Showing 12001 words to 15000 words out of 22554 words

Chapter 5 - Darajar Yayana Book 2 Complete by Halima Abdullahi K Mashi .txt

kyau ayiwa mutum
mummunan zato, kin San wannan ba halin Yaya
bane". Ta ce 'eh, to haka ne, amman fa mutum
yakan canja daga halinshi da aka San shi dashi."
na ce, a'a fa iya ita fa wannan da mijinta, kafin
ya mutu mun sha gaisawa da shi. Kuma shi
kamanni hakayake sai kiga baku hada komai ba
amman Kuna kama." ba don Iya ta gamsu ba
tace to Allah yasa hakanne. Na ce ameen. Nan
mukayi alwala muka kama nafila, addua ta Allah
ya rufawa mijina asiri Kar duniya ta gane wannan
matsalar.
Da safe lokacin da na shiga dakin tana zaune da
danta a hannunta ta tsura masa ido tamkar ba
ita bace tayi ta kurma ihu ba. Na ce 'kin tashi?"
ta ce, 'eh mun tashi, kin ga yarona sai kace
Babanshi, naji dadin haka,Dan bazai sake min
musu cewa ba cikinsa bane." da sauri na ce,
'kibar maganar nan mana, yanzu bari kuyi wanka
in na kai yara makaranta sai nazo na kai ku
Asibiti." ta yatsine baki "kin sanar da mjnki?"
nace, a'a kin San Iya tana nan ba dama in masa
zancen ki.' ta dauko wayarta tana cewa, "ina
ruwana da Mamansa taji. Layinsama a kashe
yake.' tayi tsaki ta jefar da Wayar, Ni dai na fice
na kama aiki na raina bace, ban cika ganin
laifinta ba Dan shine musabbabin komai.
Da zamu Asibiti na sauke Iya a gida na wuce
dasu. An duba su ance duk suna lfy, muka tsaya
kasuwa na siya abubuwan da basu da shi,sannan
muka nufo gida.
Tsakiyar gado na zauna sannan na soma Kiran
layin mijina, bugu biyu ya daga, nayi Sallama ya
amsa tare da cewa. "Yaya na jiki cool da yawa?"
Na ce, 'Yaya budurwarka ta haihu." budurwata
kuma? Ya fada cikin sauri. Na ce, eh Mujidat
danta yana nan namiji......zandakata a anan zuwa
wani lokacin kuma,fatan zaku kara hakuri dani
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347






Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100






Darajar Yayana2-03
Posted by ANaM Dorayi on 04:31 PM, 23-Mar-16
Under: DARAJAR 'YA'YANA
_________________NA
___________HALIMA K/MASHI
Ta soma kwalla a kwai su, amma sun zo sun
kasa kamo barawon.Ya ce, to daga sun zo ne
zasu kamo barawo kamar suna da Allahn
musuru?Ina ganin ki hakura kawai in ba a kwai
wanda kike zargi ba.Ta ce, cikin jaka ta yake a
dakin na, ni na tafigidan kawata, mama ta tana
shigowa sai kanena sun ce kuma basu ga wanda
ya shigo cikin dakin ba.Aliyu ya tabe baki.Shirme
kenan, sai ki hakura kawai.Ta mike tana share
hawaye, shi ke nan nagode.Sanan ta tafi.,har ya
gama shirin sa tsaf zai tafi sai ga wayar
commissioner yana neman sa yana isa aka dan
ka wani aiki a hannunsa.Dole ya fasa tafiya ba
don ranshi ya so ba.Washe gari ranar goma dai
dai dawowar shi ke nan daga wurin motsa jikin
da yaso xuwajiya hakan bata samu ba sai yau.
Waya ta buga daga bakin gate ne, mai gadi ya
ce, yallabai bukur jiya ce ta dawo.Cikin damuwa
take oga.Dan sanda ya kara da haka ne don don
tunanin cewa in ta fito yau ma zai sami
kwaleliyar dubu daya tamkar jiya.Aliyu ya ce ka
ce mata zan fita ne ta dawo da yamma, bata jin
dadin haka ba amma me nema yana tare da
samu, don haka sai ta hakura ta tafi.A ranar ta
saka hotonta da ainihin sunanta aaccount din
da ta bude kuma Aliyu ya amshia botar ta.Da
yammancin ranar bata zo ba domin ta dana
sabon shairi, sha biyu zuwa karfe dayan dare ta
san lokacin da take ganin shi a online ne, don
haka sai ta hau.Cikin sa'a yana nan ta soma da
tura masa hotonta a inbox, yana ganin hoton ya
gane ta.Ya ce, oh, daman ke ce kika yi mun
basaja don in karbeki?Ta ce, naga in ba haka
nayi ba ba za ka kulani ba.Kuma ina da matsala
kai ne nake ganin zaka magance mun.Aliyu ya
ce matsalar me?Ta ce, kafin in fada maka
matsalar tawa, ka fara kallon hotunan nan.Aliyu
ya ce, to.Duk a tunanin sa matsalar ta ta shafi
aikin sa ne.Matsalar farko sassan kirjinta ne,
haka ta turo gabobi duk tsiraicinta ba inda ta
babu inda ta rage.Ya ce me nene ma'anar
hakan?Ta ce, ka duba hotunan da kyau?Ya ce,
eh.Dama ina so ne ka gani da kyau don in nayi
maka saimatsalar tazo da sauki, domin tun
ranar da na ganka na haukace da sonka.Ka
taimake ni.Aliyu ya rasa me zaice don ta kaici
da bakin ciki, sai kawai yayi blocking din ta
amma mehotunan da ta turo sun hau cikin
hotunanshi.Ya dinga bin su da dai dai yana
sharewa, amma da yazo kan na farkon na
kirinta sai ya tsaya yana ci gaba da kallon hoton
har ma ya kasa goge shi.Cikin daren tunaninsa
ya soma gurbacewa, da safe karfe shida wayar
bakin gate ta shigo, bai dauka ba don lokacin
bacci yana kanshi.Don baiyi wani bacci ba can
kuma a bakin gate din shi kanshi mai gadin
yana son wanan bakuwar ta samu shiga sabo da
ya san in ta fito zai samu wani abu.Ya ce,
madan me yasa jiya da yace ki dawo baki dawo
ba?Ta lallaba jakarta ta ciro yan dubu guda
biyu, gashi kasa kati.Da sauri ya amsa ya tura a
aljihu kamar yana tsoron kada wani ya amshe
masa, ko kuma ita ta ce ta fasa.Ya shiga zuba
mata godiya, ta ce, tunda jiyaya ce na dawo ban
dawo ba me zai hana in shiga kawa yanzu?Dan
sandan ya zaro ido oga yana da ka'da sai dai in
yayi fada zaki fiar da ni?Tayi masa fari da
idanunta, kada ka damu inyayi fadan zan wanke
ka.Tun da shiga falon ta ke ta kalle kalle, falon
nashi ya birgeta duk da cewa ba wani
kayanalatu ya zuba ba.Ta zauna kan kujera ta
bude jakarta ta dauko hoda da turare ta sake
gyarawa.Sanan ta cire rigar sanyin dake jikinta
saura singilrti, ta ajiye mayafinta ta gyara gashin
dokin dake kanta.Sanan ta dauki wayarta ta
soma kiran wayar ne ya tasheshi, wata isaka yaji
tana kadawa tamkar za ayi ruwa.Windo ya nufa
ya daga labule kamar yanda ya zata, hadari ne,
yaji dadin haka ko don yakara mikewa.Wayar ta
sake kacamewa da ruri, yana dubawa yaga
number yarinyar, tsaki ya ja tare da yin jifa da
wayar kan katifar sa.Ya bude kofar nifinsa yaje
kicin ya samu abin tabawa, cak ya tsaya sabo da
ganin yarinyar gaban shi ya soma faduwa,
lokacin da zuciyar shi ke tuno mashi hoton.Yayi
karfin halin daure fuska, sanan ya ce, da izinin
wa kika shigo min gida?Ta mike ta nufosahi, da
izininka masoyi na, ka manta ka ce in dawo jiya?
Ban sami dama ba shine na dawo yau.Ya ce, to
fita a gidan nan fita, ya nuna mata hanyar
waje.Ta zauna a hannun kujerar dake kusa da
ita,da ma ka bari mun fahinci juna.Ya juya ya
shiga dakinsa a fusace, durowa yaje ya dauko
bindiga nufinsa yayi mata barazana.Ya fito da
ita ya saita ta, kwashi kayanki ki fita.Hakika
gabanta ya fadi don bindiga ko makerinta yana
shakarta.Amma duk da haka sai ta jajirce, ta
runtse ido hawaye suka soma zuba,zanfi so ka
kasheni feye da ka barni a raye amma baka
amshi soyayyata ba.Zanyi alfahari in ka kashe ni
da kanka, kuma kacewa jami'an tsaro ni na yafe
maka ko sun tsinci gawata a gidanka.Aliyu ya ce,
muje ki fita ni bana son jin komai daga
bakinki.Sun isa bakin falo Ruwa ya tsuge mai
karfi wanda hakan ya sa ya kyale ta.Ya shiga
daki ya adana bindigar, sanan ya hau katifar sa
ya kwanta.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Gurbataciyar zuciyar sa ta shiga kitsa masa wasu
abubuwa, dauko wayar sa yayi yana kallon
hoton da yarinyar ta turo masa.Cikin jikinsa
sanyi yake ratsawa na ruwan dake
sauka.Mujidat turo kofar dakin ta shigo, kasa
magana yayi lokacin da ya waiwayo yaga ta raba
jikinta da tufafi.Yayi ta maza ya daka mata
tsawa, mai makon ta fita sai ta nufo gurinsa da
gudu ta fada masa.Shedaniyar shu'uma ce
yarinyar, don haka bata samu matsala sosai ba
gurin amincewa da gayyatar da tayi masa, zuwa
ga fadawa tafkin zunubin shedan ya sake
kawata abin ga zuciyar Aliyu.
Har yake ganin haram ta shigeshi fiye da
halalinsa.Mujidat ta amince Aliyu ne irin mijin
da take so ta samu.Duk runtsi ba zata barshi
ba, sai da kanwa takar tsami kwannafi ya
kwanta.Aliyu ya shiga jin cewa bai kyau ta ba.Na
dama ta shigeshi, ya mike cikin bakin rai ya nufi
ban daki zuciyar shi yar bakin ciki tana tunanin
shi cewa, wanan wankan da zaiyi anya zai fidda
mai da dattin zunubin daya kwasa?Ya fito ya
same ta kwance, haushinta ya kamashi sosai.Ya
dauki makulli ya bude durowarshi ya ciro kudi
batare da ya irga ba yan dubu dubu sabbi ya
mika mata.Gashi an gama ruwa ki tashi ki tafi
na rokekikar ki sake dawowa gidan nan.Ta
kalleshi cikin damuwa an ce maka neman kudi
nake yi?Ta mike ta soma saka tufafinta, so da
kauna kurun nake nema a gurinka baka da
kudin da zaka iya bani.Ta fice ta dauki jakarta
yana tsaye a tsakiyar falo yana kallonta ta fita
tare da cewa sai ka sake jina.
Ranar Aliyu yajima bai fita ba, na shi ganin
mutane zasu gane abin da ya aikata, kuma sam
baya son ya tuna.Sai istigifari yake yi, in dai
haka mazinata suke ji lallai zina bala'ice, ya
gargadi masu gadinsa lallai kada su sake barinta
ta shiganmasa gida.
Mahaifiyar mujidat yar asalin wani kauye ne a
Ilorin can jahar kwara, an ce dai asalinsu fulani
ne, amma yarbanci suke yi kuma yarbawa suke
kiran kansu.Musulmine su amma musulincin
nasu sai a hankali.
Mahaifiyar Mujidat mai suna Bukolatayi aure da
Mahaifin Mujidad hakimu bayansun haifi yayan
Mujidat dan suna fari kenan, mai suna
Latif.Wanan al'adar yarbawa ce mace taje aure
amma sai ta haihu za a daura, tasu hikimar wai
a gani in mai haihuwa ce.Bayan Latifa sun sami
Sikirat sanan Mujidat, mahaifin su mujidat
direban taxi ne, mahaifiyar su kuma tana da
shago a bakin kasuwa.Tun tasowar Mujidat bata
ji sam yar karya ce da son bobo, tunda ta lura
tana da kyau ai sai ta mai da kyawun nata
tamkar abin kasuwanci. Tun tana shekara tara
ta soma amsar kudi tana fansar da mutuncin ta,
haka ita mahaifiyart fitina gareta ko yau she
tana biye da mata wanan ya sa ko karatun kirki
bata yi ba, tana secondary idanunta sun gama
budewa, manyan mutane suke daukanta.Da
farko iyayanta sunda mu don mahaifiyarta ta
sha yi mata duka sanan tayimata tsarki da
ruwan barkono, amma da ga baya da ta soma
harka da manyan mutane tana kawo musu kudi
sai suka shiga shi mata albarka.Haka nan basu
damu tayi wata bata zo ba in dai zata yi musu
aike.A zuciyar su tafi yan uwanta Latifa da Sikira
wadda take aure a garin Ilorin.Kuma dalilin
ziyarar da ta kawowa anty sikira ta hadu da
Aliyu.Kuma har ta koma gida so da kaunar Aliyu
yasa ta ta dawo Ilorin don samun muradin ta.Jin
kai da jan aji irin na Aliyu shi ne ya sake burge
ta, amma sai gashi tashin farko ta same shi
cikin sauki.Tabbas in ta nace ba da dadewa ba
zai zo hannunta.Karfe tara na dare ta kira
numbar wayan mai gadin gidan Aliyu wanda ta
amsa dan bukatar kanta.Bayan ya daga ta
tambaye shi ka ganeni?Ya ce, a a ban gane ki
ba.Ta ce, sanana Mujidat daga nan cikin gari ni
ce wace na amshi numbar ka jiya bayan na fito
gurin Oga ya ce, ok madam ce ko?Sorry madam
na gane ki, ta ce oganka ya shigo?Ya ce, eh, tun
bakwai yana gida kuma naga alamar ba zai fito
ba, sai dai yayi mun kashedin cewa ko kinzo
kada in barki.Mujidat tayi shiru tana mamaki,
me zai sa ya tsaneta haka?Duk da ta mika masa
kanta kyauta, amma sai tayi wani
murmushi.Indai kissa tana magani to zatayi
mun, ta ceda me gadi in na baka dubu biyar
yaya zan samu in shiga?Yayi shiru yana
nazari.Lallai yana bukatar kudi don yasha kan
matsalarshi da maman Bilikis, amma dubu biyar
yayi masa kadan.Yace madan zan iya dabara in
kin ban dubu goma, zan fadawa Oga cewa
mamana ba lafiya nasan zai barni in tafi.Don
haka ta ba faruwa amma nasan kafin inbar
wurin sai an kawo wasu lokacin ke zaki samu
shiga dan su basu sanki ba.Kuma kafin in tafi
zan lalata wayar cikin gidan, ta ce hakan yayi
zan sameka da kudin in ka kamla komai ka
kirani.Yana kashe wayar yaga Aliyu tsaye a
bayan shi
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Dfarko ya rude sai kuma ya tuna cewa duk sun
yi maganar ne cikin yarensu na yaroba.Aliyu ya
ce, ina ta kiran waya baka daga ba?Ya ce, oga
jikin mama ne ya tashi shine dan uwa na ya
kirani.Aliyu ya ce, jikin ta ya sake tashi?Wani
ciwo ne ke damun ta?Ya ce hawan jini ne, Aliyu
ya sa hannu ya lalubo dubu biyu ya mika mashi
tare da cewa, Allah ya kara sauki. Ya kara da
cewa kaje ba sai ka jira wasu ba, bari nayi waya
su zo.Da murna mai gadi ya fita ya kira mujidat
yace, tayi sauri kafin wasu masu gadin su
zo.Cikin sa;a ta tura kofa ta shiga, haka nan
cikin sa'a ta riske shi a cikin falo zaune da yar
shirt fara irin mai kama jikin nan.Sai gajeren
wando, kalkon labarun kasa yake yi NTA, turo
kofar ne yasa shi waiwayawa, zunbur ya mike
yana nuna mata waje.Fita la'ananiya, ta saki
jakarta ta nufeshi, haba masoyina, ina sonka
sosai tsaya kaji.Ta kai hannu zata taba shi ya ja
baya.Ki fita kawai, ta zauna kan kujera, ba zan
sake barin gidan nan ba ko zaka kashe ni.Ya
biyota ta zagaya ta fada bedroom dinsa.Ya rasa
me zai yi mata, sai kurum ya kira yaransu daga
headquarter, jin haka dama tariga ta tanaji
dabararta.Taciro wayarta ta danna wani hoto ita
da shine suna tsaka da aikata masha'a ta
dauko.Kalli hoton nan ka gani, ina da irinsu da
yawa har na kati na wanke.Aliyu ya fizgi wayar
ya kalla, duk da ya girgiza amma bai nuna mata
ba ya ce, yace amshi wayarki ba kati ba in kin
gadama in kin tashi ki sa shi a kan profile din ki
na fcbk,ko a jikina.Ke ce mace mutuncinki sai
yafi nawa zubewa.Tayi shiru ta rasa me zata ce,
ya ce fita.Ta daga hannuwa biyu, naji naji zan
fita, ta matso gunsa amma ya kamata a ce
kanayiwa mesonka kallon mutunci da kima.Ta
soma kuka, ka tuna ba nice na dorawa kaina
sonka ba, ya kamata ko baka sona saika fada
min magana mai sanyi.Ya runtsa idanu, burinsa
ta fita domin zuciyarshi ta soma
tausayinta.Sanan ga shi dan can gefe yana rada
masa wani abu.Ya bude ida nunshi, shi ke nan
naji ban kyauta ba amma dai yanzu ki fita
kawai, domin ni da ke ba hurumai bane.Ki tuna
da abin da ya faru ni dake she karanjiya laifi ne
babba, kin sani.Ta matso ta kama hannuwansa
ka min afuwa sonka ne ya sani haka.Yanzu ina
jin yunwa ko zaka tai maka min da wani abu in
ci sai in tafi?Ya ce, duba kicin sai dai in bread za
ki ci.A kicin tayi ta zagayawa tana tunanin me
zatayi ne don ta samu ta kwana a gidan.Ta
dauki wuka ta dauko bread wai za ta yanka,
amma sai ta kulle ido ta sharbi yatsanta da
gangan, sanan ta saki kara.Cikin hanzari ya nufi
kicin da ganin yanda jinike zuba ya sa shi shiga
da sauri ya rike ya tsan nata.Kasancewar yana
da yar akwatinshi ta taimakon sai ya gyara mata
ya rufe shi sanan ya ce, muje a maki Allura sai
ki wuce inda kike.Ta soma rawan sanyi wai ba
zata iya tashi ba, barinta da yayi ta dan
warware shi ne ya kawo kwananta a
gidan.Domin tuni shedan ya ribace shi, duk da
yana zargin ta yanka kanta ne dama don kada
ta tafi, tun daga ranar ta zama gidan tamkar
matarsa, wanan ne yasa ko da ya koma gida
sadiya taga canji.
Wata hudu kenan da soma shiga matsalar mu
da ya Aliyu, amma tamkar na shekara biyu, duk
na rame na lalace har bana so inyi baki don
kada suce lafiya?Cikin wata hudu ya zo so hudu
duk karshen wata ke nan kwana dai dai yake yi
ya tafi sam baya kulani in yazo magana fiska a
daure yake min.Ya manta da wani hakki nawa
da yake kanshi, domin nima mutun ce ba ice
ba, ina shan wahala da kewarsa.Darare da yawa
ina zubar da hawaye don kunci da kewa, gashi
yayi mun sabo da yanayin sa na rashin
hakuri.Usman da Anty Abida sune kawai suka
san halin da nake ciki, ko iya da amininiyata
Aisha sunyi juyin duniya amma ban shaidar
musu da ko mai ba.Usman ya ce, duk lokacin
da nake bukatar wani abu bai min ba in
tambaye shi, ni gaskiya ina da jin nauyi.Yau in
na ce gashi gobe in ce gashi ba zai yuwu ba,
abin da kawai na tsana shi ne inga arana babu
makaranta, amma don abin anfani kamar su
abinci ina maneji.Tunanin kama sana'a ya
shigeni, na ce lallai ina bukatar in kama sana'a
don in samu in kare DARAJAR YAYA NA,
wadanda a yanzu sunfahimci tsakanina da
baban su a kwai matsala.Ba kausar ba hatta
Al'amin ya san cewa mahaifinsu ya canza, don
watarana da ya shigo daki ya same ni ina kuka,
sam banji shigowarsa ba sai naji an dafa ni.Nayi
ta maza na share hawaye na na kalle shi da
murmushi, ranshi a dagule ya ce, momy waye
ya saki kuka?Na ce Idona ke ciwo.Ya ce, mama
Abban mu ne ko?Na ce, a a Abbanku bayanan?
Yace, shi ne mana, ya ce ki barshi in na girma
zan maki duk abin da kike so, in kaiki maka, in
sai maki komai.Na rungume shi tare da cewa, to
yarona naji dadi na gode kaji.Ya ce momy ki
daina kuka kin ji?
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Bayan fitar Al'amin ne na shiga sabon tunani,
lallai matsala tsakanin miji da mata tana kawo
rabuwar kan yaya, tana tauye yara.Domin zuwa
da nayi open day din su a makaranta nan
malamarsu take yi mun korafin cewa yarinyata
Kausar sam yanzu bata da hazaka kamar
da.Bata da kuzari sam, ta ce kowa ya san
Kausar Aliyu Tutur a makarantar nan ya san ta
da kokari ga surutu, ga wayo.Haka nan duk
wanda ya yi mata bata kyalewa, amma daga
wancen term zuwa wanan tazama tamkar
doluwa ba karatu.Bata iya rama fada, karamin
yaro sai ya doke ta ta tsaya kuka, sanan tsaftar
su ta ragu, a da yaran suke zuwa na daya a
tsafta wanan karon sun koma na biyu.Don haka
kiyi kokari ki canja kila matsalar daga wajenki
ne.Afili na ce, lallai daga gurin mu ne,
matsalarmu zata maida yaranmu baya, dole in
kawo canji duk yanda zanyi gidan mu ya koma
gidan farin ciki kamar da da taimakon
Allah,Wayata na dauko na soma ruga sako
kamarhaka.KALMOMI SUN YI KARANCI
TSAKAKKEN YANAYI, FADIN YI HAKURI KADAI BA
ZAI GAMSAR BA.AMMA DUK DA HAKA INA ME
BAKA HAKURI, BA DAN NAYI LAIFI BA, SAI DAI
INA DARAJA DANGATARMU FIYE DA
SHEKARUNA.DA WANAN SAKO NAKE SAKE BAKA
HAKURI TARE DA AIKO MAKA DA ZUCIYATA KA
AMINCE DASHI DON SAKE DAWO MIN DA
FARINCIKI NA.INA FATAN ZA MU KOMA FIYE DA
DA, ZUMA TA ALY NAYI KEWARKA, INA TSNANIN
SONKA.
Na tura mashi ina tsammanin ganin sako kokira
amma shiru, duk wani tunani ko dabara nayi
amma babu nasara.Wata laraba da yamma su
kausar an koro su kudin islamiya, gashi dama
abincinmu ya kare, nafita hannuna da Nera Dari
na siyo garin rogo da suga.Nufina su sha da
dare, duk da ina tunanin yaya zan sha kansu su
sha gari da dare, sai lokacin da nake dawo wa
yana ba yana a mota direbanshi yana janye da
shi.
na shigo gidan zan Rufe sai naga mutum kamar
daga sama ya nufo gida, gaba na yayi muguwar
faduwa.Sam yanzu bana son ganin shi, don
tsananin tsoron sa nike ji, ko sallama baiyi ba ya
fara da ce mun, daga

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login