Showing 15001 words to 18000 words out of 22554 words
Chapter 6 - Darajar Yayana Book 2 Complete by Halima Abdullahi K Mashi .txt
ina kike?Cikin in ina na ce
sha....shago baje can gurin hadi.Yin me?Na ce,
gari na suwo da suga.Gari?Ya tam baya tare da
zaro ida nu.Na sa dan yatsa na akan le buna na
tare da fadin yi hakuri yara suna ciki.Sai me? Ya
katse ni, na ce sai me in yara suna ciki, wato
sabon salon zubar da mutunci wanan kika samo
ko?Kamar ni a ce matata tana zuwa shago siyan
gari?Na nufi ciki raina a dagule, in ya bamu
abinda zamuci ishashshe ai ba zan fita siyan gari
ba, na raya hakan cikin raina.Kai tsaye daki na
shige na ajiye garin na fada ban daki don gudun
kada yara suji, da gudu suka rungumeshi suna
mashi oyoyo, al'amin da shi da mama, Kausar
tsayawa tayi tana kallon su.Ya dube ta ke
Kausar ba zakiyi min oyoyo ba? Ta ce sannu da
zuwa Abba.Ta juya ta nufi dakin su.Da kallo ya
bita cikin mamaki, me hakan yake nufi?Ta soma
yiwa yaran sa fanfo ne?Ya mike ya nufi dakin ni
kuma jin shiru sai na fito ina shigowa falo najiyo
muryar sa.Kausar ina tambayarki kin yi mun
shiru na ce me nene kike fushi?Sai na jiyo
muryarta tana cewa, Abba ni bana so ka dawo,
sabo da in kana nan kullum cikin fada da momy,
ni bana son tana kuka.Itama ta soma kuka, na
zaro ido cikin mamaki yarinyar,na saurara inji
me zai ce, fatana Allah yasa zancen Kausar
yazama sanadin fahimtar shi.Muryarshi ne ta
katse ni, ok wato uwarku tana kitsa muku
magana a kaina ko? Mamanku ta shirya muku in
nazo ina cutarku ko?Ya sake tambayarta cikin
daga murya, ban san lokacin da na fada dakin
ba ina fadin haba yaya.Yanzu me ya kawo
wanan tunanin?Tayaya za kayi mun wanan
zaton?Na kalli kausar fita.Ta fita na maida kofar
na rufe yana tsaye rai bace yana kallo na.Nayi
kasa da murya tare da tausasa ta, yaya wanan
sauyin da kakawo mana cikin gidan nan wlh ba
sai na kintsawa Kausar ko mai ba.Tana ji tana
gani, duk kokarin da nayi dan cewa basu
fahimta ba amma hakan bai samu ba.Saboda ka
kasa gyarawa, har takai ko a makaranta yaran
sun koma baya.Hawaye suka soma zubo min
masu zafi, na taka na isa inda yake tsaye nafada
jikinshi na kan kame shi.Yaya ka taimaka kayi
hakuri ka zubar da makamanka ka dawo mana
da farincikin mu.Ya ban bareni tare da hankade
ni har sai da na fadi, ya soma magana cikin
ihu.Tayaya kike so in yarda dake cewa bake
bace kike bata ni a wrin yarana ba?Yar wanan
yarinyar da bata gama sanin kanta ba shine har
zata san matsalar wani? To ni dake dasu munsa
hannu tunda kin zabi haka.Shiyasa sam bana
son zuwa garin nan, saboda takaicinki, kin zama
saikace sanda don Rama.
Kullun mahaifiyata tana tuhumata cewa bana
kula da ku, yanzu dan zubar da mutunci wai
kinje shago siyan gari.Na fashe da kuka yaya
yaushe rabon ka ajiye mana abinci?Tun zuwan
da ka tawo da wanan matsalar.Ya daga hannu
rufe min baki, yanzu ina yi maki magana ne a
kan shiga tsakanina da yarana.In zandau komai
ba zan dau wanan ba, ya kamata ki sani.Ya juya
ya fita bayan ya bude kofa.Kuka sosai nayi na
tsawon minti daya, sanan zumbur na mike na
fita.Mama tana kwance a tsakar falo tana ta
tsotsan yatsanta, ita bata san me ke
faruwaba.Ahmad yana zaune kan kujera ya
takure, Kausar na shiga raba ido in gani, can na
hangota gefen kujera ta makure tare da toshe
kunnuwanta, tana nufin bata son jin abinda ake
yi, ga kuka tana yi.Tayi sharkaf da majina,
dakinsa ya shige shikam naje na rumgumo
Kausar nazo na hadasu da Al'amin ina
lallashinsu.Duk da cewa nima hawaye ke
kwaranya a idanuwa na, Al'amin yazo yayi mun
rada a kunne, ki hada shi da Iya kinji Momy ta
rama maki(don duk zatonsu ni iya ta haifa ba
baban su ba) Najasu muka koma dakinsu, na
ce, Kausar Al'amin kuyi hakuri ni da Babanku za
mu koma kamar da, ba da jimawa ba kunji ko?
Kausar ta dago kai, yaushe momy?Na runtsi ido
hawaye na kwaranya na ce, bada jimawa ba
Kausar kinji?Duk suka makaleni, Al'amin yasake
cewa kin hada shi da Iya ne, da sauri na ce a a
ko ku kada ku fada mata, ba na ce muku bata
da lafiya ba?Kuna so in taji da muwa ciwonta ya
tashi?Duk sukayi shiru, nace kuna so ta mutu?
Da sauri suka ce, a'a,na ce to in kun fada mata
zata mutu.Kausar ta ce, bazamu fada ba.Na
share hawayena sanan na kallesu.Muna ciki har
aka kira magariba, na taso su mukayi salla.Tinda
na fito banga Mama ba, nasan tana gurinshi,
suna ciki ko sunfita oho.Na jika musu gari suka
zauna, Allah ya taimakeni suka kama sha.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Kausar tana cewa,Momy in nazama babba zan
dinga siyo mana kayan abinci.Al'amin ya ce,
momy ba na rigata ba.Yaya kausar nine
zandinga siyan ma Momy ko mai, na ce to tun
yanzu nagode, Allah ya raya ku, ku girma cikin
aminci da Albarka, suka ce amin.Raina yayi
sanyi yar firar nan da muka yi da ya rana sai
gashi sunyi sallama shi da mama tsam ya tsaya,
ganin suna cin gari.Na lumshe ido na hadiye
takaici na, sannan na ce sannu da zuwa.Bai
amsa ba yayi ciki, kamar in zauna sai kuma na
bishi.Ya aje mama ya zauna bakin gado tare da
dafe kai, na ce, ina maka sannu.Ya dubeni
idanu jajur.Yaya na ke cin gari da dare?Na ce,
to yaya bamu da komai ne.Na dubi mama,
zomuje ki ci gari.Ya daka min tsawa, ki daina
kira min sunan garin nan, ba zataciba.Ko
Inyamuri ya sha gari da daddare? Wanan shine
na karshe in ba haka ba rai zai baci, ban ce kala
ba na juya, cirko cirko nagasu Kausar a
falo.Kausar ta toshe kunne, Al'amin na tsaye
cikin damuwa,nakamasu muka koma na ce su ci
garin amma sai suka ce sun koshi.Kausar ta
kwanto kan cinyata, Al'amin ya kwanta kan
kujera na kwantar da kaina nima a hannun
kujera.Wai ta wace hanya zanbi gidana ya dawo
kamar da?Wa zai ban shawara dan ni ina ganin
tawa basirar ta kare kan haka.Allah ka bani
mafita.Muna nan har aka kira isha'i, na tashi
naje nayi sallah suma sukayi sai ga mama ta
shigo da nama da Holandia, na ce, suci.Al'amin
dai ya ci amma Kausar kin ci tayi waita ta koshi,
na rungumo ta, Kausar kina fishida Abbanki ne?
Tayi shiru, na ce ki fada min.Ta ce, eh momy
shima yanzu ya daina sonmu nace, a a yana
sonmu fushi yake yi in ya huce zai dawo kamar
da.Sai kurum naji ta ce, wane ne yayi masa
laifimomy?Na ce, ni ce, ta ce, bakiyi mashi ko
mai ba, ba ma kullun kina bashi hakuri ba
tunda yaki yayi hakuri ya daina sonmu.Bani da
bakin magana sai shiru ina mamakin Kausar,
yar wanan yarinyar har tana fahimtar abubuwa
kai abin da mamaki sosai.Haka na lallaba su har
sukayi bacci na kulle mana kofa sanan nima na
kwanta na fada kogin tunani.
Wa she gari da wuri na tashi nayi salla da
wanka, sanan nayi musu shirin makaranta, duk
a dakinsu.Nace suje su gaida baban su.Kausar
ta noke tare da daure fuska za ta soma kuka,
na ce, haba Kausar, kuje ku gaida Babanku
mana.Kina so ne ya j haushi irin jiya?Jiya ma kin
ki sakar mashi fuska ne shi yasayayi fada.Ta ce,
to momy yanzu tsoronshi nake ji.Na ce, daina jin
tsoro kinji Kausar, yana sonku.Daga nan ki bashi
hakuri.Ta ce, to.Amma sam fuskarta ba wani
annuri, ina biyeda su har kofar, Al'amin ya
kwankwasa daga ciki yaya ya ce, wanene?Mama
da jin muryarshi sai ta ce, Abba.Ya ce mama.Na
bude kofar suka shiga, yana kwance kan gado
da waya a hannunsa, da Alamu cht ya ke
yi.Kausar ta dan tsaya nesa dasu kanta a
kasa.Al'amin ya zauna bakin gado,Mama ta
hayekan gado, ya rungume mama da Al'amin
sanan ya tashi zaune.Al'amin ya gaida shi,
Mama ma cikin hausarta mara dadi ta gaida
shi.Ya kalli kausar daga inda take.Zo nan.Ta tafi,
ya janyota zuwa jikinshi, ta ce ina kwana?Ya ce,
ba zan amsa ba Kausar har sai kin fada mun
me mamanku ta ce maku nayi, kuke jin haushi
na?Kausar ta ce ba ko mai Abba, Al'amin ya ce
ta ce ne fa muzo mu gaida kai.Ya kalli Kausar,
yanzu kunfi son mamanku fiye dani ko?Al'amin
ya ce, muma ka daina son mu Abba.Ya ce, ok,
haka mamanku ta fada muku?Kausar tayi saurin
cewa momy bata fada mana haka ba, ta ce ne
kawai muje mu gaida ka.Ya dungurewa Kausar
kai yar karama da ke kin iya munafunci, ba zan
kara yi maki tsaraba ba.Ya kalli Al'amin, in ba
ka daukar maganar mamanku zan sai maka
keke kana so?Al'amin ya kama murna ina so
Abba.Ya kalli mama, mama na ke kuma in se
maki motar ki ta wasa ko?Na juya kicin ina kuka,
mutumin nan zai raba mun kan yara, zai kafa
min jam'iya yan partyn shi da nawa.Jin takun
Kausar yasani share hawaye, cikin sheshekar
kuka ta ce, momy kinji Abba zai sayawa su
Al'amin da mama tsaraba ban dani.Na tsugunna
na rungumota jikina ina shafa mata kai, yi
hakuri Abbanku wasa yake yi miki zai siyo miki
kinji?Ta ce, Allah momy da gaske yake yi ba ya
cein fitar masa daga daki ba?Na ce, yi shiru zai
sai maki.Da kyar tayi shiru.Na bata jug na ce,
kije wajen Iya ki ce mata in ta dama koko ta
baku, karfa ki ce mata wani abu ya faru kinji?Ta
ce to.Ta tafi nikuma na zauna a kicin cikin ta
gumi.Kausar ta sami Iya kwance ta gaida ta, ta
ce kausar menene?Ta ce, wai in kin dama koko
ki bamu, iya ta ce shine aka turoki ba Abbanku
ya dawo jiyaba?Me yasa bai rakoki ba?Tayi shiru
Iya ta ce to muje in se maki koko gidan ladi me
koko dan kulluna jiya ya kare, kice mata na ce a
jika maku gero tunda jifa jifa kuna shan kokon,
ban cika son abin siya ba.Sam iya bata fahimci
bamu da komai a gidan bane, tunda lokaci zuwa
lokaci sukanje su amshi kokon.Ta samu masu
kosai sanan ta rakata har kusa da gida.Tanaji
tana fadan turota ita kadai a wanan safiyar, ta
ce da uwarku tana tattalinku amma yanzu duk
ta canza,na rasa me ke damunta.Suna shan
koko da kosai kausar tana fada min sakon Iya,
na jika gero na ce to za a jika,suka gama na
dauki Mama na nufi kaisu makaranta, kusan
wata guda a kafa nake kaisu makaranta, don
mota tuni nayi fakin dinta gefe na rufe ta don
ba mai ba na da kuma kudin siya.Ina dawowa
na tarar da shi da Usman zaune yana
karantowa Usman laifuka na.Na gaida Usman na
shige daki, na hau gado na kwantawa,bawai don
bacci ba ko don hutu, sai don tsabar ta kaici.Can
na jiyo muryarshi yana kira na, ya kalle ni.Kin
san na fada maki ba zan dauka ba ki rabani da
yara na ba.Jiya na shigo gidan nan wai Kausar
tana yin fushi dani yar karamar yarinyar
nan.Al'amin yana fada mun na daina son su,
tayaya zan yarda wanan tunaninsu ne?Usman
ya daga mishi hannu saurara aboki na, ka barni
in gama magana ta don kada kakatse ni.Usman
ya kalleni,Sadiya me yake faruwa ne?Na runtse
ido don ta kaici, yaya Usman duk abin da ya
faru Abban kausar shine sila.Na koro mishi
komai tun daga farkon rigimar har zuwa
yau.Sanan na ce yaya Usman tsakani da Allah
kullun yaran nan suna kallon muna fada, ko
ince daga yazo sai shiga tashin hankali zasutashi
da tarbiya me kyau?Ya ce, a a.Na fada musu
yanda mukayi da malamansu. Ga rashin abinci
wane laifi na masa, ni dai yanxu tunda gani
gashi kurun ya fada min laifi na, wlh zan bashi
hakuri mu koma kamar da yaran mu suma su
sami natsuwa.Usman ya kalli Aliyu, aboki kaji,
sai ka fada mata laifinta don matsalar tazo
karshe.Aliyu yayi mun wani kallo ke dai kawai
baki son zaman lafiya ne, duk ki dauki damuwa
da bakin ciki kisawa kanki.Sau nawa zan fada
maki baki yi mun komai ba?Usman ya ce, to na
rokeka aboki ko mai ya wuce.Ya runtse ido tare
da fadin shi ke nan.Na dube shi nima in sha
Allahu ko mai ya wuce.Usman ya ce,
Alhamdulilla, yanzu sai ka tashi mushiga kasuwa
don nima abincin gida na ya kare.Nan dai suka
fita.A cikin mota Usman ya kalli Aliyu.Aboki ka
canza fa,Aliyu ya kalleshi wacce irin canzawa
nayi?Usman yayi murmushi sanan ya maida
hankalinshi titi.Kayi kiba sanan dabi'un ka sun
canza.Aliyu ya kure Usman da ido, zaiyi magana
kenan wayarsa ta soma ruri, ya ciro ya kurawa
Screen din ido,sha wara yake ya dauka ko ya
yanke,Usman ya kalle shi, daga mana abokina,
Aliyu ya katse kiran sanan ya kalli Usman,daga
jin kira sai kace in daga ba tare da kasan me
kiran ba?Usman ya ce, jami'in tsaro zai ji
shakkar daga kiran koma wanene.......Kiran
yasake shigowa, sai kurun Aliyu ya dagadan
kada Usman ya dago abinda ke faruwa.Ya ce,
yaya?Mujidat ta ce, muryarka nake sonji, nayi
kewarka da yawa, don Allah ka dawo yau.Tana
magana kamar zata yi kuka, salon dake narkar
masa da zuciya,take ya manta da wa yake tare
har ya furta cewa.Kada ki damu gobe kamar
yanzu muna tare,ta ce, to Zaki na sai mun hadu
a internet.Sai da ya salameta sanan ya tuna
yayi baram barama.Ya dubi Usman wanda bai
ce kala ba, ya soma nade tabarmar kunya.Wata
abokiyar aikina ce, muna gabatar da wani
aikine.Usman yayi murmushi sanan ya ce, sau
da dama in mutun ya shiga aikata rashin
gaskiya sai kaga ya zama makaryaci.Ita ko karya
illar ta da kayi so daya kafin ka fitar da kanka
sai kayi kusan sau goma.Aliyu ya kalle shi, me
ya kawo wanan zancen?Usman yayi dariya, ka
tsargu ne?Aliyu ya kalli gefe, intsargu da me
kuma?Usman ya hade rai, tsayar da halayenka
haka nan Aliyu.Ya gangara gefe titi yayi fakin
dazu nake ce maka dabi'unka sun canza ko?
Aliyu ya kalli titi muje zuwa da maganarka, in
wani zai fada mun aboki ba zan yarda ba,
amma gani ina zar ginka cewa kana hulda da
matan?Aliyu ya kalleshi da sauri, haba aboki,
nasancewa zaka iya bada shaida cewa ban
kasance mai shiga lamarin da mata suke ciki ba,
bare har inyi hulda dasu.Usman ya ce to amsa
min wadan nan tambayoyin.Aliyu ya cire hankici,
ya share zufar fuskarsa sanan ya ce, ina
jinka.Usman ya ce, na kira layinka sau uku wata
macece take dagawa.Na farko da dare ne gurin
karfe dayan dare, don in fada maka rasuwar
kanwata, sai kawai wata mace ta daga wai ka
shiga wanka.Na biyu da safe wata jumma'a don
mu gaisa ta ce ka fita gurin masu gadi, na uku
gargadi tayi mun in san lokacin da zan
dingakiranka yanzu kana cikin halin da bazaka
iya daga waya ba.Sai na soma lissafi giya kake
sha da har ba zaka iya daga waya ba, koko
menene?Sanan ita wanan matar yakuke da ita
har zata kasance a inda kake ciki tsakar daren
nan .In zuciyata ta zargeka sai wata ta shaideka
da cewa ba aikin ka bane, abin da bakayi ba
kana yaro ba na zaton cewa zakayi shi da
girmanka.Amma yau da matarka take fadin
yanda ka kaurace mata, sai na amince kana
neman mata, don kai ba me hakurin zama baka
tare da mata bane.Aliyu ya hade rai tare da
duban Usman, me cece shaidar ka ta zahiri?Duk
abin da kafada bai zama shaidar da zaka
amince ina bin mata ba.Ba zan iya zama ba
mace ba, shekaru nawana dauka can baya babu
auren?Usman ya ce kila lokacin baka san
amfanin matan ba,amma ni shawara daya zan
baka, inma zakayi harkar bariki to bai kamata ka
wulakanta matarka ta sunna ba.Aliyu ya ce, dan
Allah mu rufe wanan firar.Usman ya ce kafin
mu rufe sai nayi maka nasiha duk da cewa bani
da tabbas akan zargin da nake yi maka.Na san
mutun yana canzawa kamar yanda wahainiya
take canzawa zuwa duk kalan dataso.Nasihata
gareka in ka canza daga fari zuwa baki don
Allah ka saki wanan layin ka koma dai dai ko
don gudun zunubi, ko don tsoron azabar
Allah.Ko don kare mutuncin yayan mu, ko don
kare lafiyar ka daga cututukan zamani.Sanan
maganar zubewar daraja da kimarka a idon
wayanda suka san kanayi. Aliyu ya runtse ido
cikin in ina yace, muje aboki don Allah.Suna tafe
yana share zufa, lallai zancen Usman ya shige
shi.
Ko mai na abinci zuwa kayan tea sun hada
muna, lokacin da suka dawo ina kwance
kangado ina karanta littafin gidan zahra.Sau da
yawa in ina karanta littatafan Hausa sukan debe
min kewa halin da nake ciki, har na sha cin karo
da irin matsala ta.Sun ajiye min kayan abinci
suka sake ficewa, na fada kichin na shiga girki,
yarama da suka dawo makaranta sai murna
suke sun sami lafiyayen abinci.Yaushe rabon
muyi girki da kifi ko nama, yau gashi har
farfesun kan rago mukayi.Da daddare na fada
ban daki na sake wankana sheka kwalliya duk
tunanina yau za a shalabari.Sai dai muka
kwanciya ya juyya min baya, na gaji hakurina ya
kare don haka na ajiye kunyata na fada masa
cewa, yau ni ina son a faranta min.Ya ce, shi
gaskiya baya jin zai iya wani abu yanzu don duk
a gajiye yake.Nace, haba yaya, nima fa mutunce
kamar kowa, sama da wata hudu ka juya min
baya.Baka tsoron sharrin shaidan?Ya tashi
zaune a fusace, kina nufin zaki bi maza? Iye?
Fadamin zaki bi maza? Nasauka daga kan gadon,
ban ce zanyi zinaba yay, amma zuciya bata da
kashi, in na kasa jurewa fa?Na durkusa kan
gwiwowina, yaya ka taimake ni ka fiddani wanan
yanayin, ka tuna ni ban taba gudunka ba.Ya
mike ya dauki filo.Sai da ya kai bakin kofa
sanan ya ce, ina ganin kina cikin fitunananun
mata bari naje falo in kwana. Rufda ciki na
kwanta a kan gado ina kuka, wani mai kunci
daga bisani na dangana na fada ban daki na
sakarwa kaina ruwan sanyi yayi ta zuba tundaga
tsakiyar kaina.Ban fito ba sai da naji sanyi yana
ratsani, na fita naje kan gado na dukunkune sai
zazzabi da ciwon kai.Haka na kwana har safe da
kyar nayi Sallah na sha magani, sanan na fita
kicin.Shi kam a ranar ya koma kusan karfe biyu
ina kwance ya tsaya kaina wai ni fa zan tafi.Ba
tare da na dago ba, na ce Allah ya tsare, ya
ajiye kudi a gefe na tare da fadin, motarki an
gyara na ce uhm.
Duk da cewa Aliyu yana kirana a waya mu gaisa
yanzu duk abinda muke bukata yana
kamantawa, sai dai ya barni cikin kewa.Haka
nan ko a waya da mun gaisa shi ke nan sai ya
ce in bashi yaranshi suyi magana,ba wata hirar
soyaya ko ta rayuwa bare in sa rai zamu koma
kamar da.Duk da cewa yanzu yaran nan sun
dan saki jikinsu sai dai duk da haka da sun
ganni cikin takura ko damuwa yanzu zakaga
sunyi mun narai narai tamkar zasuyi kuka.Ni dai
a bisa halin da nake ciki gara ace bukatun ya
dai na yi mun ya bani kulawa da soyayya sunfi
mun duk wani abin duniya da zai sai min.Na
hakura ne saboda DARAJAR YAYA NA, sam bana
so in zube su inyi gaba.In ban rike suba naje
can inyi wahalar yayan wasu.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Wata rana naje kitso inda nake zuwa a can layin
zage-zagi wani gida, gidan haya ne maidauke da
matan aure da dama.A kulun naje gidan ina
karantar abubuwa na rayuwa da dama a gurin
matan gidan.Farko matar dake yi mun kitso, sau
da yawa mijinta in yadawo bata iya sakin kitson
taje gurinsa.Haka zai gaji da zama ya fito ya
dauki bokiti ya ja ruwa yaje yayi wanka.In kuma
da abinci ya ci ya fito in ya ciro kudin cefane ya
bata sai ta amsa a raine, yauma da nazo kitson
hakan ne ta kasance.Ya bata dari biyu ta juyata
sanan ta maida masa tana fadin gaskiya malam
bazata isa ba.Ya ce ba da garin tuwo ba, kuma
naga manja?Ta ce yau kwana uku muna tuwo,
ta kalli yaranta dake gefe suna wasa.Habu kunji
babanku wai yau ma tuwo