Showing 1 words to 3000 words out of 22554 words

Chapter 1 - Darajar Yayana Book 2 Complete by Halima Abdullahi K Mashi .txt

Darajar Yayana2-01
Posted by ANaM Dorayi on 09:52 AM, 20-Mar-16
Under: DARAJAR 'YA'YANA
___________________NA
___________HALIMA K/MASHI
Assalamu'alaikum, barkanmu da warhaka fatan
kuna lafiya,nasan kunjini shiru a cikin wannan
littafin,lallai kam kusan incemuku babu wani
kwakwkwaran dalili face rashin kulawa daga
gareku,saidai dayake ni nayi niyya dole
incigaba,da wannan nake bawa masu yawan
bibiyata hakuri,In Allah ya yarda da sannu zamu
kai har karshen littafin,
Na tashi na shiga wanka ina yan kun kunai,ko
kallona Iya bata yi ba, sosai nayi gayu atanfa fara
da sirkin purple ne. Haka takalmana da mayafina
duk purple ne, na fesa turaruka sosai.Iya ta
kalleni ta ce, da ma na san kun hada bakine shi
ne za a gwada min bariki, in dai namijine kuje
Allah ya taimaka. Ni dai nayi sororo raina babu
dadi, sannan bani da mifita.Har cikin gida Usman
ya shigo suka gaisa da Iya, sanan yace zamuje ne
ta gaida Ogansu Aliyu.Iya ta ce, menene na
shirya karya Usman ku da matarku.Nina haifeku
fa har da kukega zaku yi mun wayo, a gaida
Gyambo karshen girma kenanko? Usman ya
sunkuyar da kai yana dan murmushi cikin jin
kunya, ni dai na ce sai na dawo.Da mota yazo na
shiga, gidansa muka fara zuwa ya ce inga Abida
matarsa minti biyu. Ina yin sallama ta amsa,
sanan ta ce kai Amarya kin tsula kyau sosai, taja
hannuna zuwa bedroom din ta. Zo muyi yar
shawara,Bakin gado muka zauna.Ta kalleni a da
banyi zaton zaki zama mai taurin kai ba.Na zaro
ido ina kallonta, ta ce, ranar juma'a da daddare
mijiki nan ya ci abinci tare da mijina, ina daga ciki
ina juyo su mijinki yana fadawa mijina halin da
yake ciki na takura.Gashi kinki ki bashi hadinkai,
har yana cewa wani dare da kika ki sauraranshi
har ya dagawaya ya kira wata yar sanda dake
nacin sonshi ta kuma sadaukar da kanta
gareshi.Har ta daga sai kuma tsoron Allah ya
shige shi, Allah ya taimaka ya tashi ya shiga yin
nafila, daba dan haka ta faru ba, me kike
tsammani?Na ce, wai Allah, daga nan sai
zina.Tace kina da kwamasho ko baki da shi?Na
ce, ina dashi.Madallah.Ta dafani yanxu abinda
nakeso dake, kinga ke yar zamani ce, ki rike
mijinki, in ba haka ba sai wasu su rike maki
shi.Na ce, anty iya ce, Allah ba dan Iya ba zanyi
duk abin da yake so.Ta ce, to baga shi yau zaku
fita ba, in kin dawo Iya ganewa zatayi?In ba ke
kika fada mata ba.Nayi shiru ta ce, to kisani kina
cikin tsinuwar ubangiji, in yanxu kika mutu mijinki
yana cikin wanan halin sai kin hadu da fushin
Allah, ma tsawar ba shi ya yafe maki ba.Gabana
ya shiga faduwa, na ce, Allah anty nitsoro nake ji
ban san yaya abubuwan suke ba, nima bansan
yana fushi dani.Tayi murmushi ba wani
wahala.Ta girgiza kafadarta, ki amince da mijinki
a duk lokacin da ya bukaci haka na rokeki.Na
raunana muryata, in na sa muku aure ba?Na ce
eh.Ta ce ki ceci kanki daga halaka fa, kin san
komai ke ba jahila bace....Muryar Usman ta
katsemu da cewa wai me kike kitsa mata ne?Zo
mutafi kinji.Ta ce, jeki kada yajimu basusan naji
firarsu ba, dan Allah ki kama mijinki hannu
bibbiyu ko bakya son shi?Na sunkuyar da kai ina
sonshi mana, bari dai in gani ko zan iya ina
tsoro.Na fita muka tafi.,ban san ina muke tafiya
ba, don kaina yana sunkuye ne ina wasa da
yatsuna.Har zuwa lokacin da motar ta tsaya.Ina
daga kaina COMMAND GUEST na gani.Ya ce jirani
kadan ina zuwa.Gaba na ya shiga faduwa, koda
ban san ko inane nan ba na tabbata Hotel ne
tunda naga an rubuta guest.Bayan wasu lokuta
ya dawo yana waya, danhaka da hannu ya yafito
ni, na fito a baya nabishi yana ci gaba da tafiya
tare da tin waya.Kuma na fahimci kamar da ya
Aliyu suke magana, dan naji yana fada mai ga
mu nan yanxu zamu shiga cikin hotel din.Kuma
ni zan wuce ne dan Allah kayi hanzari muka ratsa
falon muka nufi jerin dakuna yasa makulli yana
bude wani daki.Dai dai lokacin sako ya shigo cikin
daki wayata, na ciro na duba.Cewa yayi kishiga
kijirani kadan my choice.Na kalli Usman yayi
murmushi ba da jimawaba zai zo, yanzu zaki
ganshi.Na shiga cikin dakin ina dari dari, tare da
yankalle kale, ya tako ya shigo dakin.Kada ki
damu ya dauki remote ya kunna TV, kiyi kallo ga
tashar India nan abin sonku mata.Ya nuna mata
wata takarda.In kina da muradin wani abu ga
wanan takardan ga numbe waya ki kira ki zabi
dayadaga nau'in abincin da kike so ko na sha, za
a kawo miki.Ku ziyarci blog dinmu domin karanta
Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Har ya kai bakin kofa sai kuma ya dawo, ya ciro
wallet dinsa ya bude ya ciro katin MTN ya miko
min.Gashi ki loda a wayarki.Ya sake juyawa ya
tafi, tare da cewa ki kulle kofar in yazo zai
kwankwasa sai ki bude, na barki lafiya.A sanyaye
na ce, na gode.Tunda ya fita ta gumi na hada,
tunani da zullumin abu biyu ne na farko in ya zo
mai zai faru?Sanan yaya zan kare da fada iya in
na komagida?Ban ma san takaimaimain lokacin
da zamu bar nan ba.Fim din da ake yine ya dan
shagaltar dani, don haka ban lura da lokaci ba,
sai da na kalli a gogo na rude, shida dai dai na
yamma.A raina na ce tafiya zanyi.....kwankwasa
kofar ya dakatar dani, na bude cike da faduwar
gaba, a zatona shine ashe ma aikacin gurin ne
yake tambayata ko zanci wani abu?Na ce a a yace
kada ki damu Oga ya na nan zuwa, ban tanka shi
ba na maida kofar na rufe.A raina nace wato har
sunsanshi tunda gashi suna cewa yana zuwa.Na
ce wa yasani ma ko yana zuwa da mata.....na
katse zancen da cewa a'u'zubillah, ba kyau
munmunan zato.mikewa nayi ina ta kai komo a
tsakar dakin, tunanina wa zan kira wanda
zaikaiwa iya waya in mata bayanin cewa yaya
nake jira mu dawo.Can na tuno da Bello, na kira
wayarsa dan akwi number shi a wayata, kuma
yana kiran Aisha itama tana kiranshi da layi
na.Muka gaisa, na ce dan Allah Bello in kana
kusa ina son magana da Aisha ne, tayaya zaka
taimaka min?Ya ce bani minti hudu zuwa biyar a
kai mata. Na ce nagode. Sai da na bari kusan
minti shida sanan na kira cikin sa'a kuwa ta
daga.Na ce,Aisha taimako nake nema a wajenki,
don Allah.Ta ce na me?Na ce, kin sani ne?Mun
fita har yanzu bamu dawo ba, shine nakeso kije
kicewa iya don Allah kada taji shiru mun nan
dawowa.Ta ce, keda wa kuka fita?Na turo baki
tamkar ina gabanta, nace da wanan ya Aliyun
mana.Da sauri ta ce, au, ke da mijinki kika fita?
Bata jira amsa ba ta ci gaba da cewa, to ba zan
fada mata ba, na zata ma ke da wata ce, to in
shekara ma zakuyi ina ruwanta?Ta ja tsaki.Dan
Allah malama in zakiba mijinki kulawa ki bashi
kulawa kawai, sai an jima ta kashe batare da
nasake jinta bakina ba, nayi sororo ina kallon
wayar.Shi kuwa ya Aliyu daidai wanan lokacin ya
isa gidansu iya.Tana girki yayi mata sannu da
gida, ta ce yauwa ina yar tawa?Ya ce, yace yanxu
zanje in sameta in nayi wanka daga gidan oga
xuwa gidan sauran Abokai na.Murmushi iya tayi
ta ci gaba da cewa, wai ni za'a yiwa wayo, nifa
na haifesu, ni fa duk abinku kar nake kallonku.
Shiri yayi ango sosai, sai zuba kamshi yake yi, ya
nufi masauki na comman bayan yayi tsarabar kaji
da lemuka da kalolin madara masu tsafta. Ya
gaisa da masu tarbar bakin inda wani daya yake
tabbatar masa da cewa a jiyarsa na nan a ciki,
sun lura da ita yanda ya kamata.Kwankwasa
kofar ta re da muryarsa naji, inda yake cewa
Dear my choice.Jikina ya dauki bari, naje na bude
kofar tare da yi masa sannu da zuwa.Na amshi
ledojin hannunsa, kallo yake tayi tunda ya shigo
har ya maida kofar ya rufe, na ajiye ledar na
zauna kan kujerar dake kusa da gadon.Kai tsaye
yazo ya zauna kan hannun kujerar.Dear my
choice kinjini shiru ko?Yayi maganar cikin wata
laulausar murya
Na kalli a gogo gabana ya ci gaba da faduwa,
nace gashi har magariba ta karato, yanzu iya
tana can aiki yayi mata yawa, tana kuma jira
na.Ya kama hannuna me zakiyi mata da zata
jiraki?Na ce abincin dare mana.Ya hada tafin
hannuna da nashi ya sarke.Sanan ya dan matsa,
in kin tare a gidanki wane zai dinga yi mata aiki?
Cikin raunaniyar murya na ce, zan ke aika mata
duk abin da naci.Idanu na suka kawo ruwa don
tunanin rabuwa da iya.Ya dago fiska menene na
kuka?Na ce, ina tunanin rabuwa da iya ta ne.Ya
kwantoni jikinsa.Yi hakuri kanwata, ai ba wani
nisane tsakanin mu da iya ba, kullum nasan
zatazo ta duba ki, in bata zoba kuma mu
zamuje.Na kalli cikin idanunshi, da gaske zamuje?
Ka min alkawari fa.Ya ce, in sha Allahu.Ya ciro
fari kar din hankici mai kamshi daga aljihunsa ya
soma share min hawaye.Tashi kiyi alwala muyi
sallah sai muci abinci.Gurin da na idar da sallar
ya sameni, ya bajekomai gani da shegen kwadayi,
amma fargaba ya hana ni ci.Duk hankalina tashe
yake, ya lura da haka, sai ya soma lallashi
na.Haba Sadiya my coice, me nene naga duk kin
damu?Nifa mijinkine na sunna.Nace, to ai iya ta
ce kada wani abu ya faru tsakanin mu, har sai
mun tare.Ya ce to zata sani ne, ko ke zaki fada
mata?Na soma kuka, ina kallon fuskarshi.Wlh
yaya zata gane.Zumbur ya mike daga kusa dani
ranshi a bacce, ya soma yin magana cikin daga
murya.Kina fakewa da Iya ne kurum dan kawai ki
cucheni, ba fa haramun zan aikata ba.Kinsan ina
kyalekine ina lallabaki, in nace zan gwada maki
isa ba zaki iya kwatar kankiba ko?Jikina ya soma
bari, yaya don Allah kayi hakuri.....Yi mun
shiru.Ya katsane, sai wahala kike bani kina wani
inyi hakuri, ba zan hakura ba, haka nan ba zan
matsa maki ba, amma ki sani baki ba komawa
gida ko da zamu shekara a nan harsai kin yardar
min a bin da ya halasta min.Na fara kuka wiwi
shi kuma ya fice ya zare makulli ya kulle ni ta
baya.Na fada kan gado ina kuka, wata zuciya ta
ce mun gara fa kiyarda dan sai kin dibi kunyar da
bakiso a hannunki, don dan shi namiji babu
ruwansa.Ku ziyarci blog dinmu domin karanta
Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Dasauri na dauki wayata na soma kiran layin
sa.Tayi ringing kusan sau biyar sanan ya daga,
cikin kuka na ce, yaya dan Allah kazo na
yarda....Da zafin rai ya ce, bana so, ke har kin isa
mzacen da zaki ja raina?Bari kiji wani abu, baki
son ki dade kada iya ta zargeki ko?To ina mai
shaida maki cewa nan zaki kwana, in yaso in kin
koma gida sai inga maizai faru.Ya kashe wayar,
ransa ya baci dani sosai.Daya wayarsa ta soma
ruri da sauri ya cirota don in yaji ringingi din ta
daga office ne, duk da ba ganinsa yake ba sai da
ya nutsu da ya daga ya ji muryar.Cikin sauri
sauri yake magana.ASP kana ina ne?Aliyu ya ce,
ina nan kan titin waff Road.Ya ce, yauwa kana
kusa ma, yi hanzari ka iso nan (headquarter) ka
kwashi yara ku nufiunguwar rimi layin dan marina
gida mai lamba tara, yan fashi sun shiga gidan
sunyi fashi.Sanan sunyi gaba da babban yaron
mai gidan.Ga ni nan zuwa ranka ya dade.Aliyu ya
amsa cikin izza, a duk lokacin da aiki ya taso
Aliyu yakan mance da duk lamarin dake gaban sa
matsawar ba salla ba ce.Sun isa gidan da yan
fashin suka shiga, Aliyu tare da inspector Adamu
da sajan Musa, sai kofur Bala.Cikin natsuwa Aliyu
ke kallon ko ina, kafin ya soma magana.Hajiya
sannunku da juyayi.Ta ce, yauwa.Cikin kuka da
rawar murya ta amsa, ya ce ina mai gidanki?Ta
ce, baya nan, kuma dama sunce shi sukazo
nema.Ya kalli kofur wanda tuni ya soma rubuta
komai, ya sake maida kanshi ga Hajiyar.Ta ina
suka shigo?Ta ja majina, sanan ta ce ta kofa.Ta ci
gaba, sun ga Yusuf ya shigo a cikin motar baban
su to sunyi tsammanin shine tunda gilashin mai
duhu ne.Don haka sai suka biyo shi.Aliyu ya ce,
shi Yusuf din daga ina yake?Ta ce, daga masalaci
ya ke, babansu yayi masa waya, cewa yaje ya
dauko motarsa.Don ni ya soma kira wai in kira
masa Yusuf ya dauki motar, sai na ce ya kira
layin sa ya fita masallaci.Kuma ba lallai bane
daga can ya dawo gida ba, Aliyu ya gyada kai
alamun gamsuwa sanan ya ce, motar ta samu
matsala ne?Ta ce, a a.Sau biyu ana biyo shi ana
kai masa hari a motar da dare shi ne dalilin da
yasa sam bayason karfe tara tayi masa a motar
na dare.Yau ma mitin ne zasuyi da ya taso musu
da gaggawa kuma bai san lokacin da zasu tashi
ba.Aliyu yayi taku zuwa tagar ya daga labulen
windon yana kallon harabar gidan haskenta
kamar duhun magariba baiyi ba.Ya waiwayo ya
dubeta wace mota ce daga cikin wayan nan
motocin guda uku?Ta karaso ta daga dayan
labulen windon wanacan (hondar ce) baka CRV.Ya
saki labulen yanzu mai gidan ya sani?Ta ce, a a
yana kashe duk wayoyin shi ne in zasuyi
mitin.Ina ne gurin aikin nashi?Aliyu ya bukata
cikin rawar murya ta ce, shine manaja a first
bank.
Aliyu yayi shiru kamar mai wani nazari, can ya ce
zaki iya fada mun kamannin yan fashin?Ta ce,
eh, zan iya.Babban su baki ne dogo kuma kamar
yanada yare, don hausarshi bata goge ba.Sai dai
kila muslmi ne, sauran kuma biyu fararene ina
zaton fulanine, biyun dake waje ne ban tantance
su ba.Aliyu ya jefeta da wata tambayar, yaya kika
yi tsammanin musulmine? Ku ziyarci blog dinmu
domin karanta Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ta ce, haka kawai naga kamar musulmine.Aliyu
yayi guntun murmushi.Bari mu barki haka, yanxu
bari muje mu dora bincike.Ta sake fashewa da
kuka.Ran ka ya dade ka taimake ni yanzu yaya
za'ayi mijina ya samu labari dan kada ya fito
sukama shi?Aliyu ya ce, kada ki damu, zamu
bashi kulawa da tsaro, sanan ki saurara sosai
nasan zasu kiraki ina zaton garkuwa zasuyi
dashi.Kiyi mana saving din number, in kuma ba
number ki kiramu ki sanar da mu.Ta ce, to
yallabai na gode.Ya ce ba komai kiyi adu'a.Suna
fita ya kira AC ya koro masa komai, AC ya ce, to
yanxu ku fara ji da maigidan nata, sanan kunsan
yanda zakuyi ko?Aliyu ya ce, yes Sir!Sai dai ina
kake ganin za a bashi mafaka tunda ba dama mu
barshi ya koma gidansa?AC ya ce kuxo nan dashi
daga nan sai a kaishi inda ya dace.Aliyu ya kara
cewa yes sir.Ya dubi yaran kumaje first bank.Sha
biyu da minti ashirin, Alhaji auwal ya fitoa rikice
daga cikin banki, gama mitin dinsu ke da wuya
police commissioner ya kira shi bayan ya kunna
wayarshi.Ya fada mashi cewa ga yarana nan zasu
taho dashi dan kare lafiyarsa.Alhaji auwal ya ce
saboda me ranka ya dade?Commissioner ya ce,
masu bibiyara ne suka shiga gidanka, amma ka
kwantar da hankalinka za a kama su.Suna tafe
cikin mota Alhji sai adu'a yake yi yana tunanin
me ya tarewa wadan nan bayin Allah?Kofur ya
ce, Alh kaji cewa sun tafi da yaronka?Aliyu yayi
mashi tsawa da cewa kofur?Da sauri kofur yace
yes sorry sir.Alhaji Auwal ya ce ranka ya dade
wane dan nawa dauka Yusuf? Aliyu ya ce kada ka
damu, in mun isa can zakaji komai a bakin
yallabai, kuma duk abubuwan zasuxo da sauki.
Alh. Auwal ya ci gaba da adu'a.
Ofishin commissioner yayi tsit tamkar babu
mutane sai karan (ac) da na fanka.CP ya kalli
Aliyu dake kame, ya ce nasan kana da kwazo
Alhamdulillahi,yanzu sashin binciken mu na
takama da kai.Domin aikinka kanayinsa da
karsashi gami da izza.Ya kalli Alh. Auwal kada ka
damu Alh, babu abin da zai samu yaronka.Zamu
baka kula shi kuma zamuyi dauki badadi da
su.Alh, ya ce, kana ganin ba zasu kashe shi ba?
CP ya ce, ai kudi zasu nema munsan irinsu, sai
dai yanda tayi kwatancen shi ina zaton bako ne
kila kuma ya jima yana yi bamu taba arba dasu
ba ne.Amma wanan karon in sha Allah za mu
hadu.Ya kali Aliyu ASP aje ayi shiri yanda ya
kamata.Ina bukatar barayin nan tako wane hali
sai dai banda kisa zan saurari wayarka a ko wane
lokaci kwa iya tafiya
Sai da Aliyu ya tunkari gida sanan ya tuno da
wata Sadiya, amma duk da haka bai wani damu
ba dan yasan zata sami kulawa yan da ya
kamata.Ya sake ciro waya ya kira, jim kadan aka
daga, ya ce Ibrahim dan Allah ajiyata na nan?Aiki
ya rike ni da safe zan turo aboki na ya tafi da
ita.Ibrahim ya ce ba ko mai yalla bai.Sun saba da
Ibrahim ne sakamakon wata matsala da ta taba
tasowa a Hotel din su Aliyu suka bincika case
din.Ibrahim shine me kula da dakunan kwana na
cikin Hotel din.Motar yansanda tayi faking a kofar
gidansu Aliyu ya shiga gidan da hanzari.Sai da ya
gama shirinsa sosai sanan ya nufi dakin iya.Tana
kokarin fitowa suka ci karo, yace iya na kama
hanya zantafi wajenta aiki ya taso.Usman zai tafi
ya daukota ko da gobe ne.Kar ki damu canma
gida ne gidan Oga ne.Haushi ya hanata magana,
Aliyu ya dafa kafarta, ki min adu'a iya da yan
fashi zamuyi arta bu, kin san aikin mu bakin rai
muke yin shi.Ta ce Allah ya baku sa'a.Gudu gudu
ya fito.Da kallo ta bishi har ga Allah bana son
aikin dan sanda amma bata so ta bata rai a kan
haka, dan kada ta tauye shi.Ta tabbata adu'ar ta
ita ce daukakarshi, fushinta zai iya tauye shi a fili
ta furta, Allah ka yi wa yaran nan Albarka
dukansu, ka dorasu a kan hanya ma daidaiciya
amin.Nikam a a lokacin ina can tsoro, fargaba da
bakin ciki sun isheni.Kai har da nadama.Naji
haushin kaina da naki bin umurnin mijina, gashi
yanzu ya tafi yana fushi dani.Nasan mala'iku ma
ba zasu raga min ba, kuma iyar da nake cewa
zata yi mun fada in taga na dade, to sai dai ta
kashe ni.Dan ina ganin tabbas nan zan kwana.Da
na bi umurninsa kila da yanxu mun tafi gida cikin
jin dadi.Kila ma yayi ta shi min albarka, mala'ku
suna amsawa.Naja tsaki tare da cewa, kash!
Nima ban yi ba wlh.Haka nayi kwanan zaune,
danma na rage daren da yin nafilfili, sai da nayi
sallar asubahi sanan na kwanta.Bacci ya tafi dani,
ban farka ba sai kusan sha daya.Kwankwasa kofa
ne ya tasheni, nazo na ce wanene?Ya ce, Ibrahim
ne.Na ce, ai ya rufe dakin ya tafi da makullin.Ya
ce, ba ko mai ga wani makullin, me kike bukata?
Nace ba ko mai, akwai abinci a nan dakin dayazo
dashi jiya.Ibrahim ya ce, to shi kenan.Ina jin
takun tafiyar sa, na zauna a gurin dantsabar
takaici, bani da ma ranar tafiya gida ke nan.Shi
kam dai dai wanan lokacin yana gidan Alhaji
Auwal cikin falonsu inda yake sauraron bayani
daga bakin Hajiya.Yanda sukayi da yan fashin da
suka kirata.Ta ce, kamar yanda kayi zaton zasu
kira sunkira ni yau ya da safe.Aliyu ya ce, karfe
nawa?Ta ce takwas da rabi dai dai suka ce kudi
suke so naira miliyan uku da rabi.Sun ce in har
ba a sami kudin ba zuwa jibi zasu kashe shi,
kuma sun ce basa son jami'an tsaro su shigo ciki,
kuma basa so a nemi ragi.Me kika ce musu?Ta
ce, ni kuma duk abin da suka ce da to nake ta
amsa musu. Ya gyara zama ya ce, ina suka ce a
kai musu kudin?Wai filin golf.Ina number da suka
kiraki?Ta dauko wayar ta fito da namber ga ta
nan.
Ya amsa ya dauki number sanan ya fita harabar
gidan yana sanar da CP halin da ake ciki.CP ya
ce, ka tafi da layin kamfanin su, wane layi ne?
Aliyu ya ce (MTN) ne.CP ya ce, maza ka tafi dashi
ka tambatar kayi abin da ya dace da wuri, dan
kila cire layin zasuyi ko kuma anjima su kira da
wani layin da ban.Aliyu ya ce, an gama sir.Sai da
yaje office din Usman sanan ya tuna

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login