Showing 72001 words to 75000 words out of 142577 words

Chapter 25 - WANI SALO BOOK COMPLETED by Sa'adatu Alkali D-Tsafe.txt

a ranshi kar yaya yakan
zauna yayi ta kuka yana tuna halin da Hamman na shi zai shiga randa labarin mutuwarsa ta
riskeshi, yau ma kamar kullum bayan Adam ya fitane shiko ya tashi ido cike da k'ollah pictures d'in
Hamman shi da na Ammin shi sai na Ummul ya tattarosu kan carpet ya zauna ya watsa pictures
en a gaban shi kamar zaucecce ya fara magana da surutai,
"Kaito na ni Usman tir da halin zuciyata mara d'aukar k'addara tir da zuciyar da take son matar
d'an uwana mafi soyuwa a gareni d'an uwan da yake sona fiye da kanshi amman zuciyata ta
gaza bar mishi matarshi tir da halina,
Hamma kana gujemin mutuwa a ganina itace mafita fargaba na d'ayane,
Hamma na ya zakaji randa idanun ka zasu ganema gawata wazai lallasarmin kai wazai dawo
madadina a gareka Hamma zan barka da Ammin mu kai kad'ai ko ya Ammin mu zataji randa
zata ga ba Usman sai Umar Ummul sonki shine mafi munin fargaba a gareni zuciyata ta kasa
barin sonki a matsayin ki na matar d'an uwana wayyo ni Usman naji kunyar rayuwata, son matar aure me zance da uban gijina Allah kai kajarabci zuciya ta da son Ummul Allah ka
yayemin kar d'an uwana Umar ya gane inason matarshi".

a haka yayi ta kuka da surutai har zuwa wani d'an lokaci
sai kuma kawai ya kife kai yayi ta kuka tare da tari mai tsanani cikin layi ya mik'e ya tattara
pictures d'in,
ya juyo Kenan idanun shi suka sauk'a kan fuskar......








*by*
*GARKUWAR FULANI*
📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*RUBUTACCEN AL, AMARI*

Page 2⃣7⃣

*Na*
*AYSHA ALI GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇



*A TRUE LIFE STORY*




```Masoya na makaranta ina mai baku hak'uri dan naga k'orafe-k'orafen ku amman ku sani
cewa wallahi wannan littafi nawa RUBUTACCEN AL AMARI NE MIN IND'ILLAH wannan
labarin Allah ne ya tsarawa mutanen wannan littafin rayuwarsu a haka ba k'age wlh duk abinda
kukaji na Al'ajabi gaskiyane ya faru har kuma wanda zakuji a gaba hatta dai-dai da ruwan tea
da Ummul ta watsawa Hamma Umar a ido wallahi gskya ne hatta soyayyar Hamma Umar ga
Ummul da ciwon Usman, ku bini
a hankali wallahi tallahi akwai darasi mai girma a labarin nan```


*A* kan fuskar Nenne ya dire ida nunshi,
kallon shi itama takeyi tana juya mishi kai cikin zubda k'ollah,

shi kuwa komawa yayi ya zauna ya kife kanshi jikin kujera ya rink'a kuka mai cin zuciya,
kusa dashi Nennen ta zauna a kan kujera,
jinta a kusane yasa Usman ya d'aura kanshi guiwowinta sannan ya ci gaba da kuka,
hannun tasa kan kafad'unshi cikin sanyi tace,
"Usman ashe bazaka yiwa kanka fad'aba shin haka zaka bar rayuwarka cikin garari Usman ka
manta illar abin da kakeyi shin haka zakaci gaba da son matar d'an uwanka Usman kai har sai
yaushe zaka ruggumi k'addarar ka ashe bazaka zamo mai yarda da k'addarar rayuwar kaba".
Kai ya d'ago ya rik'o hannun ta sannan ya rink'a juya kai cikin rawan murya yace,
"A, a Nenne a a na yarda da k'addarata na bar son matar d'an uwana na cireta a raina bana son
Ummul Nenne Hamma Umar da Ammina nake tausayawa Nenne zan tafi tafiyar da ba dawowa
zan bar Hamma na bari na har abadan,
Nenne Hamma na baida aboki sai ni Hamma baida mashawarci sai ni Hamma baya gayawa
kowa matsalarsa sai ni Hamma yafi sona fiye da kanshi,
Nenne ya Hamma na zaiji randa babuni ya Ammina zataji wazai lallasarmin su wazai sasu
dariya wazai shiga rayuwarsu a madani dan ya sasu farin ciki Nenne tausayin Hamma nane ke
sani kuka da k'uncin zuciya".
kuka sosai yakeyi hawaye har gemunshi itama Ammi kuka takeyi sosai dan tausayin halin
k'addarar rayuwar Usman da Umar kuka ta kumayi dan tausayawa Umar yaro ya tashi cikin
maraicin Uba amman duk da haka ya hana Usman maraici ya zame mai madadin Uba ga kuma
wata sabuwar kaddarar da zata rabashi da Usman d'in Murya na rawa tace,
"Haba Usman ka dena fad'in haka ciwo ba mutuwa ba kuma Insha Allah zaka rayu da d'an
uwanka kuma Allah ne gatan bawansa Umar,
Usman ka kontar da hankali ka".
kai ya gyad'a tare da share hawayen nashi sannan ya kalli Nenne a hankali yace,
"Nenne kukana kikaji har cikin gidane yasa kikazo?".
kai ta juya cikin sanyi ta mik'o mai magungunan shi tace,
"Abban kune ya bani maganin ka in bawa Aliyu ya kawo maka so dana fito sai na samu Aliyun
ya tafi gidan Ammin ku shine na kawo maka dan kasha sai kuma na samu kana cikin wannan
halin".
Ajiyan zuciya ya sauk'e sannan yace,
"Nagode Nenne da kike tayani b'oye sirrina dan Allah ko bayan raina kar Hamma Umarna
yasan wannan matsalar tawa".
kai ta gyad'a mai cikin zubda k'ollah tace,
"Insha Allah bazai saniba".
haka ta zauna tayi ta mai nasiha har saida taga ya d'an sake sannan ta bashi maganin yasha
ta fice ta tafi,
shiko wayarshi ya d'auka cikin k'aunar Hamman nashi ya kirashi yana d'agawa sai cewa yayi,
"Hamma na ina sonka! ina sonka! ina soka! bana son kayi nesa dani ina sonka d'an uwana ina
son Ammin mu bani da kamarku a duniya Hamma na duk son da nakewa Ammi wanda nake
maka yafi yawa ina sonka fiye da kaina".
Shiru Hamma Umar yayi jikin shi a mace da kalaman Usman a take yaji kamar an rufe mishi
jikin shi da d'anyen fata wani irin sanyi ya ziyarci rayuwarshi hannun shi ya fara rawa tuk'in da

yakeyi ya fara gararsa dan wani kasala da yaji cikin firgici yace,
"Usman meke damun ka zuciyar ka ko? Usman ka gaya min meke damun ka".
dariya Usman yayi cikin calikanci yace,
"Ni Hamma matsalata da kai Kenan kai saurin tsoro gareka ashe dan nace ina sonka sai ya
zama banda lafiya toni lafiyata lau aradu".
murmushi Hamman yayi duk da har yanzu yanayin sanyin na jikin shi,
a hankali yace,
"Nima ina sonka ina sonka sama da yadda nike son kaina d'an k'anina".
dariya sukayi baki d'aya a dai-dai lokacin kuma yayi parking a cikin gidan nashi sannan ya katse
Kiran,
ya shiga cikin gida.

Kai tsaye bedroom nashi ya wuce,
yana shiga ya fara rege kayan jikin shi wonka ya sha yana shiga
Ummul ta shigo d'akin a bakin gado ta zauna tasa k'aton cikin ta a gaba,
shiko fitowa yayi k'ugunshi d'aure da towel yana ganin ta ya matso gabanta hannun yasa ya
shafa cikin ajiyan zuciya yayi tare da kallon idonta yadda suka kumbura alamar tayi kuka zama
yayi ya jawota jikin shi a hankali ya mannan kanta a kirjinshi dake da d'an damshin ruwa jin
sanyin jikin shi yasa ta k'ara manna kanta sannan ta fara magana cikin muryar kuka da rauni irin
na masu tsofaffin ci,
"Hamma sai yaushe zaka ciremin cikin Hamma kullum sai kace min sai gobe gobe sai goben
shi gashi yanzu kullum k'uguna ciwo yake min dan Allah ka rabani da cikin nan naka".
k'ara ruggumeta yayi cikin sanyi yace,
"Ummul na kiyi hak'uri ki haifa mana shi da kanki kar in cireshi inya girma yaji kinsa an cireshi a
cikin zaiyi kukan bakya sonshi kinga fa yau saura kwana uku rak cikin ya cika wata takwas
kinga kenan saura wata d'aya ki haifamin shi ni zan raini abuna".
Rigarta ta d'aga sama ta nuna mai cikin sai kuma ta fara kuka tare da yarfa hannu tana buga
k'afa tana,
"Wallahi ni dai na gaji nayi iya taimakon da zanyi kawai ka cire min cikin tunda kai kana son
abunka ka ciremin shi wallahi ko nasha gishiri na fiddashi".
k'ara ruggumeta yayi cikin sanyin da kalaman Usman suka sakar mai yace,
"Toh na yard'a zan cireshi amman kiyi hak'uri sai gata dan gobe da safe zan kaiki potiskum gun
Nennen ki dan zamuje Abuja nida govnr akwai wasu gwaje-gwajen da zamuyi mishi da wasu
doctors d'in kwana d'aya zamuyi muna dawowa zanje in d'aukoki mu dawo sai na cire cikin ko".
kai ta gyad'a cikin jin dad'i tace,
"Toh na yarda".
murmushi yayi cikin kasala ya k'ara jawota jikin shi a hankali ya shafa cikin sannan yace,
"d'ana ina sonka ina son mamanka".
sai ya kuma tura hannun shi kan kirjin ta da suka k'ara ciccikowa a hankali yace,
"Khairi na a d'an barni nayi pakala mana wata k'il daga nan ma baby ya fito".
baki ta tura tace,
"Na gaji ni na gaji da wannan jarabar".
kai ya sunkuyar tare da cewa,

"ya isa na barki kiyi baccin ki ina dai kinci abinci? ".
"eh". tace sannan ta konta gefenshi shiko al'wala yaje yayi sannan yazo yayi nafilfilinshi tare da
karatun qura'an ya rok'owa d'an uwanshi lafiya sannan ya rok'awa Ummul enshi sauk'a lafiya
tare da mata fatan samun gajeriyar nak'uda,
Sai k'arfe 2 na dare ya konta.



Washe gari da safe bayan sun gama
shirin su,
suka nufi hanyar potiskuma dan yana sauri zai dawo su tafi Abuja,
suna isa gidan A parlour Hajjajo suka zauna gaba d'aya gidan sai ya Sadik dake kitchen din
Nenne, bayan sun gaggaisa ne ya kalli Abba cikin girmamawa yace,
"Abba zamuje Abuja nida govnr kwana d'aya zamuyi toh gida ba kowa shine na kawo Ummul
gida sai na dawo goben zanzo in d'auketa".
Kallon shi Abban yayi tare da cewa,
"Toh Allah ya kaiku lafiya Allah ya bada sa'an tafiya".
"Amin Amin". suka amasa baki d'aya sannan ya mik'e tare da cewa,
"sai na dawo".
kusan duk a tare suka ce,
"Allah ya dawo da kai lafiya".
"Amin".
yace sannan ya fito har yaje bakin kofar fitan yace,
"Ummul zo".
ba musu tabi bayan shi ganin hararakin da take sha,
kai tsaye parlour Nenne suka nufa,
suna shiga ya jawota jikin shi
ya ruggumeta kanta ya tallabo ya had'e bakinsu wuri d'aya kissing nata ya rink'ayi cikin salon so
da k'auna,
itako tureshi ta rink'ayi har saida ta zame bakinta tana haki shima yana hakin,
cikin tsiwa tace,
"Wallahi ka fiye jaraba da wannan jarabar taka ka d'irkamin cikin nan kawai ka tafi kana dawowa
ka ciremin cikin nan na huta da fitina".
duk maganganun da takeyi kab a kunnen Sadik da yake dafa indomi a kitchen d'in Nenne,
shiko Hamma Umar shafa fuskarta yayi sannan yace,
"ba matsala Ummul wata ran zakiso wannan d'an naki fiye da kowa a duniya".
baki ta tura tace,
"Bana sonka bana son cikin".
kai ya kad'a sannan ya fita ya tafi,
kai tsaye Damaturun ya koma bayan sun gama shiri da tawagar govnr suka nufi babban birnin
taraiya.

A gida kuwa Hamma Umar d'in yana fita,

itako ta koma ta zauna kan kujera,
shiko Ya Sadik shiru yayi a kitchen d'in har saida yaji tashin motar Hamma Umar d'in yana jin ya
fita gidan,
shima ya fito parlour Ammin kai tsaye gaban Ummul ya tsaya hannu yasa ya kamo nata
ya tsaida ta,
itako da take lumshe da ido jin an d'agota ta bud'e ido cikin firgici baki na rawa tace,
"y...! ya....! ya.. yaya Sadik".
k'ara ta cilla da k'arfi tare da dafe kuncinta dan jin wani irin gigitaccen marin da Sadik d'in ya
sakar mata,
shi kuwa da iya k'arfin sa ya rink'a zuba mata maruka a jere a jere ba k'ak'k'autawa marinta
yake cikin fushi da jin haushinta yama manta tana da ciki ji yake kamar ya karya ta,
tuni ya fasa mata baki,
itako sai kuka take tana kiran ,
"Wayyo ya Sadik kayi hak'uri wallahi bazan sakeba wayyo Hamma Umar ka tafi ka barni zasu
kasheni wayyo Nenne na wayyo Abba na wayyo ya Usman ".
haka ta rink'a kuka da kururuwa ba wanda yayi yunk'urin k'arbarta sai da sukaji kukan yayi
yawane suka fito duk sukazo,
ganin marinta kawai Sadik keyi sannan ya gaya musu abinda yaji tana gayawa Hamma Umar
hakan yasa gaba d'aya suka k'i kwatarta,
sai Adam ma daya k'ara zuba mata maruka duk aka resa mai karb'arta a gidan Usman ma sosai
yaji zafin yadda take nuna bata son d'an uwan nashi,
shiko Sadik mammaketa yayi har saida fuskarta ta kumbura tayi jazir,
sannan ya barta Abba ma yazo yayi ta fad'a kamar zai ari baki Nenne kuwa fushi tayi da ita tak'i
ta kulata,
Usman ma fushin yayi da ita,
haka ta wuni a wannan ranar cikin kuka da k'unci ga zazzab'i mai zafi ga ciwan kai gaba d'aya
ta jeme tak'i taci komai tak'i tasha komai sai kuka har muryarta ta disashe hatta cikin nata saida
ya yayi k'asa motsinshi ya d'an ragu,
hajjajo ce mai d'an bata abinci duk da itama fushin take da ita a haka ta kwana har washe gari
har zuwa yamma bataci komaiba duk gidan sun juya mata baya hatta Aliyu fushi yake da ita.


Shiko Hamma Umar a Abuja tunda sukaje bai samu sukuni ba haka yasa bai kirasuba sai dare
daya kira Kuma sai akace Ummul tayi bacci hakan yasa basu gaisa ba koda gari ya waye ya
kira duk woyoyin gidan basa shiga,
haka yasa suna dawowa ko gidanshi bai komaba ya kama hanyar potiskum d'in,
yana shiga cikin garin sai kuma yaji kewar Ammin shi da begen son ganin ta hakan yasa ya nufi
gidan Ammin yana zuwa ya samesu ita da Inna da uncle ensu suna tsakiyar gidan suna ta hira,
kamar ko yaushe gaban ta ya zauna ya tonk'oshe k'afafun shi sannan ya cire hular kanshi,
itako Ammin ido ta tsura mai cikin murmushi da Happy tasa hannun ta kan gashin kanshi murya
cike da k'auna tace,
"Allah yayi maka Albarka Allah ya tsaremin kai da d'an Uwanka Allah ya sanya alkhairi a
rayuwarku ubangiji yayi muku rahama duniya da lahira".

Murmushi yayi cikin jin dadi yasa hannun shi ya dafa hannun ta dake kanshi yace,
"Amin Amin Ameeeeeeeeeeeeeeeen ya rabbil izzati Ammina".
sai kuma ya juya ya Kalli Uncle en cikin girmamawa yace,
"Uncle ina wuni ya gida".
"Lafiya lau Farouq ya hanya yanzu Ammin ka ke cemin jiya kazo ka sallameta zaka tafi Abuja".
"Alhamdulillah".
yace da uncle d'in sannan ya kalli Inna yace,
"sarkin surutu yau ya naganki shiru ko dan banzo da ogan naki bane".
dariya tayi sannan tace,
"ai kaima oganane".
kallonta yayi a hankali yace,
"kin Kama gaibu gwara miki Usmanun ki".
dariya sukayi duka shiko Hamma murmushi yayi sannan ya kamo hannun Ammin shi yace,
"Ammina farcenki ya d'an taru bari in yanke miki".
murmushi tayi tace,
"toh Allah ya ma albarka Allah ya tsaftace rayuwarka kamar yadda kake tsabtace min farcena".
"Amin Amin".
ya amsa sannan ya yanke matasu ya kankare mata,
bayan ya gama ne ya kalleta cikin karya wuya yace,
"Ammina yunwa nake ji kuma yau abin cikinki nake son ci".
mik'ewa Ammi tayi da sauri ta nufu kitchen,
abincin ta kawo mai tare da roban wonke hannun,
tuwan farar shinkafa da miyar ganye yasha man shanu da nama,
gaban shi ta ajiye mai a hankali tace,
"matso kaci ka d'ena zama da yunwa bana so".
"toh". yace sannan ya bud'e abincin murmushi yayi yace,
"Tab Ammi ai wannan yamin yawa gsky bazan iya cinyewa ba sai dai in zamuci tare zanfi jin
dad'in cin".
murmushi Ammin tayi sannan ta matso sukaci a tare sannan suka dan yi hira Inna da uncle
suna ta musu dariya,
sannan ya salla mesu ya tafita,
har yaje kofar gidan ya dawo ya kalli Ammin nashi itama shi take kallo a hankali yace,
"Na manta ban gaya miki ba na kusa na samowa autanki mata muyi mishi aure yafi zaman
hakan matar zata kulan mana dashi".
murmushi tayi sosai sannan tace,
" toh Allah sanya Al,khairi".
"Amin Amin Ammina kiyiwa k'anina fad'a ya rink'a kula da kanshi".
"toh zan mishi kaima ka mishi ".
A haka suka sallami juna,
yana fita kai tsaye gidan Abban ya nufa.


Bayan yayi parking kai tsaye ya kutsa cikin gidan parlour Nenne ya wuce inda ya samu ba kowa

har zai juya ya fita sai yaji sautin kukan Ummul a cikin bedroom d'in,
da sauri ya Koma cikin d'akin kan gado ya hangota konce tana ta rawan sanyi da kuka,
cikin sauri da furgici ya k'aroso gabanta hannu yasa ya d'agota ruggumeta yayi cikin kad'uwa
yace,
"Khairi! Khairi na meke damun ki? Ina Nennen? ya gidan shiru basa nanne? ".
ruggumeshi tayi cikin kuka ta d'ago kanta,
da sauri ya tallabe kanta cikin tsoro yace,
"meya samu fuskarki inasu Nennen? ".
cikin kuka da tausayawa kanta ta, kwashe labarin abinda sukayi mata ta gaya mishi ta k'ara da
cewa,
"Nenne ma bata min magana Abba ma fushi yakeyi dani ko Aliyu sun hanashi yamin manana ya
Usman ma fushi yake dani duk basa sona basa zama kusa dani yanzu duk suna parlour
Hajjajo".
hannun ta ya kamo cikin tsananin bak'in ciki da takaici waje ya fito da ita kai tsaye part d'in
Hajjajo ya nufa da ita,
kicinb'is sukayi da ya Sadik a tsakiyar gidan,
yana ganin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login