Showing 12001 words to 15000 words out of 27623 words

Chapter 5 - Darajar Yayana Book 1 Complete by Halima Abdullahi K Mashi .txt

soma dubawa.
Tanbayata suke ina naje sun zo ba nanan? Na yi
dan murmushi, a fili na ce da kun zo gidan Iya ni
kam ba zan yi wani taro ba, sai na soma duba
nashi,duk kusan yana nuna damuwane akan ya
kira bai sameni ba. Sai na karshe da yake cewa
sun taso 9 suna hanya, akwai yiwuwar su iso
kafin 9 na safe, kuma suna tare da wasu daga
danginta dan Allah ta tanadar musu abinci. Kiran
Abida ya katse karatun sakon da na keyi, na daga
muka gaisa, ta ce min, ina na shige yau? Na ce
ina gidan Iya,tace to, ki yi sammakon tashi don
mijinki zasuyi shigowar safe ne, nace Anty me
zanyimusu?tace karin kumallo mana kiyi zuciya1
kada ki sa kishi ciki, bakin kine, kin kuma san
darajar baki a musulunci. Na ce to Aunty zanyi.
Tin 4 na tashi na fara firar dankali da nayi sallah
kuma na hau suya, har kaji biyu nayi musu
farfesu, kwai ma isasshena yi musu kwai da kwai
na dafa ruwan tea mai yawa, sannan na gyara
gidana nayi wa yara wanka na zabo musu
sababbin kaya nima na sheka nawa adon.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Takwas daida na ji tsayawar motoci,gabana ya
yanke ya yi wata muguwar faduwa,sai na hau
karanta Hasbunallahu wa ni'imal wakil. Na mike
na je na bude musu kofa gabana yana ta
faduwa,zuciyata tana maimaita addu'a.suka shigo
suna yi min sannu, wasun su suna kallona wani
iri,amma duk da haka na saki raina ina yi musu
sannu da harshen Turanci.Najee na bude musu
dakin suka yi sororo a tsakar daki don ga
al'adarsu miji ke shiryawa mace daki ya zuba
komai, ita kuma iyayenta su yi mata kayan sawa,
nan fa suka soma yare, duk da bana ji amma
ganin yanda suke magana suna tabe baki na
fahimci zancen nasu bana dadi ba ne, naje
nasoma fito musu d kuloli. Sai gasu Yaya sun
shigo, na kirkiro fara'a ina yi musu sannu da
zuwa. Falo suka je suka zauna na gabatar musu
suma da abin kari, na kula yaya ya ji dadin
yanda na saki jikina na kuma yi musu abin
kari.Nan nabarsu nayi daki,bayan Mujidat da
danginta sun gama karyawa sai suka samu su
Aliyu da Usman suna yi musu korafin ba su ga
kmai a dakin ba.Usman ya ce, Mu a nan da kaya
amarya take zuwa. Suka ce su kam ba haka ba
ne, nan suka fito masa da akwatunan amarya
har da na mijin da na Maman shi da kuma na
danginsa. Aliyu ya ce shi kenan zai siya daga
baya, amma yanzun a kwaso na dakinsa a sa
mata,sukace bakomai. Ina dakin nashi ya shigo
wanda zuwa yanzun ya zama nawa,ya zauna.
Sadiya kin ji wata sabuwa. Na kalle shi, ya ce,
Wai ni zan sai mata gado. Na ce, ina zaton haka
al'adar su take don mun taba yin zancen da wata
'yar ajinmu da muka yi N.C.E take ba mu labarin
al'adunsu, miji ke yin kayan daki kuma sadakin
su yana da tsada, amma mace za ta ja jari da su
ita ce za ta rike gida,wasu kuma jarin daban miji
zaibada, wadanda ba Musulmi ba sun fiyi,
Musulminsu kamsai sunyi aure suke tarewa gidan
mazajensu,yace,nidai yanzun ya za'a yi? Na ce su
zo su dauki wannan gadon. Na tsura masa ido
cikin mamaki,sai ya ce, ko ya ki ka gani? Na mike
na nufi dakina bayan na ce, Me zan ce kai da
abinka. Na shiga dakina na soma kallon dakin ina
lissafa yanda zan gyara shi ni da yarana da na
bar musu gadona tunda dama katifu gare su. Sai
ga shi ya shigo.Haba Sadiya,me zai sa ki
yankemin wannan hukuncin? Nazo miki da
shawara amma sai ki yi watsi da ni kitaho abin
ki? Na ce, Yaya kainefa da abinka kuma ka ba
matarka, mene ne laifina dan na taho? Yace, Ok,
kije amma ki sani kada nan gaba ki ce na daina
kawo miki Shawara,kin sani dai ke ce kurum nake
tunkara da duk matsala ta. Shiru na yi dan nasan
in hakan ta faru lallai ba zan zama uwar gidaba.
Ya mike zai fita na ce, Yaya'' ya dawo,Mene ne?
Na ce, Shi kenan ka yi hakuri. Ya zauna tare da
kamo hannuna, Nagode da ki ka fahimce ni,
yanzun ya ki ke ganin za'ayi? Na ce, Ka ba ta,ni
kawai sai naringa kwana a nan da yarana. Ya
tsura min ido, To nifa? Na ce, Ba komai ka yi ta
kwana dakinta. Ya yi dan murmushi, Har yanzun
baki huce ba.Na yi 'yar dariyar yake, Bana fushi
da kai. Yace, Zan siyo katifu yau a sa can dakin in
komai ya warware zan canza gadajen gidan.Na ce
to maimakon ka ba ta tsohon gadon ba gara ka
sai mata katifar ba? Amma yanda ka gani, Ya ce
na riga na fada musu ne na ce to su dauka bari.
In zo in kwashe kayan na wardrobe din. Ya ce,
A'a, gado kawai da katifa za ta dauka. Na ce, Shi
kenan, Allah ya rufa asiri. Ashe tashin hankali
yana gaba,sai lokacin bacci, Mujidat ta kira shi a
waya wai tana jin bacci, ya kalle ni muna zaune
kan gado,sannan yaci gaba da magana. To ki
kwanta mana. Ta ce, Ba dakin ka zan kwana ba?
Ya ce, A'a yanzun bani da daki in danginki sun
tafi na kwana adakinki. Mamaki da haushi suka
cika ni, ga kishi kamar in hade raina, na ce, Kuje
dakin naka mana? Yaja tsaki tare da cewa, Don
Allah ki bar wannan maganar. Na kwanta tare da
juya bayana na rungume yarana bankara
sauraron shi ba, shi ma ya kwanta a daya gefen
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Washe gari tun Asbahi suka soma shiri,suna
karyawa suka tafi, wata daya ce daga cikinsu
kadai ta yi min sallama da godiya, suna kama ina
zaton yarta ce dake illorin din, domin nayi
dawainiya dasu sosai ta fannin abinci. Ya tsaya
da su sun shiga gurin Iya sun gaisa duk da cewa
ba sa jin yaren juna, sannan ya wuce dasu zuwa
gareji. Ranar ne matan Yaya Sulaiman da su Anty
Abida sukayi ta zuwa ganin Amarya. Anty Abida
ta yi ta yi min fada wai ya zan sa abu a cikin
raina ga shi nan duk na rame, na ce Anty dole in
sa a raina, ba za ki fahimci zafinkishi ba, duk irin
bayanin da zan yi miki, kuma bana fatan a yi miki
ki ji.Anty Abida tace, Ameen,don Allah ina son ki
saki ranki. Amarya dai tana daki bata fito ba, da
za su tafi na raka su ganin amarya ta ci rigarta
da wando na bakin Jeans, danta yana cikin gadon
shi ta yi ruf daciki kan gadon da suka kafa tana
chatting, a yatsine ta amsa sallamar,sannan aka
gaisa,suka yi fatan alkhairi suka fita.
Daran ranar ne ya hada mu a falo yana yi mana
nasihar zama lafiya, sam ban san me yake cewa
ba, ina can gurin tunani. Yau ga shi abin da nake
karantawa cikin littattafai ya zo kaina, ji nake
tamkar cikin mafarki, ashe dai nima za a min
kishiya. Girgiza nin da yayine ya sa na dawo cikin
hayyacina,cikin damuwa ya ce, Menebe? Na
girgiza kai ba komai. Ya ce, ina tambayar ki game
da kwana,na ce, Nawa nawa? Nayi hamma
kirkirarra, sannan duk yadda kace. Ya ce, To a
bar shi bibbiyu kamar yanda aka fi yi. Na ce shi
kenan. Ita dai tana ta jijjiga danta,na sake kirkiro
hamma, zanje in kwanta bacci. Ya kalli agogon
bango; Da wuri? Na ce, Na gaji ne. Na kalli
amarya wadda ta sha leshi kai ya ji gashin doki
ya zubo har kafada, na ce, Sai da safe,ta dube ni
da 'yar yatsina eh, dama ban jira amsar ta ba na
yi tafiyata. TABDI! Daran ranar kasa bacci na yi
har zuga ni zuciyata ta dinga yi wai inje in labe
inji me suke yi, amma sai na fi karfinta inda na
yo alwala na yi ta sallah in nagaji in dauki
Alkur'ani nayita karantawa,sai da na yi sallar
Asubahi sannan na kwanat. Allah ya taimake ni
yarana suna cikin hutun makaranta ne, don haka
da na tashesu muka yi sallah sai muka koma.
Ban farka basai tara, ina tashi Mama ta tashi, sai
da na yimusu wanka sannan muka
fito.....zandakata anan zuwa lokaci na gaba,fatan
zaku kasance tare dani
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347




Darajar Yayana3-03
Posted by ANaM Dorayi on 12:12 AM, 04-Apr-16
Under: DARAJAR 'YA'YANA
__________________NA
___________HALIMA K/MASHI
Assalamu'alaikum,akaro na barkatai gani na dawo
domin kawo muku cigaban labarinmu ,fatan kuna
sane da inda muka tsaya.
Yayi shiru. Na ce Hello, kana jina? Eh, kin fadawa
Iya ne? Na ce, nanmuka amshi haihuwar tare,
Kasan cewa taso ta gano cewa danka ne? Dan
yaron yayi kama da kai fiye da duk yaran gidan
nan.Da karfi yace Haba dai! Wlh, yaushe zaka zo?
Yayi dan tsaki, gaskiya bani da ranar zuwa, zan
turo miki kudi kiyi duk abinda ya dace. Nace,
zuwan ka yana da muhimmanci, sabida Mujidat
zata iya tana komaifa, inbata gankaba. Ya ce, to
zan zo kafin suna inkuma dawo
Gurin aikina. Nace to saikazo. Na kira auntyAbida
na fada mata, haka ma Aisha kawata.Makota duk
suna ta shigowa Barka. Su kausar ma nasa sunje
sunga baby,na fada musu cewa kaninsune, suna
ta murna har da kausar. Aisha ranar datazo
barka tana daukan yaron tace, kai Sadiya yaron
nan yana kama da Abban kausar. Nace, haka ake
ta cewa, dama kin san mutane sun ce in mai ciki
tana yawan kallon mutum ta kan haifi mai kama
da shi. Ta yi Yar dariyar yake,tare da cewa,
hakane kawata.Mai jego kam ina kallon ta sai
harara take watso mana. Muna shiga dakina
tace, Sadiya anya kuwa ba kanshin gaskiya a cikin
lamarin matar nan? Kin san halin mazannan ko
dai Dan sa ne? Ki yi hakuri kamarce naga tayi
yawa. Nace, hum! Ke dai bari kawata, tsakanina
dake nasan amanace, wlh dansane ciki yayo
mata, yanzun data haihu zasuyi aure. Aisha
amana na fada maki ko iya bata San wannan ba.
Aisha ta zabura tare da fadin, kan uba! Lallai
Sadiya ban taba sanin cewa Ke sakarya bace sai
yau, yayowa wata ciki sannan ki yarda ta zauna
maki a gida? Wallahi da ace nasan haka ne in
nazo barka shegiya nake,kin ma daure masa gindi
kenan gobe ya kara.Na ce, Aisha ki fahimta, uban
'ya'yanane,mijina kuma yaya zanyi? Nawa ganin
rufin asirinshi Nawa ne, kuma na yara nane. Ta yi
tsaki bana Jin zan fahimceki, in tazo gidan ta
koreki kin ga ai sai kiji dadin rufa masa asirin. Na
ce, nasan dama bazaki fahimceniba, shi yasa tun
farko ban sanar da Ke ba, dan na sanki. Ta dauki
yarta tasa a baya,ta suri jakarta da hijabinta, Ni
kin ga tafiyata. Na bita ina fadin, "Dan Allah
Aisha ki saurareni. Ki tayi ta tafi abinta. Na ce to
shi Kenan in kin huce za muyi waya ta ce ni kar
ki kira ni. Na dawo daki na kwanta kan gado ina
hawaye, in na tuno Yaya zasuyi aure da Mujidat
Abin na daga hankalina ya kuma sani kuka.
Ranarr da suka cika kwana 5, sai ga Yayakusan 10
na dare, Ni ce ma na bude masa kofa, ya janyo
ni jikinsa,ni kaina bansan me yasa jikina yayi
sanyi ba kuma banyi wani farinciki da ganinsa ba.
Ya dago fuskata, sannan yahaskani da wayarsa,
lafiya my choice? Na sa hannu na tare
hasken,lafuya mana Yaya mai ka gani? Na karbi
jakar hnnunsa tare da cewa sannu da zuwa,bai
amsa ba sai dai ya ce, na ganki cool ne, kamar
ba kiyi farin ciki da gani na ba. Na ce, bacci na
fara. Sannan nayi gaba na bude masa daki ya
shiga. Ya zauna bakin gado tare da fadin, na gaji
yau Sosai,8 ta wuce na baro Abuja, kuma da safe
zan wuce na zone Kawai sabida kin nuna zuwan
nawa yana da muhimmanci. Na ce, to Kayi wanka
zaka warware. Ya ce to. Kafin ya fito wanka na
kawo masa tuwo daman shi nayi a daren miyar
zogole. Sai da yaci na fitar da kwanukan, sannan
na shiga gurin Mujidat tana zaune da waya tana
chatting, na ce, ya kamata fa ki dinga bacci. Ta
ce, ba zan yi hira da kawayena ba? Na ce, kuyi
tayi, akawo yaro babanshi yazo. Ta kalli yaron
sannan ta kalleni, ya yi bacci. Na Isa gurin yaron
na dauko shi, ban tsaya jiranta ba na kai shi.
Aliyu ya mike tsaye zumbur likacin da ya kalli
yaron duk yadda Sadiya Ke bashi labarin
kamannin shi da dan bai zaci har hakaba. Ya kalli
yaron kusan minti 1, sannan ya miko mini tmkr
yana tsorace,na maida hannuwana baya. Kayi
masa addu'a kamar sauran yaran ka duk dadai
baka samar da shi ta hanyar da shari'a ta
amince ba, sannan ka yi masa hudu ba,ya daga
murya rikeshi mana Sadiya. Na juya na fita. Abin
mamaki sai ga Mujidat labe tana lekenmu, na
tsaya turus ina kallonta, ita ma ta yi tsuru-tsuru
na ce, a'a dama kina min labe? Ta soma Sosa kai,
sai kuma ta shiga borin kunya, kin zo kin
daukarmin yaro ba dole inbiba? Na ce, kina
zargin zan cutar miki da yaro ne? Yaya ya fito ya
mika mata yaron "ungo yaron ki kar ku tada min
da yara suna bacci. Ta amshi danta ta tafi, ni
kam a gurin na tsaya na ma rasa tunanin da
zanyi, tun yanzu kenan kafin a daura Auren? Shi
kam bai so yanda ya yi ba kada ma mu tada
masa yara suna bacci, maimakon ya gargadeta
kan cewa Kar tasake yi min labe, bai yi hakan ba
sai ya shige abinsa. Ni kam dakin yarana na nufa
amman ko zama ban yi ba sai ga kiranshi, sai da
wyrta kusa tsinkewa sannan na daga. Meyene?
Yace, zomana,sai da na dan bata lokaci, sannan
na je. Kai kawo na samu yana yi a cikin dakin,
ina shiga ya nufo ni ya kama hannuwana. Sadiya
asirin da muka rufa zai tonu sabida kamannina
da yaron nan ya dauko,ina ganin gara mu fadawa
Iya Kawai ita kuma Mujidat ta yi tafiyarta tunda
dama dan Kar Iya su sani ne zan aure ta, ni
wallahi bana son ta, zata iya tarwatsa min iyali,na
zame hannuna daga nasa na zauna bakin gado
tare da rike kaina na ce, Yaya ba dan Kar asirin
ka ya tonu Kadai ba ne na ce ka aureta, don
gudun kada kuci gaba da haihuwa a titi babu
aure, don nasan bazaku rabuba. Shima ya zauna,
sai dai in itace baza ta rabu dani ba Sadiya,
amman wallahi ni tuni na barta,na girgiza kai,
Yaya yin Aurenku yafi a kan barin shi, don
Mujidat ta tabbatarmin da hakan kuma na San
zaku iya... hawaye suka soma zubomin cikin
rawar murya na ce. kuma duk laifin kane. Ya
kwanto ni jikinshi, wallahi Sadiya nayi nadama
matuka, kuma naji kunyarki Sosai ki yi hakuri
kidaina kuka, Kecefa kike Karfafa min gwiwa,kike
bani shawara. Ya dago fuska ta. Hankalina
yatashi da yawa ganin kamannin yaron
nan,nasan sai dai mutane su ji mu Kawai,
ammababu wanda zai yarda cewa ba yaro na
bane. Ya share min hawaye. Ki yafe min. Na ce,
Yaya ni dai alfarma Kawai zan roka a gurin ka
guda biyu. Da sauri ya ce, na miki alkawarin yi
miki su fadi inji.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Na ce, na farko duk rintsi kada ka juya min baya
ko ka wulakanta ni. Ya rike kafaduna muna kallon
juna, insha Allahu Sadiya ba zan miki ba ko bisa
kuskure insha Allahu. Nace sai na biyu, izini zaka
yi min in nemi koyarwa a makaranta, ko L.E.A ta
nan unguwar Mu'azu. Ya yi shiru yana nazari, can
ya ce, kin gane Sadiya ba wai ina son hanaki
bane, nafison ki nutsu a gida wallahi bana son
matata tana yawo. Na ce, akwai dalilina, ka ga
Kwanan nan zamu zama mu biyu a Kasan ka,
duk wata bukata da zan nema a wurinka dole ne
ka yi mana mu biyu, inko inada nawa zan yi
bukata ta ba tare da na takuraba. Ya ce, wannan
bai kai dalilin da zan bar ki ba sai dai in bar ki
sbd tun farko na amsa cewa nayi miki alfarmar
da kika nema,da dai tun farko na san wannance
alfarmar da bazan yardaba, sai dai kimarki ta
wuce in amince, sannan in dawo in ce a'a, kije
kiyi koyarwa ki, amma ki tsare mutuncinki da
nawa.Na sauke ajiyar zuciya 'nagode mijina, Allah
ya saka da Alheri. Ya lumshe ido sannan ya
bude. Yanzu wane suna za'a sa masa?
Na ce, a'a wannan shawarar tsakaninkane da
Mujidat, da safe ka sameta ku tattauna. Bai ce
kalaba sai ya kwanta rigingine.
Da safe falo ya zauna yace in kirata,ta fito tana
yatsina cikin Riga da wnd ta zauna, ya ce, wane
suna kika zaba? Ni kam mikewanayi. Ya ce,zo
mana My choice. Na ce, ina zuwa. Dakina nashiga
na bar su dan zancen na su ne.Ta mike daga
Inda take ta koma kujerar da Ke daf da shi ta
ce,Sweety kaine zaka bashi suna in dai nice nafi
son sunanka don yaron yafi kama da kai. Darling
kabiyani dakabani mai kama da kai. Ya waiwayo
ya daga mata hannu, tsaya!baki dacikakken
hankali ko? Ni ne nake bada haihuwa?Ki sawa
yaron ki duk sunan da kike so amma ban da
nawa kin gane ko? Ta ce, to ina son a samun
Abdul-kareem. Ya ce, ya yi Allah yaraya shi.tace
ameen. Sai maganar auranmu. Ya mike tace, na
zata tun ranar dana haihu zamuyi maganar shine
yanzu na kawo maganar za ka tashi? To bari kaji
daurin auren nan in ya wuce gobe za ka ji
mamakin abinda zai faru.Ya shigo daki, ina jiyo
duk yadda sukayi nace, Yaya ka amince nima ina
son a daura a wuce gurin kawai,ya ce, ba zanyi
yanda takeso ba, tana ganin itafa wata cikakkiyar
marakunyace. Bata San cewa ina daga mata kafa
bane sabida Ke,nace, dan Allah kai dai gara a yi
ko a wuce gurin. Sam ban zaci za a yi wani suna
ba, don haka ban tanadi wani batun sunaba,
kuma da zai tafi yace Usman zai kawo rago shi
ma bai yi min batun suna ba, amma muna da
kayan abinci na ce masa ya siyo mata sababbin
kayan sawa ita maijegon,yace bazai siyoba, ko
dan kyalle.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Washegari tin misalin 8 na safe naji bugun gida,
dama na rufo kofar gidan ina sauri zan kai yara
makaranta don munyi latti, kafin in bude sai ga
Mujidat ta fito da gudu tana cewa, oyoyo Momy!
Kaucewa nayi ta bude, ashe 'yan uwanta ne daga
Lagos su 4, Mamanta,Babanta, Kawarta da
Kanwarta suka kalleni nima na kallesu, don hauka
har uban suka shige cikin gidan, nasa yarana a
mota na fice cike da takaicin da ya Aliyu ya ja
mana. Har na dawo raina a bace. Mujidat
nasamu a kicin tana ta fasa kwai ita da kanwarta
suna hada abincin karyawa, ban kula su ba, na
shige dakina cike da bakin ciki. Ko da naji bugun
gida ban fito ba a zatona wadansu dangin
nasune, amma sai na ji wayata tana ruri na daga
ashe Usman ne yace Madam ki bude gida ga
Ragonnan,nabude ya shigo da Ragon muka gaisa
yace kuyi hakuri banzo barkaba, wallahi Sadiya
takaici ne ya yi min yawa bana son ko ganin
matar nan, bare Dan, sanann ga kunyarki. Nayi
murmushi tare da cewa, Haba dai, gurina
bakomai ya Usman. Aunty Abida fa? Ya ce, suna
lafiya,naji tana cewa zatazo anjima. Na ce, yauwa
Dan Allah Yaya ina jiranta yanzu, bari in kira
maijegon ka ba ta, dama danginta sun zo. Ya ce,
daga ina, oho bansan garinsu ba. Nace dashi. Na
leka dakin sunyi dirshan a kasa suna tacin abinci
suna zuba yare har da uban, a raina

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login