Showing 21001 words to 22554 words out of 22554 words
Chapter 8 - Darajar Yayana Book 2 Complete by Halima Abdullahi K Mashi .txt
kowa, nima ina zaune
nan ne dan kai daya.Aliyu ya ce, ban tabbatar da
hakan ba, tunda dana fita zaki iya fita, ta sake
dawowa ta rungume shi, na rantse bana bin
kowa kai daya nake so da kauna.Kuma bazan
daina sonka ba har na mutu.Aliyu ya zauna kan
kujera tare da rike kai, itakuma ta kwanto a
kafadar shi.Tunani take yi a zuciyarta yanda zata
ban bare ma'auratan.
Ina zaune ina danne dannen wayata, nima ina
son bude shafin nan na fcbk don ganin me
duniya take ciki?Aisha kawata da Anty Abida duk
suna ciki har Aisha tana bani labari wai da akwai
malamai sosai.In shiga nan in shiga nan dayake
ina da karanbani sai gani na bude fcbk, banyi
anfani da sunana ba ko adareshi na.Bayan kwana
biyu sai ga Aisha ta zo mun yawon Arba'n, na
nuna mata ta ce, ai na gani kin turo min sako, na
ce yau she?Ta ce duk wadan da kike da numbar
su za su gani, in kin bude, na zaro ido, har da
Abban kausar?Ta ce sosai ma, amma ba lallai ya
lura ba tunda bakiyi anfani da komai naki ba.Ta
nuna min yanda zan dinga komai, bayan tafiyarta
da dare ina kwance, na shiga fcbk nan na shiga
frnds, dinsa, mace daya na gani Mujidat.Na shiga
profile dinta hotunan da tasa nata yana daga
cikin wadan da sukayi like wani gurin ma har
yana cewa kin yi, sanan ga hotunan shi kala kala
cikin photos din ta wasu ta rubuta one an only,
wasu ta rubuta my Husband.(Tofa)
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Na tashi xaune wai ya aure ta ne? take kaina ya
sara, duk da ina cewa gara ace auranta yayi fiye
da ya neme ta sai na samu kaina cikin wani
tashin hankali mai tsanani.Na soma kiran layin Ya
Usman ba tare da na damu cewa dare ya dan
soma ba,cikin kuka nike cewa ya Usman ina ganin
fa auranta yayi bai fada mana ba. Yace,Habadai
wacece? Na karanto masa komai yace, kiyi hakuri
ki kwanta zan bincika,kada ki kara hawa fcbk
din,kurum ce masa nayi to amma muna yin
sallama dashina tura mata frnd request, cikin
sa'a ta amshe ni, da yake ita ma na ganta online.
Nace ban ga tasa marriage ba amma naga hoton
mijinta, ta ce eh za dai suyi auren ne, nace ni yar
kano ce ita fa? tace Lagos, amma yanzun tana
Illorin a gidan wanda zata aura.Kuka wiwi na
dinga yi yanzun menene abun yi? na tambayi
kaina, ta tambayeni ina da miji? sai nace mata
bama tare, tace ayya, yakamata mu daidaita.Ita
in sunyi aure bazata taba yarda su rabu da
mijinta ba don tanaji ko uwàr da tahaifeshi bata
kaita sonshi ba,ai ina gama krt na sauka daga nrt
na soma rero kuka tare da yin danasanin wannan
bin diddigin.Alwashi na sha duk randa yazo za'a
yi mai yuwuwa. Ba zan zauna ina wulankanta ba
haka kawai a debo ciwon zamani a kawo min
yarana su zama abun tausayi,na sake zama cool
ko yaushe cikin krt alkurani yana wanke min
zuciya, don haka yanzu bana daga wayarsa sai
dai in yaransa na kusa ya kira na mika ma
Kausar nace ta dauka.Ranar Kausar har tambaya
na take Mommy meyesa ba ka daga wayar Baban
ko yana mki fada ne? Nace a'ah munyi maganar
cewa yake in Kundawo zai kira ku ne,a haka
muka kwashe wata, ranar kwatsam sai gashi,
mamaki da naji banda Mama ko Al'amin bai je ya
masa oyoyo ba?nima batare da na Kalle shi ba
nace sannu da zuwa, yace Yauwa ya dubi yaran
yace Al'amin baku ganin bane, nukamun ganka
Abba sannu da zuwa.Yayi cik ba tare da ya amsa
ba ransa ya baci sosai da wannan ko in kula din
iyalanshi suka mishi,don haka ya dauri aniyar
Cima Sadiya zarafi yau dinnan, nasan dole zai yi
wannan tunanin dan haka na hada ma yara kaya
na kwana daya nace suje gidan Iya su kwana
tunda sati ne gobe, suna fita na kulle gidan na
shiga fall na kulle kaina na cire key din na nufi
daki,ya cire kaya sai gajeren wando zai shiga
wanka,nace toh Abba kausar yau fa zamuyita ta
kare a gidan nan ko ni ko kai?ya juya yana min
kallon mamaki sannan yace ke ina zaton kin soma
shan fakalin ko?nace 'eh wai don ma ba Zina
nakeyi amma ka bani kunya, ba tsoron Allah ba
kunyarshi baka tunanin darajar yayana ka aje
karuwa a gidanka Kuna fasikanci,saukar Mari naji
tau,sannan yace in ji wane makaryancin, na rike
kuncina ka mareni Akan wata 'yar iska, toh bazan
iya zama da fasiki ba ka dinga azabtar dani a kan
karuwa na warware gefen zani na ciro yar
takarda na mika mishi, ga aikenta zuwa gareni,
sannan na dauko wayata na same shi yana krt
takarda duk jikinshi yayai sanyi, nayi maza na fito
da pics dinsu da nayi saving, wannan ma karyace
ba hoton ku bane?na soma kuka ka cuce ni ka
cuci yarana haka kake nufin ayi ma Kausar?ya
daka min tsawa kina hauka ne kike ambato sunan
yata cikin wannan maganar?nace ba dadi kake
ma yar wasu?Na sake fashews da sabon kuka ka
bani takarda ta, bazan iyazama da kai ba!kina
haukane zaki ce na sake ki,toh bazan iya ba me
Zancewa Iya?nace in itace matsalar ka bazan fada
mata komai ba in baka sake ni ma zanje yanzu in
fada mata! hanklainshi yatashi ya dauki jallabiya
ya sa nikam ficewa nayi naje dakina na sure hijab
na bude Kofan falon ya rike ni kina hauka ne zaki
je ma Iya da wannan zancen?nace me zai
hana,ya kamoni na kwace nayi waje na bude
kofar gida kafin na bude ya daukoni cak,dakina
ya jefa ni kan Gado yace kina hauka ne?yace nayi
laifi kiyi hkr ki nutsu Muyi magana, nace kai ni fa
na daina Sonka kuma girmanka ya zube a gurina,
ganin zanga-zangar tayi yawa sai ya kulle ni ta
baya ya daga waya ya kira Usman yace don Allah
yana son ganinshi yanzu a gida,ina jinsu a falo
yana fada ma Usman shi bai San ina ji ba wai
duk na daga hankalinta har wai ina kwacewa ni
dole sai naje na fada ma iya.Usman yace aboki
tambaya daya zan maka kayarda kana aikata
laifin nan?yayi shiru ,Usman yace in har ka iya
amsarwa shine zai kawo karshen matsalar, yace
toh ai na fada mata cewa naji na kuma amsa
laifina don haka ta tsaya Muyi magana
taki,Usaman yace a'uzubillah, Aboki me yarude
ka ka fada wannan harka?wlh aboki kurum na
tsinci kaina a wannan halin, ka San zuciyata bata
da Kashi ga kuma sharrin shaidan, Usman yayita
masa nasiha sannan yace a jira ni na fito fuskata
suntum nace Nifa Usman na gaji ba zan zauna
ba,Usman yace yi hakuri nasan kinyi hakuri kuma
inshaAllah bazai kara ba,na kalleshi nasan zai
chigaba kawai ni gara ya aureta in son aure
suke,inkuma matan da yake bi da yawa toh ni
bazan iya zama ba.Usman ya Kalle shi gaskiya ne
Aliyu yace ita kadai ce muke tare wlh kuma itama
tsautsayi ne, Usman yace ko kayi nadama sanin
zaka koma can ku sake haduwa shi yasa ta kawo
shawara cewa taje tayi istibrai in ya so sai Kuyi
aure.Aliyu yace ina bazan auretaba ni nakuma yi
miki alkawarin cewa mun rabu da ita inshaAllah,
a gaban mu yayi waya ya kira maigadinsa yace a
fitar da Mujidat daga gidan kafin ya dawo, itama
ya kirata yace mata ya gode da wasikar da ta sa
mishi a cikin kaya don ta raba shi da matarshi
don haka maza ta bar mishi gidanshi,bai jira
takare kanta ba ya kashe dukkan phones dinsa.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ni Sam bai wani Burgeniba,suna cikin gidansuna
ta bani baki har magrib,suna fitowa nayi wanka
na sha magani nayi sallah ina zaune kan
dadduma har sai da nayi sallar Isha dama banyi
girki ba,na hau gado abuna na chigaba da kuka,
na soma barci naji ana shafa ni a wuya abunda
na jima ina kewa amma sai naji tamkar ana
shafa min kaya.Na ture hannunsa a kunne ya
rada mincewa'My choice zan zame miki sweet Aly
dini har abawa ba zan sake chanzawa ba,natashi
zaune muna kallon juna cikin ido nace yaya Sam
yanzu in ka fadi magana bana yarda matsalar
mutum ya kama karya kenan har a gane shi,na
sauka daga kan Gado naje na jingina da bango
ina kallosnshi shima ni yake kallo nace yaya ni fa
nadarmarka bata shige ni ba don nasan dole sai
Kun sake haduwa da yarinyar aurenta kawai shi
ya fi dacewa da kai,ya nufoni amma ina ce an
gama maganar nan,bazan iya auaran ta ba har
ta Haifa min yara na gari Domin ba uwa ta gari
bace,itace tayi ta bibiyata har sai da komai ya
faru kinga kuwa in na aure ta ta kuma ganin wani
shima xata iya cewa tana sonshi,ya kama
hannuna ki yafe min mukoma kamar da, Abban
Kausar na hkr amma sai Kamin rantsuwa cewa
bazaka kara aikata wannan halin ba?
Cikin sauri yace'na rantse ba zan sake ba nayi
alkawarin, nace toh shi kenan na zame hanuna
naje na kwanta sannan nace yawuce, ya Tako ya
zo ya hau gado ya kawo nizuwa jikinshi na tashi
zaune yaya kayi hakuri bazan sake iya hada
shinfida da kai ba har sai kaje kayi gwajin cutar
kanjamau!!!!! Zumbur ya mike tsaya tare da rike
kanshi Sam baiyi tunanin wani HIV ba tunda yake
tarayyada yarinyar, ya fara sintiri a tsabar
dakin,nace da baka yi tunanin haka ba ko?ya
sauke ajiyar zuciya 'ban yi wannan tunanin ba
wlh Sadiya amma bana zaton tana da shi,tunda
tsawon zamnmu ban taba ganin tayi wani ciwo
ba,nace ba a nan take na, Ance mace tana yin
shekara goma ciwon bai nuna ba,kawai kaje kayi
gwaji in ma tanashan magani a boye wa zai sani?
zufa ta rufeshi sai lumshe ido lallai kamar yana
ganin ta tana shan wasu kwayoyi har ya taba
tamabayar tace na family planning ne,fita yayi da
sauri na tashi na biyo shi ina cewa ina zaka
Abban kausa'r yace'koma asibit zanje yanzu
nan........
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
toh fa sai ku biyo ni cikin Kashi na uku don Jin ya
xata kaya shin Aliyu yana da ciwo?taku Halima K/
Mashi
Zaharaddeen shomar
Whatsapp 08168575100