Showing 21001 words to 24000 words out of 27623 words

Chapter 8 - Darajar Yayana Book 1 Complete by Halima Abdullahi K Mashi .txt

dakinki in yi kwana
dayan da ya rage,sannan in koma gurin ta,nace,
to Allah ya tsare ya dawo da kai lafiya. Yara ma
ya sallame su, kamar yanda ya saba muka raka
shi har mota,har da Mujidat din sabe da danta
a kafada,duk da ba ta zo kusa da shi ba. Na
ce,baka sallami Abdul ba.nakalli Mujidat, Ki ba
Baban shi su yi sallama. Ya ce, A'a, bar shi
kawai. Ya tada mota, sam ban so yanda ya yi
ba,domin a gabanta ya rungumi sauran yara
tare da sumbatar su, fuu! Ta juya ciki, tun kafin
ya tada motar,nabita da kallo,sannan na
kalleshi. Yaya ka daina haka, yanzun mun zama
daya kuma wannan yaron ka ne kar ka gwada
bambanci ko ka ce za ka yi kara dan ganin
idona na san dai kana son danka,ya tada motar
tare da cewa, Na tafi.Na ce Allah ya tsare.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Gaskiya Mujidat ba ta bukatar muyi zaman
lafiya yadda take mu'amalarta da yarana amma
ni na sawa kaina alwashin sai dai tayi da wani
amma badaniba, duk da cewa na san ban girme
ta ba,amma a gurina zubar da aji ne in tsaya
cacar baki da kishiya,gurin cin abinci dama tun
yana nan bai hana kowa yin na shi ba.Da farko
na so in masa magana kan cewa ya za a ce
muna gida daya karkashin miji daya, amma mu
raba girki,sai kuma na ce bari dai in bar shi
tunda shi ke nemowa.sai kuma ta tsiri fita zuwa
gurin wasu 'yarbawa yarensu,sai ta kai dare.
Randa ta fita na uku na yi mata magana,tana
shiga dakinta na bita. Maman Abdul. Ta waigo
ta dube ni,sannan ta ci gaba da kwantar da dan
ta a kan gado. Na ce, Amma kin san mijinki ya
cekar ki fita ko? Ta ce, Na fita din zan ta zama a
gida ne? Ya amsar min waya,sannan ya cezai
hana ni fita, ba zan iya zaman takura
ba,nace,zaman aure shi ne zaman takura?
Ta ce, Maman Kausar don Allah ki barni kawai,
kije ki harkar ki.
Jin haka sai na tafi na kyale ta.
Yaya bai zo ba har sati biyu,duk da yana
kiranmuta waya ko yaushe yana tambayata ko
akwai wata matsala a zamanmu da Mujidat,nace
masa babu wata matsala, ina zaton bai
fadamata cewa yana zuwa yau ba, tadaiga na
haukace da aiki,munyo kitso da lallae ni da
yarana. Ina da nacin yin lalle dan na san mijina
yana matukar so, ya ce min shi zan tayi masa a
gida,don haka su Kausar suna dawowa daga
Islamiyya suka cire kayan makaranta na shirya
su cikin sababbin kaya.Allah ya taimake ta tana
shigowa ko minti goma batayiba na ji tsayuwar
motarsa,nafito daga dakinsa inda na kai turaren
wuta nace su Kausar ga Abbanku,da gudu muka
fita ni da su, nan ta fito kallonmu, duk da cewa
ko a da ta saba gani lokacin renon
cikinta.Dukkanmu muka rungume shi,tsaki ta ja
sannan ta juya cikin dakinta. Duk hidimar da
mukeyi bata fito ba, har lokacin da muka shirya
fita zuwa gidan Iya, na ce baka duba su Abdul
bafa.Yace, Uhm! Yaushe nashigo gidan? Ni zan
je in duba su koko suzasuzo duba ni? A nan na
yi Magriba na yi Isha'i,ba ta fito ba,in ma za ta
ce ba ta sanna dawo ba da Kausar ta kai mata
tsarabar su ai ta san na dawo,nace, duk da
haka ka leka,Tsaki yaja,sannan ya fita abinshi.
Na leka dakin, tana zaune bakin gado ta zabga
tagumi ranta a bace, nace, Sai mun dawo za mu
je gidan Iya,ga mamakina sai naga taja wani
uban tsaki tare da banko min harara, sai na ji
dariya ta subucemini, don haka na yi 'yar dariya
tare da sakin labulan nata, ina jiyowa ta yi wata
kalma da yaransu wadda nake zaton zagi ne.
Iya ta yi murna da ganinmu,sannan ta ce ina
'yar uwarki? Nace, Tana gida, ta ce a gaishe ki.
Tace,Ina amsawa. Ita bata fitane bakuzo da
itaba?Yaya ya ce, Ba za ta zo ba. Iya ta ce,
Sadiya ke ce zaki dinga janta in zaki fita, don ta
saba d mutane tunda kin ga ba ta san kowa ba.
Nace to Iya. Mun je gidan Yaya Sulaiman, Yaya
Zakari, da kuma Yaya Sani, duk mun ziyarcesu,
inda Yaya ya yi musu alkhairi. Ina jin dadin
yanda Yaya ke kula da danginshi suna shi masa
albarka, sai dai bayamin kara yayi wa
mahaifina.amma na sha alwashin koya
masa.Daga nan muka dawo gida,kai har yanzun
na tabbatar Yaya yana sona.sabida irin soyayyar
da ya gwada min ta dare dayan da yayi a
dakina. Washe gari mun yini gida cikin jin dadi
da annashuwa, amma Mujidat taki fitowa, sai
lokacin bacci sannan ya nufi dakinta.
Kuka ya sameta tanayi wiwi,ya isa kusa da ita
ya ce, Lafiya? Ta watso masa kallon banza da
manyan idanunta da suka kada suka yi jajir, ta
ce, Haka dama aurenku yake? Ka nuna min
cewa matarka kawai kake so, babiba. Ya ce,
Menayi miki? Ta ce, Tunda ka dawo ka ajiye ni
kamar kashi, matarka da yaranka kadai ka sani.
Ya ce, Kece ki ka ja jikinki damu, na dawo kinki
zuwa ki gaisheni.Ta ce, Ka fada min cewa zaka
dawo? Sai na fada miki dole sannan zaki gaishe
ni? To ni ba haka tsarina yakeba. Ta ce, Eh,
amma ka iya fadawa matarka ai, tunda naga
sun shirya,nima in ka fada min ai zan shirya. Ya
ce, To shi kenan next time zan fada miki tunda
dakin ki zan sauka, dan gobe zan tafi. Ta tashi
ta dawo daf da shi tasa hannu a kumatunsa,
Aliyu ina son ka da yawa, nima ka daure ka
soni. Ya yi murmushi, sannan ya ce, Ina son ki
mana, Ya kalli kitson ta. Har yanzu ba ki cire
wannan gashin dokin ba? Bana son shi. Ta ce,
To zan cire gobe. Ta dauko Abdul tasa masa a
cinya.Tunda ka dawo ba ka dauki yaronka ba,ya
kalli yaron cikin kauna, sannan ya soma yi masa
wasa da kumatun,sai dai koyaushe ya rike yaron
gaban shi yana faduwa, kuma yana tuna masa
cewa fa akwai wani asiri da ya boye. Ya kan ji
tausayin Mujidat a irin son da take masa, kuma
yana son ya kyautata mata ko don yanda ta
hakura da rayuwar bariki ta yarda zatayi zaman
aure,har inzata zauna da su lafiya to zai mata
adalci, don haka ita ma ya nuna mata soyayya
daidai gwargwado, wadda ita da kanta ta yarda
cewa ya soma sonta.Haka nan da zai tafi ya
sake tara muya yi mana nasiha,sannan ya tafi.
Dama makarantar da aka dauke ni koyarwa
sunce sai andawo hutu, tunda tuni sun min duk
wani abini da ya dace kafin a dauki duk wani
malami, don haka ana komawa hutu na soma
koyarwa a matsayin sabuwar malama, aji biyu
na nake dauka, wato 'yan safe. Don haka tun
Asubahi inna tashi nake kammala yarana ina
sauke su in wuce tawa makarantar, sai dai
matsala daya aikin gidana dole sai na nemi 'yar
aiki kenan. Kodanayi wa Aliyu wannan batun sai
ya ce dalili kenan da baya san aiki ga matarsa,
ba danbazai iya biyan 'yar aiki ba, a'a sai dan
ba za a tsaya a duba masa gida da kuma yara
ba. Na ce ni dai zan biya mai aikin cikin
albashina, ya ce ai ba wai ba zai iya biya ba ne
ya fi son ya ganni a gida.Iya na fadawa a samo
min 'yar aiki,tace in kuna da wadatar gurin
kwanane sai ku dauko Nasiba 'yar gidan Yaya
Zakari. Na ce ai matsalar gurin kwanan ne, na fi
son wadda ke kusa da gida,in ta yi aikin ta ta je
gida. Iya ta ce haka ne. Ansamo min wata
yarinya 'yar matashiya, kullum zatazo ta yi min
wanke wanke da shara,haka muka ci gaba da
tafiyar da rayuwa da dadi ba dadi, ina kuma
yabawa Yaya yanda yake kwatanta adalci
tsakaninmu, amma kullum Mujidat gani take yi
Yaya ya fi sona da ita. Albashina na farko naje
na sayo kayan abinci da zannuwa turmi biyu.
Ranar Yaya ya dawo ya tsaya yana kallon kayan
abincin.Wanna fa? Na ce, Babana zan
kaiwa,tunda na yi aure ban taba yi masa wani
abu ba. Ina kallon Yaya ya yi shiru yana
nazari,sannan ya ce, Nawa ne kayan nan? Na
fada masa ya ce to kafin in tafi zan baki.Nace
ayi haka Yaya daka barshi. Ya ce, Nima ai 'dan
shi neko? Na yi shiru, ya ce, To zan ba ki ba zan
so ba a ce kin riga ni kaiwa mahaifinki wannan
alheirin. Na ce, To shikenan Allah ya saka da
alkhairi. Ya ce ameen. Na ce, Ni dama ko da na
kai da sunanka zan kai.ya ce, Yanzun ma duk
ba haka ba,wai ke za ki je Zariyan?
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
na ce, Eh, wai da. Ya ce, 'A'a gobe zan je in kai
musu. Na ce don Allah ka je da ni. Ya ce a'a,ina
ce ke ce na ji Iya tana fada miki bikin kannanki
guda biyu? Na ce cikin shagwaba, Allah Sarki
Yaya bikin fa sai daf da Azumi akwai saura. Ya
ce, Eh, ki hakura sai lokacin. Na ce, Shi kenan.
To yanzun in kabani kudin nan me ya kamata in
siya? Yace, Oho! Miki, ki bude account mana. Na
ce eh, tozan bude.
Cikin wannan lokacin na soma rasa gane kaina,
ba sai an fada min ba na san cewa ciki gare ni,
ban taba irin wannan cikin ba mai masifar
laulayi. Binta yarinyar da ke min aiki ita ce ke ta
dawainiyar aikinta, har ma jinyata. Mujidat
kuwa ba ta zama,bata taba yimin sannu ba, sai
dai in jiyo tana ta yi wa yara wasa.Su Khausar
su ne suka sanar da Iya cewa ba ni da lafiya sai
ga ta. Ranar ita ce ta gyara min gida,sannan ta
kira Mujidat tana ta yi mata fadan cewa. Me
yasa 'yar uwar kina ciwo amma ba za ki taya ta
aiki ba? Sai ta ce wai ita ba ta sani ba, ko da
Iyan ta shigo tana fada na ce mata kar ta damu
Mujidat ba mai son aiki ba ce, don ko dakinta
ba kullum take gyarawa ba,Iya ta ce Allah ya
kayuta, ni sai in gakamar ba kwa zaman lafiya?
Nace, Lau muke ni da ban cika zaman gidan ba,
don dai ciwon nanne. Iya ta ce, To kin sanar a
makarantar? Na ce, Har malamai sun zo duba
ni. Ta ce, Allah ya kara sauki, ga shi kinki zuwa
Asibiti. Na ce to ko na je ba wani abu da za su
yi min sai magani, to ko maganin ba zan iya
shaba, ko fa ruwa na sha sai ya dawo. Nan Iya
ta yini kafin ta tafi..
Cikin dare kuma tamkar ba zan kwana ba,
Kausar da Binta mai aikina sune a kaina. Kausar
nata kuka,ta je ta fadawa Antynsu amma ta ki
zuwa, tama ki bude kofa, duk da irin
kwankwasawar da Kausar take yi, na ce su dau
waya ta kira Babansu,sabida gani nake tamkar
ba zan tashi ba. Ya daga kiran farko, Kausar ta
ce, Abba, Momy fa ba ta da lafiya. Cikin muryar
kuka ta yi maganar. Ya ce, tabani na amsa
sannan nace sufita,suna fita cikin muryar wadda
ke cikin matsananciyar jinya na ce, Aliyu ka
yafemin bana zaton ciwon nan na tashi ne. Cikin
daga murya na ji ya kirani da karfi, SADIYAA me
ke damunki? Cikin rauni na ce ka yafe min? Bai
amsa ba ya kashe wayar. Can jimawa sai ga
Mujidat ta shigo, na san cewa shi ne ya kirata,ni
dai daga karshe bansan me ke faruwa ba ma,
ashe wai suma nayi.Ihun Mujidat shi ne ya sa
su Kausar tashi daga bacci.ta kira shi tana ihu
wai bana motsi,kila na mutu ne,ya kidime sosai
da jin hakan kuma nan take ya kira Usman,
yasanar dashi duk abin da yake faruwa, cikin
daren Usman ya zo yana buga gida Mujidat sai
tace da Binta mai aiki taje ta bude, cikin tsoro
yarinyar ta ce waye? Ya ce nine Usman bude, ta
bude. Har dakina Usman ya shigo, Mujidat tana
ta ihu ya ce takama su sani a mota, ta ce ba
mutuwa ta yi ba? Usman ya ce sai na ji daga
likita.
Asbahin fari na farka na ganni a gadon
Asibiti,an samin ruwa. Usman da Mujidat na
gani tana zaune shi kuma yana jingine da
bango,ya zo kaina yana min sannu, na kalli
ruwan na gane ina Asibiti ne. Ya dubi Mujidat ta
farfado. Mujidat wadda bacci yake fizgarta,ta ce
uhm,uhum, tare da tabe baki,ta soma jijjiga
danta, sannan ta ce, sannu Maman Kausar.
Idona yana lumshe kai kurum na daga,ina ji
lokacin da Usman ya kira yaya fada masa cewa
na farfado. Yace shi ma yanzun haka ya wuce
Nasaraw daf yake da Unguwar Ma'zu , Usman
ya ce muna asibitin Biba ne. Aliyu ya ce ka fada
min. Yaya ya rude da ganin yanda na dawo,ya
kama hannuna ya zauna bakin gadon, Sadiya
me ya same ki? Na bude idanuna ina kallon shi
ya rusuno ya sumbaci kumatuna. Sannu kin ji?
Ya kalli Usman. Sannu Aboki, na gode Allah ya
saka da mafificin alkhairi.
Usman yace , Haba dai sai ka ce wani abu? Allah
dai ya ba ta lafiya. Aliyu ya ce ameen, na gode.
Da ya samu labarin cewa ciki gare ni sai na ga
Yaya ya soma murna,tamkar cikin fari. Usman
neya taho da Mujidat wacce ke ta yin gyangyadi
a zaune. Tunda duku duku sai ga Iya wai da
Asuba Binta da Kausar suka je suka fada mata,
ita ce ma ta tashe mu daga bacci, domin bacci
ya sace mu Yaya na kan kujera ya dora kansa a
gadon, hannuna yana kan nasa kawunan mu a
hade, motsinsa shi ne ya tashe ni, suka gaisa ya
fita sallah. Sai lokacin na tuna da 'yan yarana
su kadai kenan su ka kwana.
Kafin yamma naji karfi sosai sakamakon ruwan
da aka yi ta dura min mai dauke da sinadarin
abinci,likitan ya sallamemu tare da ba mu
magunguna. Tunda muka dawo gida yaya ke
jinyata,Sallah kurum yake fita har abin da zanci
shi ne ke girka min,, ya min wanka,abin ya
kunna Mujidat har ta kai su ga fada ya mareta,
tun daga lokacin ta yi wa kanta alkawarin kawo
karshen zaman shi da matarshi ko ta halin
kaka. Yayan da zai yi kwana biyu sai da yayi
biyar ya ga nadan murmure,sannan ya tafi..
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Duk abin da nake so sai da ya tanadar min
isasshe sannan ya tafi. Kullum gidan ba ya
rabuwa da 'yan dubiya. Aisha ta yi ta yi min
iskanci wai na narke sai ka ce cikin fari, Yaya shi
kuma ya daure min gindi tun da tazo ta ga yana
ba ni abinci a baki shi kenan fa,nace na ji dai ai
ko wane ciki na fari ne tunda wuyar dana ke ciki
da wannan na fari ban sha ta ba.
Na rarrafa kicin ina dafa taliyar Hausa, sai ga
Mujidat daga yawonta an zugo ta ta shigo da
fushi, Mama tana wasa da abin kama shanyar
ta da ya fado daga igiyar yaronta, ban ma lura
da shi a gurin ta ba sai na ga ta kwace tare da
rankwashin ta a kai tana zagin ta da Turanci.
Maama ta yanka ihu raina kuma bace na ce
mata. Ke! Na nuna ta da yatsa. Ki shiga
hankalin ki, wannan 'yar yarinyar zaki doka?
Wallahi ba zan dauka ba. Ta harareni tare da ce
min ta doketa, kuma kada in ga wai nayiwa
mijina asiri yana mata wulaqanci in dauka za ta
tafi ta bar shi, to in sani ita fa ba inda za ta,
domin shi kadai ta gani miji,sannan in shirya
barin gidan bada jimawa ba. Na yi dariya. 'Ke
ko Agumin ku yayi kadan bare ke, ba da tsafi ku
ke takama ba? Mu zuba ni na riqe Allah.Ta
shiga daki fuu! Na yi mutuwar tsaye ina
mamakin lamarin,wannan ai ke ce kwarkwasa
fidda mai gida a gidansa,iInshaAllahu ta Allah
ba ta ki ba.
Haka muka ci gaba da zama cikin husuma
kullum sai ta tsokaneni,in na yi kamar in hada
ta da mijinmu sai in kyaleta. Ashe ita kullum aka
yi saita kirashi a waya. Sai da ya yi wani zuwa
yake min zancen wai me ya hada mu da Mujidat
ne?nace me akayi, tace anyi wani abune? Ya ce,
Eh tace kin canza yanzun kintsaneta, kiyi ta
zaginta kina mata gorin bana sonta,in ko har
hakane bazanji dadiba, domin batun ina sonta
ko bana sonta tunda yanzun ita ma matatace
bai kamataba. Yafa bata rai wai dole sai ya kare
mutuncin matarsa,inzaiyi adalci ai nasan ya fi
nuna so da kauna gare ni. Nayi 'yar dariyar
takaici, sannan na ce, Tunda ka mance halina
har ka yarda da batunta shikenan. Amma in har
adalcin zakayi kamataya yi ka tara mu,dama
'yan sanda da bangare daya suke aiki in sun ji
ta bakin me kara ya isar musu hukunci? Ya yi
shiru sannan ya ce, To muje falo a kirata, Na ce
a'a a barshi ni nayarda na dauki nauyin
zunubin.ya ce ni dai na ce ku fito falo.
A gabanta na maida komai kuma ba ta musa
ba,baisan tana fita ba sai lokacin danace ina
taje aka zugota. Nan fa ya zaro ido ina take
zuwa? Na ce ga ta nan ita ta sani, hankalinshi
ya tashi ya ce mata gurin wani take zuwa? Ta
zaro ido wai a'a gurin yaren su ne, dama shi
irin wannan auren haka kullum a yi ta zargin
juna, nan na tashi na bar su suna ta masifarsu.
Kafin ya tafi sai da ya kafa mata dokoki har da
na fita, amma yana tafiya ta sa kafa ta shure
dokar,sabida jarabarta ma ni na lallaba na soma
zuwa aikina, yara ko na kwaso su sai in kai su
gidan Iya in bana gida bana barin su a gida.
sai dai wani abu da na lura da shi shi ne wata
dinkewa tsakanin Yaya da matar shi Mujidat,
duk da cewa bai canza min ba, amma ina
mamakin sabuwar shakuwar in yana dakinta har
wani zumudi yake yi,sannnan ya kan dauki
danta ya fita da shi wani dare ma har saloon ya
kai ta, ko da dai ya min tayin zuwa na ce a'a,
sannan ya kan dauke ta da yara su fita shopping
duk da dai ya kan min tayin zuwa,ce masa nake
a'a sai sun dawo. Haka nan zasu zomin da
tsaraba,abin yana ta damuna hatta abincin ta
da yake cewa ba zai ci ba yanzun nadeshi yake
yi. Wani zuwa da ya yi sai na yi niyar gwada shi
ranar da ya dawo dakin Mujidat zai sauka sai na
yi tuwon shinkafa da miyar Ogun, bakwai da
wani abu ya iso gidan. Taliya ta dafa dama
girkinta bai wucetaliya da shinkafa da miya ba,
ga shi ta zabga uban attaruhu, ta saka wando
da riga an je an wanko kai, dan ma ba wani
gashi neda ita ba da na doki ake gayun, kuma
ya hana sawa,da in ya dawo ni yake fara nema
a ko yana dakinta, yanzun kum in dakinta yake
can yake yada zangoi,sai daga baya sannan ya
zo. Ina sallar Isha'i ya leko, sai kuma ya shigo
ciki ya zauna,sannan na gaida shi ya amsa tare
da tambayar jikina na ce da sauki sosai, na kalle
shi. In kawo maka tuwon shinkafa miyar ugun
ce? Kafin ya yi magana sai wayar shi ta soma
kara, da ya daga sai ya ce, Ya? Ina jin haka na
san Mujidat ce, ko me ta ce sai na ji ya ce'O.k,
gani nan, Ya kalle ni.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Mujidat ce take jirana muci abinci, na so cin
tuwon amma yaya zan yi tunda girkin ta ne zai
fi kyau mu ba ta hakkin ta ko? Raina ya sosu
matuka, amma sai na danne na ce, Haka ne, na
ga ai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login