Showing 6001 words to 9000 words out of 22554 words
Chapter 3 - Darajar Yayana Book 2 Complete by Halima Abdullahi K Mashi .txt
a
jikinsa, inji wa yace bani sonki?A zaman da
mukayi baki fahimci matsanancin son da nake
maki ba?Na ce, to me yasa zaka tafi ka barni?Ya
ce, ina canne amma na rantse maki zuciyata tana
tare dake.Yanxu ni dake bamu san haihuwa ba,
gashi yanayin aikina ba na za,ma bane bugu da
kari ba mu san kowa ba in haihuwa ta zo maki
bana kusa yaya ke nan?Nayi shiru a raina na
tabbata haka ne, amma damuwa ta daya, yaya
na nasan ba zaka jure zama ba mace ba, don
nasan yanayin ka.Ina tsoron matan zamani.Ya ce,
au, dama dan wanan ne?Nayi maki alkawarin ba
zan kalli wata ya mace da sunan so ko wani abu
ba, baki tunabaya ba?Na tsare kaina kuma Allah
ya tsareni, ba wanan a raina, nace to ya ya
zakayi?Ya ce, azumi mana, ko can shi na tayi ta
irin na annabi dauda.Inyi yau gobe in huta, kada
ki damu ki kyautata min zato, bani da sha'awar
aikata kazamin laifi irin su zina da
makamantansu. Na kalleshi na yarda da kai
mijina, kuma ni da kai mutuwa ce zata raba
mu.Zan jira dawowarka, amma za ka dinga
yawan kirana?Yace, kema na yarda ki kirani duk
lokacin dakike so, nace to amma dai mu kwana
abinmu a nan da safe in katafi sai na tafi nima.Ya
ce, sammako zanyi, na ce, eh, duk da haka, ya
ce shi kenan, sai muje da daddare mu kai
kayanki ko?Na ce, eh.
Hakika yaya na sweet Ali ya tafi ya barni da
tsananin kewarsa. Kafin ya kai munyi waya yafi
sau goma.Haka nan na hakura na saba da kwana
ni daya, daran wata lahadi na farka da wani
matsanancin ciwon ciki da baya.Kafin in tashi iya
yaya na soma kira, ya daga a rude na ce yaya
zan mutu ka yafe mun, nayarda wayar saboda
ciwon mara da ya murdo min.Kalamaina suka
farkar da iya, tazo tana cewa haihuwar ce Sadiya?
Yaya ya kashe ya sake kira a rude, iya ta daga ya
ce Iya don Allah............Kuyimin hakuri indakata
anan zuwa lokaci nagaba sai mudira daga inda
muka tsaya,fatan zanga comment dinku
rututu,kafin nan nake cewa zaku iya ziyartar blog
dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100
Darajar Yayana2-02
Posted by ANaM Dorayi on 09:51 PM, 02-Apr-16
Under: DARAJAR 'YA'YANA
_________________NA
___________HALIMA K/MASHI
Irin tarbar da kikayimin ta mutunci shi yasana
boye kalatata,boye kishinki zaifi alheri, sama da
bayyanashi don yanda na yi mani bakikaini son
mijinki ba, haka na yi imani na fi ki kishin sa,in
kina musu lokaci zai tabbatar miki dahaka. Kije
kiyi aikinki sannan ki kunna min T.V Na harareta
tare da jan tsaki na nufi dakin yaran. Sun gama
cire kayan, Kausar tana linkewa, Al'ameen ya
ce,'Mama wace ce wannan??? ..... Na ce 'Bakuwa
ce, Na kunna musu T.V dinsu, na ce kar su fito
sai an kira sallah. Nima na shige dakina na fada
kan gado. Maganganun yarinyar sun ratsa ni, har
na rasa tunanin dayakamata inyi. Ina buqatar
shawara, domin na lura da 'yar iskar matar nan
batazo dawasa ba. Wa zan kira don neman
shawara? Aisha ko Abida? Aisha ba ta san d
wannan zancen ba, bari kawai in kira Anty Abida
tunda ta san da matsalar. Ringing na uku ta
dauka na ce, 'Anty Abida ya gida da yara. 'Ta ce,
Lafiya lau. Na kwashe komai na fada mata, ta
cika da mamaki, sannan ta ce, 'Shawarar da zan
ba kikar ki bari ta gane lagon ki kar ki nuna
fushinki, kuma kar ki kulata kuyi tashin hankali,
ballantana ta yi furucin da yaranki za su gane,ki
jira zuwan shi muji hukuncin da zai yanke. Na ce,
'To shi kenan Allah yayi mana jagora.'Ameen, Ta
ce. Na kashe wayar ina nazarin maganganunta.
Ita ko 'Yar Gwari, Mujidat tuni ta ciro wayarta ta
soma chatting da abokanta. Murfat ke
tambayarta wai yanzuntana ina? Mujidat ta ce
tana Kaduna. Murfat tace, 'Ashe muna kusa ni
ina Abuja jiya muka zo tare d Alhaji Karimu zai yi
meetina na kwana biyu.. Mujidt tace lallai kina
cikin kudi, murfat tace sosai ma, abokinshi Alh
muslimu ya tambayeki .Mujidat tace yakiranima
bandaga wayar ba, kinsan ina ina yanxu? Murfat
tace ba kin ce kaduna b? Mujidat tace ina gidan
officer Aliyu,Murfat tace kina hauka ne? Zaki je
gidansa? sai matar sa ta kasheki a banxa?
Mujidat tace ai matar tashi wawiya ce, har ruwa
ta bani nasha, bayan na gaya mata cewa mijinta
ciki ya min, tace ina baki shawara ki cire cikin
nan kixo gurin masu sanki, officer ba sanki yake
ba. Mujidat tace , ni inasonshi, zan tsaya nai fada
a kanshi, saboda ko nadawo zanta tunanin shine,
bazaki fahimta bane saboda bakitaba shiga
tarkon So ba, ni kuma na shiga tarkon So mai
tsanani.Murfat tace to yaya akayi kika gane
gidan?ina kwance Hotel ba lafiya , sai ga wayar
direban shi wai Ogafa an canxa shi zuwa Abuja,
yanxun haka ya tafi in gaya miki duk sai na rude,
take na miqe ina roqon Adewale ya taimakeni ,
yace sai nabashi kudi, bani da kudi sai dana roki
samarina , suma shegu ban samuba sai dana
musu alqawarin basu kaina, ina bashi kudin yace
naje kaduna zai turo wani dan sanda daga can
Headqurter su, yayi Tanbaya kan Aliyu Tukur aka
fada masa sunan unguwar su, sannan na nufo
Kaduna, nasha wahala kafin na iso, sabida motar
dana shiga me arhace, inazuwanan na samu wani
dan sanda da Adewale ya hadamu , shima akwai
kudin da akayi alqawarin xan bashi, sai daya dafe
shi,sannan yayi min jagora zuwa unguwar su
Aliyu, nan ya bar ni wai in nemi gidan, wai in
mun shig unguwar tare, asirinsa zai tonu, na
Adewale ma haka,nadade ina yawo, sannan na
samu gidan mamanshi, na shiga bata nan, sai
nace a kai ni gidan matarshi, Murfat tace ke yar
neman bala'i ce, bari tasa miki guba a abinci kici
ki mutu, mujidat tace shi yasa bazan taba cin
abincita ba,Murfat tace kidai yi ahankali, garinsu
kikazo, tace a garinnasu sai in karbe mijin kuma
na zauna lafiya.haka suka yita chat har xwa wani
lokaci, Niko munyi sallar magariba har na zubawa
yara abinci, 9 da yan mintina yya Aliyu ya iso
gida,da ita ya soma cin karo a falo, ckin zafin rai
yace me zakiyi agidana?itam cikin daga murya
tace goyon cikin dakayi min, abinda naji kenan,
na miqe ina kallon yarana,Kausar ce kawai idanta
biyu tana yin homework dinta, na miqe na fito da
sauri, dai-dai lokacin yana cewa, zan nuna miki
kurenki na biyoni gidana yar iska
karuwa.nakamashi ina fadin yaya yara fa? itama
tace yan iska dai, namijin karuwa. na dafa kaina
dan takaici, yar bariki tana zagin mijina da nake
girmamawa a gabana, najashi zuwa dakinsa,
nace, haba yaya, kamanta cewa kana da yara a
gidan nan?dubi yanda yar bariki tazo har cikin
gidanka tana zaginka?sabida mutuncinka daka sai
da,ai dama haka ne, dukwanda yabar maganar
ubangijinsa dole ya fadawa dana sani, da wace
rana zaka iya hada yau a gurinka dan bakin ciki?
ni dai a gurina babu, ya dago kai ya dubeni,
Sadiya nayi nadama sosai wallahi, ba sai ta
kanjamau kadai Allah yake kama mazinaciba, in
Iya taji batunnan na shiga uku, nasan bazan kara
yin daraja ba, kila ma ta cireni daga yayanta, ga
wannan matsiyaciyar da alamu fallasa tazi
min,nace to yanzu dai nema mata masaukin da
zata kwana, in yaso da safe sai mu zauna da ita
mu kafa mata sharuda,ya kama hannuna,
wadanne irin sharuda za'a kafa mata?kara min
haske, sai musa mata sharudan cewa ka yarda
zaka amshi dan,amma za'a rufa asirin cewa ba'a
son kowa ya ji, dan haka za'a ce mijinta ne ya
rasu, iyaynta suka koreta saboda ta
musulunta,na tabbata duk wanda yaji haka zai
tausaya,to inta haihu sai ta bamu yaron ta tafi
abinta,yace wazai rike yaron?nace ni mana, Yya
ko ban aure ka ba ai xan rike maka da, bare
kuma ina matarka na kasa rike jininka? yadan yi
shiru yana nazarin batuna , can yayi dariyar yake
yace,Sadiya baki tunanin me mutane zasu ce?in
sun gammu da jariri?me zamu fadawa yaran mu?
idan sun tambayemu nan gaba? nace ai zamu
fada musu dan mu ne, amma bani na haifeshi
ba, tunda dama a musulunci bai da
gadonka,kaga ba zamu sami matsala ba, ya sake
yin shiru, can yace ina ganin fadin gaskiya kawai
shine mafita, saboda duk rintsi karya bata kaiwa
ko ina baki tunanin cewa nan gaba zata zo nemn
danta?kuma asiri zai tonu? nace Allah zai rufa
asiri, kai dai da safe mu sameta da batun muji
yanda za'ayi.yace shikenan, Allah ya rufa asiri,to
yanzu ina zata kwan?ka kaita dakinka,yace a'a,
sai dai yara su dawo dakinki, ta kwanta acan ,
amma bazata kwanar min a daki ba, araina nace
yanxun ba, amma da ai tare kuke kwana ma.
yace kota kwana a falo? a'a ,bari in kaita dakin
yaran.haka kuwa akayi,muka kaita can.Da safe
dana kai mata abin kari sai tace a'a, tanada
maltina da kuma biredinta, bata cin abincin
kowane guri, da kanta takeyi, nace good, sannan
na fita.mudai sama-sama mukayi bacci, kuma
sama-sama muka karya, duk sai tunani muke,
yaya kuwa sai nadama yake, dan dadin da yabi
na watanni yaja masa zubewar mutunci na kila
tsawon shekaru.misalin sha dayan rana yace in
kirata ,muka zauna yara suna makaranta lokacin,
ta fito sanye da riga da siket na jeans, kanta
babu dankwali, cikinta kuwa har ya turo, ta
zauna tana taunar cingam, yaya yace Mujidat
dama mun kira kine don mu tattauna dake,
shawara ta farko zanbaki dubu dari biyu ki zubar
da cikin nan,ta daga masa hannu, ban amince ba
,koda zaka bani duniya da kayan cikinta, inbaka
mantaba nafada maka, badan kudi nake tare da
kai ba, sonka da kauna ce kawai, kuma cikinnan,
(tasa hannunta ta shafa cikin)ribar soyayya ce,
taya zan zubar dashi?kawo wata shawarar dai
muji,kalamanta sun konan raina tamkar in tashi a
gurin,amma sai na shanye.yace to naji, zaki
zauna damu ki haihu, amma da sharadin baxaki
fadawa kowa komai ba,duk abin dana fadawa
mutane zaki tsaya akan haka ne?ta dan yi tsai
tana tunani can tace ,zan yarda, amma idan na
haihu meye makomata? zan tafi da danne?ko
kuwa zan barshi anan?sai lokacin nasa baki , zaki
tafi ne kibar yaron a wurina, sai ki tafi
abinki,wata ran,xaki iya xuwaki ganshi duk bayn
wani lokaci, tayi min wani kallo, tare da yin kwai
da cingam dinta kato, sannan ta fasa shi taci
gaba da tauna duk muna kallonta, tayi yar
dariya, in naki fa? cikin zafin rai Aliyu yace , sai ki
tafi da cikinki, danma kin samu zan amsa? nasan
uban dayayi miki? tace , ka manta dararen daka
yi ta kwana dani?cikin bacin rai yace in baki yarda
ba malam kizo ki fice min daga gida kije kiyi duk
abunda zaki yi. tace zan fi son haka , dan zama
gidan mamanka ze fimin wal-wala, dan haka zan
je na fada mata ina dauke da jikanta, ta bani
masauki, ni dashi muka kalli juna, yace kije man ,
zanfi san haka.nace , a'a ,kedai barshi a wancan
tsarin,tace in dai har za'a barshi cikin sirri,
tonima zan kawo nawa sharadin?Aliyu kam takaici
ne ya hana shi daga kai, ban taba ganin shi cikin
wannan yanayinba, na takaicida bakin ciki.nace
fadi sharadinki muji?tace sharadina sai dai in na
haihu zai AURE NI.... kalamanta na karshe suka
tafi da numfashina, tsawon kiftawar ido, huhu,
nayi nasarar janyo nimfashi na,idanuwana suka
futo sukayi jajir, zufa ta ketomin, ta tuntsureda
dariya har Aliyu ya dubeta, nima lokacin na
dubeta, tace ,ya kika yi saurin firgita?naga keda
mijin naki kamar tagwaye, shawarar ku daya, kun
burge ni, kuma nasan yana sonki, kuma nima ina
san shi dan nasan qualities dinshi, na baku zuwa
gobe kuyi shawara.
(Uhm!Allah yakayuta,ANaM Dorayi)
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Aliyu ya harareta, Allah ya kiyaye ni Aliyu na
aureki,ai ko zan yiwa matata kishiya na nemo
mata yar mutunci bake ba karuwar titi,tir Allah
ya tsareni, ya miqe, na baki awa daya kibar
gidana, ko kuma yan sanda su zo su fita dake, da
kyar na miqe kafafuna sunyi sanyi, dakina na
nufa don ko ganin gabana banayi,zuciyata tamkar
ta faso ta fto,rigijif na fadakan gado, inasan yin
kuka amma na kasa, lallai kuka ma rahama ne,
tunda idan kayi shi zaka samu sauki,
Hannuwanshi naji a gadon bayana, ji nake tamkar
ya doramin wuta,zuwa,yanxu nasoma tsanar
yaya Aliyu,gaskiya hakurina yana son ya kare,
danzan iya danne komi, amma banda batun
kishiya ,zan iya hakura ya aureta, amma kuma
zan juri zama da ita?(Mata kenan,da kishiyar
gida!..Allah ka karemu daga bin soye-soyen
zukatanmu.....Ameen.ANaM Dorayi) Birkitonin da
yayi shine ya katse min tunanina yace, haba My
choice, kada wannan ya dameki, zanyi waya
yanxun xa'a turo min yara su tafi da ita, xuwa
ynxun ban damu duk duniya tasan cewa na mata
ciki ba, ai nima dan Adam ne kamar kowa, ban
wuce kuskure ba, nace aika riga ka tafka
kuskure,dole ne ka aureta, kuka ya subucemun,
naci gaba da magana cikin kuka wane hali Iya
xata shiga in taji wannan labarin?ita da ba
cikakkiyar lafiya ba, me zaka cewa y'ay'anka ?
wadanda tun jiya suka damu dasan sanin wacece
wannan bakuwar? y'an 'uwanka, wane idan kake
dashi da zaka kallesu?su da sukeyimaka kallon
mutunci da kima? ga abokai da sauran mutan
gari?kada ka manta, shi fa mutunci madara ne,
in ya zube sai dai a kwashi kasa,ka riga kayi
abinnan da hausaw ke cewa TSALLE DAYA ME
JEFA MUTUM RIJIYA....ya rike kanshi, sadiya na
yarda duk wanda ya bar layin da aka ja masa a
matsayinsa na musulmi dole yayi nadama mara
amfani,danasan abubuwa zasu zama haka da
banbi san zuciyata ba ,dam malamai suna gaya
mana zuciya wata tsoka ce ajikin dan adam me
hadari in kabi sonta sai ka halaka, ya dube ni,
yanxu kin yarda? kinaga ba wata mafita sai ta
auren ta? nace to inban yadda ba ya xanyi ,nasa
masa kuka ina fadin na amince ka aureta,
,kallona ya dinga yi tamkar na zame masa wata
sabuwa a sanyaye yace"nasan kin hakura ne
saboda ni, amma nasan bakya san kishiya,amma
kina ganin cewa nan gaba bazaki damu ba?na
runtse ido, zuciyata tana wata irin tafasa nace,
batun zan damu ko bazan damu ba a ynzun ba
shine mafita ba,na bude jajayen idanuwana ina
kallonshi, sai dai ina fatan daga baya ba zka
canzamin ba? ya rungume ni, Sadiya kada kiyi
tinanin haka kada kiyi fatan haka, ki tayani
addu'a Allah ya bani ikon yi miki irin halaccin
dakikayi mini,banda kamar ki har abada,kuma ke
kadai nake so ke daya kwal. Haka ya yi ta fada
mini maganganu masu dadi da kwantar da rai,
har zuciyata ta dan sauka. Yaya ya fito ya fita,ni
kuma na kira Anty Abida na fada mata, ta ce
hakan ya yi in ta haihu ya aure tan zai fi sauki a
bakacin ta haihu ta ba ku yaron. Na ce, To ya zan
yi tunda shi ya janyo. Nan dai muka yi sallama
nafito na kuma dora abinci,sai dai ina gamawa
ita ma ta soma dora nata,ban damu ba tunda
neman sulhu muke. Misalin hudu yara suna
Islamiyya suka shigo shi da Usman falo suka
zauna, na kawo ruwa da abinci.Usman ne ya sha
ruwan shi kam gogana har wata 'yar rama ya yi,
ya kalle ni ya ce, Kira yarinyar nan. Na ce to. Na
daga labulen dakin yara tare da yin sallama, ba
ta amsa ba sai dai ta dago ta dube ni,rufdaciki ta
kwanta kan katifar su Kausar tana chatting, na
ce, Ki zo in ji Mijina. Ta yi min kallon kishi zan ce
ko na tsana, sannan ta ja tsaki. Ni dai na juya na
ce musu tana zuwa. Zan tafi Yaya ya ce in zauna,
na samu guri na zauna. tafi minti shida sannan
ta fito,munyi jugum-jugum kamar masu zaman
makoki, ta tsaya kerere , gani. Ya harareta
.Kizauna mana kin ce wani gaki? Ta zauna tare da
fadin .yau kuma da wacce aka zo? Duk muka yi
shiru, irin zaman nan da ake cewa mutuwa ta
ratsa. Can Aliyu ya ce"Usman wannan ita ce
Mujidat,kuma na maka bayanin komai,dan haka
sai ka dan ce wani abu".Usman yace"bani da ta
cewa,sai dai ke.ya nuna Mujidat,karkisake kice
zakici zarafin wannan baiwar Allah ko nan gaba
"yakalli Aliyu"ya kamata wannan ya xama cikin
sharudan da zaka gindaya" Aliyu ya kalli
Mujidat"na yarda in kin haihu zan aureki, amma
ki sani so daya tak inayiwa matata ne,dole ki
bata girma da daraja,musamman data soma
bazaman aure ba, sannan zaman haihuwarki ina
gani can wani waje zan nemamiki haya" cikin
sauri na ce ban yar da ba, ai ta zauna anan,
kada a dinga zagayawa "Usman yace "haka ne
kuma,amma kina ga batakura? Na ce "bakomai"
Mujidat dadi ya rufeta ,kuma nan take ta nuna
murnarta, ta kuma sake bayyana tsantsar san
data ce tanawa mijina,dan haka dole tazauna
dani, ban bari ta kai karsheba natashi nayi kicin
abina.tsayawa nayi tsakiyar kicin shuru,anya
kuwa ban yi wautaba?ban zalunci kaina ba?ban
debo rvmuwan dafa kaina ba?amma sai wata
zuciyar tace kedai kada kiyi wannan tnanin, tunda
kin sadaukar da kimai ne dan asirin mjinki y
rufu,Allah ya sani Zuciyarki daya da ita,kuma
Allah zai shige miki gaba. Nasauke ajiyar xuciya
nace Allah gani gareka,sai da suka fito ne naji
muryar Usman na cewa"Madam na tafi"nace "ka
gaida min su Ummulkhairh dasu walida"yace
xasu ji.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
A ranar Aliyu ya koma Abuja,sabida an dameshi
da kira,gida ya koma sai ni da ita saikuma
yarana,a daren nan naje na fadawa Iya yanda
muka tsara zancen,tayi ta tausaya mata,tare da
shiwa yaya albarka tace ai gara daya taho da
ita,tace in an barta sai ta koma ruwa, tabar
musulinci, nace "ai shine" Iya tace Allah sarki,
naxo in yi mata ta'axiyya,banda abinku, daba
nan kuka kawota ba? Tunda ni kadai ce?nace"Iya
ki barta can kawai,sabida bata jin Hausa sosai"
tace"to shkenan ,kema Allah ya biya ki" na ce
amin.
Daren ranar mun kusa rabashi a waya yaya yana
shimin albarka tare da yi min alkawuruka kala-
kala na riqe ni amana,tare da kyautatamin daji
dani duk wani dadin zaman aure,har sai da aka
kira shi, yace minxai fta gurin aiki1 nce Allah ya
tsare.
Haka muka zauna da Mujidat,bata min
magana,sai dai ni in mata.innayi kamar in
shareta,sai na tuna da haramcin gaba,dan haka
in lokacin sallah yayi tana falo sai in ce
mata"lokacin sallah yayi" wataran
tace"to"wataran tayi min banxa ,sai dai ko ta
amsa ba dole ne ta tashi tayi sallar ba.abinci
kuwa,da kanta take yi,takanyiwa yara
magana,amma ba wai wasaba, sai dai in tana
san abu tace kai bani kaza, ko ke bni kaza. Sun
dameni wai yaushe wannan bakuwar zata tafi?
bata da kirki su suna san ta tafi,nce musu bazata
tafib,Antyn su ce baban su ya kawota ,kuma tana
da kirki,dan dai yanxun bata da lfy ne
shiyasa.suka yi shiru badan sun fahimce ni
ba,intaji fita tana san zaga gari sai dai kawai inga
ta fice bako mayafi. Sai dai nayi masa waya nce
ka fada mata in zata fita ta dinga saka hijabi ko
mayafi, saboda an ce ta musulunta, in tana fta
haka asiri zai tonu.ya ko kirata yace ta
kiyayeshi.kar ta bari tayi abinda zai toxartata,tace
ita bata da hijabi.yayi min waya wai in bata
hijabai guda 2, sannan yace ya hanata fta,kuma
ta sani ya zuba masu sa mata ido a unguwar,
dan kar tai xaton cewa xata fita wani gantalinta
ta dawo masa gida,ko kuma zata yo wani mugun
abun.tace karya damu,dama ita burinta aurenshi,
kuma tunda ta samu bata da matsala da wani
namijin can waje, tana zuwa matsa jikine.
Duk wani zaman kunci na dauka a zaman
Mujidat, sai dai ban damu sosai ba.ganin Aliyu
baya sakar mata fuska sosai.komai tace masa
tana so sai yace ta tambaye ni,bai cika zuwa
gidan bama, sai daiyazo ya debemu da yara mu
tafi can Abujan, akwai lokacin da sai da muka yi
sati uku saboda yara sun samu hutu. Ranar da
muka dawo har da shi ,mun samu ta tana kuka
wiwi, wai bata da lafita,nce masa muje Asibiti,
amota fadi yake Allah yasa ckinnan ya fta, na ce
dan Allah kabari, ka mata addu'ar alkhairi, bayan
dogon bincike likita ya