Showing 18001 words to 21000 words out of 22554 words
Chapter 7 - Darajar Yayana Book 2 Complete by Halima Abdullahi K Mashi .txt
sai suka rugo da
kansu gaskiya baba yau bazamuci tuwo ba.Ya ce
to me ni dai kudin nan ke nan.Ta ce, ko tuwon
ne ma kudin nan ba isar muzaiyiba, ya ce haba
Tasallah, ba kifi ba nama kice dari biyu baza tayi
miya ba?Ya shura takalminsa yayi gaba.Ta daga
murya sai dai ayi maka ciko kuma kana zuwa
zaka bani kudi na.Yaran suka hau mita, shi
baban nan kullun tuwo.Na kalleta cikin mamaki
sanan na ce, na kusan daina zuwa kitso gurinki,
ta ce zaku tashi ne?Na ce a a na ce nagaji da
yanda kike daukar mijinki ba a bakin ko mai
ba.Dubi yanda kike sa yaranki suna yi ma
mahaifinsu rashin da'a da raini, wanan tarbiya
ke nan?Tayi yar dariya hajiya kenan, Allah hajiya
ba haka bane, ace mutun kullun ba ci gaba, ba
ya neman wata sana'a a caba yake.Na ce, na
lura baki da godiyar Allah ta salla. Ranan fa ina
kallonki da yaranki kuka ce masa kun gaji da
shinkafa, san nan baki sanin mijinki ya dawo ki
bishi daki ba.....
Allah sarki Rayuwar Aure,kowadai da tasa
matsalar,damadai haka Rayuwar take,tanada
manyan matsaloli guda hudu wadanda duka
daya takan haddasa rashin jin dadi daga
bangare daya,Immadai -:
Mijin baya jin dadin zama da matar,misalin
Tasalla me kitso da Mijinta,kokuma...
2:Matar ake zalunta ,Misalin Aliyu da
Sadiya,Kokuma ...
3:Suna zaune lafiya a junansu, Amma dangin
matar ba kaunar mijin,shima Wannan Babbar
matsalace a auratayya,Wacce ke Haifar da Babar
Matsal..kokuma...
4 angin mijine basu son Matar, wanda nasan
da yawanku kunfi sanin wanna matsalar,..
Lallai dukanin gidan auren da suka samu kubuta
daga dukkanin matsalolinnan nazama wajibi Su
godewa Allah,akarshe Dukkani gidan Auren dake
da matsalar makamanciyar wadannan Ya Allah
ka kawo musu agaji,mukuma Ya Allah
kahadamu da abokan zama nagari
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Zaharaddeen shomar
Whatsapp 08168575100
Darajar Yayana2-04
Posted by ANaM Dorayi on 06:34 PM, 29-Mar-16
Under: DARAJAR 'YA'YANA
___________________NA
___________HALIMA K/MASHI
Assalamu'alaikum, fatan kuna cikin koshin
lafiya...
Sagir Ali, Shamsusdden Usman,Fatima
Ahsan,Maman Ummi,Shamsiyya,Ummi
Amal,Aisha and Aisha Kaka Zanna nagode da
kulawarku,sannna inna jin dadin yanda kuke
kulawa da shige da ficena,shirun da kukaji
yafarune sakamakon ayyuka da sukaimin
yawa,fatan zakucikaba da bibiya dakuma hakuri
dani. nagode zamu Dora yanzu.....
Ruwan wanka sai dai ya diba yaje yayi, wanan
rashin dabi'ar har ina?tasake yin dariya, to ni in
nashiga dakin in ya dawo me zan masa?Na ce,
auran kiyayya aka maki?Ta ce, a a ni na kaishi
gidan mu, ta ci gaba kin sani ni gaskiya ko ya
dawo bana shiga, shi yanzunnan zaice zai
rungume ni, niko na tsani haka,ka debo rana ka
wani ce zaka rungume ni, salon su Habu su fado
dakin?na ce menene dan yaranku sun ganku
rungume da juna?Kai ke dai baki da dabi'a,irinku
ne ake kwacewa miji cikin sauki,daga baya kizo
kina ya ci amanar ki,ni dai in baki canza haliba
zan daina zuwa,ta ce;to Hajiya za'a sake, ai ku
hajiya cikin daula kuke baku da matsala.Nayi
murmushi Tasalla kenan.Shiyasa na ce, kina da
hange, ki kalli kasanki mana,Misali waccan
Maman Rashidan kuke ce mata ko wa?Tunda
nake zuwa gidan nan bai fi so nawa naga ta
daura tukunya ba.Kullun in kazo zakaga yaranta
suna cin dumame, ko garin rogo amma ban taba
ganin mijinta ya dawo ta barshi ya dibi ruwan
wanka da kanshi ba, ko ta shareshi taki shiga
daki.Sanan sau biyu na taba ganin mijinta nasan
yayi sa'ar mata, duk cikinku 'yan nan sasan da
na taba ganin shigowar mazajenku da fitarku ita
kadai ke yi wa mijinta sannu da zuwa da yi mashi
addu'a in zai fita.Tasalla tayi yar dariya, hajiya
kenan, ita waccen ai bata san kimarta ta ya mace
ba, in banda haka yaushe zan zauna babu
abincin kirki.Amma kina like da mutun kullum sai
tayi wankan asuba don jaraba.Na ce, tafi ku
godiyar Allah ne da biyayya.Sanan zakuga
cigabanta kuna nan, sanan yaranta sunfi naku
tarbiya da tsafta.Tasalla ta bata rai,Hajiya mu bar
maganar nan, amma ko su maman Auwal zaki
tambaya matarnan tana shiryawa yaranta kinaya
ne don in mutane sunzo su rinka gaidasu don a
ce suna da halin kirki.Na ce, ba wani bayan aike
ma ina kallon naku yaran amma baku aikensu
don kunsan cewa bazasuba, sai dai ku kira
nata.Daga nan Tasalla tayi kus, niko na ce in sha
Allahu duk randa zan kuma zuwa sai nayi wa
yaranta kwalima tunda naga yaranta basu fi
girman su Kausar ba, a raina na raya hakan.Ina
Mota na kusa isa gida da motar dama naje gidan
kitson da mota ne, sai ga kiran Aisha aminiyata,
cikin hanzari na daga ina fadin.Kin haihu kenan?
Tayi dariya yau andace kullun na kiraki zancenki
daya ne kin haihu?To ga yarki nan a gado.Na ce,
Alhamdulillahi ga ni nan.Na kira layin Abban
kausar kamar yanda na zata har ta tsinke bai
dauka ba, na sake kira.Muryar mace naji cikin
harshen turanci tace wakike nema?Sai da sitiyarin
ya kusa kufce min, na samu na tsaya tunda cikin
unguwa ne, na sake yin sallama cikin rawar
murya.Ta ce kina bukatar taimako ne?Na katse
layin zufa ta soma tsatstsafo min.Na rude
matuka, na kifa kaina a kan sitiyarin ina fadin
Allah yasa mafarki nake yi.Na kuma kallon wayar
ina shawaran in sake kira ne ko in barshi, sai ga
kiranshi ya shigo da sauri na daga amman na
kasa magana, Muryarshi ne yanzu ya ce hello!!
Dazun bakiyi magana ba sai wata irin muryanake
ji.A sanyaye na ce dazun ba kai bane wata ce ta
daga.Da sauri ya ce wata wa?A wayata?A'a sai
dai in network ne yasa ki kika ji haka.Ya saki
zancen da cewa, lfy dai?Na ce eh dama ina
dawowa daga gidan kitso ne sai Aisha ta kirani ta
haihu.Ya ce wace Aishan?Na ce, ta mamana.Ya
ce, Allah ya raya, kin cika son yawo.Na ce to yaya
in banje yanzun ba dole in sake fitowa don inyi
gabadaya.Ya ce to shi kenan ina yaran?Na ce
sunje yiwa iya wuni, ya ce ban son fa kina tafiya
ke daya fa.Ko mama bakya iya yawo da ita sai ke
daya tsura?Na ce, to yaya sun kwana biyu ne
basu je sunyi mata yini ba.Ya ce, to shi kenan
kardai kiyi dare don na sanku in kuka sami surutu
na ce to.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Bayan ya kashe wayar ya nufi gurin Mujidat da
ke zaune kan kujera tana dafe da kumatu, inda
Aliyu ya watsa mata mari sakamakon shigowa da
yayi ya ganta ta daga masa waya.Ya kalleta in
kika kara yi min gangancin daga min waya sai na
mugu saba maki, don zaki koma inda kika fito.Ta
mike tsaye kana jin tsoron matarka ne don kar
tasan muna tare ta ce ta fasa aurenka?Cikin
gatse Aliyu ya ce haka ne.Don haka kada ki kara
daga min waya.Ya juya ya shiga dakinsa rai a
bace.Mujidat ta mike tsaye tana kai kawo, wai
mutumin nan yana nufin duk son da nake masa
yafi son matarshi a kaina?In ma yana boye mata
ne sai nayi sanadin da zata sani, in sha Allahu.Sai
dai ta mutu ko ta bar mun shi, don na yi imani
na fita son shi, zanyi komai don naga na rabasu
da makircina kawai,ta hada yatsanta babba da
na tsakiya taja suka yi kara, wanan wata Alama
ce da take yi duk lokacin da ta ma kanta
Alkawarin aikata wani abu cikin izza.Ni kam
kwana nai da motata zuwa gidan Aisha, amma
zuciyata cike take da wasi wasin abin da kunne
na yaji wai netwok ne.Anya kuwa ba binne ni
yaya yayi da rai na ba?Nayi murna da ganin
Aisha cikin koshin lafiya tare da jaririnta.Na dauki
yarainyar ina juyyata, mashaAllahu,Bello ya fiki
karfin jini daga ita har Najib shi suka biyo.Na ce
haka dai su mama suka ce, na ce, ina angon
karnin?Ta ce ya fita na kwantar da yar na kalleta
a Asibiti?A gida kafin ya samo mota har kai ya
fito.Innarsu da mamanmu da ma suka zo sai
kurum suka amshi haihuwar, na ce shi kenan
Allah ya kawo shi cikin sauki.Na nufi wata kula
dake gefe, na ce me suka barararaka miki?Na
bude kular, ta ce tuwo ne, miyar kuka, kinsan
tsaffin nan sai suce wai maijego sai da
tuwo.Muka sa dariya, na ce a ni na horu da tuwo
gurin Iya, haihuwar kausar har wani baki nayi
nayi muni dan uban nan.Muka sa dariya.tace, ai
daga baya Anty Abida ta hada maki sabulu, na ce
ai ta min kokari yanzu ba abin da bana hadawa
da kaina.Ta ce zaki hada min sabulunma nace to,
haka mukai ta fira har shida, sanan mukayi
sallama naje gidan Iya na kwashi yayana muka
tafi gida.
Na kasa bacci cikin dare sai juyyi nake kaso
hamsin da daya na zuciyata, yaya Aley yayi
min.Tabbas zan zama wawiya in ban amince yaya
yana neman mata ba.Yaushe rabon da ya dora
yatsansa kan nawa?Kullun dare ina kwana da
kewa, hawaye na suna kwaranya.Na tashi zaune
in ko haka ne wane mataki zan dauka.Zuciyata ta
dauki zafi ina fidda wani huci, lallai in ya kasance
haka zamuyi rigima ba karama ba, don ba zan
dauki wulakanci a kan matar banza ba.
Washe gari da safe ina ta tunanin yanda zansake
cewa yaya zan sake komawa gidan Aisha, saboda
in na haihu kulun tana hanyar har ayi
suna.Amma ni ko haihuwar Najib dinta banyi
mata wani sintiri ba, yaya hanawa yayi.Kuma
bana son fita batare da izininshi ba.Don nayi
imani shi baya kallona Allah da ya halicceni yana
kallona.Text na tura mashi cewa zanje gidan
Aisha lokacin suna tare da Mujidat suna
karyawa.Ya dauka ya karanta, sai ko ya hade rai
ya soma kiran layi na na daga.Tunkafin in karasa
sallama na ji ya ce, ban amince ba kullum fita,
saboda ki dinga kallon maza ko? Na zaro ido na
mike da sauri na nufi daki dan su Kausar suna
nan gida don anyi musuhutu.Kuma bana so suna
jin matsalar mu.Ya ci gaba da fadan shi, na ce
wacce irin magana kake yi yaya?Don in dinga
kallon mazaje fa ka ce?Kana nufin in na fita haka
nake yi?Ya ce, oho miki, amma ban yafe ba in
kika leko waje, nace naji ai tunda ka hana ba zan
fita ba, amma cewar da kayi wai ina kallon mza
nike son inji hujjar ka.Kana ga don ka shuka
fulawa ta fito kaki kayi mata ban ruwa sai ta
mutu?Na ci gaba, haka ne zata mutu amma
kasani ni nasan DARAJAR YAYA NA.Ko don su zan
kare mutuncina kai shaidane budurwa gar ka
bare ni a leda, ka san haka kuma kullun ina
Adu'a Allah ya kare ni daga sharrin zamani.Ban
jira amsarshi ba na kashe, sanan na fada kan
gado ina kuka.Sai kurum naji hannun kausar a
baya na tana fadin.Momy kiyi hakuri ki kyale
shi.Da sauri na share hawaye na taso kausar
bana ce in ina waya a daki ba ku daina biyo ni?Ta
ce momy ki daina daga wayar Abbanmu, ko ya
kiraki ni bana so yana saki kuka.Na ce naji muje
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Kwana uku da yin sunan yar gidan Aisha ya ta ci
sunan Fateema, sai ga yaya da rana tsaka ina
mamakin yanda yanzu yake son yimin dirar
mikiya.Ko yana zargin ina fita ne?Oho.Nayi masa
sannu da zuwa ya amsa na ce, baka fada ba
gashi banyi abincin rana ba.Jiya sun bar
shinkafar da na dafa da dare, sai kawai nasa a
firiza yau na duma ma, amma bari in maka ko
macroni ce.Ya ce barshi bani da yunwa, in na fita
zan siyo fura.Sai da yayi bacci sanan ya tashi yayi
wanka ya fita.Duk ina dakina ina karanta littatafi
,tinda nalura bai bukatar ganina kusadashi, nima
hakan yafi min sauki don in yana gari nafi jincewa
nima macece in kwana cikin kewa.Washegari ya
fita zuwa gidan su Iya na dauko jakarshi, don
kwashe kayan wanki wanda ya dawo dasu kamar
yanda na saba.Ina daga suit din shi zan rataye
wata takarda ta fado, na dauka har zan maida
masa cikin Aljihun rigar sai wata zuciyar ta ce
bude mana ki gani, na bude.Yar wasika ce aka
rubuta da harshen turanci, ga abin da yake
rubuce.ZUMA NA KA TAFI DA TUNANINA, HAR
KAJE KADAWO KASANI ZA KA BARNI CIKIN KEWAR
LALLAUSAR FATAR JIKINKA.BA ZAN GUSHE BA HAR
SAI KA DAWO KA SAME NI CIKIN KEWAR LEBUNAN
KA MASU SANTSI TARE DA (YAWUN) KA ME
ZAKI.ALLAH YA DAWO MUN DA KAI
LAFIYA.....Kafin na kai karshe tuni na jike da
zufa, ina gamawa na ga gari yana juya min, ban
an kara ba sai dai naji ni a kasa ribin jikina a
gado rabi a kasa.Kusan minti biyar sanan na tashi
zaune sa sake karanta takardar ina kuka wiwi har
da majina tabbas yaya mata yake bi,domin
takardar ta nuna haka, mata ce kawai ya dace
tayiwa mijinta irin rubutun nan, wata zuciyar ta
tambaye ni ko dai ya sake aure ne?Duk da uban
kishi na sai nasami kaina da cewa inda ma auran
yayi zanfi son haka, da bin matan banza.Na soma
kaikawo cikin gidan ina tunanin matakin da zan
dauka.Shawarar wa zan nema?Na shiga dakina
na fada kan gado na dauki wayata na shiga
kiranshi, amma sai wani tunani ya fado min.Bari
kawai in kira Hajiya Baida'u, marubuciyar littafan
da nake karantawa danneman shawara.Dan ita
bata sanni ba balantana inyi zaton zancen zai iya
yaduwa, sanan tana da basira nasan zata sani a
hanya.Ringing na biyu ta daga, ta daga muka
gaisadama na saba kiranta, na ce Anty ina
nemanshawara ne.Leta na gani a jakar me gida
na wanda ke Alamta cewa yana tarraiya da wata
mace.Ta danyi shiru na dan lokaci.sanan ba yan
wanan letar kina da wata shaidar?Sanan can
dama halinsa ne?Na ce, a to a da can ba na
zarginsa, sai da ga baya na soma zarginsa domin
Anty kwata kwata ya kaura ce min kusan wata
shida zuwa bakwai yanzun,kuma Anty shi mutum
ne mai zurfin sha'awa, ba zai iya daukar ko
kwanaki ba ba tare da mace ba bare watanni.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ta ce kuma ba gudan sa kike ba har hakan ta
faru?Na ce wlh Anty Allah ya sani ban ta ba juya
masa baya ba, har matsalar nan ta shigo.Ta ce,
kuma kina gyara jikinki ba ji yayi kin zama wata
iri ba?Na soma lissafo mata abubuwan da nake
hadawa, ta ce, lallai kina kula da kanki.Na ce,
anty yanzu in yazo in fada mashi takardar don
yasan na sani?Ta ce, a a tunda kinga zarginsa
kike yi kenan baki da tabbas, ki boye takardar
kuma ko a idonki kada yaga damuwa.Ki bishi a
hankali, ki boye sirrin nan tunda uban yayanki
ne.In shaAllahu sai kiga Allah ya dawo maki dashi
kan hanya, na ce,Anty zanyi yadda kika ce, amma
zan ci gaba da bincike.Ta ce, za ki iya amma ki
sani tsananta bincike shima matsala ne, don zaki
iya ganin abinda zai saki hawan jini, na ce anty in
na tabbatar da gaskiyar zan tunkareshi ne in
nuna masa nasani.In ma zai aureta ne gara ya
aureta da zaman banzan nan, ta ce haka ne,
amma kada ki manta da adu'a, na ce insha
Allahu, ina magana cikin kuka.Ta kwantar mun da
hankali da cewa, ki daina kuka, na ce anty me
nene maganin bakin ciki?Ta ce karatun Alkur'ani
zuciyarki zata wanke sarai.Na ce, to anty na
gode.Muka yi sallama na kwanta nayi kuka sama
da minty biyar sanan na tashi na boye takardar
na ci gaba da aikina ina kuma ci gaba da
kuka.Wanan wane bala'ine Abban kausar ke son
jefa ni, ni da 'YA'YA NA?Ya manta cewa duk abin
da kayi da Dan wani kaima sai anyi da naka?Da
na koma daki sai naji komai nasa kyama yake
bani, shi kansa yanzu kyamarsa nake ji, na
karasa kwashe kayan nasa ina yi musu kallon su
kansu suna dauke da zunubin zinar da yake
yi.Tunda su Kausar suka shigo naga sun tsura
min ido ita da Al'amin shine ya soma
magana.Momy me yasameki a ido?Na ce, ba
komai, ciwo yake min.Sai naga sun kalli juna.Na
tsugunna tsakaninsu menene?Na tambaye su
tare da yin dan guntun murmushi da na kirkiro
ko nace yake.Al'amin ya ce, yaya kausar ce tace
bata so Abba yazo in yazo yayi ta saki kuka, kuma
fa ko an tambayeki sai kice ba komai shi ne nace
ai yanzu ya daina.Amma muna zuwa sai muka
sameki kinyi kuka, ku,ma muka tambayeki sai
kice ba komai.Kausar ta ce, na canka ko Al'amin?
Abban nan ni bana sonshi yanxu.Al'amin ya bata
fuska, nima bana sonshi, bakin ciki ya turnike ni,
bana son kallon da yara suke yiwa
mahaifinsu.Nace kausar ku daina cewa bakwa son
mahaifinku,bana fada muku in kunyi Sallah ku
rinka adu'a Allah ya kawo sauki cikin lamarinba?
Allah yana amsar adu'ar kananan yara, sukace
munayi sosai Momy kullum.
Ko da ya shigo kasa kallonsa nayi, ganinake zan
iya cin kwalarsa, don haka na sa kaina a daki na
rufe tare da sa sabon kuka.Ya kalli su Kausar, ina
mamanku?Al'amin ne ya ce, tana dakinta, yazo
ya buga kofar kamar kada in bude amma sai
nafasa na bude
Ya tsura min ido lafiya?Na kalleshi, me ka gani?
Ya ce, fuskarki na gani a kumbure, na taba baki
sanan na shafa fuskata.Kila baccin da nayi dazun,
ya ce wanan kumburin baiyi kama da bacci ba,
ya fi kamada wanda yayi kuka.Na mai wani irin
kallo.Don yanzu bani wani ganin girman shi, na
ce ai ban san tsawon lokacin da kuka na zai
dauka ba kafin ya tsaya.Ya ce to Allah ya kyauta,
ya juya tare da fadin to a zo a bani abinci.Sai da
na dan bata lokaci sanan naje na shirya komai na
dawo abina.Ku ziyarci blog dinmu domin karanta
Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Washe gari ya fita, sai dai duk Aliyu a dame ya
bar garin ya rasa gane kukan da Sadiya take
zabgawa, nashi ganin bai san yayi mata wani abu
ba tun zuwan shi.Rashin kulata ai ba yanzune
farko ba, to kukan na menene?Dole Akwai wani
abu, abin da yasake birkita masa lissafi yanda ko
wayarta yakira sam bata iya dagawa.Rana ta
hudu da komawarshi, ya gaji ya kira kayin Usman
ya fada masa halin da ya bar Sadiya, da kuma
rashin daga wayarsa da take yi.Yamma likis
inayiwa kausar kalaba na wanke mata kai ina
cewa sai gobe zan kaita kitso, sai ga Usman.Muka
gaisa sannan na ce, shigo falo, kausar kuma nace
suyi wasa a nan tsakar gida.Usman ya kalleni,
mijinki ya ce baki daukar wayarshi, kuma ya tafi
ya barki cikin kuka.namike naje na dauko mashi
takardar da na gani cikin kayansa.Shi kanshi
Usman kasa dago kai yayi ya dube ni, can ya ce,
lallai abin da nake zargi ya tabbata, amma don
Allah ki kara hakuri kuma in sha Allahu ko mai zai
wuce. Yanzu bari inje da takardar nan saboda
bincike, na ce yaya kayi hakuri kabar takardar
nan a hannuna saboda ta zama shaida a duk
lokacin da na masa zancen ya musa.Usman ya ce
nima da ma don hakan naso na aje ta guri na,
amma ajeta gunki, na amsa sannan mukayi
sallama.Ya kira Usman dan jin yaya?Usman ya ce
ta ce mun ba komai tana bukatar hutu ne da
dago waya, Aliyu yayi shiru, mamaki yake ji,
kuma yana ganin kamar da wani abu sun hada
bakine ita da usman.Aliyu ya ce, amma bakayi
mata fada ba, in ita ta manta cewa mijinta nake
ya kamata kai ka tuna mata. Usman ya ce, aboki
yanzu kaga aikinike, kasake kirana wani
lokacin.Ya katse wayar ba tare da ya jira amsar
Aliyu ba.Afili ya furta cewa, tabbas akwai wani
abu.
Tabayanshi Mujidat ta rungume shi.Dear wai me
ke faruwa ne?Tunda ka dawo na kasa gane
kanka.Ya kalleta cikin zargi kin sake daga wayar
matata ko?Tayi rau rau, wlh Honey ban daga ba,
ta somayi masa wadan su wassan ni tana rada
mishi a kunci me yasa ba zai mata irin son da
take yi masa ba?Ita fa zata iya mutuwa a kansa,
amma shi yafi son matarsa da ita.Ya hankadeta
tare da fadin dan Allah barni ta yaya ma zaki
hada kanki da matata?Matar sunna wacce ke
zaune don ni kadai, ta soma kuka tunda na hadu
da kai na daina hulda da