Showing 1 words to 3000 words out of 16870 words

Chapter 1 - SANADIN KIDNAPIING CMPLTD BY ESHAAT.txt

ESHAAT   

23 Dec 2024

2662




COPY N COMPILED
BY
ESHATT SMILER HOM OF HAUSA NOVLS DOCUMNTS
WASAPP 08066360176 FOR MORE






馃巰馃巰馃巰馃巰馃巰馃巰馃巰馃巰
*SANADIN KIDNAPPING*
馃巰馃巰馃巰馃巰馃巰馃巰馃巰馃巰






*ZAHRA SURBAJO*




*亘爻賲 丕賱賱賴 丕賱乇丨賲賳 丕賱乇丨賷賲*




*Kirkirarren labarine,banyishi dan wani ko wataba,dan haka akiyayi juyamin shi ta kowacce siga,duk wanda yayi na barshi da Allah*






*Gani Allah ya nufa nazo muku da wani sabon karatun,littafine daya kunshi abun tausayi,Yaudara,Nishadi,fadakarwa,uwa uba zazzafar soyayya,kubiyoni cikinshi kusha mamaki,dan da yardar ubangiji,babu kamarsa ajerin littattafaina,takowacce siga,comnents dinku shi ze bani kwarin guiwar yinshi akan lokaci,kubiyo yarnufawa domin jin wainar da zaa toya,#nice de dinnan Surbajo for life*




*1-2*




"Who is he?"ya tambaya cikin kakkausar muryar dake nuna tsananin tashin hankali da bacin ran da yake ciki.


jiki na bari,wanda aka tambaya ya matsa kusa dashi ya duka yace.


"Sir,He is a contract killer,he can do anything for Morney"


"Oh God,how can we find him now"ya fadi yana yamutsa gashin kansa.


"Sir the solution is,we have to be very smart first ,dan mutum ne shi me hatsari in aka nuna masa karfin mulki ze iya kashe Sanaya kuma ya gudu batare da anganshi ba"


Se a lokacin matar dake zaune a gefe tana ta shirgan kuka,tace cikin kukan.


"Alhaji,ni ba komai nakejiba,se Sanaya,nawane milyan dari,kayiwa girman Allah kabasu su sakomin yata,kana ganin Yadda hankalin Munaya yatashi sabida rashin yaruwarta"




Shuru yayi yana kallonta,zuwacan yace.


"Ba naki bada kudin bane,kawai inaso naji muryarta ne,to kuma sunki bata wayar tai mgn,amma tunda hakane zan basu,hajiya ki kwantar da hankalinki"


Dubansa yakai gurin me tsaron lafiyarsa yace cikin kakkausar murya.




"After given them the Ransom Morney,you guys i want you to find the person who was behind this kidnapping,if you find him chop him in to tiny pieces,so that no one can recognize him,this is an order"ya fadi cikin kakkausar murya.yana kaiwa nan ya fice Daga falon kamar kububuwa.


Da sauri me tsaron lafiyar tashi ya bishi a baya.


Ita kuma hajiya mikewa tayi ta nufi dakin Munaya domin ta rarrasheta ta samu taci abinci.




*DAJIN KUDARU*


Wani babban dajine me manyan dutsuna,da bishiyoyi,ga duhu,kwata kwata dajin beda kyan gani ko a ido ne,dajin na kan hanyar pambegua zuwa Saminaka.


Wasu gungun matasa ne zaune cikin wani kogon dutse,sunkai su ashirin dukansu babu alamar imani atattare dasu,inka cire daya daga cikinsu wanda ke zaune can gefe rike da bindiga ya takure,


Wata kyakkyawar budurwace zaune a tsakiyarsu sun daureta se kuka takeyi,ko suturar jikinta kawai ka kalla kasan yar manyan masu kudice.


Wani bakin mutum ne mummuna rike da kwalbar giya ya nufeta yana tangadi,sharab ya zube agabanta yana dariya,Hannu yakai ya shafo fuskarta yace.


"kaga wata jar fulawa,gaskiya ko babanki ya bada kudin bazan sakekiba,sena huta ajikinki"yayi maganar cikin muryar maye,


Hannu yasa yana kokarin shafo boobs dinta,ayko a zafafe wannan matashin yataso ya iso gabanshi ya ture yarinyar daga kusa dashi yace cikin bacin rai.


"haba oga ya zaka bata mana ayki,bafa daukota mukayi dan haka ba,kawai mun 蓷aukotane dan kudi,to meyasa kakeso kaci mutuncinta?"


Dariya ogan yayi sannan yace.


"kaga shegen yaro,Wlh wannan fulawar se na mata ban ruwa koda so biyune kan ta bar gurinnan,"


Gabadaya sauran dariya suka kwashe da ita,shiko matashin shuru yayi yana binsu da ido,yayinda ita kuma yarinyar ta tsananta kukanta jin abun da ogan yace.




"Wannan ba daidai bane,kuma wlh hakan bame yiwuwa bane,babu wanda ya isa cikinku ya taba mutuncin wannan yariyar matukar ina numfashi"cewar saurayin cikin kakkausar murya.


Wani ne daga cikin sauran yataso da sauri yazo gurin saurayin yace.


"Haba Safwan kasha kwayane,ka tunafa taimako ka nema agurina na kawoka gurin oga,dan kasamu kudin biyawa mahaifiyarka kudin operation din da zaa yimata,shine dan rainin wayo har oga na fadi kana fadi wlh kashiga hankalinka"yafadi yana me nunashi da yatsa.


Cikin matsanancin fushi,yace.


"Don't point your fingers at me or else i will cut them,ina danasanin haduwa dakai hafizu,kar ka kara fushina kasa na saukeshi akanka"


Sanin halin safwan na bakar zuciyane yasa hafiz jan bakinshi yayi shuru.


Sauran dayake abuge suke ba wanda yay mgn,guri safwan yasamu yana huci.


Jan duwawu yarinyar ta dunga yi har tazo kusa da safwan din,Bayanshi taje ta lafe,tana hawaye.


Waigowa yayi yana kallonta,sosai tabashi tausayi,hannu yasa yacire mata plasta din da suka rufe mata bakin.


Muje zuwa.




Surbajo for life.
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*SANADIN KIDNAPPING*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀




*ZAHRA SURBAJO*




*Fatima Abubakar Radda,kina da guri na musamman a zuciyata,ina sonki ina kaunarki,Allah ya dauwamarmin dake cikin farinciki har iya karshen rayuwarki,ya raya mana zuria,Wannan littaffin gaba dayanshi sadaukarwane gareki*


*Auta Inna ibrahim kime😝,ina gaisuwa*




*3-4*






Lumshe ido tayi tana ci gaba da kallonshi hawaye nabin fuskarta.


Daure fuska yayi dan shifa beson raini kuma karma wataran su hadu ta tona masa asiri,dan kallon yayi yawa.


Hannu yasa yaja rawanin dake kan wuyanshi ya rufefuskarsa,Tsab Sanaya ta fahimci manufarsa,ita ko bakomai yasa take kallonsaba,sedan ganin gashi dan iska amman yasan daraja da mutuncin yamace.


Haka suka zauna zugum zugum,har dare yayi,da yake Safwan beyi bacci ba yana gadin sanaya shiyasa da dare yayi yakwanta tunda sauran sun tashi daga baccin buguwar da sukayi.


Oga Jagan shine sunan shugaban kungiyartasu,Jagan mutumne mara imani,beda tausayi ko kadan,inyamurine daga Delta state,


Ya gagari akamashine sabida tsabar asirin dake tattare dashi,amman babu wani state da jagan beje yayi barna ba,contract killer ne shi na sosai,kuma gwanine gurin yin kidnapping,


Haduwarshi da Safwan tasamo asaline daga abokin safwan din Hafiz,wanda ya kasance yaron jagan dinne kuma unguwarsu daya da Safwan.


Mahaifin Safwan ya rasu da jimawa,dagashi se kanwarsa kawai iyayensu suka haifa,suna zaune a unguwar tudun wada dake kaduna.to kwatsam se Allah ya dorawa mahaifiyarsu,ciwon cancer ta nono,


Sun kashe kudi sosai gameda ciwon har mashin dinshi ya siyar amman suk da haka abun ya faskara.




Safwan yayi karatu tundaga primary har zuwa matakin degree akarkashin jagorancin mahaifiyarshi shiyasa yashiga damuwa dan yakasa taimaka mata shima,dan ko ayki bedashi.




Alhaji Khabeer Umar, shine Mahaifin Sanaya,wanda ya kasance kuma shine zababben gomnan jihar Kaduna na wannan lokaci.


Mutum ne shi da beda tausayin na kasa dashi ko kadan,kanshi kawai yasani da iyalinshi.


Cikin ikon Allah se Safwan yasamu Aykin share office din gomna,da taimakon takardunshi,shima yasha wuya kan yasamu,


Sede Alhaji Khabeer irin mugayen gomnonin nanne masu kin biyan albashi akan lokaci,wani sain ma har na wata biyar rikewa yake be biyaba.


Matsalar da Safwan ya fara fuskanta kenan dan ga mahaifiyarshi kwance a gida ba kudin zuwa koda ganin likitane,


Hakannw yasa ya yanke shawarar tuntubar gomnan aduk sanda ya ganshi.


Yau monday da wuri gomna ya iso office dinshi,sabida akwai wasu yan kwangila daze sawa hannu,


Safwan yana sane yaki yin aykinsa da sauri dan so yake yaga gomnan dan inde yasake yafita kan ya shigo to bazaa barshi yashigo gurinsa ba.


Shigowar gomnan keda wuya shida mukarrabansa,Safwan ya nufeshi,da Sauri masu tsaron lafiyarshi suka dakatar dashi.


Cikin kuka safwan yadaga murya yana rokon gomna.




"Don girman Allah ranka yadade kayi mana albashi haka,wlh mahaifiyatace ke gida zata mutu sabida ciwon cancer gashi babu kudin zuwa Asibiti"




Tasowa gomna yayi cike da izza yazo gaban safwan din,yasa hannu ya kifeshi da mari,sannan yace.


"in uwarka ta mutu ba damuwata bace,tunda ba tawa uwar bace,da rayuwar uwarka da mutuwarta ni agurina bata da bambanci da ta karen dake gararamba a titi,bazan biyaka albashi ba,baya ga haka ma na sallameka a ayki,wawa dan matsiyata kawai"




Safwan akwai zuciya,haka yashiga dambe da masu gadin gomnan,har yasamu ya isa gareshi,janshi yayi da karfi ta yadda suka hada goshi,a haka safwan yace.


"Kare irinka,be isa ya ambaci sunan mahaifiyataba,dan haka ko tanzu daka ambata nasan da taka kake ba tawa ba,kuma albashina dole ka biya ni dan bana yiwa karnuka ayki abanza"yana kaiwa nan yasakeshi taga taga gomna yayi kamar ze fadi daga bisani ya tsaya kam.


Tsananin mamakin karfin hali da jarumtar safwan ce tasa gomna kasa bada umarnin a kamashi,koda securities suka bi bayanshi zasu kama,da Sauri gomnan ya tsaida su.


"Ku barshi,zamu gana watarana"cewar gomna yana murmushin mugunta,shide safwan ko kallonsu beyiba,yasa kai yafice daga office din zuciyarshi na tafasa.


Ba komai yasa gomna yace akyale safwan ba,sedan tausayinshi da yaji,dan yasan bakin talaucine ya rufe masa ido har yaci mutuncinsa haka,




Bayan sati guda da faruwar lamarin,jikin mahaifiyarshi ya tsananta dan zuwa yanzu har tsutsotsi ke fita a nonon.


Haka zasu sata agaba shida kanwarshi rahama suna kuka,ga wani arnen wari dake fita ajikinta.


Haka suke kula da ita,kwatsam se Safwan ya hadu da hafixu,inda ya karanta masa damuwarsa ya bukaci daya ranta masa kudin daze kai ummanshi Asibiti.


"karka damu safwan,munada kungiya me kawo mana kudi shafshaf,in kanaso zan kaika gurin oganmu ya taimaka maka,sede da sharadi baa fita acikin kungiyar dan in kace zaka fita kasheka oga zesa ayi"


Da yake soyayyar mahaifiyarshi ta rufe masa ido,kai tsaye ya amince da sharadin,ayko hafizu yasadashi da ogansu jagan.




Hannu bibbiyu suka karbeshi,dan lokacin suna gab da fita wani opretion ne,dubu dari oga jagan yaba safwan,akan yaje yakai ummansa asibitin yazo su fita operation din.


Dan dadi har kuka safwan yayi haka yazo yadauki,Umman da Rahama zuwa asibitin Barau Dikko dake unguwar rimi kaduna.


Be baro gurinba seda yaga ummansa ta samu kulawar data dace,dan likitocin sun shaida masa sede yakaita shika dake zaria,su zasu kula da ira na iya yaune kawai.


Bayan Safwan ya koma gurinsu oga jafan,da.misalin karfe hudu na yamma,suka fita operation din,


Airport suka nufa,domin Ranar ne yaran me girma gomna,twins munayada sanaya ke dawowa daga kasar England .




Sunyi shiri na musamman,dan haka tawagar masu dauko yaran na zuwa,sukuma suka bude musu wuta,kan wani lokaci sega gawarwakin yansanda akasa.


Da gudu twins din suka fice daga mota,kasancewar dare yafarayi dan magribane lokacin kuma gurin ba haske.


Sanaya gudu take ko waige batayi,seji tayi taci karo da mutum,Safwan ne tsaye agurin,dan duk kashe kashen da akayi babu shi agurin,oga jafanne yace yatsaya agurin in wani yazo guduwa ya kamashi,


Sanaya na ganin safwan da gudu tayi bayanshi tana kuka tana fadin.


"Don Allah kataimakeni zasu kasheni"


Murmushi yayi gamida jan hannunta ba musu tabishi,wata mota yasata aciki sannan shima yashiga yatada motar ta fice da gudu daga airport din,yana fita dakarun sojoji na isowa,


Su jagan dakyar suka sha,sojojin basu rutsasu ba,jin jiniya na tashine yasa munaya fitowa daga inda ta boye,tana neman sanaya amman bata ganta ba.




Shiko safwan ko motar ɗayasa sanaya ciki ta oga jagan ce shi yabashi for emmergency,danhaka daita tay amfani gurin guduwa da sanaya.


Ganin bebi hanyar gida da ita bane yasa tafara ihu,ayko parking yayi kamin yakai marabar jos ya fita yasa igiya ya daureta ya manna mata plasta abaki.


Da yake kan akai maraba akwai checking point na sojojine yasa yadanna kan motar ta cikin daji,yadunga tafiya cikin duhun dajin har yafado kan titin daze kaika pambegua,tafiya yake aguje sosai dan haka be jimaba yazo pambeguan dauke kan motar yayi yafara bin daji dan can gaba akwai checking point,da taimakon wayar da sukeyi dasu oga jagan ya isa mahadar tasu lafiya dansu tuni sun jima da isa.


Ba karamin jin dadi sukayiba sanda suka ganshi da sanaya,dan da sun dauka sunyi fitar banza ne.


Acan kaduna ko tuni ankai munaya gida,ansa matakan tsaro akoina dan neman sanaya,hankalin gomna in yayi dubu ya tashi dana iyalinshi,sabida ba abinda yakeso arayuwarshi kamar sanaya itace farincikinshi.


A wannan yanayinne yasamu kira daga oga jagan akan cewa yarsa na hannunsu se ya bada ransom morney milyan dari.


Wannan shine abinda ya faru abaya,labarin ze dora


muje zuwa




surbajo for life.
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*SANADIN KIDNAPPING*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀




*ZAHRA SURBAJO*






*Autah Inna ibrahim kime🤣😜wlh dadin kiran sunanki nakeyi me babies face😝*


*Dedicated to Fatima Abubakar Radda*




*5-6*




Safwan baccinshi yake cikin kwanciyar hankali.


Sanaya lallabowa tayi ta matso inda yake kwance,ta dora kanta agadon bayanshi,tana feeling much comfortable in yana kusa da ita duk wani tsoro na kaucewa,dan ita fyade ne bataso ta gwammace ta mutu da hakan ta faru da ita,to ta fahimci baze bari ayi mata ba.


tana kwantar da kanta wani bacci yayi awon gaba da ita.


Oga jagan duk abinda ke faruwa akan idonshine,ganin tayi baccine yasa ya mike yanufi inda take,


daukarta yayi cak,se wani lungu acikin kogon dutsen,ya ajiyeta,yana ajiyeta ta farka,zatayi kuka ya rufe mata baki da plasta.


Nanfa yafara rabata da kayanta,da yake sanaya akwai manyan boobs to sune sukafi daukar hankalin oga jagan,jikinshi har bari yakai gurin son fito dasu daga cikin bra din jikinta.


Sanaya naji na gani bata da ikon hanashi domin adaure take,


Bayyanar boobs dinta awajene yasake dagawa jagan hankali,da sauri ya nutsa fuskarshi a tsakankaninsu,wata sassanyar ajiyar zuciya yasaki sanda yaji laushinsu.


Safwan nacan kwance kamar wanda aka tsikara ya farka,,waige waige yafara yana neman sanaya.


Ganin bata agurinne yasa yamike zumbur ya dauki bindigarshi yafara zagaye cikin kogon dutsen,duk sauran matasan se dariya suke masa.


Yana cikin zagaye gurinne ya iso inda oga jagan yake shida sanaya.zuwa lokacin har ya fara cire kayan jikinshi.


Itako boobs dinta sunyi jajawur sabida matsasu da oga jagan yadunga yi,se zafi suke mata.


Idon safwan na sauka kan boobs dinta da suri ya runtse ido,ya furta.


"Noooooooooooooooooo¡!!!!!!!!!!!"wanda sabida karajinshi har kogon dutsen seda ya dauka duka.


Da gudu ya nufi oga jagan sede kan yakarasa sauran matasan sun taso sun rikeshi.


Duk yadda yaso subarshi sun hana shi,gashi yana kallon yadda boobs din sanaya keshan tsotsoagurin oga jagan yana imagining ace Kanwarsace Rahama awannan yanayin yazeyi.




Wani kukan kura yayi ya kwace daga rukon da suka masa,nanfa yashiga kaimusu duka ta koina,


Fada ake bana wasaba,safwan dukansu yake suna ramawa amman dayake azuciye yake ko ji baya yi.


kan wani lokaci tuni,ya musu likis,wani irin tsalle yayi wanda har se da yayi tambul asama sannan ya dira akan gadon oga jagan.


Hannu yasa ya kamo hannayen dake matsa boobs di ya banƙaresu baya jikake kas,sun karye🤣


Dagashi yayi ya mikar ashi ya rike kanshi yadunga bugawa ajikin dutsen seda ya tabbatar da babu wani sauran hakori da yayi saura abakin sannan ya kyaleshi.


Hannu yasa ya kinkimi sanaya yasata akan kafadarshi,ya dauki bindigarshi,yayi nufin ficewa daga kogon da ita


oga jaganne wanda yake cikin mawuyacin hali dakyar ya iya furta.


"Don't let him go free"Ayko nanfa sauran yaran suka mike suka dauki bindigoginsu,suka mara masa baya.


Gudu yake da Sanaya akafadarshi,yayinda yaran oga jagan keta harbi da bindiga,tsananin karar harbinne ya haddasawa sanaya sumewa,


hak yake gudu da ita,hannunshi daya yana harbi dashi,


Duk wanda yasan dajin kudaru yasan dajine da har yanzu akwai ragowar mugayennamun daji dasukai saura aciki.


Safwan bedamu da kallon gabanshiba bayanshi kawai yake kallo yana harbi.


cikin saa wani daga cikin yaran oga jagan yasameshi da harsashi akafa,


Dagashi har sanayan wanwar sukai akasa,azabar da yaji bazata misaltuba,kwance yake rike da kafarshi,daidai lokacin akayi wata walkiya.


Idonshine ya hango masa sanaya kwance kasan wata shirgegiyar kasa,ta fasa kai tana shirin yin kalaci da sanaya,wacce alokacin tafarka daga suman datayi ganin macijitarne yasa tasake komawa suman,a raina nace tokode irin abunnan na kanawa tayi damacan wato likimo🤣😝.


Wayyo safwa,waigawa yayi ya hango yaran oga jagan sunkusa tarad dasu,wanda yasan in suka zo kasheshi zasuyi su tafi da sanaya,suyi abunda suka ga dama da ita


Tofa,ga sanaya kasan macijiya kasa,ga harbi a kafar safwan ga yaran jagan sunkusa cinmusu,koya zata kasance?




Muje zuwa




Surbajo for life.
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*SANADIN KIDNAPPING*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀




*ZAHRA SURBAJO*






*Ruqayya Hassan gaskiya kinsani nishadi,narasa bakin gode miki,Allah yasakamiki da alkhairi yasa kifi haka,Allah ya bani ikon kwatanta abunda kikamin,ngd ngd ngd,ilove you so much more my sis,just keep burning the light,the sky is your limit,#me laya kiyayi me zamani♥♥♥♥♥*


*Dedicated to Fatima Abubakar Radda*




*7-8*




Waige waige kawai yakeyi yama rasa abunyi,hannunshine ya sauka kan wani dutse kato,ay beyi kasa aguiwaba ya dauki dutsen


Be saukeshiba se akan macijiyar,take kan macijiyar ya fashe,jini ya zuba jikin sanaya,wanda yasanya ta farfado.


Ganin gawar macijiyar ajikintane yas ta kwalla wata kara wacce ta sanya yaran oga jagan fahimtar inda su sanayan suke,


Ganin sun nufo gurinne yasanya Safwan yamike da kafa daya yana dingisa dayar ya dauki sanaya wacce gaba daya afirgice take,yaci gaba da gudu da ita.


Tuni yaran jagan suka hange shi,dan haka mara musu baya sukayi,




Haka sukai ta gudu cikin dajin Allah,har suka iso bakin wani kogon dutsen,ayko safwan wuf yayi ya fada ciki,batare da tunanin koma meye aciki ba.


Suna shiga ya sauke sanaya suka labe ajikin dutsen,yaran jaganne suka karaso gurin,daidai bakin kofar shiga kogon suka tsaya,suna nemansu.


Sanaya jin wani tayi me sanyi yana bi mata kafa,ayko azabure tafara diddire kafar,gamida daka wani uban tsalle ta makale kafadar safwan ta kankameshi jikinta na bari.


Hannu yasa ya gyara mata zama ajikinshi gamida tallafe mazaunanta gudun karta fado🙊.


Sanaya sake shigewa jikinshi tayi dan sanyin dake gurin yayi yawa harma yafi na waje,hakanne yasa ta dora kanta akan kafadarshi gamida sakala hannunta awuyanshi.


Hakanne yabawa kirjinsu damar haduwa irinta no gab,Safwan jin da yayi abu me laushi na taba kirjinshine yasa yakai hannu danjin komeye,an be zaci boobs din Sanaya bane.


Yana kai hannu da sauri yasaki,sabida fahimtar ko meye da yayi,itako sarkin tsoro batamasan yayiba,addua kawai take akan Allah yafiddasu.


Yaran jagan sunkusa awa guda agurin,sannan suka wuce,jin motsin wucewarsune yasa Safwan fitowa daga ramin koramar da ya shiga batare da yasani ba,wanda da yayi gaba ba makawa cikin ruwa zasu fada.shiyasa sanyi yayi yawa agurin.


Cikin sanda yake tafiya,dauke da sarkin tsoro dake kankame ajikinshi,Sannu a hankali yake tafiya zuwa lokacin jiri yafara daukarsa sabida raunin kafarsa,jinine kawai ke fita,har yafara barin cikin duhuwar dajin,yafara zuwa gurin gonaki.


wani ginin daki guda daya ya gani a cikin wata gona wadda yasan na masu gonarne suka gina sabida in sunzo aykin gonar.


mukulli yagani ajikin kofar sanda ya isa bakin dakin,so yayi yasauke sanaya dan ya samu damar balla mukullin amman inna kankamo🤣 fafur taki sauka,karshema kuka tasa tana fadin.


"wlh bazan sauka ba,nide bazan saukaba"


Harda kara makalkalewa,kyaleta yayi ahaka yayi iya dabararsa ya bude kofar,suka shige.


maida kofar yayi ya kulle,sannan yafara laluben abinda ke cikin dakin.


Wayarshice tai kara,wanda dagashi har sanaya seda suka firgita,wanda shi sam bema dauka wayar n jikinshi ba,dakyar yaciro wayar,yaga rahama ce ke kira.


Dakyar ya dauka,yana dauka yaji ta rushe da kuka tana fadin.


"Yaya safwan kazo umma zata mutu,wayyo Allah na shifa uku don Allah kazo"


Tashin hankali baasa maka rana,zaman dabaro safwan yayi,wasu hawaye na biyo fuskarsa,cikin kuka yace.


"Rahama,bazan iya zuwa ba wlh yanzu haka harbine na bindiga a kafata,gashi ina guri me hatsarin gaske,don Allah kisawa umma wayar akunnanta nai mgn da ita bazata mutu ba da yardar Allah"


Umma dake cikin mawuyacin hali,dama tunda taji Rahama ta ambaci sunanshi take mata alama data bata wayar.


Samata wayar tayi akunne tana kuka,


Dakyar umman ta furta


"Safwanullah kana ina?"


cikin kuka Safwan yafara yimata bayani,br boye mata komaiba ya sanar da ita duk abinda ya aykata.


Cike da tausayin halin da ya jefa kanshi sabida soyayyarta tace masa.


"Karka damu safwan,ni Allah yayi ba rayayyibace,yar mutane daka dauko lfy kayi kokarin sadata da iyayanta lfy,karka bari acutar musu da ya,na yafe maka dana,Allah yayi maka albarka,ka kula da rahama,safwan daka aykata mummunan ayki dan sama muku abinci gwanda kabari yunwa ta kasheku,kamin alkawarin maida yarinyar nan gida"ta karasa mgn cikin haki daya taso mata.




Tunda ta fara mgn safwan ke kuka sanaya na tayashi dan tanajin duk abinda umman

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login