Showing 24001 words to 27000 words out of 27623 words
Chapter 9 - Darajar Yayana Book 1 Complete by Halima Abdullahi K Mashi .txt
kuna ta dasawa. Ya kalleni, Kamar yaya?
Na ce,gani na yi kana ji da ita. Ya ce, Lallai
Sadiya,harma zakice haka yanda na fifita ki a
kanta kuma ta hakura? Nayi guntun murmushi,
Ni ba ni san ka fifita ni a kanta, na fi son ka yi
adalci, ni na san dama duk zance ne da ka ke
cewa ba ka sonta. Ya hade rai, 'Wannan wace
irin magana ce? Kin san ai matata ce, batun ina
son ta ko ba na son ta ki aje shi. Ya mike tare
da fadin. Banason irin zantukan nan kowacce ta
zauna a matsayinta. Ya fice abin shi. Na jima
ban iyatashi ba, eh na san ba laifi ba ne dan ya
nuna kulawa ga matarsa,amma abin da ke ban
tsoro yanda na ga yana son hada matsayin da a
da ya ce ni kadai ke da shi ya raba mana. Anya
nan gaba Yaya ba zai bijiremin ba? Wata zuciyar
ta ce haka wane shi, zai manta asirin da Allah
ya rufa masa kuma ke ma ki ka rufa masa.
Da safe muka shirya da yara zan aje su a
makaranta nima in wuce gurin nawa aikin,sai
lokacin suka bude kofa muka gaida shi, sannan
muka wuce. Ko a makaranta a ranar tunani
nake ta yi in zan lura da kyau yanzun ma bai
cika nema na ba sosai, ga zatona don ba ni da
lafiya ne, amma yanzun na gane ba haka bane.
Da muka tashi na kira shi na ce zan biya gidan
Anty Abida,sai cewa ya yi shi fa ya tsani wannan
yawon,daga can bai ce in je koina ba, na ce to.
Cikin kuka nake fadwa Anty Abida matsalata,
dariya ta yi tare da cewa, 'KISHI ke damun ki
Sadiya ga shi kin fada kin ce mijinki bai canza
miki ba,dan ya nuna kulawa ga matar shi ya ci
abincinta sun fita tare laifi ne? Na yi shiru. Ta
ce, ko yana miki sababbin dabi'u? Na ce, Eh, to
jiya dai da na yi masa korafin cewa yanzun yana
sonta kinga yanda ya bata rai,yana ta fada. Ta
ce, Kar kikara yi masa zancenta, ba ruwanki da
harkarsa. Na ce to shi kenan,amma fa bai cika
son Taliyaba ko na dafa sai na yi masa abin da
zai ci,amma ita sai ta yi masa yayi taci. Anty
Abida ta ce, Na ce miki babu ruwanki. Nace,
Yanzun duk ba shi da laifi? Ta ce, Babu. Na ce,
shi kenan. Tace ki kauda kai ga tunanin zai
canza kiyi ta kanki da lafiyarki. Na ce to Anty shi
kenan. Na nufi gida ina zaton sam Anty ba ta
hasashi abin da nake hasashe ba.
Tsakiyar falo muka same su ya dora Abdul
saman kafadar shi yana yi masa wasa, yara
suka yimasa sannu da gida,su ka nufi dakin
su,nima dai sannun nayi masa zan wuce yace,
Abdul yana ta kallonki MY CHOICE. Na dawo na
daga masa hannu tare da yin dan yake,nawuce
dakina.Ina kwance kan gadona ya shigo baifi
minti biyar da shigowa ba, Sadiya! Ya kira
sunana,bayan ya zauna bakin gado, na amsa da
na'am ba tare da na taso ba. Ya ce, Ni na ga
kamar kin canza min? Na ce, Kamar yaya? Sai in
ga kamar idanunki suna tuhumata a duk lokacin
dana kalleki? Na ce, A'a kai ne dai ka ke zargin
kanka. Yace,shikenan, ya jikin naki? Alhmdllh.
Ya ce, To haka akeso.Yakai hannunsa ya shafi
cikina,ya babyna? Ban tanka ba dan ni fa
yanzun abu kadan ke bani haushi, ya juya zai
fita kenan sai karar shigowar sakonni cikin
wayata, ina ji na san daga facebook ne,na kai
hannu zan dauka shi ma ya kai, saiya riga ni
dauka, gabana ya fadi dan na san cewa ya ce na
goge,ban goge ba. Ya dawo ya zauna, 'Sadiya.
'Na waiwayo na dube shi. Bana ce ki rufe
wannan account din ba? Na ce, 'Zan rufe ai. Ya
ce, ba kida niyya. Ya soma fada. Ni fa bana son
taurin kai,wata nawa da cewa ki rufe,mekikeyi a
internet?na ce 'Karuwa! Nima cikin zafin rai na
fada,ya ce in ban da shashanci dubi yadda
maza suke requesting dinki. Na ce, sai ka duba
ka gani na yi accepting? Ya ce, Ina ruwana, na
dai ce ki rufe kuma kin ki don haka yaune
karshe, in ba ki rufe ba sai kin daina rike
babbar waya. Zuciyata ta tunzuro na ce, O.K,
sabida nice zakace ma haka, amma matarka da
yake ita kana shakkarta ba yini take yi chatting
ba? Ya ce, Ita ma tunina hana,ita da har wayar
na amshe na ba ta karama me ta ce? Na dago
na kalle shi, Har yanzun chatting take yi. Ga
mamakina sai na ji ya ce, Karya ki ke, 'yar Nokia
ce a hannunta,ina ruwanki ma in me take yi? Ke
dai ki hanu mana da abin da na hana ki? Ke
yanzun kin kama taurin kai,nema kike ki canza
hali ko? Kinfi son a yi ta fitina? Fuu! Yafice
abinsa. Sai na samu kaina da jin zafin
kalamansa,kuma na dauke su a matsayin
wulaqanci da tozarci,wata zuciyar tace me yasa
tuni da ya ce ki rufe account din kika qi? Ina
kokarin amsa laifi na ne sai wata zuciyar daga
gefen hagu tace shi ne zai fadamiki kalaman
batanci har da kiran ki shashasha? Bayan ita
waccan tana yin chatting ma bai hana ta ba har
da cewa karya ki ke mata, to kema kar ki rufe
duk abin da zaiyi yayi. A fili na ce, Ni da nake
karanta abubuwan karuwa a ciki ma ba zan rufe
ba.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Har ya tafi sama sama muke, amma duk da
haka yana kiran wayata sai dai ba na iya yi
masa hira dan haushisa. Tabbas in ma ya hana
Mujidat hawa internet to tana yi a boye dan
tana yi a gabana, sannan ba ta daina zuwa
gurin yarensu ba. Ni kam yanzun ba abin da zai
fi min illa in yi watsi da su in yi ta kaina. Kwanci
tashi cikina ya shiga wata na biyar,na dan
gyagije daga laulayi,kuma na soma siyayyar
kayan babyna. Tabbas Mujidat tana jin haushin
cikina,don ina lura da irin yanda take yawan
zabga min harara, sannan in ba ni ce na yi
mata magana ba itabata yi mini. Haushin da
take ji nawa a yanzun ko da da yayan bai damu
da ita ba ba ta ji kamar yanzun. Wata Litinin na
dawo daga aikina tare da yarana, na kai minti
biyar ina buga gida ba a bude min ba, har
nasoma zaton ko ba kowane a ciki, sannan aka
zo aka bude, sai dai wani rainin wayo ashe suna
zaune a harabar gidan ita da wadanda take
zuwa gurinsu su ma yau sunzo gurinta. Cikin
fushi na kalleta. Maman Abdul kina nufin
zamanku a nan bajuji duk bugun gidan da
nayiba? Ta yatsina fuska, Na ji mana ba gashi
na bude mikiba? Na yi kwafa tare da juyawa na
nufi ciki,sai na ji sun yi wata magana cikin
yarensu,sai kuma suka kwashe da dariya, na
dawo baya cikin zafin rai na ce Maman Abdul ki
ce da mutanen nan su fita,tace yazakice su
fita,wurin ki suka zo? Na shiga kicin na dauko
muciya nanufe su. Ku fita daga gidan nan maza
maza.Cikin sauri suka fita suna yare, itama
tabisu, na maida gida na rufe, na koma ciki, ina
ta huci. Hatta su Kausar sai kallona sukeyi
tamkar na zamar musu sabuwa. Kusan awa
daya na ji tana buga gidan, banza na yi da ita
har Al'ameen sai da ya zo ya ce Momy ana
buga gida, shi ma na kore shi, kusan minti
goma waya ta ta soma ruri na gane Aliyu ne,
dan ringing din shi daban ne, na daga raina a
cushe,ban raini shi yasa dukwanda ya yi min
raini nake jin zafi. Ya ce, Sadiya yaya za ki rufe
mata kofa, ki bar ta a waje? Na ce, Wa? Ya ce,
Au! Ba ki ma san kowace ce ba? Bari ki ji
Mujidat fa matata ce kuma ina son ta kamar
yadda nake sonki tayaya zaki hana ta shigowa
gidana, duk rigimar da kukayi dai ai kin san ba
ta da inda za ta. Zantukan shi suka zafafa
zuciyaa,sai kawai na kashe wayar, yayi ta kira
na ki dagawa,can sai ga kiran Anty Abida, ta
soma min fada wai me yasa na canza, mijina da
ke yabona ya koma korafi akaina. Na ce, Allah,
Anty ba zan bude ba, ni za ta maida 'yar iska?
Shi kuma dayaji ta bakinta baya tuntuba ta, sai
kurum ya kira niya fara masifa, nagaji, shi
kanshi fa ya'isheni ke! Anty Abida ta katse ni
'Kina hauka ne za ki ce mijinki ya ishe ki? Shi
kuma wannan cikin da masifa ya zo miki? Ki
bude mata gidan ta kira shi ta mafada masa, ya
kira ki kin ki sauraron shi shi yasa ya kira ni,
nima ba ki saurare ni ba? Shiru na yi mata tace,
Shi kenan. Ta kashe wayar, ni kaina ina
mamakin kaina yanda zuciyata ke ta
tafasa.Kamar daga sama su Kausar suka ce
Momy ga Iya fa. Na buga kafa,ashe shi ya kira
Iyan ya fada mata, jikina na rawa na je na
bude, ta kalleni ranta a bace. Sadiya lafiyar ki
kuwa? Yaya za ki koro abokiyar zaman ki waje ki
kulle gida? Na kalli Mujidat wadda saboda
makirci har da yin hawaye, na ce,Iya akwai abin
da ya faru. Iya ta kalleta jeki dakinki kinji? Na
soma kuka. Yaya za a ce kowa ba zai tambayi
ba'asi ba sai kawai a yita ganin laifina? Iya ta
ce, An gani, sakarya, a gaban kishiya za ki yi
kuka 'ya'yanki suna kallon ki. Fuu! Na juya na
nufi daki raina a bace, ina gunjin kuka, Iya ta
biyo ni cikin daki tace, Sadiya yaushe ki ka zama
haka? Na ce, To, ni Iya shi kenan ba wanda zai
tsaya ya ji dalilina? Ta ce, Eh, ba wanda zai ji ke
bake ce babba ba? Ko me ta yi miki sai ki tura
ta waje? Me mutanen unguwa za su dauke ki?
Na ce, Wallahi Iya ni ban tura ta waje ba, ki
fada mata ita ma in na buga kofata ringa bude
mini. Na kai minti biyar ina buga kofa suna
wurin sunki bude min, da ta ga dama ta bude
na yi mata magana nace meyasa ta barni tsaye
ina ta buga kofa ga yara ni kaina na gaji fa, sai
ta ce min wai batajiba. Na tafi kuma suka yi min
dariya suna yare, ni ko na cewa wadancan su
fita shi ne ta bi su ni ko na rufe kofa. Iya ta ce,
shi kenan zanyi mata magana,amma kema ki
dinga tausan ranki dan naga kina fama dazafin
rai,ina zaton kuma ciki ne ke saki saurin fushi.
Na ce ko ba ciki dole inji haushi,Shima yaya ba
bincike ya kira ni yana ta min ihu shiga mai
mata,har da fadin cewa wai gidan shine, to ina
ruwana da gidan shi? Na soma sabon kuka, Iya
ta ce ki yi hakuri zan yi masa bayani, na san
cewa har da ciki wannan saurin fushin ki dinga
yawan salati kin ji? Na turo baki nawa ganin sun
dai ki fahimtata ne, na ce ita ma ki gaya mata
fa? Shi ma ki gaya masa. Ta ce zan fada musu.
Ta dinga tausa ta har zuciyata ta sauko sannan
ta tashi na raka ta,ta shiga dakin Mujidat ni
kam na yi bakin gate jiran ta.ta iso ta ce na yi
mata fada ita ma,don haka a zauna lafiya. Na
ce to Iya na gode, da na rufe gidan na dawo sai
naga Mujidat ta shiga kicin tana kumburi,nima
na yi cikin dakina. Iya tana isa gida Aliyu ya
soma kiranta,sai da ta zauna, sannan ta daga
wayar ta ce, Na dawo ai ta bude mata,dama
ashe ba ita ce ta koro ta ba. Ya ce, Ita din ma
za ta iya saboda yanzun Sadiya ban da neman
fitina ba abinda take yi, shi yasani yanzun ko
son zuwa Kaduna banayi. Iya ta ce, Ita ma
Sadiya ba laifinta ba ne kowane da irinsa,kuma
ba sabon abu ba ne kowa ya san mai ciki da
saurin fushi. Ya ce Iya ba ruwan ciki kada ku
goyi da bayanta, na soma tunanin damar dana
bata ne take zuwa koyarwa,can ake zugo ta, don
haka in na zo zan soke. Iya ta ce, Kull Ban yarda
ba,ba abin da ya shafe ka da batun aikinta, ka
dai yi hakuri har ta haihu,kuma wannan rikicin
tsokanar ta Maman Abdul din suka yi ita da
yaransu, shi ne ta kori wadancan ita kuma ta bi
su. Aliyu ya ce, Amma da na kira ta ba sai ta
fahimtar da ni ba, shi ne zata tsaya yi min
taurin kai? Iya ta ce, Na dai kashe wannan
wutar zancan kuma ya mutu.Ya ce shi kenan.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Goman dare ya kira ni na daga ciki ciki muka
gaisa, ya ce ranar Litinin zai turo da kudin
abinci, na ce muna da abinci mai ne da su
maggi ya kare, sai Indomie.
ya ce to bayan nan ba wata natsala? Na ce
babu, sai kudin asibiti zan soma zuwa
awo,sannan sai kudin siyan kayan baby. Ya ce
to na ji nawa zan bada? Na ce to ka san dai
komai sai na siya sabida bakamar na Mama ba
da na yi amfani da wasu abubuwa na Al'ameen.
Ya ce, Ni dai kudin na tambaye ki, Na hade
fuska kamar yana gabana. Na ce, Dubu Hamsin.
Ya ce,hamsin? Na ce, Eh, kila ma ba za su isa
ba,in kuma in bari sai ka zo mu je to. Ga
mamakina sai na ji ya ce, Me yasa haihuwar
Abdul ba a kashe wannan kudin ba? Wani bakin
ciki da takaici da ya zo min wuya, kawai sai na
kashe wayar, Ina jefar da wayar yana sake kira,
na daga ya ce, Lallai na yi kuskuren barin ki ki
fara koyarwa, daman can kika koyo sababbin
dabi'u kin rainani, ba ki da buri sai ganin nuna
husuma, to zaki dai na koyarwar in ga tsiya. Duk
da qoqarin da nai in danne maganar,ashe ta
fito,sai kawai na ji na ce, Sai me in daina mana?
Ya ce, Iye! Lallai kin rika ba laifin ki ba ne
nawaa ne da na kira ki. Sai ya kashe wayar.
Sororo na tsaya ina kallon wayar zuciyata tana
ta yi min fadan cewa ban kyauta ba, mijiki yana
son kyautata miki amma na kasa yin abin da ya
dace.Hawaye ya soma zuba a idona,na dauki
wayar da nufin in ba shi hakuri,amma sai wata
zuciyar ta ce da Allah bar shi ya karata. Sai ko
na yi tsaki na share.
Allah sarki ranar Litinin ina zaune tare da
Malamai kawaye na muna hira,sai ko na ji
shigowar sako,ina dubawa sai na ga alert ne
dubu sittin kamar minti goma sai sakon shi ya
shigo kurum cewa ya yi goma na asibiti,tausayin
shi ya kama ni. Tun ranar damuka wannan
husumar ba mu sake yin waya ba,don ya ki
kirana,take na soma kiran layin shi amma har ta
katse bai daga ba,sai na ji haushi tare da jan
tsaki. Da na koma gida ban samu Mujidat ba
duk zatona tana can gurin yawan gulmarta,sai
na ga har dare bata dawo ba, duk da cewa ba
ma shiri sai naji na damu,na kira Iya na fada
mata,ta ce ina ta je? Nace na dawo bata nan.
Ta ce to duk inda ta je ta dawo,tun da ba
yarinya ba ce. Wasa wasa har washe gari nakasa
hakura na kira shi ya ki dauka,sai na tura masa
sako cewa Mujidat fa ba ta kwana a gida ba,don
Allah ya kira ta ya ji in da take, dan ba ni da
lambar ta. Kamar mintibiyar sai ga amsa. Kar ki
damu muna tare. Shiru na zauna ina nazari, har
mun zo lokacin da Yaya zai min haka? Nan na
kira Anty Abida da kuka ina karanto mata
komai,tun daga wancan rigimar da muka yi ta
kudi zuwa yau. Ta ce abin da yayi shine daidai
ya barki kici masifarki. Cikin kuka nace, Kunki
fahimtata. Tayi tsaki sannan tace, Tunda kin rika
har kina rigima da mijinki sai ki yi ta yi. Ta
kashe wayarta. Na yi dogon tunani don in gano
laifina,amma kwanyata ta toshe,don haka sai na
watsar.
Kwanan su goma sai ga su ta zo tana ta isa da
bunkasa,ita ga 'yar gaban goshi. Allah ya
taimaka ranar zuciya ta sumul, na musu sannu
da zuwa har da ba su abinci, su Kausar suka
soma rige rigen daukar yaronta,don in bana nan
ya kan basu shi, duk da cewa ita bata so,daga
nan na koma dakina na kwanta. Shi kan shi bai
zaci zai gan ni wasai har in kalle su ba. Ya shigo,
Ya jiki? Na ce ba inda ke min ciwo, ya ce kin je
Asibitin? Na ce eh, Na nuna masa kayan da na
siyo na baby na ce ga kayan can, ya kalla. Allah
ya raba ki lafiya. Na ce amin. Ya ce,saura wata
nawa? Na ce, Eh to, EDD dinasunce watan sha
biyu ne, yanzu kuma muna watan tara,saura
wata uku. Ya ce, An kusa, ina san nema in
canza gadajen gidan da kujeru,tunda na samu
na sai filin can.
Na ce, Au har an siya bamu da labari? To Allah
ya sanya alheri. Da sauri ya ce ta waya muka yi
komai na tura kudin ta banki ko Iya bata sani
ba tukunna. Na ce, Allah yasa alheri. Ya ce
ameen. Can kuma sai me? Ya ce, Nasan na miki
laifi na kira Mujidat bada sanin ki ba....... Da
sauri na daga masa hannu, Yaya dan Allah duk
abinda ya shafi batun matarka bana son ji
sabida bana buqatar bacin rai, don bana son in
yi wata magana ka yaba min baka Matarka ce
ku karata.sai na mike na bar dakin zuwa falo na
zauna. Aikuwa washe gari ya tafi..
Yadda akai Mujidat ta tafi Abuja kuwa, tsohon
saurayinta mai nacin sonta wanda ko yaushe
suke yin waya, shi ne ya fada mata zai shigo
Abuja tayi kokari su hadu mana. Aminiyar ta
Murfat ta dinga yi mata famfo ta je ta shirya
mata yanda zasu hadu.Don haka ta kira Aliyu
cikin kukan ta wiwi, yatambayeta dalili sai ta
fada masa kewarsa ce ta dameta, yaushe zai zo?
Yace bashi da rana domin yawan rikicin su ya
isheshi. Ya ce, Kin cika tsokana da mata ta ba
ruwanta amma zuwan ki kin maida min mata
mafadaciya. Ta ce, ba ruwa na kishin matar ka
yayi yawa, alhalin kuma ba ta kaini son kaba. To
yanzun ya zan yi don bazan iya riqe kaina har
zuwa wani lokacin ba. Ya ce, to ki taho gobe zan
zo in dauke ki,za muyi tayin waya har ki iso.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ranar da ta cika kwana hudu a can ne suna cin
abinci wayar ta ta soma ruri, ya fi kusa da
wayar don haka sai ya dauka, Uncle ya gani an
rubuta, ya ba ta ta dauka da murna ta ce,
Uncle yaushe za ka shigo Nigeria? Ya ce, Bakiga
lambar da na kira ki ba? Ina Nigeria ai, ina
Abuja. Ta fara ihu ai ita ma tana Abuja gurin
maigidanta, ga shi ma su gaisa. Aliyu ya amsa
suka gaisa,amma shi sam bai ji abin ya shige shi
ba, yana jin su har ya yi mata kwatancen inda
suka sauka, Aliyu ba inda bai sani ba, don haka
ya ce ya gane gurin,sai dai ba za ta ba, ta dinga
rokon shi wai kanin Mamantane da ke zaune a
Germany,sun dade ba su hadu ba. Da kyar ya
yarda gobe zai kaita. Washegari ya kai ta dakin
shi har suka gaisa da shi da wata da ya gabatar
masa wai iyalinsa ce, nan Mujidat ta rungumeta
tana fadin, Anty. Shi kuma ya dauki