Showing 123001 words to 126000 words out of 131003 words
Chapter 42 - DAUDAR GORA BOOK 2 PDF COMPLETE BY bilyn Abdull .txt
A mamakinta sai jin tattausan tafin hannunsa tai a saman nata ya zare jakkar hanunta, cikin takun nan nasa daddaya cike da izza ya rabata ya wuce.Numfashin da ta rike a kirji da makoshinta ta saki da karfi, sai kuma ta bude idanunta tabi bayansa da kallo har ya bace ma ganinta. Dan tarin dake neman rike makoshinta ta fara, dole ta nufi dining room ta samu ruwa ta sha. Daga haka takai zaune tana sauke numfashi. Sai da ta dan samu nutsuwa sannan ta tashi tabi bayansa tana addu'a a ranta.
Bata da tabbacin a inda yake, dan haka kawai ta nufi inda zuciyarta ke raya mata da fatan ALLAH yasa ba'a nan din yake ba. Sai dai kuma da alama ta taki rashin sa'ar. Dan tana shiga taci karo da shi zaune a kan gado da lap-top kan cinyarsa. Dakin babu haske mai karfi, sai hasken screen din laptop dinne ya haske kyakykyawar fuskarsa ma'abociyar kamewa da
kwarjini. Sum-sum ta wuce hanyar bathroom tana dan turo baki. Sai da ta gama tsaftace kanta ta fito cikin bathrobe, yana a yanda ta barsa, hakan sai ya bata damar tsayawa ta bayansa ta shirya cikin kayan barci masu dan kauri da turarruka. A take kamshin dakin ya sake karfi. Fahimtar kamar fushi yake ya sata takowa inda yake cikin sanda, zaune takai gefensa amma ya share abinsa bai ko nuna ya san da zamanta ba. Cikin dan bata fuska da jin haushi sharetan da yay ta zame ta kwanta tare da dan ture lap-top din tasa kadan ta daura kanta a cinyarsa ta kwanta. Da kyar ya iya cigaba da rike kansa yaki kulata. Ganin ya cigaba da aikin dai ya sata kurama fuskarsa idanu, sai kuma ta kai hanunta kan kwantaccen gashin kumatunsa ta fara masa tafiyar tsutsa. (@) Yarinyar nan da tsokale-tsokalan masifa kike * ). Yayi kokarin ganin ya danne ya cije amma aikin na neman gagararsa, baima san sanda ya cije lips dinsa da rumtse idanunsa da dan karfi ba.
" ALLAH kayi hakuri bazan sake ba.ALLAH banyi zaton zan dade ba na samu Mammy batajin dadi ne fa".
(Yarinyar nan sai ta kasheni zata huta) ya fada a zuciyarsa dake faman bugawa da sauri-sauri cikin kaikawo. A hankali ya janye hannayensa dake sarrafa lap-top din ya daura na damar kan nata dake cigaba da shafa fuskarsa. Rikesa yay yana kokarin son gain ya janye amma sai tai wani irin juyi ta maida fuskarta saitin cikinsa ta sakalo dayan hanun nata a bayansa ta kankamesa.
'"Kasheni kawai ki huta" ya fada cikin subutar harshe jikinsa na saki gaba daya.
Iffah da bata fahimci ita mima yake nufin ba ta kyalkyale da siririyar dariya har yana jin dumin numfashinta a kan Fatar cikinsa. Ita a nata shirmen kankamesan da tai ne yaji zafi. "dan na kasheka dawa zan zauna?". Ta fada cikin dariyar tana kara cusa kanta jikinsa. Dole ya ajiye lap- top din ya kai kwance tare da dagota gaba dayanta ta hau saman jikinsa. Fuskarsa take kallo cike da dakewa kamar yanda shima yake kallon tata idanunsa a shanye. "Miyasa baki son a zauna lafiya?". Ya fada a hankali yana sake kankance idanunsa cikin nata. Idanun ta juya tana shagwabe fuska da dan cuna masa lips dinta. "Toni mi nayi? In dai zuwa wajen Jaddah ne ai nace kayi hakuri".
Dariya maganar ta bashi amma sai ya gimtse baiyi ba, ya dan tabe baki da tsatstsareta kaifafan idanunsa. Cikin dan dage gira
"Har na kai ki?".
"Hu'um, ni a suwa kuma, kana kallon kanka a mirror kuwa da kyau?. Badan kar ace nayi karya ba sai nace kafi kowa kyau a kasar ruman". Harga ALLAH ta bashi matukar dariya yanda ta fadi maganar cike da yarinta, yayinda zuciyar sa tai wani irin shiga farin ciki, domin kuwa bawai yafi kowa kyau din bane kamar yanda ta fada a zahirance, ya fahimci ta fara caukar karatunsa son sa ya fara shiga zuciyarta. Domin abinda kake so ne kawai kake ma kallon kasancewarsa a sama dana kowa. Shi kansa duk da yasan akwai kyawawan da suka fita ganinta yake samada kowa saboda kawai ita kadai yake so,kyawuntane kawai ke kayatar da shi. Bai fahimci murmushi yake ba sai da yaga yanda ta kura masa ido. Ya dan waro idanun waje alamar miye kuma, ita kuma sai ta girgiza masa kai tana murmushi da dan kauda idonta dake cikin nashi."Murmushi na maka kyau, gashi kuma baka son yi".
Hannayensa duk biyu ya doro a saman bayanta ya sake matso da ita ta kwanto jikinsa sosai, fuskarsu ta koma gab-gab har hancinsu na gogar na juna. "A komai k ta dabbance my sohaa".
"Kaima haka ai".
Ta fada tana dan sumbatar lips dinsa, sai tai saurin jan jikinta zata sauka dan sai da tai babban kokari wajen masa kiss din, amma kunya take ji. A hankali ya rikota bayan ya fisgo numfashinsa da ya nema kufcewa da kyar.Mirginasu yay suka koma saman hannayensu suna fuskantar juna, batare da jiran wani abu ba ya manne lips dinsu waje guda..
🥱🏃♀️Anfi karfin alkalamina anan.
Babu alamar wasa tattare da shi, da ga tsayen da yake a kofa yana dubanta a yatsine ya ce,"Kifadi abinda zaki fada ina jinki, dan bazan wuce minti ashirin ba anan".
Rai bace Ameera Haifah ke duba Miran Arshaan mai maganar, tai karamar kwafa da tabe baki," Arshaan kenan, idan kana ganin Kanada mafitar da zata iya kwabemin ne ma,dan har da kai sai dai ka shirya mu duka zata kwabe Dar harda kai, idan har ban tsira ba da ga yarda ka maida Jasim kaima zan bude maka aiki ne. Zan kuma tabbatar maka na fika iya makirci dan mace sunana idan ka manta".
"hhhhahh! Ni kike tunanin zaki iya budema aiki Haifah? to ina baki shawarar fita a hanyata da ga yau, in ba hakaba why zan kasheki na binne gawarki a cikin masarautar nan kuma na kashe banza".
"Oh really? To Dan ALLAH ko zaka gwada ne? Nace ko zaka gwada kashenin muga!!!".
Tai maganar cikin tsananin hargowa tana wani hahhankada kirji a gabansa. Wani irin tafarfasa yaji zuciyarsa nayi, dama a wuya yake, a fusace ya kaima wuyanta wani irin shegen shaka na tashin hankali. Cikin kankanin lokaci manyan idanunta suka sake yowa waje ruku-ruku, ga kakarin mutuwa da ta fara da mutsu-mutsun ganin ta fisge hannunsa da ga kan wuyanta. Sai dai kuma hakan ya gagara, dan karfinsu ba daya ba. Tafiya ya dingayi da ita cikin rufewar ido har jikin bango, ya kara matse wuyan da karfi tare da wajigata ya buga kanta jikin bango. Wata irin wahalalliyar kara ta fasa da ta jawo hankalin Jasrah dake daki kwance ta farka tana nemansa, dan su suna'a falon baki ne kasancewar cikin shigar badda kama Ameera Haifah tazo a nufin bako tasa amintaccensa imata iso saboda baya daga mata waya yanzun. Sai da yazo yaga itace. Gaba daya idon Miran Arshaan da alama ya rufe, dan tuni ya sake jijigata ya buga a bango, jini ko ya samu hanya ya balle.
lya karfi da budewar murya Jasrah ta daddage ta kwalla wata irin kara na firgita, dan ganin jini ya wanke fuskar Ameera Haifah ga Mijinta shake da wuyarta sai ta dauka ta mutu.Wani irin wancakalar da Haifah Miran Arshaan yayi yana duban Jasrah data yanke jiki ta fadi. Har rige-rigen shigowa hadiman masu tsaron sashin keyi, ganinfa abinda ke faruwa tuni wani ya firgita ya kyalla a guje ya sanarma jami' an tsaron gidan dan wannan faninsu ne...✍️[6/1, 1:18 PM] +234 703 445 5862: DAUDAR GORA
Book 2
Chapter: 62
...…….Tofa dan-dan-dan, da alama dama irin wannan damar Iffah ke jiran samu, dan cikin
kankanin lokaci duk da darene masarautar ta dauki dumi, yayinda aka kwashi Ameera Haifah da Jasrah zuwa asibiti, Miran Arshaan kuwa da jikinsa ke tsumar toro gaba daya ya gama
gigicewa, dan sai zuwa yanzu ya dawo a hayyacinsa. Tuni kuwa ya tsure da ganin abinda ya aikata, sai kawai ya bige da borin kunya.
Sudai jami'an babu wanda yace da shi komai,sun tattara komai akan sai zuwa da safe za'a kai
maganar ga Shahan-shan. Abu dai mafi daure kai shine miye tsakaninsa da Ameera Haifah din
har haka a irin wannan tsohon daren, dan a kala fa karfe biyu na dare kenan.
大大
A lokacin da duk ake waccan dambarwar anan ta-kurya ce ke ganawa da manomin ganyayyakin shayin Shahan-shan. A cikin badda kamarta take, dan haka shi bai san wacece ba.Hasalima magana da Jazaa sukeyinta ita dai tana hakimce komai batace ba. Da farko yaso ya, amma ganin wata lukutiyar jakkal da zinare ga barazanar halaka zuri'arsa kunne tuni ya mika wuya akan an gama. Malikat Bushirat tai murmushin basawa ta dauke kanta.Kwalayen ganyen shayin da uwa ta kawo kan ya fara kaiwa sashen Shahan-shan din kafin wanda zasu noma ya tsiro nan ma Jazaa duk ta ajiye masa su har uku..
Hummm🥱🚴
**
Zaune take bayan idar da sallar asuba, yanda ta kurama waje daya ido zai baka tabbacin tunani take. Sai lokaci zuwa lokaci da takan saki murmushi, harda cusa kanta cikin kafafunta kamar mai jin kunyar wani da ke gabanta. Ta dan jima a hakan kafin ta mike kamar wadda aka tsikara idonta kan agogon dakin. Tasan yanzu kam yana Gym ne tunda har ya kai yanzu bai shigo ba. Itama tsaf ta shirya cikin kayan motsa jiki ta, sun mata matukar kyau da fidda ainahin surarta komai dam. Dan wani bana ta saka a kanta siriri kalar kayan sannan ta daura talda daura after dress saman sport wears din. Shiru tai tana bin Gym din data shigo da kallo, babu kowa komai ma a kashe yake, da alama banan yazo ba. Fuska ta dan bata da tura baki gaba, har zata koma sai kuma ta tuno randa ta samesa a can sama yana wasan takobi shi da Miran Arshaan. "Yes!" ta fada tana wani kashe ido daya da yin juyi sannan ta nufi can cikin takunta na nutsuwa
Shelanta sunanta da na'urar kofar tayi kamar yanda ta saba duk wanda zai gitta ta cikinta ya sashi dakatawa da jujjuya takobin ya juyo a hankali. Tuni hadiman wajen sun jujjuya bayansu sukam. Yanda take takowa garesa kamar wata tarwada yasa shi gagara cigaba da abinda yake yi.
"Good morning
Ta fada cikin rashin tsoron nan nata na bayyane tana daura yatsanta saman tsintsiyar hannunsa ta zano a hankali ta dire kan kyakykyawar takobin da ya rike rikon kasaita da kwarewa. Da kallo kawai ya bita batare da ya amsata ba. Itama sai bata nuna tasan yana kallonta ba ta zare takobin a cikin hannun nasa fuskarta da murmushi. kin sakar mata yay, sai ma cike da salo yay wani irin juyata bata ankara ba ta dawo saman jikinsa takobin a wuyanta sai dai bai daura a kan fatar jikinta ba. Iffah jitai zatayi fitsari na neman kufce mata tsabar yanda ta tsorata har yana jin yanda jikinta ke tsuma. Dan dukowa yay kansa a kafadarta bakinsa saitin Kunnenta ya furta, "k takamarki tsokala ko?".
Idanunta da ke kawo kwalla ta shiga kikkifatawa da girgiza masa kai a hankali. Cikin rawar harshe ta ce, "Eshaan Akhi na tuba".
"Daga baya kenan".
Ya fada yana kara matsar da takobin jikinta gaf.Sake tsurewa tai. Shiko sai faman danne dariya yake.
"Ki fanshi kanki".
Da sauri ta ce, "Da mi?".
Dan lumshe idanunsa yay ya bude yana mai busa mata numfashinsa a wuyan. A dan salon tabe baki ya ce, "Komai ma".
"Shike nan, shike nan naji na amince, amma dan ALLAH ka janye sau daya fa ake mutuwa, rai daya ne". Yanzu kam kasa daurewa yay sai da murmushi ya subuce masa. Ya janye tare da dauke hanunsa dake saman cikinta ya juyota suna fuskantar juna. Hawaye fa da gaske sun cika mata idanu. Da kyar ya iya gimtse dariyarsa. Idanunsa ya maida ga hadiman wajen da suka juya bayansu tun dazun, dasss daga yatsunsa sau biyu, cikin abinda bai sakkani ba sun bar wajen a ka barsu su biyu. Da baya-baya yaja zuwa table din gefensu kadan,wata takobin ya dakko a cikin kyakykyawan kufanta ya dawo gabanta, hanunta ya riko ya daura mata takobin sannan ya zare abayar ta ya ajiye tare da mata alamar bismillah. Kamar ba ita ta gama hadiyar hawayeba yanzu ta wani dubi takobin shima ta dubesa ta dan murguda baki. Kansa ya maida gefe yana murmushi, tare da ajiye tsinin tasa takobin bisa kasa ya fara zagayata. Yana a tsaye daga bayanta ya juya takobin cikin salon tsokanarta kawai a bazata yaji tama kanta garkuwa. Idanu ya dan waro waje, da bin takobin da kallo kawai ta zuke ta maida masa harin. Cikin zafin nama ya kare kansa shima mamakinta na nan kasheshi.
"Dama kin iya wasan takobi?".
Ya tambaya da mamaki idanunsa cikin nata Murmushi ta sakar masa da kara zukewa ta kai masa suka ta kasa. Nanma baya yay cikin zafin nama yay wata irin bahaguwar zukewa. Dariya tayi da dire takobinta ta fara zagayashi kamar yanda ya mata dazun, cikin salon dage gira da kashe masa ido daya ta ce, "Zaka cigaba da tsayawa tambayar a ina na iya ne na kaika kasa?". Tsaiwarsa ya gyara da kyau yana murmushi da kamo lips dinsa na kasa ya tura ( paki suka cigaba da zagaye juna. Sai kowa ya yinkuro cikin ragabza akai tsaiwar zakaru. Cikin kwarewa da nuna bajinta ga kowa suka cigaba da wasan mamaki na nan kashe Tajwar Eshaan a zuciya. Duk da ya fita kwarewa yanda ta iya din itama na bashi mamaki matuka.Sai dai ya bita da salon saffa-saffa yanda bazai cutar da ita ba dan karfinsu ba daya bane
Tamkar wanda aka jeho kawai sukaji sallamarsa a kusan tsakkiyar wajen, dan kamar sai da ya matso gab da su ne ma yake sallamar.Da ga shi har Iffahn juyowa sukai, musamman Iffah da kamar wadda ta ma firgita, dan jikinta har rawa yake wajen neman abinda zata yafama jikinta, tsabar yanda ta rikice tama ki ganin after dress din nata. Bata san yanda akai ba, tayaya ma kawai jinta tai a jikinsa, jin kamshinsa ya sata kankamesa da sauri tana kokarin boye kanta.
"Miya kawoka nan babu neman izini? Kabar wajen nan Aam!!" ya fada a matukar tsawace shima yana kankameta da juyawa da ita suka bama Miran Arshaan da yay mutuwar tsaye baya.
"I say out!!!".
Ya sake fada da wata irin mummunar tsawa mai karaji da har jikinsa na girgizawa, ga idanunsa sun yi wani irin kadawar masifa kamar wanda ake kadama gangi. Miran Arshaan har tuntube yake yi tsabar firgicewa da tsawar Tajwar Eshaan din. Bai taba sanin yaron nan dan bala'i bane irin yau. Next surar yarinyar nan ta matukar kidimashi, ashe abinda Jasim kenan ya gani kullum yake cikin sambatu da santin yarinyar, shi manemin matane tun yana da kananun shekaru, yayi mu'amula da mata kabila daban-daban a duniya da bai san adadi ba. A sanda yake ji da rashin ji har order din mata suke ta online, yaga matan ma da sukafi Iffah kira amma wannan jikin dabanne. Ji yake yama kasa cigaba da tafiyar yanda jikinsa ke bari, sai kawai ya samu bango ya manne yana sauke numfashi gudu-gudu. (Humm)
Yanda Iffah taji zuciyarsa na bugawa da sauri- sauri kamar zata ballo kirjinsa ta fito ga tsawar da yayma uncle din nasa ya matukar sake rudar da ita fiye da tsoron ganinta a yanda take da tai gudu. Kanta ta shiga jujjuya masa da kankame hanunsa, sai kuma ta dan dago ta kalli fuskarsa. Ta wani irin kadawar masifa jazur hakama idanunsa gaba daya sun juye mata cikin canjawar kammani. Dole ta maida idanunta kasa jikinta na rawar toro da yanayin nasa. Jitai kawai ya wani irin fisgar hanunta zuwa hanyar kofar da ta shigo, bai tsaya da ita ko ina na bedroom. Yarfar da hannun yay yayi shigewarsa bathroom. Da kallo ta bisa hankalinta a tashe itama, dan ita kadai tasan kalar wutar masifar data gani a cikin idanunsan. Raya mata zuciyarta ta dingayi kawai tabar dakin nan karma ya fito ya sameta...
Koda ya fito bayan tsahon lokaci da ya dauka a bayin bai nema Iffah ba dan yana bukatar kadaici saboda ya shiga bacin rai, shi mai kishi ne, tabbas yanada matukar kishin da yake ji akan yarinyar nan zai iya badda mutum. Wata irin tsanar Miran Jasim da Miran Arshaan yake ji irin wadda bai taba ji a kansu ba a dukkan abubuwan da suka aikata masa a baya, ga wani irin sara masa da kansa yake yi na ciwo. Jikin window ya karasa hannunsa goye a bayansa batare da ya cire ko bathrobe din jikinsa ba yana kallon sararin samaniya da ke hada was irin manyan bakaken giza-gizai na hadari, du da safiyar tayi sosai garin yaki washewa sai ma rinewa yake sake yi kamar za'ai wata sabuwar magriba. Kiran waya ne ya shigo, ya share kamar bai jiba, aka sake kira nan ma kamar zai share sai kuma ya nufi wayar a fusace ya daga. Sai dai yay shiru baice komai ba. Da ga can Sayeed Fayzul-haq ya gaishesa cike da girmamawa.Haushin kowa yake ji, duk da bashi yay lefin ba ya samu rabonsa. Dan maimakon amsa gaisuwa a dake ya ce, "Ya akai". Dan rikicewa Sayeed Fayzul-haq yayi, amma sai cikin dauriya da sake kankan da kai ya shiga masa bayanin abinda ke faruwa tsakanin Miran Arshaan da Ameera Haifah tun a daren jiya. A zafafe ya ce, "Kaima jami'ai magana su kamashi a hadashi da dayan sakaran, a saka na'urar daukar magana cikin akin kurkukun kuma.Itama Haifah din Doctors su sallameta idan babu wata matsalar data shafi lafiayarta jami'an tsaro su rufeta",. Daga haka ya ajiye kan wayar yana huci. Duk yanda yake kokarin rike kansa da bin komai a sannu ya fahimci ba haka makiyansa suke bukata. Fushinsa suke son gani, ainahinsa suke bukatar ya nuna musu. Ya barsu da yarinyar nan ne kawai domin shi din shugaba ne, shugaba kuma da hadiyewa aka sansa, amma tunda so suke shi ya fito musu a Eshaan In Haysam Abdul-majeed Aliy Qutb din sa to yanzu ne wasan zai fara..
😆🥱TOFA ran yan maza