Showing 30001 words to 33000 words out of 131003 words

Chapter 11 - DAUDAR GORA BOOK 2 PDF COMPLETE BY bilyn Abdull .txt

19 Jul 2024

31122

gwarazo ne. A ƙirjinsa bugu yake kamar zai hantsilo waje, a zahirinsa kuwa babu mai iya fahimtar komai koda daga fuskarsa ne. A hankali matan da ke zagaye da ita suka dare, dan sune suka sanar cewar Zawjata-almilk ce, shugaban jami'ai ya faɗa a rufe ne saboda shakkar isar da saƙon kai tsaye ga Shahan-shan ɗin. Suma kawunansu duk a rissine suke, cikin rawar murya ɗaya daga cikin matan data kasance amintacciyar hadima mai ƴanci dake da alhakin kaiwa da komowar duk wani abinda ya shafi Shahan-shan da matansa ko makusancinsa (kamar jakadiya a ƙasar hausa) ta ƙarasa zubewa cikin gurfana,
“ALLAH ya huci zuciyar shugaban sarakunan ƙasar ruman da al'ummar cikinta. Umarninka muke jira domin taɓa Zawjata-almilk, dan rayuwarta zata iya salwanta.....”
Idanunsa da ke ma Iffah kallon ƙasa-ƙasa ya ɗan lumshe, cikin jarumtar son danne zillon da zuciyar ke masa ya ɗaga ƙafarsa da ƙyar yay taku ɗaya biyu da ya sake saka matan darewa cikin rawar jiki mamaki na neman halakasu ganin gadan-gadan Iffah ya nufa. Dai-dai yana ƙarasawa ɗaya da ga cikin jami'an wajen da yay wata irin zabura ya sunkuto ɗaya daga kujerun dake a wajen ya dire masa, da sauri aka ɗaura hiramin sayeed Fayzul-haq daya fincike a kansa. A hankali ya kai zaune shanyayyun idanunsa na sake tar-tar a kanta cikin ɗan hasken da garin ya fara. An lulluɓe jikinta da mayafi kasanwar kayanta dake jiƙe zai iya bayyana ainahinta, kallon kusan sakanni biyar yaja numfashi ya fesar yana mai kai yatsunsa biyu saman hancinta, babu alamar numfashi, ɗaukewa yay ya maida a jijiyar wuyanta, nan ma bata harbawa, cikin jarumta da zaburo da sanyin da ke sauka a jijiyoyin jikinsa ya ɗan ɗaga mayafin ya ciro hanunta. A kan tattausan nasa ya ɗaura yana mai ɗaura yatsansa akan jijiyar tsintsiyar hannun ya lumshe ido. Da sauri ya buɗe sai dai ga mai kallo bazai taɓa fahimta ba. Dan a nitse yake sarrafa hannunsa dake motsi kawai a jikin nasa. Shugaban jami'ai da Sayeed Fayzul-haq dake ɗan satar kallonsa kasancewar duk wani hadimi da sauran jami'an tun zamansa a kujerar duk sun juya bayansu suka ɗan waro ido ganin ya kusanta ƙyaƙyƙyawar fuskarsa da ta Iffah har hancinansu na gogar juna. Ya lumshe idanu tare da sauke tausasan lips ɗinsa kan nata, ai dole suma suka sake rissinar da kawunansu duk da sun san bawani abu zai yi ba illa bata taimakon gaggawa.
Shiko da bai ma san sunayi ba da harshensa yay nasarar raba lips ɗinta da haƙoranta dage datse cikin na juna ya turashi cikin bakin nata, sai kuma ya kai yatsunsa biyu kan hancinta ya matse. Iskar bakinsa mai ƙarfi ya hura mata cike da salon ƙwarewarsa akan iya ruwa da ceton duk wanda ya samu accident a dalilinsa. Da wani irin ƙarfi ta zaburo ƙirjinta na ballaƙowa sai ruwan bakinta bulla a kan fuskarsa. Idanu ya lumshe a hankali yana mai sauke wata irin nannauyar ajiyar zuciya daga cikin maƙoshinsa da ɗan jan fuskarsa data wanke da ruwan bakinta.
Cikin sauri Ama. Ta miƙama Sayeed ƙaramin towel cikin wanda ke hanunta, amsa yay ya matsa kusa da Tajwar Eshaan kansa a rissine ya miƙa masa. Bai motsa ba idonsa a kanta tana cigaba da amayo ruwan saboda ɗan danna ƙirjinta da ya cigaba dayi har tsawon kusan mintuna biyu, kafin ya miƙama sayeed hannu batare da ya juyi ba ya amsa. Kan fuskarsa ya kai ya tsane ruwan da tuni yama gangagare har wuyansa har ya ɗan jiƙa jallabiyar jikinsa mai tsananin ƙyau da ɗaukar idanun kai kallo.
“Duvet”.
Ya faɗa a hankali ganin jikinta ya fara karkarwa har ɗan gadon agajin gaggawar da aka daurata na ɗan jijigawa. A cikin ƙanƙanin lokaci aka kawo, yanzu ma da kansa ya rufa mata. Sannan ya miƙe gaba ɗayansa yana ɗan duban Sayeed. “A maidata gareni”. Ya faɗa can ƙasan maƙoshi tamkar bashine yay maganar ba yana ƙoƙarin barin wajen. Sai yanzu ya lura da cikar garden ɗin da duk masu faɗa ajin masarautar a wajen. Idonsa ne ya sauka kan Malikat Bushirat da Malikat Haseenat da ke kusan tare da juna. Dan Daneen Ammarah da Malikat Ashwaq ne suka ɗan shiga tsakaninsu. Ɗauke idanun nasa yay ya cigaba da takunsa na bajimta. Dan kowa a wajen kansa a rissine yake har su Malikat Bushirat ɗin kansu domin tabbatar da girman da ALLAH ya bashi na shugabanci....
A gaban idon kowa aka wuce da Iffah sashen Tajwar Eshaan ɗin tare da Doctor da zata sake bata taimakon gaggawa, a hankali ƙus-ƙus ya fara tashi a wajen kowa na jimanta al'amarin da jinjina faruwarsa kasancewar duk wanda ya kwana ya tashi a gidan yasan Iffah na kurkuku ne, kuma a yau za'ai zaman shari'a ta biyu, hakama abinda ta faɗa a zaman waccan shari'ar kowa ya jisa. Sai dalilin faruwar al'amarin yau ya saka zukata fara rarrabuwa a kan al'amarin ta, masu ganin a wancan zaman shari'ar ta faɗi waɗan can kalamanne danta kuɓutar da kanta ko sharri, sai a yanzu suke ganinfa akwai ƙamshin gaskiya tunda a karo na biyu kenan ana yunƙurin kasheta. Idan babu rami to miya kawo rami? Wannan shine tambayarsu...........✍️




*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*


*DAUDAR GORA Billyn abdul*


*KI KULANI hafsat xoxo*


*A RUBUCE TAKE Huguma*


*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*


*IDON NERA Mamuh ghee*




_LITTAFI DAYA: 400_
_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_


_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_


_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_


_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_


_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_


_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_


_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_


ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN


MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171


SAI A TURA SHAIDAR BIYAN


09033181070


IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA


09166221261


*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*


+227 96 09 67 63


Books biyar 1250CFA
Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA


KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI.


MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.






*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*
[5/31, 7:46 PM] +234 703 445 5862: 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲




✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)






𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻






𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (15)




........“Wlhy gaba ɗaya kaina ya kulle Akia, shin yarinyar nan wani ƙulli ne take son yi dan ta kuɓutar da kanta saboda tasan babban burin kowa sanin mai kashe matan Abni ne? ko kuwa gaskiya take faɗa? Idan gaskiya take faɗa taya akai tasani mu a tsahon shekaru muka gagara ganowa? Anya kuwa shigowar yarinyar nan cikin masarautar nan tun farko bada wata ƙullalliya ba?”.
Shiru babu alamar Malikat Bushirat zatace wani abu, hakan bai damu Jasrah ba ta cigaba da faɗin, “Al'amarin Mammah ya cigaba da bani tsoro a wannan gaɓar. Anya ba akwai abinda take ɓoye mana ba daya kamata mu sani?”.
A karo na farko Malikat Bushirat ta ɗago ta dubi Jasrah. Sai kuma ta miƙe cikin yanayin ƴar zabira. “Kamar mi kike tunani?”.
“Abubuwa da yawa Akia. Ciki harda halayyarta ta yanzu dake bayyanar da ita a mara gaskiya. Zuciyata na rayamun abubuwa da yawa fiye da yanda kike zato. Abin tambayar anan miyasa take goyawa yarinyar nan baya? Miyasa take son bata kariya? Bayan gudan jininta ta shirya halakawa? Ki duba kiga yanda taƙi bamu goyon baya akan shari'ar nan ita da Ammarah. Yarinyar nan ita aka fara kaiwa sashen Abni, kuma ita ta kaita, batai ko ciwon kai ba aka kai wata daga baya ta rasa ranta. Mi hakan ke nufi? Kaɗan daga cikin zarge-zargena kenan”.
Kai kawai Malikat Bushirat ke jinjinawa alamar gamsuwa da bayanin Jasrah, dan itama wannan tunanin ya jima yana mata kaikawo a zuciya. Taƙi fiddashi ne saboda tuna halayen Malikat Haseenat ɗin masu yawa kafin yau, amma yanzu kam zuciyarta na mata rawa akan a bubuwa da yawan gaske......


★★.... ★.....


Barbushi dake kwasar dariya bayan gama sauraren Miran Jasim da Miran Arshaan ya tsagaita dan kansa ya tamke fuskar tamau kamar bashi ne yayi ba. “Ƙwarai kuna a tsaka mai wuya, tsakar da in har bakinta ya buɗe ta furta ƙarshenku yazo. Abu ɗaya zamuyi akanta, idan mun taki sa'a kun tsira. Idan akasin hakan ya kasance ku zargi kanku....”
Komai basu iya sunce ba, dan zuciyarsu ta fara saka musu shakku akan gazawar Barbushi. Inba gazawa ba taya ƴar yarinya ƙarama zai dinga nuna kamar ta gagaresa. Bayan a da ya musu ayyuka manya da har a yanzu suke taka rawa da bazarsa. Ransu ɓace suka baro wajen nasa, zukatansu na matsanancin ƙuna, kowa kuma da abinda yake tattaunawa da ransa akan matakin ɗauka. Dan ko ana ha maza ha mata bazasu bar Iffah ta cigaba da numfashi ba a wannan gaɓar. Kai hatta da uban gayyar za'ai ƙurun-ƙus a wuce wajen dan sun gaji da gafara sa basuga ƙaho ba. In ba hakaba yarinyar nan zata ɓallo musu aiki....


★★... TA-ƘURYA ★★...


Tun zaman shari'ar nan ta kasa zaune ta kasa tsaye. Ta rasa makamar kamawa. A lissafi bayan boka Ruƙuƙi ta ziyarci manyan bokaye a ƙalla huɗu amma amsa guda suke bata bazasu iya mata aiki ba ta koma ga UWA. Tsabar takaici har kuka tayi, kuka irin wanda ake kira kuka data ɗauka tsahon shekarun da bazata iya tuna sanda tayi makamancin sa ba ma. Jin tsanar Iffah take fiye da komai yanzu a duniya. A kwanaki biyun nan da suka gabata bayan zaman shari'a ta yanke shawarar gwada kasheta amma duk hanyar da tabi sai ta sameta a toshe. Wannan ne ya sake ƙona mata rai da sake jin raɗaɗi mafi girma.
(Ki ajiye komai ki sake komawa ga uwa, karki bari wahalarki ta wuce a banza) shawarar aminiyarta ta sake dawo mata a karo na babu adadi. Jagwab takai zaune, cikin don danne hawayen dake ƙoƙarin zubo mata tace, “Mike shirin faruwa da ni ne haka? Shirin dana ɗauka shekaru kusan arba'in inayi ne wata mitsitsiyar halitta zata zama sanadin rushemin, micece ita? Mi take takama da shi?” hawayen da take dannewar suka zubo saboda radaɗin da take ji. Bata da sauran zaɓi a yanzu face sake nemo UWA. Zumbur ta miƙe tamkar wadda aka tsikara. Ta lalubo kayan surkullen da take kiranyen uwa da su, da ƙyar ta gano robar da hayaƙi ke ciki ta bulbula a burner, take ɗakin ya harmutse har baka iya ganin komai, ita kanta numfashinta har wani fisgar yake tsabar ƙarfin hayaƙin. Idanunta ta rumtse tare da zubewa bisa gwiwunta ta fara hurwa na kiranye cikin yaren surkulle. Amma tsahon lokaci babu alamar uwa, har hayaƙin ya Kore, bata gajiya ba ta cigaba tana mai sake ninka rauninta (Wa'iyazubillah).
Ta share tsahon awa guda tana abu ɗaya babu uwa babu alamar ta. Sai ranta ya ƙara sosuwa, ta dunƙule kanta waje ɗaya tana mai jin hawaye nason zubo mata. Amma ta hana hakan saboda taurin zuciya. Har karfe biyu na dare da masarautar ta nitsa bakajin motsin komai alamar anyi barci, in ma da wanda bai barcinba ya kasance a killace ƙarƙashin inuwar karamin motsi. Waya ta ɗauka tai danne-danne ta kai kunne, a bugu ɗaya aka amsa mata. Kafin ace komai da ga can cikin bada umarni ta furta, “Ki sashi ya jirani a garden”. Daga haka ta yanke kiran. A gurguje tai shiri cikin ɓadda kama ta fice, bazaka taɓa ɗauka mace bace, ta canja kammani cikin kayan jami'an dake aiki bada tsaro a masarautar. Dan haka babu wanda ya maida hankali kanta harta isa babban garden ɗin masarautar dake a ɓangaren kudanci. Wajen nada ƙarancin haske, sai kukan tsuntsaye da ake kiwo jefi-jefi. Da sauri ya fito da ga maboyarsa, ya zube a gabanta yana miƙa gaisuwa. Nuni tai masa ya miƙe batare da ta amsa masa ba. Mikewar yay, kansa a rissine, dan haramunne a garesa kallonta.
Sai da ta gama ƙare masa kallo sama da ƙasa ta mika masa anvelope ɗin hannunta. “Daga daren yau zuwa safiyar gobe ina buƙatar jin kuka, ina buƙatar naji kukan mutuwar Zawjata-almilk. Idan aka samu kuskure kuwa kukan mutuwarka ahalinka zasuyi. A jefata a babban ruwan swimming pool na garden ɗin gabashi”.
“Umarninki shine abin jirana da cikawa”. Ya faɗa da sauri cikin matuƙar girmamawa. Bata sake tankawa ba ta juya tabar wajen. Sai da ta ɓacema ganinsa ya iya ɗago kansa dake a risine yana sakin nannauyar ajiyar zuciya. Ba yau ya fara mata aiki ba, sai dai a shi kansa har yanzu bazai iya sanin ainahin wacece ba. Dan a koda yaushe cikin ɓadda kama take bashi umarni ko ta saka amintacciyar ta ta bashi, sai dai a duk lokacin da ita ta bashi da kanta ya san ba aiki bane ƙarami. Anvelope ɗin ya buɗe, ya wani zaro idanu da ganin makudan kuɗin da ke ciki miƙaƙƙu sababbi ƙal sai ƙamshin sabunta suke. Fuskarsa washe da murmushi ya sumbaci kuɗin, ransa fes da samunsu. Duk da dai yasan bazai cisu a banza ba, dan wannan aikin bazai taɓa zama mai sauƙi ba a garesa kasancewar matsanancin tsaron da kurkukun da Zawjata-almilk ke ciki, amma kodan waɗan nan taurarin dolene ya cika umarni.......


★★......


Ya kai mintuna goma yana kallon yanda masu tsaron kurkukun ke kaiwa da komowa, kowanne kuma da makami tare da shi. Ga haske ƙal tamkar rana dan ko allura ka yar ka duka ka ɗauka abinka batare da ka nema ba. Bugawar ƙaton agogon masarautar da ake iya gani tako wace kusurwar daular ta ruman ya sashi jan numfashi a sarƙe. Karfe uku dai-dai kenan, awa ɗaya garesa kacal na kammala wannan aikin. Dan huɗu nayi zaka fara jin motsin hadimai na tashi domin fara ayyukansu, musamman masu share-share da goge-goge. Zaman ɗammarar ƙugunsa ya gyara da ƙyau, hakama hular kansa kalar kayan jikinsa na ainahin amintattun jami'an dake cikin sashen Tajwar Eshaan. Ya ƙara saita kansa da ƙyau cikin dakewa ya tunkaresu hannunsa ɗauke da babbar jaka. Duk da sanin matsayin masu waɗan nan kayan a gidan gaba ɗaya sukai masa ca. Bai nuna razana ba duk da zuciyarsa na faman dukan dari-ɗari ne. Cikin sake matse kansa ya sara musu alamar girmamawa yana mai miƙa musu I'd card ɗinsa.
“Umarnine da ga shugaba, zan sada kayan nan ga Zawjata-almilk domin sakasu a gobe idan zata fita, na kwashe na dattin dake tare da ita”.
Kallonsa suke kawai suna sake kallon katin domin tantance shi ɗinne a hoton kokuwa. Sai dai hoton ya ɗanyi duhu, duk da kuma hasken wajen dai rana bazata taɓa zama ɗaya da hasken lantarki ba. A dake ya sake faɗin, “Ba tantancewar kaɗai ake buƙata ba. Ya kamata ku kira sashen shugaba domin tabbatarwa, wannan shine cikar aikin masu tsaro”.
Kalamansa sun ɗanyi tasiri garesu, sai dai duk da haka wani ya tubure akan sai ya fara zuwa ya tabbatar bawai kiran waya ba. Dan ko ƙuda an tabbatar musu su kasance masu himma wajen hanashi gittawa zuwa inda Iffah take sai da ƙwaƙwƙwaran dalili. Tsabar ƙarfin hali na hadimin nan, babu ko nuna gezau ya bada goyon baya. Hakan ya ƙara saka sauran jin sun yarda da shi, sai dai wancan ɗin babu alamar hakan. Sai ma tabbatar musu da yay su cigaba da tsaresa zaije ya dawo”.
Tsahon mintuna goma da tafiyarsa sai gashi ya dawo, batare da yace komai ba yay masa nuni da ya shiga. Wata irin wawuyar ajiyar zuciya ya saki da ɗan kashe ido wa jami'in da a yanzu yake ta faman sinne kai kamar wani munafuki. Sauran basu damuba dan su dama sun aminta tun dazun, dan haka ya wuce hankali kwance.


Tana tsaka da ɓarawon barcin da ya sace ta bayan ta idar da sallar da take tsaiwar yi duk dare domin miƙa kukanta ga UBANGIJI taji kamar numfashinta na fita a fisge, firgigit ta farka da ƙoƙarin kai hannunta saman hancinta, sai dai aikin gama ya gama dan ya riga ya shaƙa mata abinda ke cikin handkherciff ɗin. Duk yanda taso sake yunƙurawa hakan ya gagara sai ma jikinta dake saki baki ɗaya. Daga haka bata sake sanin inda kanta yake ba.
Jikinsa na ɗan ɓari ya sakata a babbar jakar hanun nasa tare da zuge zip ɗin. Bai tsaya ɓata lokaci ba ya saɓeta kasancewarsa ƙaƙƙarfan mutum babu alamar da zai tabbatar maka mutum ya ɗakko. Gashi dama Iffah ta rame sosai duk da dama ba wata mai jiki bace can. Sai dai kuma duk da hakan ƙarfin haline kawai irin na masu busashshiyar zuciya dan sumar da itan da yay jikinta duk ya saki ta sake nauyi. Sai da yay musu sallama da sanar da su ya kwaso kayan dattin wajenta ne bisa umarnin Tajwar Eshaan sannan ya wuce.........✍️


Hummm



*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*


*DAUDAR GORA Billyn abdul*


*KI KULANI hafsat xoxo*


*A RUBUCE TAKE Huguma*


*RUMBUN K'AYA

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login