Showing 3001 words to 6000 words out of 35109 words
Chapter 2 - AFIF BOOK COMPLETE DOCUMENT Writing by oum yasmeen.txt
time (long time kundai San turan cin y'an daba basu iyaba suce sai sunyi) yana shigarmin hanci da k'udundune yace.
"inaso in fyeto dashi"
"nabaka dama"
yace.
"Godia nake oga yahad'a hannaye alamar jinjina"
Jagwa yace.
"karka damu aikai nawane zanburuta"
tuni zanburuta yanufi kan ali vigilanty AI kafin kace mai tuni yasaki futsari.
Cike da tsoro ali yace.
"dan girman Babar ka tasallah dillaliya Kai hak'uri"
tuni jikinsa yayi sanyi domin duk abunsa yana son mahaifiyar sa yace.
"nahak'ura amma da sharad'in inka k'ara kayan wankina zanbaka kaimin dana _mahaifiyar_ kayarda...?"
Cikin rawar baki yace.
"nayarda bakomai wllh ko yaya jagwa aikasan ni maibiyayya ne agare ku"
Jagwa yace
"To tafi k'wallan shege ko wasa naji wata magana abakin malam ko inna wllh yazaro harshan sa yalashi huka"
Jagwa yace.
"Wallahi sai kasan dani kake zance yasin saina maka b'alli b'alli"
"totoo bazama takai da hakaba wallahi baki na k'anin k'afata"
Jagawa yace.
"wannan kuma kai tashafa domin yasin naji wani abu hmmmmm ko mai taba ne zaidawo daga lahira sai nayi maka abinda nayi niya we"
yace.
"to bama tsala."
" wama ya biyoka ka tsoratar da yarana..?"
"daman abokanan rufa'i ne dan uwan mu suka zo gidan mu suna yimana abinda be dace ba shine nayi musu na siya basuji ba har d'aya da cikin su yace su biyoni suyimin duka"
"Shugaban vigilanty kenan nasan halinka inbaka Kula suba bazasu yimaka komai"
cikin rawar murya yace.
"hmmm gaskia nafad'a maka yaya jagwa"
"dahallacan ware ko inyi fil'la fil'la da kai katsaya kana cikamin kunne"
to yaya jagwa bara intafi. nabarku lafiya nagodai da afuwar da kukai min"
"Yasin kak'ara cemin yaya sai na b'alla maka k'afa
karasa ta ya wan vigilanty"
Ali vigilanty yace.
"to jagwa nadai na insha Allah natafi yana ruk'e da wandon sa yana d'igar fitsarin dayayi"
*cikin gidan maitaba kuwa*
Inna hadiza ce tafito tace
"yau mai zan gani?"
y'an daudo agidan nan kee zoki ban kud'ina cikin yananin.''
Zarah tace.
"to inna"
"takawa takeyi tamkar kazar da k'wai yafashe mata aciki taci ro kud'in a k'ugunta ta miki mata"
zarah ta durkusa tace.
"gashi inna"
karba tayi tana k'irgawa cikin fusatar zuciyata ta finci kota tace.
"nizakiyiwa d'iban albarka baki saiyar minba ko?"
Inna hadiza tace.
"kuma kwaiyah daya tabata wllh duk inda naira ashirin take saikin nemomin..?"
Zarah tace,
"dan Allah inna kiyi hak'uri wllh nazaga ba'a siyaba"
cikin tsoron abinda. zaibiyo baya tace,
"ba b'ata tayiba duna ne d'an gidan kahu Manu ya d'auka"
Inna hadiza tace,
" wllh bazan yardaba duk inda duna yake saikin nemoshi yaban kud'ina"
tana fad'ar haka
ta kifa mata mari jikake Tass Masha Allah irin matan nan ne masu kama da maza tana da k'iba sosai.
cikin ikwan Allah lalu'arta ta tashi tayanke jiki ta fad'i
kafin kace me.
"tuni y'an gidan sun dare ganin haka y'an daudo dashi mara lafiyar suka fita aguje suka shiga d'akin jagwa suka rufe..
"inna hadiza kuwa dayake tana da k'iba duk sun gudu sunbar ta tarasa inda zata sa ranta duk addu'ar datazo bakinta tayi take..
Tun tayi azuci har nadawo na fili jika ke tac.
"alu'anbaki wauzal labbaika humma labbai sunma ina alaina bayyana.''
duk da tsoran da suke cikin be hana y'an daudo shek'ewa da dariya ba.
_tofa yau inna hadiza taga ta kanta_
Bishira tace.
"Hhhhhh wannan tsohuwa da abin dariyah take yo ko daban yi ilimin *addini* ainasan wannan ba addu'a bace"
cikin gida kuwa inna laira ce zaune akan sirikar ta baraka bama tasan ta zauna ba sabida tsabar tsoro batasan lokacin data Saki tosaba tace.
" wllh fa'izah ta cucemu ta haifa mana jaraba ni tsorona Allah kar aljanun nan su kama mu"
Hindatu tace.
"kedai yaya bari duk yaya babbace ta jawo mana Allah isa su shanye mata kafa"
"wani uban ihu tasaki "
ai kowa saiyayi shiru gidan yayi sit tamkar ruwa yacin yesu.......✍️
*AFIF*
Oum yasmeen
*My first novel is return back*
Chapter 28-31
https://whatsapp.com/channel/0029VaLdFeg4SpkQ9xyW5c0k
"tuni inna hadiza takara
diriricewa"
tarasa inda zatasa kanta domin inba idon ta kizo yake mata ba gani tayi kan zarah ya dawo baya haka ma hannayanta
"dakin jagwa ta nufa saidai me arufe taji shi"
cikin daga murya tace.
"larai hindatu kofito kucece ni"
jinshiru inna hadiza tace.
"kona jina kukai min jishu..?"
"kahu Manu ne yashigo yana saba babbar riga duk Ta kod'i da alama yadawo daga yawan ba'arsa gawani ta kalmin yafi karfin kafarsa gawata hula yawa yakifa kamar kwano"
kahu Manu yace.
"gafaran kodai masu gida ga shugaban marukan garkun kowa yace bani ba nima ince dashi bashiba saini d'an maitaba ikwon Allah saini waddah yake zuwa gidan mai gari yimai kirari cau cau wllh anjada ni an,barni saini waddah yaje
*MASARAUTAR ZAKI*"
"mai idonshi zai gani zarah yagai akwance kamar matatciya amma hadiza anyi mara imani yanzu marainiyar Allah ta'alah kikai wa haka?"
GA yarda kikai mata walmukalifatu
jinshiru kahu manu yace.
" tsahare tsahare tsahare"
cikin fusatar zuciya yace.
"yau kenan iskancinki ya motsa to wllh kifita a idona in rufe"
"duna ne yashigo yana shan rake"
duna cikin dauki yace.
baba daga gidan su bintalo nake
"cikin jin kunyar karya yajanyo rigasa tazarce fa'ar shadda ce ajikin sa amma takuma milk ya rufe fuskarsa wai yaji kunya,
duna yace.
"babantan yace infito"
cikin kunar rai kahu manu yajuyo yace.
"ashe duna haukan naka har yakai haka bansani ba?"
duna yace.
"baba hauka kuma"
kahu manu yace.
" yo duna inba hauka ba ina kaga kud'in aure ko gona baka zowa ko nayi maka karya ne...?"
duna yace.
"baba tace zata dinga ciyar da ni tunda tana sana'a kuma akwai tuminin takaba na tsohon mijin ta da akaraba akabata"
tuni kahu manu gumin ya wanke mai mutsassiyar fuskarsa
domin yagane shida d'an sa suna son abu daya
"cikin xuciyar sa cewa yake kaga shegen yaro ina jira ta gama takaba inje ya rugani zuwa ashe bana lissafi dai dai"
haku manu yacire hulalsa ya sharce gumi yace yace.
"duna ina kai ina bazzawara duna ba y'ar gidan malam d'an ladi bace tsohon driver?"
tuni duna ya zunb'uru baki yace
"Eh baba itace"
Kafin kahu manu yace.
"wani abu tuni zarah ta kara zuba wani ihu tare da yin kar karwa har anajiyo sautin hakoranta
duna ne ya kalle kahu manu tuni sukayi idu hudu da kahu manu"
kahu manu yace.
"duna me nake gani ?"
cike da tsoro duna yace.
"baba na kaga abinda nagani ko idanu nane suke fad'a min karya ?"
Kahu manu yace.
"Duna zara'u ta kanan nad'a wllh"
Cikin tsoro duna yace.
"Baba ashe ba karya su inna suke fada ba dasu kece wa zarah tahadu da cutar nan ta aljanu wato *farfadiya*
Kahu manu yace.
" hmmm duna mune mi gun tsira tunkafin ta shafa mana domin ni wallahi ban shirya mutuwa ba yasin inta kaina kaima kaita kan ka"
Inna hadiza kuwa tasami makafa dakin tsahare tashiga tahau kan wata a kwaiti ta dakin tsahare
"tsahare kuwa tana cikin akwaiti abin duniya ya isheta domin ta rantsai in komai ya lafa tana fitowa saita bugawa inna hadiza tab'arya"
topa gidan malam Yusif mai taba suna cikin wani hali yaya zata kaya da kahu manu da dansa duna
Cikin ikwan Allah kuwa komai ya lafa itama zara tashi tayi da alama bama tasan tayi ba
cikin dakin ta tsahare kuwa inna hadiza yace ta tashi tana sharce gumi
Inna hadiza tace.
"we yau Allah yayi da kwana na agaba"
mik'ewa tayi aikuwa tsahare ta fito a fusace tana neman inda tasa tab'arya domin tarantsi inbata ludawa hadiza ba yau bata haifuba
Ita kuwa inna hadiza bata luraba can taga nema yayi yawa ta magantu
Inna hadiza tace.
"kedai tsahare ba arabaki da abin haushe yanzu makike nema ne ?
tsahare tace.
" Hmmm kibari inna fito da abinda nake nema kya' gani ganin idonki"
Cikin fusata inna hadiza tace.
"Tsahare ni kike fad'awa haka ko...?"
aikafin ta karasa taji saukar tab'arya agadon bayanta wata ƙara ta saki
Tsahare sauke wani wahallan numfashi tace.
"Ba keba mara hankali baki san da mutum aciki ba kika zauna wato kina so ki kasheni ko?"
Tuni inna hadiza ta dafa bayanta ko magana ta kasa sai dai taci al'washi saita buga tsahare da kasa
Jin bata tanka ba tsahare tace.
"So kike in mutu to ta Allah bataki ba kika wani sh'irgamin duwawunki masu kama da dala saboda girma kina so in mutu ki aurawa manu yar uwarki ko..?"
Karasa warta keda huya inna hadiza ta dagata sama abinka da ba wata mai kiba ba irin siraran matan nan ne zubin taliya yar murji
Jika ke tim ta bugata akasa Allah yasa ta sauka akan gadon k'arfenta
ciken nishin wahala tsahare tace.
"Wllh dani kike zance sai na kara buga miki tirmi"
Inna hadiza tagyara d'aurin zanin ta tace.
"Hhhhhh tsahare kenan kin manta da koni wace ko?"
"to wllh in kin manta bara in tuna miki lokacin muna da jini ajika ni nake miki duka "
tsahare ta saki ajiyar xuciya bawe ta hak'ura bane aa ajiru zuwa rafi wataran tulu zai fashe
kahu manu ne yashigo yana buga kofa yace.
" keeee tsahare wannan wanne irin tsorone kunbi kun k'unshe adaka ina zuwa naga abinda ke faruwa na nad'ai hannun rigata"
"ganin tsahare da hadiza sunyi shiru alamar zancan nasa yasami matsuguni a zuciyar su
kahu manu yace.
" dana nad'ai hannun rigata nafara ce musu
wllh k'arya kuke ni ne dan gidan malam mai taba mai tsittin goma sha biyu zaku nutsu ko saina ko naku ai tuni sukai shiru "
inna hadiza tayi k'arfin halin cewa.
"manu ba'a tab'a mutum inyana farfad'iya wllh mutum dauka yake yanzuma gun datayi sai anzuba toka"
Kahu manu yace.
"Mahaukatan banza waya fad'a muku wannan zance ko kowa zai d'auka banda mu jiniin malamai kakana *MALAM SULE ME TURAK'AR YASIN*
"ganin sun nutsu suna jinsa yana kwararo musu karya domin be bud'i ido yaga kakansa ba koshi kansa mahaifinsu mai taba besan shiba ya mutu
kuma sana'ar sa itace saida tawada ba malami bane"
kahu manu ya kara da cewa har d'aukan aljanu yake ya bugasu da k'asa
har aik'en su yake yasin abin sai waddah yagani
"k'arasa warsa keda huya duna yashigo yayiwa su inna alama da ido suyi shiru ya rufe mai ido da wani farin yadi dayake har ankira sallah magariba to gari yayi duhu abinka da kauye "
duna ya mak'e murya yace.
"nine Shugaban aljanu *ni sarki turk'wa* naji kana anbatar sunan kakana sule lafiya kana ihu yasin saina shanye maka allon kafad'a"
Kahu manu yace.
"kuyi hak'uri Dan Allah wllh bansan sunan kak'an kabane a yimin afuwa"
Duna yace.
"Muba musan wata afuwa ba zab'i daya yarage gareka ko yau ka kwana bak'ai ba bacci ko mutsutsai maka ruwan kwakwalwa "
Duna yamak'e muryah yace.
"wanne ka zab'a?"
Cikin rawar murya kahu manu yace.
in kwana banyi bacci ba
Jika ke duna yasaki wata mahaukaciyar dariya yace.
"ba iya nan yatsa ba kaso auran d'anka da yar gidan malam d'an ladi muga kana so ka hanashi in kak'i zan hadaka da d'an autan aljanu ya cire maka hanji ciki karayu ba hanji "
kahu manu yace.
hakama bazata faruba na aminci zan shig'e mai gaba ayi bik'n
Duna yace.
Hhhhhhhhhhh tsoho kanasan duniya dayawa to rufe idon ka zantafi
Cikin rawar murya kahu manu yace.
"To to to"
" cikin sanda yafuce ad'akin"
Dankin jagwa kuwa koda komai yalafa yand'audo su kace sunga gun zama
suna ciki ba waddah yayi tunanin zuwa yayi sallah sai maida zance suke
"Wani ub'an gangi aka fuga ga ihun karunnuka nan alamun cewa jagwa yashigo cik'in gid'an kai tsaye d'akin sa yanufa sai dai me zai gani ?"
Cikin cije laib'e jagwa yace.
"lalle yau layira zatayi baki Dan wllh yasin ba waddah zan bari yafuta acikin ku"
daya daga cikin yada kata da cin cingum yace .
yo kuma bakace mufita ba ba inda zamu munga gu wllh yana yarfa hannaye sunci zobuna da awarraro yayi fari da idonsa ya saki kwai jikake tush kas
"Bishira ta kama zancan da cewa .
Katambayi d'an uwanka ya muk'ai dashi yasin karo damu badadi
Jinjina k'ai jagwa yayi yafuta daga d'akin yasa muk'ulli ya k'ulle kofarsa ya fita kirawo yaran sa ...........✍🏼
*AFIF*
*Oum yasmeen*
*My first novel is return back*
*The writer of BINTA YAR JAGALIYA*
https://whatsapp.com/channel/0029VaLdFeg4SpkQ9xyW5c0k
Chapter 32-40
*POV RUFISS*
Cikin yanayin zazzabi yace.
Zuly bishira tun kafin jagwa ya dawo kufito mu tafi Dan wallahi jagwa jiyake da d'akin nan tamkar ransa ko tsinke baya so ya shigo d'akin sa kuduba can makamai ne fa ni dai wallahi ban shirya barin dunia ba
Zuly tace.
"Hmmm rufiss kenan kin manta suwaye mu d'an uwaki ma mun mai duka balle shi da shayeshaye yagama cinye shima"
AI kara sawar ta keda huya sukaji ruwan billet a jikin su tun suna ihu har suka galab'eta
Jagwa yace.
Kai budai musu kofa kuma wllh wllh wllh ko minutes daya ban yarda su k'ara ba kai kuma rufa'i rufa'i rufa'i
"Jagwa yace saunawa nakira sunan ka?"
Tuni muryar sa ta dawo dai dai yace.
"Sau ukku ya Hamza"
Jagwa yace
"To wllh k'arka kuskura ka bisu in kak'i hmmm a kwai ranar hadu war mu
Rufa'i yace
" to to bazan bi suba"
Tuni suka tafi cikin su duk yayi sanyi domin suna ji dadin zama da rufiss
________________*new world*
Babban birnin ZAKI
Wata benz car's ke shiga wani haddan estate tare da jirin motocin da ke biye da ita suna doso gate din wasu majiya karfi suka wangale gate din mai zanan MASARAUTA iya tsaruwa ya tsaru Masha Allah gaskiya bawaddah zai kalli MASARAUTAR MAI ZAKI yace akasar nan take yawa a k'asar waje gawasu shuke shuke a wani part ta tsaya tuni wasu Maza biyu suna sanye da kayan bayin gidan suka fito suka bud'ai mata kofa
"Masha Allah wata
hamshakiyar mace kyan Jikinta bazaka iyace wa takai wayan nan shekarun ba farace tas kamar kafasa jini ya futo kallo daya zakai mata kakirata da jinsin larabawa sai zuba sassayan k'amshe taki cikin takun kasai ta take tafiya har ta isa kofar da zata sadata da shashinta tana sanye da alkhabba ash amintattun bayinta mata suna biye da ita
Wani mayalwacin parlor ne iya yadda zan fad'a haduwar sa k'auyanci ne domin anzuba dukiya gawasu Royal chairs masu shegen kyau cike da nutsuwa tasami daya daga cikin Royal chairs din parlor ta zauna tana sauke numfashi yawa tayi tsaire duk da air conditioning din data ke aiki zufa take kamar ba a motar alfarma ta fito ba
" daya daga cikin hadi manta ne ta dur kusa tace.
" barkan ki da dawo wa uwar gijiyata ga ruwa kisha ta miko mata wani haddan Kofi mai tambarin masarautar ZAKI
"Hannu kawe ta daga mata ta amsa shatayi saida ya isheta tayi musu alama da sufita zata huta"
Mun barki lafiya zuka sukace sum sum suka fita domin basa iya hada ido da ita
"Cikin takun kasai ta tanufi bed room din ta bakinta dauke da sallamah ta shiga Masha Allah gaskiya komai na marautar zaki daban yake yawa ba mutuwa gaban wani tamfatsaesan gado ta nufa ta zauna tashiga tunanin zuci
" tambas komai yana shirin kub'u ce mata yarda tayi zatan duk k'an wasu al'amura nata zasu saitu ashe yanzu aka fara wasan tambas zata daina bacci tayi tsayuwar dare domin tana ganin a wanna karon tana Neman rasa ko mai har d'an datake tak'ama dashi duk da makiya sunyi tasirin rabata dashi ga kuma mai martaba duk da shi tasan duk rintsi bazai gujeta ba yaza madole ta binci kowa ya yake aikata haka har ranar girk'inta ashigo da guba cikin shashinta azuba a abinci mai martaba duk da kasance warta matar sarki amma da kanta take girki abin mamakin shine kafin abin ya faru da minutes ukku har jaridar masarautar ta wallafa to wake mata haka amsace dabaxata iya bawa kanta ba
"GA gimbiyah rumaisa tana zargin da sa hannuta a bawa sarki mansur guba"
"Wasu xafafan hawaye ne suka zubu Mata tace.
Ya ubangiji na nasan baka bacci ya Allah kaxama gatan mu ya Allah ka gwada ikwonka awannan karan kafini sanin ko suwaye kanu na musu baza su karfinka kar suyi nasara awannan karon ya Allah ka kare min Aliyu daga sharrin su
Jitayi andafata da saurin ta dago tayi saurin goge hawayanta tace.
"Nusaiba har kunta so ina nur take?"
Cikin damuwa nusaiba tace.
"Ke uwa ce ga mutan birrin ZAKI ke uwace mai adalci mamy ki fa matace ga adalin shugaba kuma sark'in sarakuna mamy zubar hawayanki bara zana ne ga al'ummar birrin *zaki"* mamy dayar d'ar Allah komai ya kusan zuwa k'arshe duk da inwasu sun yarda bake kika zuba guba a abinci ba wasu zasu yarda
Wata ajiyar xuciya tasa ki tace.
Nusaiba we ni zanje duba mahaifin ku gimbiya saudat su hanani shiga nusaiba suna zatan ni na aikata tunda ranar girki na ne ina tsoran k'ar abinda yafaru shekara talatin ya mai maita k'ansa wannan karun nasa *anni* zata d'auki munmu nan mataki ak'aina cewa zatayi ina so inkashe Mata da tunda abaya hakan ya faru
Nusaiba ta ja dogon numfashi tace.
"Mamy k'arki yarda maganar su tayi tasiri a wajanki kok'insa suna bak'in ciki k'infisu agun sarki k'inyi zarrah acik'in su k'arki yarda suga tsoro a idonki mamy kinuna musu cewa ke k'inyi ruko da Allah bada bokayeba *anni* kuma inta gano gaskiya zata soki *anni* zata gane cewa su munafuk'ai ne
" gimbiya asiya bintu Osman tace.
"Allah Yayi miki albarka
Cike da jidadi tace.
" amin mamy bara in cirewa nur kayanta tana d'aki na"
Kai mamy ta daga mata
*___________________*
*Addis Ababa Ethiopia*
"Tafiya yake Cikin izzah yawa mai tausayin k'asa ya karasa gaban wata matattakalah gabaki dayanta silver ce Masha Allah ashe parlor k'asan sa be haduba kamar wannan domin gaba ki d'ayan sa glass ne kuma baka iya ganin Kai saidai waddah yake cik'in sa yaganka gaban wata sliding glass door ya nufa yana xuwa ta budai gaskia parlor ya hadu komai nasa milk da ash color ne gawasu lcurtain masu kyau color din jik'in su milk anyi sanda sanda da ash color daga b'arin hannun sa na dama anyi crystal curtain masu shek'in demon suna bada colors biyu wato ash da white gaban wani tamfatsaesan fridge freezer mai color ash ya nufa yabud'ai ya dauko wine amma ba na giyaba yasami daya daga cikin sofa ya zauna yabud'ai ya fara sha tamk'ar baya so ...
Wayarsa ce ta yi k'ara alamar shigowar message dauka yayi domin tun da ya ga number