hizmal da sunaila ya buɗe tafkeken baƙin sa mai kama da kofar gari, sannan yace cikin kakkausar murya,
"Da farko dai suna na Marhutul-Azab kuma nine hadimin dake kula da wannan gidan tsira yau fice da shekaru dubu bakwai,
Ya ku waɗannan bil'adama ma'abota gudun tsira kuyi sani cewa na bayyana gareku ne domin na fitar daku daga cikin wannan gida na kai mu duk inda kuke bukata a fadin duniya,
Koda jin wannan batu daga bakin aljani Marhutul-Azab sai Hizmal da sunaila suka cika da mamaki ,
Sunaila tace "Yakai wannan aljani haƙiƙa munyi farin ciki maral misaltuwa bisa wannan taimako da zaka yi mana,
Amma fa wani hanzari ba gudu ba, ina so kayi sani cewa tafiya damu abu ne mai matukar wahalar gaske da zai iya jefa rayuwar ka a cikin tsaka tsaka mai wuya,
Ina ganin abinda zai fi kawai shine ka nuna mana hanyar da zamu fita kai kuma ka cigaba da gadin wannan gida kamar yadda ka saba ,
Koda jin wannan batu daga bakin sunaila sai Aljani Marhutul-Azab ya bushe da yar karamar dariya mai kama da haniniyar doki sannan yace
"Yaku waɗannan bil'adama kuyi sani cewa fiye da shekaru dubu biyu nasan da labarin bayyanar ku a cikin wannan gida dama abinda zai kawo ku nan ɗin
Da kuma abinda zaku tafi nema,
Bisa al'adar wannan gida kowa ne mai gadi zai shafe tsawon shekaru dubu huɗu ne cif,
Kuma a yau ne shekarun kammala aiki na suka cika na samu yanci zan iya shiga ko ina a duniya
Babban muradi na shine na sadu da jarumi Hibairu SARKIN SADAUKAI wanda shine kuka fito ne ma
Tsawon shekaru na shafe ina jiran zuwan ranar da zan sadu daku domin na cika burina na ceto rayukan al'ummar kabilar mu,
Wanda a halin yanzu ruhikan su ke ajiye a can fadar Sarkin bokayen duniya DURUSUL-FANNAR
A bisa cikin wata akwatu ta baƙin ƙarfe,
Kowa ce rana Sarkin bokayen duniya sai na tsafe ruhikan kabilar mu da wani sinadaran sihiri,
Da zarar ya kammala sihirin waɗannan ruhikan zasu koma nasa,
Ma'ana kenan zai zamo cewa yana ɗauke da rayuka guda dubu arba'in, Kowa ne ruhi guda ɗaya zai shafe shekaru dubu huɗu kafin ya mutu,
Baban burin Sarkin bokayen duniya shine ya cigaba da rayuwa da waɗannan ruhikan bazai mutu ba har abada, zai cigaba da kasancewa SARKIN SARAKAI,
Bisa binciken da na gudanar bisa halarar tsafi na na gano cewa babu wani mahaluki da zai iya zuwa fadar Sarkin bokaye ya ceto ruhikan kabilar mu face SARKIN SADAUKAI Hibairu,
Sannan babu wani abu dazai iya buɗe wannan akwatin baƙin ƙarfe face ZOBEN SHIRIn dake hannun jarumi Hibairu kuma zoben ne zai karya sihirin dake jikin ruhikan kabilar ta mu har ya dawo zuwa gangar jikin su su cigaba da rayuwa kamar kowa,
Sa'adda aljani Marhutul-Azab yazo nan azancen sa sai hawaye suka zubo daga idanuwan sa,
Al'amarin da yayi matukar bawa su saurayi Hizmal tausayin sa kenan,
Hizmal ya dube sa cikin matukar damuwa yace
"'yakai Marhutul-Azab kayi sani cewa haƙiƙa labarin ka akwai ban tausayi duk da ka bamu shi a takaice,
Ina mai tabbatar maka dacewa ni da abokiyar tafiya ta zamu taimaka ka har mu sadu da jarumi Hibairu SARKIN SADAUKAI tun da dukkan bukatar mu kusan ɗaya ce
Koda jin wannan batu sai farin ciki ya lulluɓe zuciyar Marhutul-Azab ya buɗi baki karo na uku yace
Yaku abokanan tafiya ta kuyi sani cewa ina farin cikin sanar da ku cewa
Ina ɗauke da dukkan taswirar fadar Sarkin bokaye,
Wacce babu wani mahaluki dazai shiga wannan fada face yana tare da taswirar,
A halin yanzu nasan cewa kowa ya ɗora idanun sa akan taswirar,
Wacce ko shi kansa Sarkin bokaye basan cewa ina ɗauke da wannan taswira ba ,
Tsawon shekarun da na shafe ina gadin gidan tsira domin na mallaki wannan taswira ne,
Na ji ajikana cewa wannan tafiya tamu cike take da nasara,
Tun da gashi muna tare da taswirar fadar Sarkin bokaye da kuma yaro Humair makaho wanda shine kaɗai a faɗin duniya ya iya magana da Yaren Hibairu SARKIN SADAUKAI,
Sa'adda aljani Marhutul-Azab yazo nan azancen sa sai kowa ya cika da matukar farin ciki maral misaltuwa,
Gama faɗin hakan ke da wuya sai Marhutul-Azab ya shimfide gadon bayan sa Hizmal goye da yaro Humair da sunaila suka hau suka zauna,
Sannan Marhutul-Azab ya yunkura ya tashi izuwa sararin samaniya ya na mai keta gajimare cikin matsanancin gudu tamkar giftawar tauraruwa mai wutsiya ya ɓace ɓat tamkar bai taɓa wanzuwa ba,
Wannan shi ne abinda ya faru tsakanin jaruma Husnaila da saurayi Hizmal a cikin gidan tsira domin tseratar da rayuwar yaro Humair makaho,
****
Lokacin da boka Dargas da sauran tawagar matsafa biyar suka bayyana a ɗakin sirri domin gudanar bincike bisa bayyanar bakuwar jarumar da ta ceci rayuwar al'ummar kasar daga GOBARAR DAJI wato gimbiya Hushriba bintu ishwar,
Bayan binciken da bokayen suka yi suka gabatar da jawabin binciken su
Sai sarkin bokaye Dargas ya dube su yayi gyaran murya yace
"Bisa ga dogon nazari da kuma abinda bincike ya tabbatar shine jaruma Hushriba ba tazo domin ya cutar da mu ba kawai dai taso ne mu haɗa karfi da karfe domin kowanne mu ya kai ga biyan buƙatar sa,
Amma sai dai ba zamu saki jiki da ita ba domin kunsan cewa ba'a bawa mata yarda a cikin al'amura
Matukar baku mallake su ba shin ina cewa kun taɓa karanta Littafin KUNDIN MATSUBBATA Hikayar jarumi Hilairu da Baiwa luzra
Kun ji irin cin amana da yaudarar da tayi masa daga karshe m
Bayan ya siyar da rayuwar sa ya ceto ta da ma mahaifan ta,
Koda jin wannan batu daga bakin Sarkin bokaye Dargas sai sauran maysafan su kayi na.am
Boka Dargas ya ɗora dacewa "wani abun takaici da na gani a cikin halarar tsafi ma shine tuni su saurayi Hizmal sun samu nasarar fice daga cikin gidan tsira sun bazama izuwa duniya bisa taimakon wani hatsabibin aljani mai Marhutul-Azab da halin yanzu babu saurayin aljani mai tashen balaga kamar sa a fagen karfin damtse da jarumtaka,
Yanzu batare da bata lokaci ba zan umarci hadimin aljani na domin ya dawo dasu mai girma sarki Shazwan domin a halin yanzu jiran gawa babu rai suke yi a can gidan tsira,
Sa'adda Sarkin bokaye Dargas yazo nan a jawabin sa shafi wani gurun tsafi a damtsen hannun sa
Take wani aljani mai kama da tsuntsun batoyi ya Bayyana gare sa, ya kwashi gaisuwa
Boka Dargas ya dubesa ya kai Haulatul- infal kayi sani cewa ban kirawo ka nan ba sai domin ina so ka tafi izuwa gidan tsira ka ɗauko mai martaba sarki Shazwan da tawagar sa acan inda ka dauko mu a ɗazu ni da jama'a ta,
Koda jin wannan umarni sai Aljani Haulatul-infal ya risina sannan ya ɓace ɓat tamkar bai taɓa wanzuwa ba.
Daga wannan jawabi ne kowa ya kama gaban sa ɗakin taron ya watse,
Wannan shi ne abinda ya wakana acan birnin zawatul-ifdal.
Lokacin da aljani Marhutul-Azab ya tsala da matsanancin gudu a sararin samaniya ɗauke da Jaruma Husnaila,saurayi Hizmal da yaro Humair makaho,
Sai ya wanzu yana mai keta gajimare tamkar giftawar tauraruwa mai wutsiya,
Nan fa Saurayi Hizmal ya kama kalle-kalle yana mamakin yadda sararin samaniya yakasance domin wannan ne karon sa na farko a rayuwarsa da ya taɓa tashi sararin samaniya bisa kan aljani,
Tsawon daƙiƙa hamsin ana wannan tafiya babu wanda yace ƙala,
Sai daga bisani ne jaruma Husnaila ta katse shirun da ya wanzu ta hanyar buɗar baki tayi gyaran murya sannan dubi saurayi Hizmal tace"Yakai Hizmal shin kana ganin cewa yanzu kai tsaye zamu huce ne izuwa hanyar da zata sada mu da dajin Baitul-shamshan?,
ko kuwa zamu jira ne har izuwa lokacin da SARKIN SADAUKAI zai kammala karanta ɗalasiman tsafin dake jikin ZOBEN SHIRI?
Koda jin waɗannan tambayoyi Daga bakin Husnaila sai Hizmal yayi gyaran murya yace
"Ya sunaila haƙiƙa kin kawo maganganu masu muhimmanci daya kamata muyi dogon nazari akan su,
Amma dai bisa shawara ta ina ganin zai fi kyau ace mun tunkari dajin Baitul-shamshan domin a halin yanzu,
Dalili na na faɗin hakan kuwa shi ne a Kowa ne hali bokaye,sarakai cikin farautar yaro Humair suke
Idan muka ce zamu tsaya sai ranar da jarumi Hibairu zai kammala karanta ɗalasiman tsafin dake jikin ZOBEN SHIRI zai kasance waɗansu sun riga mu isa dajin Baitul-shamshan,
Haƙiƙa dai masu iya magana na cewa a bari ya huce shine ke kawo rabon Wani,
Koda jin amsar tambayoyin da ga bakin Hizmal sai sunaila tayi shiru tamkar tana nazari
Daga bisani ta dubi aljani Marhutul-Azab tace"yakai Marhutul-Azab mene ne ra'ayinka akan wannan magana,
Marhutul-Azab yace cikin kakkausar murya"Tabbas maganar da Hizmal ya faɗa shawara ce mai kyau,
Domin abinda baku sani ba shine,
Daga nan izuwa dajin Baitul-shamshan tafiya ce ta tsawon shekaru ɗaya bisa saurayin aljani mai tashen balaga,
Amma ni zan iya gajarce mana tafiyar cikin kwanaki sittin da huɗu,
Domin ahalin yanzu a kaf jinsin aljanu babu aljani mai tashen balaga da karfin gudu tamka ta,
A yau saura kwanaki sittin da huɗu cif jarumi Hibairu ya kammala karanta ɗalasiman tsafin dake jikin ZOBEN SHIRI.
Kun ga kenan ranar da zamu isa dajin ranar ne SARKIN SADAUKAI zai bayyana a sararin duniya,
Bani da tabbacin akwai wanda zai riga mu isa dajin Baitul-shamshan ɗin,
Koda jin wannan wajabi daga bakin aljani Marhutul-Azab sai Hizmal da sunaila suka cika da matukar farin maral misaltuwa,
Daga wannan furuci ne kowa yayi shiru aka cigaba da tafiya,
Wannan shi ne abinda ya faru da Jaruma Husnaila da saurayi Hizmal da yaro Humair makaho,
Bayan aljani Marhutul-Azab ya dauko su daga cikin gidan tsira,
*****
BAHREN
A Can ƙasar bahren kuwa, al'amarin sarki uslaim kuwa tun ranar da boka ƙarzum ya bayyana gare sa,
Domin ya yi masa bayani game da batar yar sa gimbiya zarifa,
Bai sake bayyana a gare sa ba sai wata rana da hantsi sarki uslaim na zaune a bisa karagar sa ta mulki a fadar sa,
A wannan lokaci fadar ta cika Maƙil da al'umma babu masaka tsinke kowa na zaune bisa kujera,
Kwatsam sai aka ga wani bakin duhu ya bayyana a tsakiyar fadar
Sannu a hankali sai duhun ya riƙiɗa izuwa wani dattijo fari kakkaura ma'abocin kwarjini,
Fuskar sa cike da ƙasumba da gemu farare sol
Sanye da jajayen tufafi, hannun sa riƙe da kwagirin tsafi dake canza launi izuwa siffa daban daban-daban,
Ba wani ba ne wannan dattijo ba face boka ƙarzum
Da bayyana sa sai ya zube ƙasa ya kwashi gaisuwa
Ga sarki ƙarzum,
Bayan sarki ya amshi gaisuwar sai boka ƙarzum ya miƙe tsaye tsam ya nufi wata ƙasaitacciyar kujera dake kusa daf da inda karagar mulki take yana mai dogare da kwagirin sa,
Ya na isa ya zauna abisa kujerar, sai ya juya ya fuskanci sarki uslaim fuskarsa babu yabo babu fallasa cikin wata irin kakkausar murya yace"ya shugaba na kayi sani cewa bisa binciken da na gudanar bisa halarar tsafi na na gano cewa lokacin gudanar da tafiyar mu yayi domin saduwa da SARKIN SADAUKAI domin ka bayyana masa buƙatar ka na son ya ceto maka yarka gimbiya zarifa daga fadar Sarkin bokaye,
Ya shugaba na kayi sani cewa a halin yanzu ilimin tsafi ya tabbatar mini da cewa babu wani mahaluki dazai iya magana da Yaren Hibairu SARKIN SADAUKAI face wani yaro da ya kasance makaho ana kiransa da suna Humair,
A halin yanzu wani hadimin aljani da ake wa laƙabi da Marhutul-Azab ya dauki yaro Humair tare da waɗansu jarumai biyu domin su isa dajin Baitul-shamshan domin saduwa da jarumi Hibairu SARKIN SADAUKAI
Domin su ma su bayyana ma sa nasa bukatun,
Saboda a halin yanzu ba mu da wani abin farauta da huce yaro Humair makaho,
Domin dole shine zai iya magana baki da baki da Sarkin sadauki,
Ya zama wajibi agare mu mubi sahun aljani Marhutul-Azab domin mu riski yaro Humair,
Sa'adda boka ƙarzum yazo dai dai nan a jawabin sa sai sarki uslaim ya cika da matukar farin ciki maral misaltuwa bai san sa'adda murmushi haɗe da yar karamar dariyar farin ciki suka suɓuce masa ba
Cikin hanzari sarki uslaim ya mike tsaye zumbur ya shiga izuwa gidan sarauta domin ya kimtsa,
Jim kadan sai gashi ya bayyana sanye cikin gagarumar shigar yaƙi tare da dakarun rakiya gudu dubu ashirin, haɗe abin guzuri da kuyangi masu hidima,
Batare da wani ɓata lokaci sarki uslaim ya miƙa rikon sarautar sa ga wazirinsa,
Sannan aka dunga aka fita izuwa wajen faɗa, bayan an fita ne sai boka ƙarzum ya kwalawa hadimin aljanin kira har sau huɗu,
Aljani ya bayyana gare sa ya faɗi ƙasa ya kwashi gaisuwa
Aljanin yakasance gabjejen kato mai tsawo da kwarjini sosai,
Komai jarumtakar Mutum idan yayi arba dashi sai ya ɗimauce saboda tsanin munin sa
Boka ƙarzum ya dubesa yace
"Yakai Darmanu ibn kauƙas kayi sani cewa bakomai ne yasanya na kirawo ka izuwa nan ba
Sai domin ina so ka ɗauke mu ni da wannan tawagar
Kabi sahun aljani Marhutul-Azab da halin yanzu ya durfafi dajin Baitul-shamshan,
Ina so ka cimmu su a Kowa ne, ya Darmanu ibn kauƙas kayi sani cewa matsawar ka gudanar da wannan aiki yadda na buƙata,
To zan yan taka da bauta da ka shafe tsawon shekaru kana yi agareni,
Koda jin wannan umarni daga bakin boka ƙarzum sai Aljani Darmanu ya sake risina agareshi yace
"An gama ya shugaba na yana Gama faɗin hakan sai ya shimfiɗe gadon bayan sa take sarki uslaim da boka ƙarzum suka hau bisa kan sa suka zauna,
Dakarun rakiya, guzuri gami da kuyangi suka koyi koyi dasu suka hau bisa gadon bayan Aljani Darmanu,
Cikin kuzari da karfin damtse Darmanu ya yunkura ya tashi izuwa sararin samaniya tare da kaɗa manyan fuka fukan sa,
Jama'a na ɗaga musu hannu tare yi musu fatan samun nasara har suka ɓace ɓat a cikin gajimare tamkar basu taɓa wanzuwa ba,
Wannan shi ne abinda ya faru da sarki Uslaim na Birnin bahren
wanda sarkin bokayen duniya ya sace masa yar sa gimbiya zarifa
Kuma a halin yanzu ya fito farautar yaro Humair makaho domin ya samu nasarar saduwa Hibairu SARKIN SADAUKAI.
Lokacin da aljani Haulatul-infal ya ɓace ɓat daga ɗakin sirri domin zartar da umarnin sarkin bokaye Dargas,
Kamar yadda boka Dargas ya umarce sa haka al'amarin ya kasance domin cikin abinda bai huce daƙiƙa hamsin ya bayyana a kofar gidan sarauta ɗauke da sarki shazwan da tawagar sa,
Bayan Haulatul-infal ya sauke su sarki shazwan sai ya yunkura ya sake tashi izuwa sararin samaniya ya ɓace ɓat
Sarki shazwan bai samu ganawa da Hushriba ba sai da gari ya waye bayan ya kammala kalaci sannan Hushriba da waziri Rufyan Sarkin bokaye da sauran tawagar matsafa suka iske sa a cikin turakar sa ta ganawa da baƙi,
A wannan lokaci sarki shazwan na zaune bisa wata ƙasaitacciyar kujera ya caɓa ado irin na hamshakan sarakai,
Kyawun surar sa ya bayyana a fili, jikin sa na fitar da wani irin kamshin turare mai daɗin gaske,
Lokacin da gimbiya Hushriba tayi arba da fuskar sarki shazwan sai taji zuciyar ta ta buga da karfi a karo na farko ta kasa gane shin mene ne abinda ya sanya zuciyar ta zata buga da karfin,
Shin ta faɗa farkon soyayya ne ko kuwa tsananin kwarjinin sarki shazwan ne
Amsar tambayoyin da Hushriba ta kasa bawa kanta kenan
Ta samu waje ta zauna bisa kujerar da aka tanadar mata dake fuskantar sarki shazwan,
Bayan kowa ya zauna ne bisa wajen zamansa
Sai sarki shazwan ya shiga kallon su ɗaya bayan ɗaya kamar mai nazarin wani abu,
Duk wanda sarki shazwan ya kurawa idanu sai kaga ya sunkiyar da kan sa ƙasa,
Amma bisa mamaki koda ya haɗa idanau da Hushriba sai ya ga ita ma ta ƙura masa idanun ko kiftawa bata yi,
Al'amarin da yayi matukar ba sa mamaki kenan yace a ransa shin wannan jarumi bata san Mene ne matsayi na ba ne ta ƙura mini idanu batare da ladabi ba
Wani ɓangare a zuciyar sa kuma na cewa shin baka lura da nau'in kallon da Hushriba ke yi maka ba ne,
Tabbas kallo mai ɗauke da alamun shauƙin so
To kai ma meyasa ka cigaba da ƙura mata idanun fiye da ƙima
Sa'adda sarki shazwan yazo Nan a tunanin sa sai yaji kunya ta kama sa,
Kawai sai ya dawo da duban sa ga Sarkin bokaye yayi gyaran murya sannan ya fara magana akaro na farko cikin nutsuwa
"Da farko ina yiwa dukkan waɗanda suka hallara a wannan waje Barka da zuwa tare da yiwa bakuwar jaruma maraba,
Bayan haka dalilin daya tara ku wannan waje shine domin na saurari dukkan bayani game da wannan musiba da ta afka mana ta GOBARAR DAJI da kuma karin bayani akan hanyar magance wannan al'amari,
Koda jin wannan batu daga bakin sarki shazwan sai sarkin bokaye Dargas ya yi gyaran murya yace"Ya shugaba na dukkan wani bayani da Ya kamata nayi maka nayi maka shi game da bayyanar wannan jaruma wato Hushriba,
Abinda ya rage dai yanzu kawai shine mu saurari bayani daga bakin Hushriba akan hanyar da zamu kawar da wannan annoba,
Sa'adda sarkin bokaye Dargas ya zo nan azancen sai