Showing 3001 words to 6000 words out of 22554 words

Chapter 2 - Darajar Yayana Book 2 Complete by Halima Abdullahi K Mashi .txt

da
Sadiya.Bayan sun gama magana akan abin da ya
kai shi, dama usman MTN yake aiki, sanan ya ce,
wanan yarinyar mai shegen tsoron tsiya, kuka
tayi ta min na barta na tafi abina.Idan ka tashi
dan Allah katafi ka taho da ita don ni ko ganinta
bana son yi.Usman yayi murmushi, sanan ya ce,
kayi mata uzuri, kasan yarinya ce sai a
hankali.Usman ba da bata lokaci ba ya sanar da
manajan su, nan take aka soma gudanar da
bincike a kan lambar.Sun gano layin a yanzu baya
kan waya, amma sun hada komai yadda da an
dora shikan waya zasu gano inda mai layin
yake.Nan take kuma ya kira CP yayi masa
bayani.CP ya ce, good! Kara zage damtse in kuma
kana bukatar yara duk sanar dani.Yes sir!Inji
Aliyu.Ku ziyarci blog dinmu domin karanta
Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Na idar da sallah azahar ke nan sai naji alamun
ana bude kofa, fatana Allah yasa yaya Aliyu ne,
in sha Allahu yanzu nan zan bashi mamaki
Sai dai kashi!Ya na budewa sai naga yaya Usman,
ya ce tattaro kayanki muje gida.Na dauki jakata
da mayafi, sanan na gaishe shi, ya amsa tare da
cewa ki kwaso lemukanmana.Na ce, na kishi da
su. Ya ce, ai kya kai wa iya tsara ba ko kina nufin
gidan Oga ba a baki ko mai ba duk da cewa kin
kwana?
Yayi tambayar cikin zolaya, na dawo na dauka,
har ya taya ni sai lokacin naga Ibrahim din da
suke nagana, gajere ne baki.Sai da muka tsaya
Marhaba Store ya kara min tsaraba wai harda
turmin zani matar Oga ta ce a ba Iya.Da zan fita
nace masa nagode, ya gai da anty Abida, ya ce
zata ji.Sanan ya ce, ki saki jikinki don kada ta
gane ba can kika je ba.Ina yin sallama iya tana
zaune, cikin faduwar gaba na isa gurinta ina yi
mata sannu, ta amsa fiska daure.Jikina yayi
sanyi, nayi karfin halin cewa.Iya kin ganni sai
yanzun?Tun da yaya ya kaini ya Aliyu bai zo ba
har sai da na kwana, wai suna aikin wani case ne
a hannun sa.Iya ta ce, kai ma dallah da jin haka
sai nayi shiru, don na san zance na bai shiga Iya
ba, na mika mata leda.Gashi inji matar ogan yaya
din wai in baki tana gaida ke.Sai naga iya tayi
murmushi ta girgiza kai, sanan ta ce an gode.Tun
lokacin ban sami bakin magana ba sai daki da na
shige na kwanta.Har yanzu haushin kaina nake ji,
da na sani nabi umirnin miji na, gashi wanda
naki don ita bata yarda ba, kuma nayi imani ko
da mezan ran tse ba zata yarda da ni ba.Aliyu
yayi nasarar kama dan fashin nan tare da
taimakon masu layikan wato network na
waya.Don yan fashin sunyi anfani da layika
dabandaban, ya kama oga tare da wani yaronsa
guda daya, jim kadan bayan an basu kudi sun
saki yaron.Sun dauki hanyar kawo da a lamun
zasu bar Kaduna ne, ya harbi tayarsu sanan ya
harbi ogan a kafa.Sauran sun gudu shi kuma
dayan tsayawar da yayi zai dauki kudin daga but
din motar shi ya kawo Aliyu yayi nasarar kama
shi.Wanan gaggarumar nasarar ta sa an karawa
Aliyu girma daga ASP zuwa DSP, inda aka tara yan
jaridu suka watsawa duniya.
Duk kwanakin nan da aka dauka sam Aliyu baya
shiga harka ta, in na gaida shi zai amsa amma ko
kallo ban isheshi ba.Haka nan har daki na same
shi don inyi masa murna kan karin girman da ya
samu, amma sai ya ce dan Allah in fitar masa
daga daki.Har Iya ta na ce mun Allah ya kara,
tun da na ba da kaina ba loka cin da ya da ce ba
ai yazama dole in jure wulakanci, bani da hujjar
yin musu dole in yi shiru.Gadan gadan ya tada
aikin gidan sa, da alamu ya sami kudi, ranar
wata a Abar bai fita da wuri ba.Sai da suka shirya
sanan sun fita hanya sanan ta soma yi masa fada
me yasa yake yiwa marainiyar haka?Ya ce, bata
jin magana ne, gara ma ki mata fada tun yanxun
don ba zan dauki gaddama ba.Sunje iya nata
santin gidan, ta ce gobe kawo kayanta ko?Aliyu
ya ce, amma na dakin anjima zan kwasosu har
da TV da su Radiyo, kema na sai miki TV.Ta rinka
godiya.Washegari makota da yan uwa tare da
matan yayan mu sukazo suka yi mun jere, da
dddare kuma aka yi mun rakiya.Iya tayi mun
fada sosai, kuma ta kara nanata mun cewa tunda
ni na dage da son ya Aliyu lallai in lallaba
halayanshi.Don bata so in kawo mata wani kara'i
sananta sa mana Albarka tare da yi mana adu'a
tagari.Kowa ya tafi sai ni daya, nayi sallar isha'i
da shafa'i da wutiri, sanan nayi wanka, kwalliya
sosai nayi duk da cewa ina cike da fargaba zai
kalleni ko ba zai kalle ni ba.In ma ya kalleni ni
me zai faru?Goma da wani abu naji ana
kwankwasa kofar gidanmu.Da sauri naje na bude,
shi daya ne kuma sanye da kakinsa na dan
sanda, ke nan shi Abokanai ba zasu rakosa ba
kamar kowane ango.Na amshi kayan hannunsa,
jakace da leda tare da yi masa sannu da zuwa,
ban zaci zai amsa ba, amma ga mamakina najini
a jikinshi ya rumgumeni tsam.Sanan ya amsa da
yauwa sannu.Ina makale a kafadar shi ya kulle
gidan mu.Ina mamakin halin yayan mu sosai,
tamkar bashine yake gaba dni ba.Abaki yayi ta
bani kazar da ya shigo da ita tare da madarar
holandia.Duk fargaba ya cika ni, amma haka
naita sha har sai da yaga kamar zanyi amai, ya
ce, kin koshi?Na ce eh.Munyi Sallah inda ya dafa
kaina yayi mun addu'a.Bai bata lokaci ba gurin
ibadar aure, wasanninsa sunyi mun nauyi.Don
haka na soma rokonsa yayi hakuri, mai makon
haka sai yaji kamar wata sarewa nake busa
mashi.Nasha wahala a wanan daren nawa na
farko, domin duk wani haushinsa sai da ya huce
shi, sanan ya dawo yana tausaya min.Don shi da
kanshi bai sai saita kanshi ba.Shi ya taima ka min
na gyara kaina.Ku ziyarci blog dinmu domin
karanta Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ba mu jima da kwanciya ba aka kira sallah, ya
tafi masallaci nima nayi tawa sallar.Naso
kwanciya amma sanin cewa zai fita da wuri yasa
ni shiga kincin don hada abin kari.Lokacin da ya
dawo zatonsa zai sameni a kwance, sai ya ganni
kicin.Ji kawai nayi an rumgumeni ta baya.Na
gaida shi ya amsa ya ce, naje nayi bacci don
yasan ina jin bacci, na ce ba komai inya fita zan
kwanta.Tare muka karya, sanan ya ce, inzo in
cuda masa bayan sa tun ina jin kunya har na
gyare don kuma yariga ya tsomani cikin
ruwan.Tundaga ranar komai tare muke yi, wata
masifafiyar soyaya yake nuna min har na dinga
mamaki, sai dai ina gyaruwa wajen kwanciya.Don
ya Aliyu mabukaci ne fiye da zatona, rana, safe,
dare office ma sai ya dawo, haka nayi ta jurewa,
saboda yana ririta ni kamar ya hadiye ni.Satin
mu biyu nayi fari fiye da da, fatata ta goge,
amma na rame.Dan Almajirin da ya so min shine
ke min aike, kullun sai na saka mai abinda muka
ci ya kai ma iya.Ranar da nacika sati biyu ranar
iya tazo, dukinda nayi iya tana da ido, bayan na
bata ruwa da abin tabawa sai na zauna kusa da
ita ina cewa iya nayi kewarki sosai ke fa?Ta ce,
Sadiya kewa ai ba a magana.Amman kuna zaune
lafiya?Na ce lafiya lau, Iya.Yaya na ji dani, baki
gani ba.Tace Sadiya ni sai naga kin rame, kina cin
abinci kuwa?Na ce, ina ci mana.Aka kwankwasa
gidan, na ce gashi nan ma.Da sauri naje na
bude, ya manneni a jikin sa na ce iya tazo.Ya ce
tana nan?Na ce eh.A zatona zai sake ni amma
har fallon mu saida ya zauna sanan na zame na
barsu suna gaisawa da Iya.Na kawo masa ruwa
da abinci, yace my choice ba zan ci abinci ba,
dama nazo ne in dubaki kawai don na kira
wayarki a kashe.Nace yanzu aka kawo wuta, ka
kuma san batir din baya rike chaji.Ya ce, haka
ne.Zan chanja maki wayar ma, Iya ma in sai
mata.Tace ni yanzu gadanga in ka hada ni da
waya ban san yaya zanyi da ita ba.Na ce, zaki iya
mana, mun gode yaya.Yayi murmushi tunkafin a
siyo?Ta ce, ai nasan tunda ka furta zaka
aikata.Iya ta ce, gadanga kai naga kayi bul ka
kara kiba ita ko yar tawa duk ta rame.Ya kalleni,
ashe bani kadai nake ganin wanan ramar ba, to
ko Asibiti zamuje?Na ce, yaya babu inda yake
min ciwo sai muje Asibiti?Yace rama ciwo ne My
choice, zasu baki magani.Iya ta ce, ni da na zaci
ko rigima kuke.Ya ce, haba dai, ai yar taki tana
da biyayya.Iya tayi murmushi sanan ta ce, haka
nike so,Allah yayi muku albarka, ya baku yaya na
gari.Yaya ne, ya amsa da amin.Tare da dago
haba ta.Iya ta ce bari na tafi.Naje daki na dauko
dubu daya na ce, iya gashi, ta ce ina kika sami
kudi?Na ce, in abokan yaya suka zo suka bani, ko
na bashi sai ya ce in ajiye abina.Kuma ni ko katin
waya shi ke loda min.Ta amsa tare da ce min
Allah ya anfana.Na ce, Iya da kin dan bari sai
anjima.Yaya ya harareni ke zakiyi mata aikinta a
gida?Na ce, (cikin shagwaba) ba ina kai mata
kullum ba, ia yana isarki ko?Ta ce har ma in rage
in ba wani.Sai dai duk da haka ina yin girkin
saboda almajirai ko yan ciranin nan na
mokatanmu.Na ce, har yanzu iya kina ci dasu?Iya
ta ce, wanda ka bada shine naka.Nace to ki tsaya
zanyi da yawa sai in sa miki.Aliyu ya kawo hannu
ya dan mintsineni gefen ciki na, tare da cewa
sauran aikin ke zakiyi mata?Iya ta nufi hanyar
fita tana fadin Sadiyayyena kina in zauna shiko
gadanga korata ma yake.Da sauri kuma cikin
dariya ya ce, lah, iya bankoreki ba, nima yanxu
zanfita nazo duba ta ne kawai, kuyi zamanku ni
bari na tafi. Duk muka sa dariya, Iya ta ce a a
yayan nan ni dai naji dadin yanda na sameku
haka, fatana Allah ya kauda shedan tsakanin
ku.Ta bude kofar gidan ta fita, ya bita nikuma
nayi mata alkawarin xuwa inyini in an
kwanabiyu.Ku ziyarci blog dinmu domin karanta
Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Bayan ya dawo daga yi mata rakiya ya sameni
ina gyara gurin, ya makaloni jikinsa ya dago
fiskata.Sarai kinsan abinda ya kawoni, shine kike
rokon iya ta zauna ko?Gaba na ya fadi, amma sai
nayi yake tare dafadin ba haka bane.Muka nufi
dakinsa.Na rasa duk lokacin da yaya zai zo mun
da wanan batun gabana ya dinga faduwa
kenan.Na kasa sabawa.Ko shi ke sani rama?
Oho.Kawaye na duk wace tazo sai tayi zancen
ramata, haka Aisha, ta damu da son jin dalili
Na dage kan cewa ba ko mai, tunda bai kyautu in
fada mata yanayin mijina ba.Munje Asibiti likita
shima ya sha mamakin jin banda matsala kuma
ba inda yake min ciwo, amma na rame.Sai dai ya
ruvuta mana magunguna masu sa cin abinci,
amma duk da haka sai a hankali.Wani dare anty
Abida ita da Usman sun kawo mana ziyara
munata hira, sai Aliyu ya kawo batun ramata, aka
danyi zancen har Usman yana tsokanata da cewa
ina tsoron kishiya ne ki daina tunani, aboki na
naki ne ke daya.Nayi dariya sanan na ce, nasan
haka shima yasan haka.Yaya Aliyu yayi dariya.My
choice ban maki alkawari ba fa.Na ce, yaya kaima
kasan ko bakai min alkawari ba kai nawa ne ni
daya.Abida taja ni bed Room dina muka zauna
bakin gado, ta kalleni wai me yake damunki? Na
ce, ba ko mai wlh.Ta ce, ki fada mun ban sani ba
ko zan iya taimakonki.Nayi shiru ina nazari, can
nace anty ba ko mai, Allah sai dai ina zaton ko
dan yaya yana da yawan buka ta ne?Kin san
Allah anty na yaya bashi da hakuri hatta kai da
na ganshi ya dawo gaba na ya dinga faduwa ke
nan.Ta kada kai zancen ke nan, amma wanan ba
abin damuwa bane, da farko ki daina tsorata har
gabanki ya dinga faduwa.Kisa haka aikin da ya
zaman maki dole, aure bauta ne, in zakiyi sallah
gabanki na faduwa?Na ce, a a.Ta ce aikin gida fa?
Na ce, a a.Ta ce, wanan ma kisashi cikin dolenki,
tunda zama ne ba na kare ba.Gashi baki son
kishiya.Tayi dariya sai dai zan fada maki wasu
abubuwa da zasu taimakeki, dauko biro da
takarda.Na ce, to.Na tashi na dauko memo, ta
soma bayani kamar haka:
ki samo Dabino,Zuma,Aya, da Cukui zaki maidasu
gari ne, sanan ki dinga zuba madara peak da
zuma kina sha kullum safe da yamma.Kinji daya?
Na ce eh, na rubuta.Ta ci gaba, ki samu,kankana
ki dinga yawan shanta har kwallon,na ce gashi
kankana bata dame ni ba, ta zaro ido to kuwa ta
dame ki, kuma kya iya yanyankata ki zuba mata
madara peak ki dinga sha shima har
kwallo.Sanan a kai na kan Akuya, ki dafa shi da
romo, sai dai bazaki zuba mashi mai ba,
maimakon mai ridi zaki zuba da yawa ki cinye ke
daya.Haka kuma zaki sami garin dabino ki fasa
kwai da madara peak ki juya ki shanye.Nace wai
zan iya duk wanan?Ta ce, ki gwada tun gobe zaki
sanya ya nemo maki amma karki fada masa
dalilinki na son kayan, kawai kice zakiyi anfani da
su ne.
Kan batun ramarki kuwa, ki canza abin kari, da
me kike karyawa?Na ce,Tea ne sai Bread da Kwai,
watarana inyi kunu da kosai, ko indomie da
kwai.Ta ce ki koma cin dankalin turawa da
agada,ko doya da kuma kwai, in da hali harda
farfesu.Shayinki kuma ya zama yaji sugar da
bota, milo da madara.Ki zuba sosai yayi kauri
kisha.Sanan kirinka baccin rana shima baccin
yana sa kiba, sanan da daddare kici abinci
sosai.Na ce, to anty na gode.Ta ce, ba komai, ke
dai kada kiyi wasa, in kinyi su da kyau na tabbata
sai kin dawo neman wasu.Ko da yake ban fada
maki na tafin hannu ba,kin san hannu yana daya
daga cikin mai aikawa da sakonni.In mijinki mai
yawan kama maki hannu ne, ki samu zautun ki
kwaba da suga ta narke, kullun in zaki kwanta ki
rinka shafe hannunki.Sanan ki rinka shafawa a
lebunanki, nace to na gode anty sosai.Sallamar
yaya ce ta katse mu, ya ce, me ta baki kike ta
godiya?Nace abubuwan karin kiba ne wanda zan
rinka karin kumallo da su.Ya kalli Abida dama
zaki iya wanan taimakon amma kika share mu?
Muka sa dariya harda shi.Ya ce, mun gode.Ta ce,
ba wani abu bane wanan har da za ayi mun
godiya.Kai dai ka dage da siyo wa.Ya ce, in sha
Allahu ko su ke nan kudin za a siya, me nene da
me nene za a siya?Na ce, na rubuta zan nuna
maka.Yayi murmushi, to da kyau, yace kizo, abiki
yace zaku biya ta gidan yar uwarki ko?Ta ce, eh,
tare da mikewa na shiga dube duben me zan
bata, turare na bata mai kyaunace ta kaiwa
Ummulkhairi.Ka fin ya dawo da ga rakasu, har na
gama rubuta abinda ta ce na rinka karyawa da
shi,ya ce agada da dankali sai da safe, nayi
godiya da cewa Allah ya kaimu.Cikin satyn na
hada duk wani abu da anty Abida ta fada mun,
na shiga anfani da su.Kafin wata daya naga canji
sosai, yanzu bana wahala da duk dawainiyar da
miji na yazo mun da ita.Sanan nasoma cika ina
cika kayana gwanin sha'awa.Shi kanshi yaya wani
sabon ji dani ya sake ko mai tare muke yi in har
yana gida ni dashi mun zama abu daya.Ko tari
nayi sai ya tabbatar ba na cutarwa bane, haka
nima ina binshi sau da kafa, da ya nuna ra'ayin
abu zan masa balle ya ce my choice ina son
kaza.Ai in na soma sai ya gundire shi, duk abinda
bai so na kiyayeshi har abada.Shinfidar da muka
yiwa rayuwar mu ba zan iya bada labarinta ba,
kowa yana mamakin mu tamkar mun shafe
shekaru goma muna soyayya kafin muyi
aure.Muna cikin wata na uku iya ta matsa masa
wai sai ya maidani makaranta, form din (N.C.E)
ya sai min bada bata lokaci ba na zama daliba a
makarantar horas da malamai dake riga
cikun.Aliyu ya ce, ya zama dole in nemi avin
hawa ko don ke.Na ce Allah ya bada iko.Ba da
jimawa ba kuwa ya ,mallaki motarsa dai dai ta
talaka.Ku ziyarci blog dinmu domin karanta
Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Don haka bani da matsala sai dai yanayin aikin sa
ya ce in ya sami lokaci zai rinka koya mun, na ce
to.Ban jima ba na iya mota, sau da yawa ni ke
kaishi gurin aiki in dawo, sanan in tafi
makaranta.Kai yaya ya nuna mun dukkan gata, a
lokacin jini ke babu matar da ta kaini sa'ar zuwa
duniya a zamaninnmu. Wata safiya na farka da
zazzabi, mura, ciwon kai da sauran su, gashi
ranar yaya ba gida ya kwana ba, saboda wani
case da ke hannunsa.Bana kiranshi in dai yana
wurin aiki, amma shi in ya sami lokaci yana kira
na.Ina kudindine a kan gado naji ringing waya ta,
da kyar na lallaba na dauko, na daga.Ya ce, my
choice kin wuni lafiya?Cikin wata murya na ce,
lafiya lau.Ya ce, me ya same ki naji ki haka?Wani
dan kukan shagwaba ya subuce mun na ce,
zazzabi.Nanfa ya rikice sai gashi a gida bayan
minti ashirin.Banyi ko wanka ba ya sani a mota
sai asibiti, gwajin farko ciki ya bayyana, murnar
da ya Aliyu ya dinga yi ta rinka bani mamaki.Kula
da tarairaya ina ganinsu gurin sweet Aly na da
iya, cikin ya sa ni yin kyau, duk da na sha wahala
kafin yayi kwari.Sanan na bude nayi kiba gwanin
sha'Awa.Lokacin da cikin ya tsufa sai kuma na
kumbura abin da yayi matukar daga hankalin
yaya.Duk da cewa likitan ya ce babu
matsala.Cikin haka aka chanja yaya zuwa kogi,
ranarda ya zo mun da maganar na sha kuka.Duk
da ya zaci dama zanyi rigima bai tsammaci har
haka ba.Yayi ta lallashina da cewa, sadiya my
choice,ki kwantar da hankalinki.Ai duk matar mai
kaki San sanda ko Soja da sauransu, dole ta
kwana da sanin akwai yawon zaga duniya.Banzaci
zan dade haka ba tare da an canzani wani gari
ba.Na shafa cikina yanzu baka nan zan haihu?In
katafi yanzu sai yaushe zan sake ganinka?Ya ce
da na sami sarari zanzo, na kwanta a jikinshi.Ni
dai zanbika sweey Ali kaji yaya na?Ganin yanda
na rikice sai ya ce, to shi ke nanmu tafi tare ko?
Na ce, to sanan nayi shiru.Ana gobe zai tafi yaje
suka hada baki da iya,na zage ina ta hada kaya
har yana taya ni, sai ga iya tayi sallama.Na ce,
sweet yaya na dubi iya tazo kamar tasan zamuje
sallama.Iya ta shigo har cikin daki na, ta kalli
kayan da akwatinan ta ce, wanan fa, kwalima ce?
Na ce iya kin manta gobe ne fa zamu tafi can
jihar kogi inda aka tura yaya.Iya ta ce, zakutafi ko
zai tafi?Ina zaki tafi da wanan katon cikin ga
kumburi?Na kalli yaya na wanda ke ta aikin jera
min kaya na a cikin a kwati.Ni ina kwasowa daga
cikin sif.Kin kallona yayi, sai da na ce yaya!Ya
kalleni na ce, kaji kuma wai ba tare zamuba, inji
iya?Ya ce, eh, a a ai kinji ta ce saboda cikinki na
ce, tabdi jan!Ni kam ba zan zauna ba.Iya ta ce,
lallai Sadiya ba inda zakije yar dadi muji, ni yanzu
ma zuwa nayi in tafi dake.Na saka kuka, iya
sororo tayi tana kallona, shi kuma sai ya tashi
tsam ya dawo kusa dani.Iya kije gida zan kawo
ta.Iya ta mike ai ba wani lallashi ba in zata zo
dan ma kada ka sake yi mata karya.Ke ko yanxu
ance ki bishi kya je?Na ci gaba da kuka na iya dai
ta tafi tana cewa sai kiyi ta yi.Tana fita ya
rungumeni, haba my choice ni na lura iya tafimu
gaskiya.Ki bari in kin haihu sai muje, ina zo zan
tafi dake.Yanzu kinga dole inje in ga yanayin
garin.Na ce, yaya dama na san cewa baka damu
dani ba, can na san baka sona.Ya manneni

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login